Kenza eBookz

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 114

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 114

A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 114: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 114. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA…

4,206 words

ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , ,

IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH , , , ,

Washegari da kyat na shirya muka kwasa saigidan su mama gurin shagalin bukin da akeyi na samu yan uwan mama saura sun iso nan na shiga gaisawa dasu cikin mutunci da girmamawa. Na samu guri na kai zaune don indan huta saboda tafiyan da nayi sai ga mama ta fito daga cikin dakin ta tana ganin mu tace , a, a kun karaso ashe. Nace eh mama nai mata ina kwana tare da tambayan ta ya gajiyan jama, a ta amsa da fara, a da alhamdullahi. Maryam ta rigani isowa sai gata tafito da alama a tare da mama suke a dakin. Nan muka shiga gaisawa da ita tana min ba, a wai bata tsanmani ta gannin ba yau yadda na gaji da jigila jiya. Muryan mamane mukaji tana cewa Fatima ke da maryam kuzo ba bata lokaci muka bi bayan mama din data shiga dakin ta. Zama tayi saman kujera yayin da ta umurce mu da zama a bakin gadon ta sai dai kafin mu kai ga zama tace maryam kira min wanan yar butsar maryam tace wa anty Amira? Mama tace ita mana a takaice maryam din ta fita ta barmu ni da mama a dakin sai dai babu wanda yai magana a cikin mu dagani har mama din har suka shigo dakin. Kowan su guri ya samu ya zauna muna sauraren abin da mama din zata fada muna. Fatima dafarko dake zan fara abinda ta fada yasani saurin dago kaina da sauri na dan kalle ta sai kuma nai saurin mayar da kaina a kasa. Tace ban san irin godiyan da zan wa Allah ba da yahadani dake a matsayin diya kuma sarakuwa ta gari a cikin zuria ta. Fatima ke alheri ce a gare mu abin alfaharin kasancewa a cikin zurian gidan nan a baki daya. Jin yadda mama take yabona bamu san dalili ba dukan mu yasa Amira saurin daga kai tana kallon mama da mamaki may yakawo wanan yabon haka ne wai. Mama taci gaba da fadin fatima kin yi abinda ko wace sarakuwa take gurin gani ga ko samu ga matar da danta ya aura a cikin zurian ta. Nasan baku san abinda yasa nake mata wanan yabon haka ba sai na fada maku. Yau da asuba yayan ku ya kirani yake fada min cewa Fatima ta kirashi a cikin tashin hankali tana mashi magiya kan lalai sai ya sayawa Amira gida nata na kan ta inda zata zauna. Yamzun dai in takaice maku tsohon gidan shi daya gina ya tashi a ciki ke maryam na kusa daku ya mallakawa Amira shi halal malak. Ke kuma yace idan ya dawo za, a duba gida kwatankwancin wanan din ko ya gina maki naki a matsayin naki kema maryam. Gaba daya sukayo kaina da murna suka rike ni nayi mamaki yadda yau Amira ta sauko haka lokaci daya kan abin duniya. Tace cikin muryan kuka Bintu ban san godiyan da zan maki ba duk da dai bake ya kamata naiwa godiya ba amma kuma ke ce silar hakan. Nace anty babu godiya a tsakanin mu don ku yan uwa nane na jini dole mu taimakawa junan mu idan ya dace amatsayin mu na uwa daya uba daya duk dai ni din bare ce acikin ku amma banda uwa da uban da suka fi min baba da mama a duniya har lahira don sun min komai a rayuwana nakarasa a cikin kuka nace don may nima bazan dinga kokarin gani saka dan uwan mu a hanya ba tunda Allah ya hore mai abinda zai kula damu. Fatima mungode da wanan karamcin don ba kowane akewa alheri ya samu ya tuna baya ba haka. Yayan ku ya fada min baki taba rokon shi da ya taimakawa kowa naki ba a duniyan nan ba sai idan shi yaga ya dace yai masu wani abin. Amma mu sai gashi kina ta iya kokarin ki gurin ganin ya kyautata muna nasan ko alherin da yaiwa iyayyen shi kwanaki shawaran kine wanan. Nan dai mama ta kara ja muna kunne na mu hada kan mu da zurian mu koda bayan ta don haka shine tabbacin dauruwan zumunci mai karko. Nan dai muka dan taba hira akan yadda za, a bullowa al, amarin bukin da saura kwana daya a saka lalle. Nice nace mama yanzu shi Ibrahim din ya kamata mu kira muji tashi shawaran ko zai yarda da hakan ko ? Da sauri anty Nafisa take cewa kamar yaya zai yarda idan bai yarda basai a fasa ba don ni wallahi Allah ban zama a wanan gidan nasu na yawa. Kinji halinki ko inji mama ta fada a cikin fada da sauri na tare nace anty don Allah kibi al, amarin nan a sanu shi fa sauri baya haihuwan alheri ke da Ibrahim dai kuna son junan ku baida shine ne anty yanzun kuma tunda Allah ya hore mai ai ba zaiki ba ko. Abar maganan a hannun yaya shi yasan yadda zai bullo mashi da maganan don kin ga wanan magana ce ta maza. Haka yasa kowa yai shiru dakin don sun san magana ta gaskiya ne mama tace mu tashi mu tafi shi ke nan . Maryam da ta riga mu mikewa take cewa sai muje gidan muga abinda ya dace ayi ciki ko don kayan dake ciki yaya za, ayi dasu kuma ? Nace wanda za, a cire aba su mama Abu mana bashi ke nan ba sai dai kwasan su daga nan zuwa can ne aiki ai inji maryam nace ba wani aiki da anyiwa yaya bashar magana suna da manyan motoci sai a kwasa akai masu har gida. Mama kan dadi ya hanata magana don bats san may zata fada kuma irin wanan alherin haka samun dan uwa shine samun kowa ai namike ina fadi nabar dakin. Kamar yadda muka tsara din ina fita na kira yaya akan yaiwa ibrahim din maganan tare da kuma yi mashi godiya sosai. Yace haba queen nine fa ya kamata na gode maki bake ba kin kuwa san irin albarkan dana sha kan wanan zancen gurin mahaifa na. Idan baki halkantar dani ba hakan yaushe tunane na zai barni na kai ga tuna hakan da akayi kinga ai yanzu an wuce gurin ko? Ya kira ibrahim din yai mai magana tare da bukatan idan ya dawo ya kawo takardun shi zasu samu ida suka sakashi a maikatar su. Ya tun kari mahaifiyar shi da maganan taso ta musa mashi amma a hankali ya fadakar da ita alherin dake cikin yin hakan dole ta yarda data ji cewa harda aiki za, a sama mai. Karshe cewa tayi ya daiyi adalci a tsakanin iyalin shi yace insha Allahu mama. Shi da kanshi yazo har gida da yamma yai muna bayanin amincewar mahaifiyar shi a kan zancen wanda dama muke hasashen matsalan komai daga gare ta ne don bata son yabarsu. Ba bata lokaci aka tafi gidan tare da masu gyaran guri decoration din gida mun masu bayani komai yadda zasu gyara mata shi wanda a shagona aka sayo duk kayan da aka saka mata a gidan na miliyoyin naira. Sosai akai ta shagalin bukin da har su Umma ance mai hali baya barin halin shi har sun fara gulma akan zancen. Amma da sukaji gidan sadauki tsoho za, a aje Amira kuma ba gidan iyayyen mijin ta ba sai kuma sukai gum. Anyi angama lafiya shima sadauki ya dawo ran daren daurin aure sune suka shugabanci bukin. Amarya ta tare gidan ta lafiya kowa sai murna da farin ciki yakeyi yadda dan uwanta ya kashe mata kudi haka na.

****** ********* ******

Bayan buki da kwana biyune na tashi ban jin dadin jikina nasan dan jigilan bukin da mukasha ne dole naji ba dadi haka dama don yawancin event din ma a gidana akayi shi. Gashi washe gari yaya zai koma Abuja gurin aikin su don yanzu sam baida lokaci ko kadan yanzun ma don shagalin bukine ya dan dauki hutun kwana hudu kawai. Har yafita motsa jikin shi wanda yanzu bai faye fita waje ba yi akwai kayan motsa jiki kala kala da ya sayo yakeyi saboda tsaro. Kwance ya samay ni yarda ya fita ya barni da farko yana cire rigan jikin shi hankalin shi yana akaina. Lafiya kike kuwa har yanzu baki tashi ba karfe kusan tara fa yanzu na safe. Na dan bude idanuwana da sukai min nauyi nace a hankali wallahi ban dai jin dadin jikina ne sosai yace zan shiga wanka hada min abincina kafin nafito ina son zuwa gurin baba ne nagan shi. Da kyat na samu na mike zaune yana shiga bathroom din lokacin na sako kafana kasa da zuman na mike tsaye. Yadda naji an tokare ni ban san lokacin dana sake yar kara ba na koma na dunkule guri daya. Jin karan da nayi ne yasa shi saurin fitowa daga bathroom hankali a tashe yana tambaya cikin kidimaywa may nene may ya faru ne wai ? Cikin daure wa nace ba komai bane mara nane kawai ya yanka min da dan ciwo. Yace oya mike mugani aiko mikewa ya gagareni na sake jin an kara yankoni kasan marana da karfi na sake wani dan kara again. Yace cikin rudewa O god kingani ko ina ta fasa maki cewa kiyi a hankali kin san condition din ki amma duk baki jiba yanzu gashi zaki jawowa kanki matsala kuma. Yace barin watsa ruwa sai muje asibiti a gani ko may nene matsala ya juya yana min sannu ya shige bathroom da kyat na samu na mike zuwa dakina. Dakyat nake iya daga kafana zuwa daki ina shiga kamar an kara min ciwon maran ne a lokacin. Tsaye nayi na dafa mirrona ganin abin ba na wasa bane yasa na dan duka a gurin wasa wasa nakai durkushe cikin tsananin ciwon mara dake damuna. Shigowan shi yana fadin kin shirya mu tafine yai arba dani cikin wani hali sai zufa ke karyo min tako ina da sauri ya karaso inda nake duke yana fadin subbahanallahi. Abinka ga geant din mutum ya yunkura zai dauke ni da sauri cikin wani murya nace mai ya dakata don Allah. Ido ya kura min daga gurin da yake tsaye yana kallona danaji abu tafe min ban san lokacin dana rike shi gam ba iya karfina na nisa da karfi sai ga yaro ya fado kasa rikon da nai mai duk da karfin shi sai da yaji shi sosai a jikin shi. Ganin yaro ya fado ne yasa na dan sasauta rikon ina mayar da numfashina a hankali take yarude hankalinshi ya tashi sosai. Ga yaron yana ta faman tsala ihu a kasa saman ties na nuna mai zanina dake gefe ya miko min na saka yaron a ciki. Shi kuma yafita daga dakin da sauri hankali a tashe yana kwallawa iyya kira cikin tashin hankali. Iyya tafito dakin da sauri hankali tashe ganin yadda ya rude bakin shi na rawa yake fadin don Allah Iyya shigo da sauri ki taimakawa Farima ta haihu yanzu a dakin ta. Haihuwa Alhaji haihuwa fa takara fadin hakana cikin sauri ta nufi dakin hankalinta a tashe sosai takaraso inda nake tsugune. Reza take fadi nace tabude drower akwai reza a ciki da sauri ta dauko ta yanke cibin yaron dake ta faman kuka cikin zani. Ta juyo inda nake tana fadin sannu uwar dakina ke kuma haka haihuwanki yake wata bakwai. Tsab tagyara ni ga gyara yaron shi yana falo ya kasa zama kuma tsoro ya hana shi ya shigo daga ciki. Yana ganin iya tafito diban bakin sabulun da ta hada a dakin ta ya tare da sauri yana fadin. Iyyya yaya dai tana lafiya ko kuma yaron zai rayu kuwa yana ma dai rai kuwa ? Tace insha Allahu zai rayu ba haka ta haifi magidana ba yau bagashi kamar zakaran turawa ba. Haka nata haihuwan yake wata bakwai take haihuwa ita ke nan. Ya sauke ajiyan zuciya nan ya jawo waya yashiga fadawa su mama can gida. Yan uwan mama dake shirin tafiya suka tanbaye ta da sukaji tana fadin ikon Allah ta haihu fa kace yace wallahi ko mama yaro namiji ta haifa. Nan kuma gida ya rude kowa yana mamaki suna tausaya min sai cewa suke yi boyar Allah bata zauna ba duk jigilar bukin nan da ita akayi shi ashe tana jin abinda take ji a ran ta . Nan aka kwaso zuwa gidan mu ba bata lokaci kafin duk su iso maryam ta riga kowa zuwa ta samay ni na fito wanka ina saka kaya a jikina. Tace madam haka kuma abin ya kasance dake ashe ta nufi inda yaron yake dan karami dashi ta dan bude zanin da iya ta nade shi a ciki tana kallon shi. Tace wanan ai duk Amir ne aje wallahi duk uban su suke kwasowa yaran basu biyo ki. Nai murmushi ina kaiwa zaune nace yafini karfin jini ne shiyasa hakan tace yadai fiki kwazo ragguwa kawai nace nadai ji. Shigowa yan gida yasa gida ya kara rudewa lokaci guda sai sannu suke min. Yace wa mummy sai mu tafi asibiti aji idan na shirya don a duba yaronkuma aga lafiyan shi. Dole haka na fito muka kwasa sai asibiti ni dashi da mummy da maryam. Anyi duk aune aunen da za,ai muna antabbatar dagani har yaron muna da lafiyan mu. Haka yasa hankalin shi ya kwanta sun so wai a aje yaron amma mummy bata ba da surport ba kan hakan muka dawo gida. Nan kuma na fara jego ba shiri don haihu a bazata sosai ake kulla da yaron yadda aka kafa muna doka akan shi. Wanka sau daya ake mai a wuni koshi ba kamar yadda akewa sauran yara ba towel ne za, a dan dinga jikawa cikin ruwa dumi ana goge shi dashi a hankali wanda mummy ce keyiwa yaron . Babu mai daukan shi don wasu saboda kwakwafi sai suce abasu yaron su gani. Mummy ta hana ko mama Asiya dake zama da dare a gurin mu nan take kwana a tare da mu. Naga yan uwa da abokan arziki masu zuwa barka don wasu ma ba sanin su nayi ba . Shiko sadauki duk hankalin shi bai kwanta ba yana ganin yaron zai mutu ne ba zai rayu ba. Ranan suna yaro yaci sunan mahaifin Umma watau Abdullrahaman nima sunan nawa mahaifin ke nan amma shi Abdullahi yake. Sai da komai ya koma normal ne ya samu komawa gurin aikin shi tare da jaddada muna akan mu kula da yaron wanda a hankali yake ta hiling. Nan dai komai ya koma normal a gare mu anyi auren su anty Nafisa wanda mijin dake son ta ya bukaci anyi da wuri sadauki ne ma yadan ja lokaci don ta samu tayi istibira,i kafin auren. Nan ta dawo gidan mu ta zauna kafanta kafana ko tafiya zanyi tare muke zuwa da ita. Har Allah ya taimaka tagama aka saka ta lalai muka sha buki muka kaita kano gidan Iyayyen mijin ta muka barta can. Mutane ne masu matukar addini da sanin darajan bako don ko sun daraja mu sosai ga abin arzikin da mukaje mata dashi sai dai ita a Abuja zata zauna a can mukai mata jeren kayan takayan gara ne kawai muka kai kano gidan mijin ta. Ko a kanon ma an gyara mata dakin ta na can kano din sosai komai acan acan dashi. Bayan kamar wata hudu akai bukin Raiha aka kaita maiduguri gidan mijin ta shima dai a Abujja yake aikin shi na soja. Itama dai zama tare yasa sadauki ya taimaka mata sosai don yai mata goma na arziki sai da tai kuka don murna. Iskancin su bai bari sun aje komai ba na kasan su sai iskanci da bushasha kawai suka saka agaba ashe. Itakan Nuriya bata da ranan aure a rayuwan ta cewan ta ai aure tauye rayuwane kawai ba incin kai. Wanan dalilin yasa na daina hurda da ita don naga bata da alaman kintsuwa tare da ita. Ko tazo bani ma bari ta gan ni har tagaji ta daina zuwa dama don Nafisa muke mutunci yanzu kuma Allah ya rufa mata asiri takama kan ta. Nan dai al, amarin sadauki ya bunkasa ya zama daya daga cikin miloniyan matasa na kasa masi fada aji yanzu. Yarana sunyi wayo sai masu kyau dasu kamar diyan turawa gashi bamu faye zama kasan ba ko yaushe muna kasan waje tare dai da iyya muke tafiye tafiyen da mukeyi don kula da yaran mu. Na kara samun wani ciki shima da namiji na kara haihuwa wanda naso ace diya mace na samu don ina son diya mace a rayuwana sosai. Sunan shi ya sakawa yaron sai dai duk yafisu zatin girma sosai. Gaba dayan su yaran kamar su daya idan ka gansu gwanin ban sha, awa dasu ga kula suna samu sosai dani dasu a gurin mahaifin su. Naso ace na huta hakanan wanan karon amma sai dai ina sai kuma ga wani cikin ya kara samuwa again. Na tayar da hankalina sosai kan hakan amma babu yadda zanyi dole na hakkura dashi. Don ya bata ranshi kancewan da nayi zan zubar da cikin har karana yakai gurin mama inda tai min fada sosai dole na hakkura takuma ce na bashi hakkuri. Na bashi hakkuri amma sai da yai min fada yana cewa wai kila shine banso yasa nake gudun haihuwa dashi yanzu. Nace haba yaya idan ban son ka wa zanso kawai dai naga abin ne ba hutu ko yaushe daga goyo sai ciki nasone kawai na dan huta har gaba. Yace basai ki jira gaban ba amma ciki ya zama rai don baki da imani zakice wai a zubar dashi akan may zan biye maki muyi kissan kai a tare. Nace ni dai ayi hakkuri abar zancen hakana tunda ankai karata gurin mamana har tai min fada. Ikon Allah wanan haihuwa ban haihu wata bakwai ba kamar sauran sai da cikin ya cika wata tara da dan kwanaki na haifo yar diyata mai kama dani sak. Yana shigowa dakin ya kalli yarinyar yaji wani sonta ya matukar shiga ran shi sosai a lokaci daya. Yadauke ta ya rugumay ta ajikin shi yana mai jin dadi a ran shi take ya kira yarinyar da uwata nan nagane sunan mama ke nan yarinyar taci. Ranan suna aka rada mata hauwa, u suna kiranta Ummi kowa na gidan. A ran daren suna ne jikin baba ya motsa mai akatafi asibiti dashi amma kafin safe yace ga garin ku. Allah yasa sadauki yana gari a lokacin don haka yayi sa, a a hannun shi kamar yadda baba ke da gurin ya cika dan shi na gari. Allah ya karba mai ya rasu a gaban shi cikin yadda ake son ko wani musulmi ya cika da kyau da imani. Sai bayan sun yi sallah asuba ne suka fara sanar da yan uwa da abokan arziki rasuwan baba din. Ya bugo waya ya sanar da mu ni da kaina najamu zuwa gida hankalin mu a tashe don rashin da akai muna. Take gida ya cika fam da yan uwa nesa dana kusa an kawar da baba akai zaman kwana uku kowa ya watse. Baba ya tafi ya bar iyalin shi a cikin rashin jittuwa a tsakanin su yadda yaso. Sai bayan sati biyu ne aiko yaya Ahmed ya tayar da kayan baya akan a raba gado abashi nasa. Haka ya kara tayar wa kowa da hankali sosai lokacin sadauki baya gari amma an buga mai waya yace abari yazo. Amma yaya Ahmed da matar shi ta zugo shi yace bai san wanan ba dole araba ai sadauki ba girmuwar shi yayi ba. Haka ne ya tunzura ran sadauki yace ana iya rabawa amma banda gida da gona don baba ya sayar mai dagona tun yana da rai yace sagir ya kai takardun kowa ya gani. Ai kuma sai zance ya koma wani sabon tashin hankali don dama gidan yakewa da gonan a raba a bashi ya sayar sai ga zance ya koma kasa kuma. Ya buga kasa yace sam shi bai san zancen baba ya sayar da gona ga wani sadauki can ba. Mummy tafito tace anyi haka kuwa don ita tasan da zancen don ita sheda ce a hakan. Ya sayar ya gina masalllatai da kudin shi yayi gyaran wasu kuma duk da kudin. Babane hanata ya ce kada ta fadawa kowa sai bayan ranshi za, a sani don haka kowa yaje ya nemi takansa. Sai na kashe sadauki wallahi yaya za, ace yafi mu kudi yafi mu komai kamar shi kadai ne kawai dan da aka haifa a gidan nan. Ya zare kamar wani sabon mahaukaci yana cewa idona idon wanan mugun guy din sai na halakashi wallahi. Hankalin maji ya tashi sosai yadda taga Ahmed din ya zare masu a lokaci daya ya koma kamar wani mara hankali dashi. Wayana ta kira take ce min naiwa masu gadin gidan mu magana su kula ga abinda Ahmed yace zaiyi kada yazo bai samu sadauki ba yaiwa jikokin ta illa. Nima hankalina ya tashi danaji nace a kidimay mama kefa dake gidan kada fa yazo yai maku wani illa a gidan. Mama tace Fatima niku nakejiwa dai don naku yafi damuwa na sosai wallahi hankalina a tashe yake Fatima da kalamin yaron nan gashi na kira mijin ki ban samu layin shi ba. Nace mama bazaki samay shi ba don suna meeting ne da tun safe da suka shiga yace sai uku zasu fito. Bayan munyi sallama nima sai hankalina ya tashi don nasan yaya Ahmed mugu ne zai iya yi komai daya fada. Nakira sadauki na samay shi a waya nake fada mai abinda yaya Ahmed yace akan shi din Dariya yayi yace kai Ahmed din may can insha Allahu bazai iya komai ba da yardan Allah. Duk da haka ya kafa matakan tsaro sosai a kan mu ganin hankalina dana mama yai matukar tashi sosai a gidan. Ranan da sadauki ya shigo gari ya tafi gida gurin mama take kara fada mai yadda akayi da Ahmed din yace mama Kwantar da hankalin ki Ahmed ba abinda zai min naso ya bari mu rabu lafiya dashi kamar yadda nake fatan mu rabu lafiya da kowa. Haka dai ya kwantar mata da hankalin ta sosai har ta aminta da zuciyar ta sosai. Bayan tafiyan shi da kwana biyu yara zasu tafi makaranta mai daukan su yazo har sun fara hanyar fita na ji zuciyata tana halbamin. Namike tare da cewa Nura direba ya bari nazo mu tafi tare mu sauke su a school din. Tun bayan fitowan mu a layin mu ne na hankalta da wata mota dake bin mu a baya na fadawa Nura driver abindana gani waya muka bugawa security din mu suka biyo mu a baya aiko mu motar kebi da gakiya don muna shiga titin da zai kai makarantan motar tasha gaban mu suka take mu da bindiga wai mu fito. Muna kokarin fitowa ne Allah ya takaita muna wahalan mu security din suka iso gurin aka fara musayan wuta dasu na tara yarana a jiki na kwanta masu sai rokon Allah nake yakawo muna agaji. Allah ya rufa muna asiri yansanda suka kawo muna agaji nan Allah yabada sa, a aka kama wasu daga cikin mutanen. Mu kuma aka tafi damu gida cikin tsaro ai kafin wani lokaci labari ya karade gari. Sadauki yana samun labari hankalin shi yai matukar tashi sosai duk da yaya bashar ya kwantar mai da hankalin shi amma bai hanashi dawowa gida ba hankali a tashe. Nan ya sa na shirya yara yana fadin garin zai bari damu baki daya duk yadda naso ya barmu bai yarda ba tare muka bar garin dashi muka kwasa har da Iyya sai Abuja. Sai bayan tafiyan mu ne muka samu labarin ashe yaya Ahmed ne ya turo mutanen nan suyi kidnapping din mu Ran yaya sadauki yai marukar baci bai san kiyayyan ya kai haka ba har ga iyalinshi sai da wannan abin ya faru akan iyalin shi. Kuma wai dan uwanshi najini uba daya yasa ai mashi wanan irin aika aikan haka. Da Ahmed zaice ya bashi duk abinda yake dashi da zaifi mashi sauki akan dauke mai iyalan shi daya saka ayi ko kuma shi yai mai wani abin can ba yaran shi da matar shi ba. Anso a daure Ahmed amma yaya sadauki ya hana karshe ma ya bashi kudi masu yawa a matsayin jari a gare shi don yasan talauci ne ya jawo mai wanan batar haka. Daga wanan lokacin zaman mu ya koma rabi Abuja da anyiwa yara hutu kuma mubar kasan zuwa waje. Haka rayuwan ya dinga ci gaba iyayena da yan uwan mijina kowa yana moriya daga gare shi har ni da yarana. Kowa yana alfahari da samun shi an manta da baya abubuwan da suka faru adduan iyayye yayi amfani Allah ya shirya kayan shi ta yadda ba, a zata ba. Don haka Addua mahaifa take da amfani ga yaran su komai dadewa insha Allahu zamu samu riban adduan iyayyen mu. Dafatan Allah ya bamu ikon yawaitawa yayan mu addua ta alheri don ganin cigaban rayuwan su a kullun.

Readers Also Read