Kenza eBookz

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 107

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 107

A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 107: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 107. Munyi arbain yaro yayi matukar kyau dashi gashi sai kara…

2,667 words

Munyi arbain yaro yayi matukar kyau dashi gashi sai kara murjewa yakeyi yana kara haske da kiba sosai. Ga sadauki yanzu sai ahari,a akan gidan su sukeyi da dan masani wanda yaja sosai a kan zancen. Anyi nasaran kama yaya Ahmed an kulle shi a cewar Baba ma kada a sake shi a rufe shi don matsayin shi daya da barawo a gare shi. Tunda gidan shi ya shigo mai ta dakin shi ta baya ya fasa ya shiga ya kwashe mai duk wani abin kwarai nashi a lokacin. Don haka sata yazo yai mai a gida kuma ya kwashe mai takardu da ga baya yazo ya kwace mai gida. Hankalin mama Asiya yai matukar tashi sosai jin irin hukuncin da baba yace a yankewa yaya Ahamed. Sai gata a gidan mu tunda farar safiya ta sallama muna lokacin na gama shiri na tsab nayi kwalliya Iyya tayi wa Amir wanka takawo shi ya sha nono. Don shan nono kawai ke kawo Amir gurina da ya gama kuma zata goya shi sai idan ya falka ko tana daki su kwanta tare. Haka nake fita na barsu zuwa school don ina semester karshe yanzu ga karatuna. Sallaman mama yasa mu fitowa daga dakina ina rike da yaro a hannu ina bashi nono muka fito falon. Mama Asiya ce zaune saman kujera ta rafka uban tagumi cikin damuwa take. Nace a,a mama sannu da zuwa ashe kece mama shine kika zauna a falo baki shigo ba. Tace Fatima ba zama nazo ba mijinki na zo gani Allah dai yasa yana gida bai fita ba ? Nace yana nan mama tace yi min magana dashi don Allah Fatima kice gurin shi nazo. Na nufi dakin tabini da kallon yadda na koma wata fresh dani sosai kamar ba Bintu ba can. Yana kwance ya kifa ciki yana barci na,shigo dakin na samay shi a hakan . Sai da na zauna bakin gado na dan fara taba shi a hankali ya bude idon shi ya dago kai yana kallo na. Ina zaune ina kallon shi ina gyara yaron a nono nace ina kwana ina dare da fatan an tashi lafiya ? Ya dan goga kan shi a filo ya gyara mirginowa yana kallon mu yace my friend har ja tashi kai wanka ni ina kwance ko ? Nace tuni mukai wanka kaima ka tashi kai wanka sai ka karya sai dai mama tana falo tana jiran ka. Yace mama tare da kallon agogon bangon dakin shi da ido yace wata maman ke nan ke jira na kuma ? Nace mama Asiya ce mana Asiya kuma may kuma ya kawo ta nan gidan ko dama takanzo ne wai ? Nace gaskiya bata taba zuwa haka ba babu wani dalili sai yau kawai tazo ya ja tsaki ya mike zaune da kyau sai da ya shiga bandaki yai brush yafito daga dakin. Ya karbi Amir a hannu na ya fice da shi ina bayan ta jin motsin fitowar mu daga dakin ta dan gyara zama da kyau tana cewa kafitu Sadauki ga mamakin shi sai yaga yau itace ma mai gaisheshi kafin ya gaida ita. Yace lafiya dai mama naganki da sasafe hakan ga ko wani abu kuma ya faru ne a gida. Maimakon mama tayi magana sai kawai ta fashe da kuka mai tsuma rai sosai. Yace haba mama may yafaru ne ban son wanan kukan da kikeyi ni fa dan ki ne mama don Allah may ke faruwa ne please. Mama ta dan tsagaita kukan ta tace sadauki nazo gurin ka ne neman taimako akan dan uwanka da ke a tsare. Don Allah sadauki ka saka baki wa baban ku ya dan sasauta kalamin da yayi akan wai a daure Yaron nan da yace. Yace mama amma dai kin san Ahmed bai kyauta wa Baba bai kuma kyautawa mu yan uwan shi ba. Babu abin kunyan da yafi ace wai dan uwanka yasayar da gidan ku na gado ga kuma mahaifin ku da rai. Tace na sani sadauki yaron nan bai kyauta ba ba ku kadai yaiwa tozarci ba har ma dani mahaifiyar shi tunda ina a cikin gidan yanzu. Tace kaiwa Allah ka taimaka a tsare shi a lalabeshi ina sauran kudin suke aji idan yaso idan zai biya sauran da gabaya ne sai muji yadda za,ayi. Sadauki ya gyara rikon yaron dake a hannun shi yana cewa mama ai antambaye shi babu kudin a hannun shi yanzu yace yayi sayayan kayan part da yake sayarwa saura kuma matar shi ta sai abubuwan bukatan ta. Tace da karfi dama na,sani aidama nasan wanan shegiyar matar tashi yarinyar banza itace ta saka shi a,wanan halin. Sadauki yarinyar nan tun farko na fadawa yaron nan ba matar auren shi bace ita yarinyar da ta san kaduna tasan lagos itace zata zauna zaman aure agidan wani. Ko fa,abinci bata iya yi mashi gashi nan kullun cikin yawon zuwa saye ko yazo gurina yaci sai Alhaji yai mai fada yanzu ya bari. Idan dai tace ga abin da take so duk inda zai shiga ya samo shi sai ya shiga ya samo mata shi ake zaunawa lafiya in ba haka ba ko ba,su da zaman lafiya ita dashi ke nan. Yace kai amma gaskiya bata kyauta ba wanan aiba so bane kamar ba auren soyayya sukayi a tsakanin su. Mama tace soyayyan may can kuma dama aiba son shi takeyi ba karya yai mata shi mai kudi ne kuma dan mai kudi. Kakaga ko akwai karya acikin wanan yanayi koba gaskiya ba . Yace Allah ya kyauta mama tace amin cikin damuwa tare da nisawa takara fadin yanzu don Allah jika kaida Fatima gwanin ban sha,awa da ku ga zuria Allah ya fara baku a tsakanin ku. Kowa yaga yadda zaman ku yake sai yai maku sha,awa sosai don ga yi nayi bari na bari ba irin wancan mai bakin auren tsiya ba da duk ta halakamai rayuwan shi ko. Mama yanzu ki koma gida naji bukatan ki insha Allahu zan san abinda akayi abin yazo da sauki ai Ahmed dan uwana ne najini ba zan so naga ya,wullakanta ba nima. Godiya sosai mama tai mashi har da saka mai albarka da fatan gamawa da duniya lafiya (kudi ke nan) Nan dai ya mike itama ta mike yai mata rakiya har kofan gida ta,shiga motar ta wanda ya fara jin jiki yanzu sosai. Sai da yaga fitan ta daga gidan ya sauke ajiyan zuciya ya tsaya suna gaisawa da su maigadi har suna tambayan lafiyan Amir dake a hannun shi.

****** ********* ****** Mama tana komawa gida dakin maji ta shiga ta samay ta,a zaune tana karyawa ganin ta a,shiri kamar fita zatayi yasa take kallon ta da mamaki. Sai da ta samu guri ta zauna take cewa daga gidan sadauki nake yanzun haka. Gidan saudauki maji ta tambaya tace eh na tafi na samay shi ne kafin ya fita akan zancen yaron nan. Don ya taimaka Alhaji ya jaye zancen daurin da yace sai anyi mashi nasan yayi laifi mai muni amma sai ina ganin daurin da yace aimashi kamar zai iya kara jefa shi a cikin fitina kuma ya kara hinjirewa yafi haka. Don Allah idan sadauki ya shigo ki ka taimako na hjy maijidda kiyi mai magana duk da dai yai min alkawari akan na kwantar da hankalina zai duba al,amarin da idon basira in Allah ya yarda. Maji tace ai tunda kin mashi magana zai duba din da ke dani ai duk daya muke a gare shi don duk uwanshi muke Ahmed kuma ai dan uwan shi ne. Tace amma zan kara mashi magana nima akan magana don ya duba al,amarin. Tace nagode tare da mikewa tana fadin barin tafi na duba yaran nan na barsu basu ko tashi ba na fita daga gidan. Allah ya sauwaka mama tace mata tace Amin tana tsaye take cewa aini godiya na ga Allah shine sadauki yana da abin hannun shi da zai iya taimakawa dashi. Hakane inji maji tace da yanzu ai duk munsan inda muka nufa tunda mai gida yace yana bukatan gidan shi da,wuri haka. Sai da ya gama abinda yake ya shirya ya fita daga gidan ya nufi gidan su ganin iyayyen shi. Ya samu mama a dakin ta suka gaisa nan take cewa dashi sai ga hjy Asiya kun gani da sassafe haka yace eh tazo dazun itace ma ta tayar dani daga barci ai yau din nan. Nan yake fada mata yadda suka kwashe da mama din tace tunda taje har ta ganka sai kasan yadda zakayi da shi yanzu. Kayi kokari ka taushi mahaifin ku yayi hakkuri akan maganan da yayi yace ai babu damuwa maji. Ya nufi gurin mahaifin su don ya gaidashi ya samay shi zaune a keken dake taimaka mashi ga tafiya wanda shi sadaukin ne ya kashe kudi masu yawa ya saye shi don baba din ga shawaran da likita ya bashi a can. A mutunce ya durkusa ya gaida baba din sanan ya tambayi lafiyan jikin shi ? Baba yace Alhamdullahi can baban yace yaya zancen kotun naku yakaya ne cikin maganan shi da ba fita yake sosai ba. Kan shi ya dago yace Baba ai mun yi magana ta fahinta da mutumin yace a jaye karan idan har zan biyashi kudin shi na,kara mai riba a sama. Baza,a kara mai ba inji baba aiko shi mai laifi ne don ba gaskiya bane yasan ina a raye ya sai mingida ga hannun dana. Sadauki yace hakane baba ai yanzu shi lauyan tanan ya bullo mai shine yasa hankalin shi ai ya tashi sosai. Don da da farko yana ganin zaici riba ga maganan amma yanzu jikin shi ya fara sanyi kan case din. Ance halinshi ke nan ko mutuwa akayi sai ya kwace gidan marayu ya,saye a araha ya cuce su. Baba yace shine ni bai jira na mutu ba yazo cin nawa ko? Kayi hakkuri baba kaddarane duk haka ba kyau ma gana tuna aanan zancen a zuciyar ka don kara tayar ma da hankali kawai maganan zaiyi. Insha Allahu gidan ka har yanzu yana a matsayin naka illa iyaka mubashi kudin shi daya,bashi Ahmed din shike nan a zauna lafiya. Shiko Ahmed din ku kulle dan banza can yayi iya rayuwan shi a gidan yari don banga amfanin haihuwan shi ba ni. Hakkuri dai za,ayi baba ai yanzu shima a cikin tashin hankali yake ko yaushe. Wanan yarinyar da ya,aurace ke kaishi ga halaka akace don ba yarinyar kirki bace wallahi. Bashi ya aurota ba inji baba sadauki yai dariya yace baba kaine fa ka,yarde mai bayan mama ta hana abin . Shiru baba yayi yana daya sani a,ranshi don yai nadaman zaman Ahmed da,wanan yarinyar mara mutunci da ita. Yana fita gurin baba bayan sun gama magana dashi kotu suka nufa shi da yaya bashar sun samu danmasani ya ce idan zai samu kudin shi ya janye maganan shi. Ba bata lokaci sadauki ya saka hannu akan zai ba mutumin kudin shi miliyan bakwai da Ahmed ya karba a hannun shi. Nan aka zauna ranan ya biya kudin a ka rufe case din tare da sako yaya Ahmed yakai shi har gidan shi gurin matar shi ya nufo gida don lokacin har duhu yafara yi ko. Bai shigo gida ba sai da aka sallamay sallah yashigo gida agajiye dashi. A sanyaye ya samay mu a falo muna hira Amir yana hannun Sa,ade tana mashi wasa. Sannu muke mashi yana karbawa da kyat ya fada saman kujeran dake kusa da wanda nake zaune. Na kalle shi yadda na ganshi a wahale dashi nace ko zakai wanka ne ka ji dadin jikin ka ? Yace shine daidai tun safe muna koto ana zirgazirga kan zance yanzun dai mun samu ankashe case din mun karbi takardun mu ko. Nace masha Allahu yau baba idan yaga takardan shi a hannun shi kila hankalinshi zai kara kwantawa hakanan. Ya lumshe idanuwan shi yace ban tafi na,kai mai ba,sai da,safe idan Allah yakaimu. Nace Allah ya kaimu na mike na nufi dakin shi na hada mai ruwan wanka a can kafin ya taso yayi. Sai washe gari ne ya shirya tafi gurin baba ya kai mai takardan gidan nashi da,aka anso gurin mutumin da ya sai gidan hannun Ahmed din. Sai da baba ya tara kowa diyan shi da matan shi da,aka kirasu a,waya yake cewa dama akan zance gidan nan ne gashi yau Allah yayi Sadauki ya karbo gidan a hannin azzalumai macuta. Don haka daga yau ina son ku sani gidan nan ba gida na bane gidan sadauki ne da uwarshi don haka ko bana raye kowa ya rike wanan zancen a ran shi. Duk suka dago kai suna kallon baba da mamaki don jin abinda yace wai gida na sadauki ne da uwar shi yanzu. Sadauki ya tare baba da cewa haba baba gidan nan na kowa ne baba tunda gida nakane har yanzu ni bawai na karbo bane don ya zama nawa ba. Baba ya daga mai hannun shi da kyat yana cewa wanan magana danayi ba fashi a cikin shi sadauki gida nakane yanzun ba nawa ba. Idan kuma kana,son ganin bacin raina ne a yanzu sai ka matsa da magana mu gani. Dole yaja bakin shi yai shiru yana gudun yai magana wani matsala ya faru da baba. Baba yace Ahmed dai yanzun sai kuyi kuka dashi da uwar shi don shine yaja ma kowa wanan bani ba. Don ni Allah ta gani nayi yadda ya dace nai maku muhalli wanda ko bayan raina iyayyen ku daku zaku iya zama a ciki am.a ya,sa kafa ya take tausayin kowa dani daku yasayar wa banza irin shi macuci. Don haka yanzu na fada maku gida yana a zaman sadauki ne bani Abubakar ba kuma. Sai kowa ya,watse na gama magana na ke nan ya juya inda mummy take zaune tai tagumi sai sauraren shi ta yake yace ke turani ki maidani dakina nagama maganan da zan yi kenan. Mummy ta mike duk jiki ba kwari ta fara turashi zuwa uwar dakin shi cikin rashin kuzari. Nan ya barsu a,zaune kowa jikin shi ya mutu ana shigewa dashi Nafisa ta fara mikewa tana fadin yau dai shi ke nan tafaru ta kare kurun kus kan kutsu sai kowa ya fara neman madafa. Maganan ta yai matukar ba kowa haushi uwarta ta kalle ta tace ke kan anyi sakariyar yarinya wallahi nan. Ke kan baki san ciwon kanki ba ko kadan yau wanan abin tashin hankalin da may yai kama harda kike fadin wai takare. Takare mawa ke nan kike nufi yanzu mu ko ku da baku da madafa kamar kowa. Ai mu muna da gidan iyayye sai mu koma can mu zauna ku kuwa ina zaku kuda baku da gidan uba. Mu dai wallahi ancuce mu anzalunce mu sai dai muce Allah ya isar muna kawai ancuci na kauye. Saboda hainci da zalunci dan gidan ma da za,a tsira dashi akama a sayar wa mutane su rasa matsuguni sai rabe rabe. Sadauki ya mike tsab ya fara fita daga dakin bayan fitan Nafisa yabi bayan ta. Sai mama da Amira da maryam suka mike suma suka fice daga dakin ran su a bace. Lokacin Umma ke fadin muna fukai kawai kun kai ga yadda kuke so ai dama gurin ku su ke nan duk su mamaye gidan to gashi Allah ya cika maku ai gida ya zama naku. Sagir dake zaune kasa saman carpet yace haba haba Umma yanzu may yw laifin yaya sadauki a gidan nan. Mai laifi daban wanda bai da laifi ya taimake mu ya raba mu da gararanba a saman titi kuma za,aga laifin shi a banza. Gaskiya wanan ba adalci bane kuyi wa kanku nasiha ku san may ke a gaban mu ba,wai mu zauna kuma muna cusa kiyayyan junan mu ba a haka. Ya mike yafita daga falon shima,ranshi a bace ya,saka takalman shi ya bar falon. Nan dai sukai ta watsewa daya bayan daya a falon kowa jikin shi ya mutu don basu taba zaton wanan hukuncin baba zai iya yankewa akan su ba.

Readers Also Read