Kenza eBookz

A gidana complete novel - Chapter 17

A gidana complete novel - Chapter 17

A gidana complete novel Chapter 17: A gidana complete novel Chapter 17. Tsallakawa yai ya wuce, ta ajiye abin sharar ta kalleshi tace "wai ni sai yaushe…

4,500 words

Tsallakawa yai ya wuce, ta ajiye abin sharar ta kalleshi tace "wai ni sai yaushe zaka dinga sallama in zaka shigo guri ne?"

Karasa wa yai ya zauna akan katifa yace "ni abinda ke damuna ya isheni dan Allah karki kara mun da wani."

Juyowa tai rai a bace tace "gidan uban wa ka kaimana madara da milo?"

Kallanta yai, da sauri tace "meya sameka?"

Ta fad'a tare da tasowa da sauri zuwa inda yake, kwanciya yai yace "ki bari kawai Goggo saura kadan a halakani, daga shiga adaidaita ba kudi"

Kallansa tai tace "ina kaje? Ki meya kaika shiga mota ba kudi?"

Gun Zainab......

Zainab?

Da sauri ta kalleshi tace "bakada hankali?"

To ya kikeso nayi, ni gaba daya wannan zaman ya isheni, sam abokaina basa darajani, da duk inda naje girmamani ake yanzu ko matsayin magana ta gaskiya ma bani dashi, ni na gaji wlh.

Kallansa tai kamar ta makeshi sai dai kanshin dage dage ya gama sa karfinta ya tafi, tace "wato kaidai wlh ban taba ganin mutum wanda baya nazari irinka ba, ko uban me Zainab ta gani anan harta aura ni bansani ba."

Fuska ya hade yace "koma meta gani shine silar jin dadinki kema."

Mikewa tai tace "ni banida lokacin haukarka, yanzu ka mike ka fita ka nemo mana na abincin rana."

A ina zan nemo? Ko ana rabo a makota ne?

Wani kallan takaici tamai tace "eh duk gidan da ka gani kaje kace kazo amsar rabanka."

Dariya yai jin zafin bakinsa ne yasa yace "Goggo mekila daukeni me?"

Sai na fada? Akai a shashashu ma kaine sarkinsu.

Ransa ne ya baci ya kwanta baice komai ba, tace "billahi lazi tashi zakai kasan yanda zakai muci abinci dan yunwa nakeji kamar me."

Nimafa yunwa nakeji, ina nasan yanda zamuyi?

Sai ka dau kayanka kalai kasuwa ka samo mana kudi.

Tab kayan dana ajiye bansan batasu shine zan siyar?

Tace "dole ka siyar kuwa."

Mikewa yai ya shiga daki ya sauke labule.

******

Khalid shiru yai yana kallan yanda Zainab ke tafiyar da Presentation dinta, shi kuma yana danna mata slides din, gaba dayan mutanen gun sunyi shiru suna jin yanda ta ke watso musu ideas wanda duk wani wanda ke gun tabbas sai yayi sha'awar yi.

Duk tambayoyin da suka jefo mata cikin dabara da jan ra'ayi take basu amsa wannan yasa Chairman din Company din amincewa a take a gun, nan Khalid ya mikamai takardar contract itama ya mika mata daya sukai signing sannan ya amsa yai switching suka sakeyin signing.

Cikin jin dadi Chairman din yace "am looking forward to this project."

Cikin confidence dinta tace "you will never regret your decision."

Nan aka tafa sukai sallama suka fito.

Tana shiga mota ta sha ruwan dake hannunta sannan tasa hannunta akan goshinta ta lumshe idanunta.

Khalid ya shiga yaja, a hankali ta kalli agoggon jikin motar tace "lokacin tashina yayi, bari na ajiyeka na wuce gida."

"Bari na ajiyeki sai na wuce."

Bata musa ba ta dau waya ta turama Director Kabir text na hoton contract din da sukai, sannan tadaura da sauran maganar mayi gobe.

Ganin contract din da zasu samu uban kudi yasa yace to Allah ya kaimu.

A kofar gidanta yai parking, Bala ya bude ya shiga da ita.

Kallansa tai tace "nagode."

Bakomai, ya bude motar ya fita.

Yana fita daga gate suka gagaisa da Bala sannan ya wuce, yana tafe yana tunanin dole yana bukatar sake dagewa, dan yau ya fahimci bai maida hankali ba ko kadan, duk da ba abinda ya karanta ba kenan anma yasan in ya maida hankali sosai komai mai yiwuwane da izinin Allah.

Zainab har ya fita bata mike daga zaunen da take ba, haka kawai ta samu kanta da jin haushin yanda ya mata, tana ganin shi zai rakata ta dauka yanasan ya mata maganane amma sai ya nuna bashida ra'ayin hakan?

Meye nawa a ciki? Kar ya tambaya din, kowa ya sha xamansa.

Muryar Nabila taji daga gefen ta.

Murmushi tai sannan ta tuna hutunsu ya kusa karewa gashi bata nemi babbar mai aikin da Dady yace ba.

Ahhh da alama tana da abubuwa dayawa a gaba.

*********

Goggo tadan leko, su Asabe ta gani ana tacin shinkafa da dage dage, tace "Asabe nikam kin san waya iya kitso a nan kusa?"

Asabe ta kai loma tace "Karimatu ta iya anan makota take."

Goggo tace "Allah sarki, nagode."

Kallan yaranta dake cin abinci tai tace "oh anatacin abinci ne?"

Asabe tace "eh, ya akai?"

Dariya Goggo tai tace "bakomai, nima inzo in daura dan ganin kunacin abinci ya sani jin yunwa."

Asabe ta kalli yaranta biyu mata dake cin abinci tare, ga danta namiji a gefe wanda ya mike yace "ni nakoshi."

Asabe cikin gatse tace "ko zaki d'ana wannan kafin ki daura? Dan banda wani sai wannan da babangida ya rage."

Ga mamakinta ganin Goggo tai zuruf ta mike tazo ta amsa tana cewa "bari na dan taba, haka kawai yunwa taxomin yanzu."

Asabe ta tabe baki a ranta tace sanda kuke cin tsire a daki, ku soya dankalu ai ko kwaya baki taba ba ko 'ya'yan mu ba.

Ita dai Goggo ta shige daki, tana shiga ta cinye, haushi ya kamata tace "ai da sai ka rage dayawa, na rasa meyasa yara ke da uban ci ina laifin suci kadan, wani sa'in sai ka rasa ina suke kaiwa."

Adam ne ya fito yana neman fita yaganta tana sud'e hannu, da sauri yace "Goggo kinsamo mana abincin ne?"

Kwanon ta turamai tace "eh gashinan ci."

Yace "wannan ai bakomai, ina nawa?"

Wani kallo tamai tace "kasan Allah? Idan baka fita ka saida kayanka ko dako kayi ba, ranka ne zaiyi matukar baci."

Dako?

Yanda yai maganar a zabure yasa tace "to fadamin inba jikinka ba uban me kake dashi."

Dariya yasa yace "nine zanyi dakon? Adam din? Mijin Zainab?"

Mikewa yai yana cewa "zanje indawo ki samarmana abin ci."

Haushi ne ya kamata ko amsa ma bata bashi ba.

Yana fita majalisa suka tsareshi, ina hoton? Nasan ai yanzu ka dako.

Kallansu yai ya zaro wayarsa.

******* Ayusher🏌🏻‍♀[12/9, 9:48 PM] Ayusher Muhammed: 🍀A GIDANA🍀 .........................

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

#OneLove❣

{41}

Nuna mana, kallansu yai yace “nawa kuka sa.”

Dariya sukai nan kowa yasa aljihu, yana nuna mai kudin dake aljihunsa, ido suka zubamai suna san ganin hoton.

Bude musu hotonsa wanda sukai shida Zainab bayan auransu kadan, baki suka sake suna kallo, cikin hadara yace “yanzu kun yadda?”

“In kuma a hanya ka ganta kuka d’au hoton fa?”

Cikin bacin rai yce “ to wannan fa?” Nuna musu wanda sukai ya rike kafadarta yai.

Idanuwa suka firfito dashi, cikin mamaki yace “ku bani kudin”

Ba musu haka kowa ya mikamai abinda ke aljihunsa, baki ya washe cikin jin dadin ganin ya hada dubu uku da dari biyar daga nuna hoto.

Kamalu yace “bani wayar na kara gani.”

Mikamai Adam yai tare da hard’e hannu ya zauna yana girgiza kafa irin sarkin nan.

Kamalu ya faki idanunsu ya tura ta whatsapp dinsa, sannan ya mika mai wayar.

Suna rabuwa ya daura hoton a instagram tare da cewa ko kunsan wanene mijin Zainab Aliyu Tahir? Sannan ya daura wani wanda sukai shida Adam.

Ya dan rufe fuskar Adam da hrt emoji kan kace me hoto ya fara yad’uwa a instagrams, whatsapp da kuma facebook, kowa yana san ganin mijin.

Dariya yasa ganin yanda yake ta kara samu followers gashi anata tambayashi ya nunashi.

Kamalu cikin jin dadi ya kara rubuta, ko kun san Zainab da Mijinta basa zaune a gida d’aya? Ai kan kace me ta ko ina gulmar abin ake, ko ina ka leka maganar kenan.

Zainab kam batasan me ake ba dan bata whatsapp bare instagrams gwara facebook tana shiga taga labarai, bare su Nabila wanda ta hanasu da kanta acewarta su bari sai sun gama skul.

Da safe ta shirya ta nufi office, sai dai tana shiga taji ana gulmarta, bata wani bi ta kansu ba dan tasan maganar jiya ce suke kara riritata.

Khalid wanda ke rike da wayar Afreey yana kallan hoton data zo nuna mai ya kurawa hoton ido dagowa yai ya kalleta yace “inada magana dake.”

Kallansa tai sannan ta bi bayansa ba tare da tace komai ba.

D’an dakin da suke cin abinci ya shiga, kallanta yai yace “menene hakan?”

Tace “ina na sani nima, ganinshi nai tun jiya yana yawo shiyasa na nuna ma.”

Idanunta ya kalla sannan ya kauda idansa, dan matsowa tai tace “Khalid tun jiya dana ganshi nake tunanin nasanshi, sai dai na kasa gasgatawa, Ba Adam awala bane?jiya dayazo na ga fuskarsa.”

Kallanta yai, baice komai ba, dariya tai tace “Dagaske Adam ta aura kenan?”

Fuska ya hade yace “Dariyar me take nufi?”

Guntse dariyarta tai tace “ina mamaki ne dan ban taba kawowa Adam bane, yanzun ma na tambaya ne........”

Kallanta yai yace “koma menene aranki karki kuskura ki soma, nasanki sarai nasan akan wani ra’ayi nake ba abinda bazaki iya yi ba.”

Kallansa tai tare da hade fuska tace “shaidar da zakamin kenan?”

Ba haka kike ba?

Kallansa tai tace “kasan shekara nawa nai ina nemanka?”

Wani kallo ya mata tace “Khalid plz ka bani dama na gyara barnar danai a baya, bansan meye tsakaninku da ita ba amma kai kasan bazan taba hakura da abinda nake so ba, dan haka in har ba abinda nake zargi bane tsakaninku ka bani dama.”

Kallanta yai kawai baisan sanda yasa dariya ba, ya shafi kansa sannan ya kalleta. Zainab wacce tazo daukan cup ne ta kallesu tacikin glass din kofar, dariyar dataga Khalid nayi ne yasa ta tsaya tana kallansa, shiru tai kafin ta juya tabar gun.

Khalid ne ya kalli Afreey kamar zaiyi magana kawai ya wuce.

Zainab taje shiga office dinta taji muryar Director Kabir taji yace “Zainab!”

Juyowa tai ta kalleshi, yace “inada magana dake.”

Kallansa tai sannan ta nufo office dinsa, tana shiga ta zauna, kallanta yai sannan ya juya mata da laptop dinta saitinta, kallan hotonta dana Adam tai, sannan ta kalli rubutun kasa, da sauri ta dago ta kalleshi, fuskarsa a hade take, wanda bata taba gani ya hade mata rai ba yace “meya rabaku dashi?”

Kallansa tai tace “kome ya rabani dashi wannan personal matter dina ne.”

Personal? Wannan shine personal? Yai maganar cikin fada.

Kallansa tai tace “me kake nufi? Nina sashi yai kenan ko me?”

Ko ke kika sa shi ko ba ke bace alama ce ta kin kasa controlling dinsa, kinsan daga daren jiya zuwa yanzu mutane nawa ne suka kirani suna tambayata abinda ke faruwa? Akarshe sai wayata na kashe?”

Kallansa tai abin takaici tana kokarin magana taga an kara posting din wajen gidan dasu Adam ke ciki a kasa ansa “ko kunsan nan ne gidan da Zainab ta kori mijinta yake zaune shida mahaifiyarsa? Me kuke tunanin ya mata?”

Comment ne suka fara bayyana ta ko ina, Director Kabir ransa a matukar bace ya rufe laptop din da d’an karfi yace “bazan yadda da abinda zai kawo dakushewar gidan tv din nan ba, dan haka ki gaggauta gyara komai, in ba dan ke nace bama da korar wanda yai zanyi.”

Kallansa tai idanunta suka fara yin jaaa, mikewa tai ta fito ta nufi office dinta ranta a matukar bace, farcenta ta shiga karza dayan farcenta dashi tana tunanin abinyi.

Can yamma bayan la’asar ganin gaba daya yau ta kasa yin komai dan dama haryanzu bata amshi shirinta ba tunda ta dawo, tana so ta gama gyagyara matsalolin su kafin nan.

Wayarta ta dauka ta kalli number Adam, ranta na kara mugun baci, waya ta dauka ta kira staffs room, ana dagawa tace “akira mata Khalid.” Tana kainan ta kashe.

Khalid wanda ya zauna yana harhade takardun da za’ai shiri dasu gobe ne ya kalli Ramatu datace ana kiranshi.

Mikewa yai yazo fita, Afreey ce ta kalleshi fuskarta cike da kishi da takaici, baibi takanta ba ya wuce.

Zainab na zaune akan kujerarta tana kara kallan abinda ke faruwa ta facebook, tare da kokarin bude account na instagram dan ganin abinda ke faruwa sosai.

Knocking Khalid yai sannan ta bashi izini ya shiga.

Kallansa tai bayan ya karaso ciki tace “kana instagram?”

Kallanta yai dan ya fahimci ta gani kenan, shiru yai yana kallanta, sannan ya girgiza kai alamar a’a.

idanunsa ta kalla bayan ta kauda nata idan ne tace “it seems like kaima kaga abinda ke faruwa.”

Uhmm ya fada tare da d’an daga kai

Shiru tai kafin tace “before reporter’s su tare Adam suyi hira dashi i have to do something.”

Kallanta yai yanzu kam baice komai ba, dagowa tai cikin dauriya tace “Bantaba tunanin Adam zaimin haka ba, duk da ynda muka rabu amma atleast na dauka zamu rikema juna sirri.”

Kallansa ta karayi tace “zaka iya dubomin inda yke zama?”

Kai ya daga alamar to, samun kanta tai da jin haushin yanda yaki mata magana bayan yanzu ta ganshi yana dariya da Afreey koda yake dama tasan maza duk daya suke daga sunga mace yar kwalliya magana ta kare.

“Barshi kawai, na kula bakada niyyar yi, just pretend you haven’t heard anything from me, jeka kawai.”

Ga mamakinta gani tai ya juya, cikin kufula tace “tafiyar zakai?”

Juyowa yai yace “I thought that’s what you said?”

Ranta a bace ta mike tace “yaushe ka fara yin abinda nace?”

Bata jira amsarsa ba tace “in magana ce dakai ka fito ka fada, just be your self.”

Shiru yai yana kallanta kafin yace “abinda aka riga aka batashi banaji magana zata gyara shi.”

Zama tai sannan ta Kalleshi tace “me aka bata?”

“Hotuna sun riga sun shiga wayoyin mutane da dama, sannan kowa a matsayin mijinki yake daukansa, inhar bake zaki........”

Da sauri zatai magana ta zubar da juice din data zuba a cup akan laptop dinta duka ya zube a jiki.

Da sauri ya karaso kusa da ita, zama yai a kujerar da ke gabanta sannan ya ja laptop din.

Da sauri yace “tissue.”

Kallansa tai zatace yana can taga yana miko mata hannu alamar ta bashi.

Kallan tissue din dake kan shelf tai sannan ta kalleshi, d’aga laptop din yai yana kallanta ganin bata da alamar daukowa.

Kallansa tai kamar zatai magana sai kuma ta nufi inda yake.

Ranta a bace ta dauko tana tunanin tunda take an taba sata miko abu? Mikamai tai ta hade fuska sosai.

Baibi ta kanta ba ya amsa ya fara goggewa, sai dai ganin ya shiga ciki yasa ya kalleta yace “inada screwdriver?”

Eh, dan bani.

Kallansa ta sakeyi tace “yana can.”

Kallanta yai yace “taimako fa nake?”

Tace “ko taimako kake a kasa na kake na dauko tissue yanzu sai ka dauko kaima”

Kallanta yai kawai sai taga yasa murmushi, fuska ta daure sosai tace “meye?”

Yace “badai ba’a tava saki dauko abu ba?”

Kauda fuskarta tai ta dan matsa daga kusa dashi tare da zama a d’aya kujerar tace “how do you know?”

Sake murmushi yai yace “rike wannan to, dan inba haka ba wanda ya shiga sake shiga zai.”

Kallansa tai tace “wai sai dai ka sani aiki?”

“Ko na tafi?”

Cikin hade rai ta amsa tare da kauda kai, ina yke?

Tace “can.”

Can ina?

Ya tambaya yana sake kallanta, haushi ya kara kamata tace “dawo ka rike na dauko.”

Da saninsa dan ya gani komawa yai ya amsa ita kuma ta mike fuska a daure ta dauko, da karfi ta ajiye a gabansa.

Yazo dauka ta janye tace “kana san cemin baka ganshi ba?”

“In na ganshi mexaisa na dawo?”

Harararsa tai tace “ya akai nake ji kamar da saninka?”

Hannunsa ya mika mata yace “kin tabbatar ba ra’ayinki bane yasa kike jin hakan?”

Mikamai tai da karfi, amsa yai ya fara kuncewa.

Kallan abinda yake tai sannan tace “karasa maganar ka ta dazu.”

Bai kalleta ba yace “ki sanar da komai da kanki, even though it will get harder at first, amma atleast ba wanda ya isa ya shiga miki bincike tunda kin riga kin rufe bakinsu.”

Nayi wannan tunanin amma in yan jarida suka nemishi suka tambayeshi dalilin rabuwar mu fa kafin nai magana da kaina? Ko kuma suka nemi yarinyar fa?

Dagowa yai yace “Raziyya?”

Ganin yanda ta kauda kai yasa yace “Raziyya bazatace komai ba, am sure dan da dama ba cutar dake tazoyi ba, sannan bazataso tayi abinda iyayenta zasuji ba.”

Wani kallo ta mai sannan tace “da alama kasanta sosai tunda harkasan abinda zatai da wanda bazatai ba, ko da yake wanda ya tsaya yana dariya da wace bai dade da saniba meye bazai ba.”

Kallanta yai duk da bai fahimci kalamanta ba amma yasan magana take gasamai, mikewa tai tana neman komawa daya bangaren, da sauri yace “rikemin wannan.”

Kallansa tai ranta a bace tace “naki na rike.”

“Tunda taimako nake zan iya tashi nima.”

Tace “jeka kafi ruwa gudu.”

Dagowa yai ya kalleta yace “ gaskiya ce bakyaso a fada?”

Gaskiya? Hakan shine gaskiya? Hannunta ta daura akan desk din tace “ace ma gaskiyar kake fada kai baka iya magana cikin sanyi ba?”

Kallanta yai idanunsa na cikin nata yace “na iya.”

“Ni kadai kake ma kenan?” Ta fada tana kallansa

Kallanta ya sake yce “Ummm”

Haushi ya kamata tace “Then why?”

Mika mata keyboards din yai sannan yace “I don’t know.”

Amsa tai ta ajiye akan desk din sannan tace “you don’t know?”

“Hmmm I don’t know why”

Komawa tai daya bangaren ta zauna tare da dauke kanta daga inda yake.

Cigaba da gogewa yai yna cewa “in na samoshi zaiji abinda zaki cemai?”

Shiru tai kafin tace “I don’t know”

Yasani sarai ramawa tai hakan yasa ya kalli agoggo karfe 6 ce ta buga.

Shiru sukai ya karasa gyarawa sannan ya mike yace “zan nemo inda yake, i will send you the address.”

Harya kai bakin kofa ya juyo ya kalleta yace “amsar da kike nema tana gunki, trust your self”

Dagowa tai ta kalleshi, juyawa yai ya fita.

Kofar ta zubawa ido shiru tai tana tunani, meyasa da bata taba neman taimako agun wani duk runtsin da zata shiga kuwa, harsai ta samo yanda zata warware komai, amma yanzu me yasa take san jin ta bakin Khalid?

Kallan screwdriver da tissue din tai sannan ta kalli laptop din.

*****

Yana kokarin fita yaji Afreey tace “sai yanzu ka dawo?”

Juyowa yai ya kalleta cikin mamaki yace “baki tafi ba?”

Kallansa tai tace “kace bakomai tsakaninku.”

Kallanta yai dan baisan sanda ya fadaba kuma baiga dalilin amsawa ba.

Wayarta ta mikamai bani number Adam, kallanta yai yace “kimai me?”

Ince ya maida matarsa.

Ido ya kura mata sannan yace “Please Safiyya, karki soma yin wani abu, I don’t know what you are thinking amma koma meye a ranki i ask you to please stop, in kuma har kikai abinda zai sa mutane shiga matsala saboda ra’ayinki i will never forgive you.”

Yana kaiwa nan ya juya ya fara tafiya, ranta ne ya kara baci tace “in ka aureni ka yafemin.” Ta fada cikin kishi.

******* Da sauri Raziyya ta mike zaune tana kara kallan hotunan, kafa tasa ta ture hannun Jamil da yake shafa mata mai a daya kafar, cikin takaici tace “bai saketa ba kenan ko me?”

Kallanta Jamil yai yace “na dauka kin tabbatar bazata dauki raini ba?”

Tace “haka na dauketa da alama nice nake mata kallan jaruma.”

Hoton ta kurawa ido ranta a bace tana huce.

Yace “yanzu me zakiyi?”

Tace “kome zanyi sai nayi dan Allah sai auran nan ya rabu.”

Shiru Jamil yai kafin yace “nifa inaga akwai abu a kasa, in ba haka ba me zaisa ta koresu?”

Shiru tai tana tunani kafin tace “fita ka nemomin inda zan sameshi.”

Kallanta yai yace “yanzu?”

Wata muguwar harara tamai tace “dazu”

Mikewa yai da sauri ya fita.

Cikin kuluwa ta cilar da wayarta gefe.

********

Washe gari da safe

Goggo dake tajin dadin kudin da suka samu dan jiya shinkafa da miya tai itama yau kuwa indomie suka dafa da kwai soyayye, ta kalli Adam tace “ashe dai d’an nawa jarumi ne ban taba tunanin daga fita xaka dawomin da makudan kudi ba.”

Cikin isa da mulki ya kai lomar indomie yace “ai ki bari kawai, daga nuna musu hoton auranmu nida Zainab suka cake min kudina.”

Shiru tai tana tunani, karfa abin ya jawowa Zaimab matsala? Sai dai can tace koma menene ai ita taja data bamu gida ai duk da ba haka ba kome ya sameta muma ba hannunmu a ciki.

Kallan Adam tai zatai magana sukaji ana magana a tsakar gida, kallansa tai tace “wanene?”

Loma ya karayi sannan ya leko yace waye?

Kallansa mutumin yai Kamalu yace “shine.”

Adam ya kallesu cikin rashin fahimta, mutumin cikin jin dadi ya mikamai hannu yace “d’an jarida ne ni sunana Aliyu Giss ma’aikacin gidan tv na Farin gani.”

Adam ya kalleshi yace “sai akai me?”

Dan Jaridan yace “muna bukatar yin hira dakai ne in har ka amince zamu baka dubu talatin kudin yin hira dakai.”

Da sauri Adam yace “dubu talatin”

Goggo dake daki ta leko da sauri tace “dubu Talatin?”

Yce “eh.”

Kallan Goggo yai itama ta kalleshi.

Mikamai complimentary card dinsa yai yace “inkayi shawara kamin waya da number nan.”

Adam y amsa hannu na rawa, Aliyu Jiss ya juya ya fita, waya ya daga ya kira wata number yace “Hajiya mungode da taimako.”

Kashe wayar yai cikin jin dadi, dan dama sun dade suna bakin cikin aikin da Zainab take da d’aya gidan tv din wanda sun tabbatar saboda itane suke ta samun cigaba wanda a yanzu su har mantawa ma ake da su.

******* Ayusher🏌🏻‍♀ [12/11, 9:08 PM] Ayusher Muhammed: 🍀A GIDANA🍀 .........................

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

Wattpad link👉🏻 https://my.w.tt/FKRWfhajS1

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

#OneLove❣

{42}

Kamalu ya kalla da sauri bayan ya matso kusa dashi, yace "me ya faru zai ban wannan uban kudin sannan yai hira dani?"

Kamalu yace "Da alama tambayarka yake sanyi akan matarka."

Da sauri ya kalleshi yace "akanta?" Goggo ta fito da sauri tace "akan Zainab zaiyi hira dashi? Meyake san ji?"

Kamalu da sauri yace "bansani ba nima."

Ganin yanda Goggo ke kallansa yasa yai saurin yin waje. Kallan su Asabe ta da suka leko, ta kalli Adam tace "wuce ciki."

Shiga yai ya zauna yace "Goggo me kike tunani suke san ji?"

Kallansa tai tace "meke faruwa wai?”

Shiru yai cikin rashin sanin abinda ke faruwa shi kansa yace “bansani ba wlh nima Goggo amma dubu talatin haka kawai?”

Shiru tai tana nazari, kafin ta kwace complementary card din dake hannunsa tasa a lalitarta, da sauri yace “Goggo.”

Tace “ka bari inyi nazari.”

Dan baki ya tabe sannan ya jawo abincinsa ya cigaba daci, shiru Goggo tai tana tunani.

*******

Kashe wayarta Afreey tai sannan ta dawo cikin office ta xauna, producer ne ya shigo ya nemeta data zo ta shiga cikin shirin da za’ai a wannan lokacin.

Kallanta sukai dukansu dan tunda aka daukesu har yau ba wanda ya fara gabatar da wani shiri.

Zainab ce ta mike bayan ta gama nazarinta, office din Director Kabir ta nufa wanda tun shigowarta ya aiko yana kiranta.

Shiga tai bayan an bata izinin shiga sannan taja kujera ta zauna.

Kallanta yai itama ta kalleshi, dauke kai yai yace “kinyi sorting matsalarki?”

Tace “banida wata matsala da zanyi sorting.”

Kallanta yai fuskarsa ta bayyana bacin rai yace “Me kikeso mutane su daukemu? Kinsan kananan maganganun da ake akan ki?”

Kallansa tai ba tare da tace komai ba, ya cigaba “ance kunyi fada hartakai ga saki, sai dai dayake kece kike rike da auran korarsa kikai ya bar miki gidan, a cewar wasu ma kece kika gaji da auran kika sakeshi.” Cikin d’an daga sauti yace “me kike so mutane su daukemu a matsayinki na idan gidan tv din nan?”

Itama yanzu fuskarta dauke take karara da bacin rai tace “dan ina aiki anan sai akace ban isa na samu matsala a rayuwarta ba? Meye hadin harkar aiki da rabuwar aure na? Mun rabu ya tafi inda zai zauna sai hakan ya jawo matsala?”

Ransa a bace yace “kinsan ba haka nake nufi ba kema ai.”

Tace “am sorry amma ban fahimci menene hadin aikina da rayuwata ba.”

Takardun hannunta ta turamai gabansa tace “ga wad’an nan ka duba kasa hannu, zanzo na amsa gobe.”

Tana kaiwa nan ta mike ta fita, cikin kuluwa yabi bayanta da ido, ai yanzu tunda dai ta bashi ideas kala kala na yadda zasu cimma manufarsu na kusan shekara hudu zuwa biyar tabbas wannan karan ko da bala’i sai ya koreta, sam ya gaji da yanda kowa yake mai kallan a karkashinta yake kowa kallan wanda baisan komai ba yake, ko meeting suka shiga kowa abinda Zainab tace kawai yake bi ba wanda ya damu da nashi ra’ayin.

Zainab na shiga office dinta ta runtse idanunta tare da kwantar da kanta akan desk dinta, wayarta ta dauka tama Khalid text. “Ka samu inda yake?”

Ganin ba reply yasa ta maida idanunta ta rufe ranta na kara baci, jin alamar shigowar sako wayarta ne yasa ta bude ido da sauri ta dauka Khalid ne ya mata reply.

“_Ha Ha Ha! Ya kike ji? Gashi kema rayuwa tana neman yin juyi dake?_”

Kallan number tai batama santa ba sai dai murmushi ne ya bayyana a fuskarta tace “it seems I have alot of enemies” Maida idanunta tai ta rufe cikin kunar zuci.

Khalid kam yana can suna ta aikin editing sam bai kula da wayarsa ba sai wajen lunch da suka gama ne ya fito, yana daukan wayarsa yaga sakonta, har zai mata reply kawai sai ya danna call tare da d’an fitowa daga dan corridor.

Jin bata d’auka bane yasa ya kashe sannan ya koma ciki.

Afreey dake tsaye ne ta bishi da kallo har ya koma, haka kawai jikinta ya bata Zainab yake kira.

Ranta a matukar bace ta fito daga Station din ta shiga motarta.

Waya ta d’auka ta kira Giss, yana d’auka tace “ya kiraka?” Yace “tun dazu nake jiran kiranshi harynzu bai kira ba.”

“turon Address dinsa.” Haka kawai tace ta kashe wayarta.

A kofar gidansu Adam ta tsaya, kallan unguwar ta shiga yi tare da tabe baki, cikin sa’a sai ga Adam ya fito yana sosa cikin sumarsa, kallo daya tamai ta gane dan ta kara ganinshi sanda yaje gun Zainab.

Horn din motar ta danna sannan ta sauke glass din inda take zaune.

Kallan motar yai cikin santi yake kara kallan motar,yarinyar dake zaune a ciki ya kalla, tasha ado sosai kamar yanda ta saba, sam bai ganeta ba harya karaso, ya cire hannunsa daga kansa tare da dan dafa motar yana kallanta yace “wa kike nema?”

Murmushi ta sakar masa sannan tace “wali walawa baka ganeni bane?”

Kallanta yai cikin mamaki kafin yace “Afreey?”

Murmushi ta sakeyi yanzu kam har hakoranta ne suka bayyana tace “shigo.”

Cikin jin dadi ya bude motar ya shiga ya zauna sannan ya kalleta yace “ikon Allah, Afreey dana ki........”

Jan motar datai ne yasa ya kalleta yace “ina zamu?”

Batace komai ba har sai data bar lungun ta hau kan titi sannan ta ganganra gefen titi tai parking.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull