Kenza eBookz

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 40

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 40

A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 40: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 40. ****** ********* ****** Tunda sadauki ya fita zuwa dakin shi…

3,883 words

****** ********* ****** Tunda sadauki ya fita zuwa dakin shi bai fito ba ya,samu guri ya kwanta,tare da,karewa,dakin da yasha gyara kallon mamaki. Don yasan ba aikin su Amirah bane wanan wa yan nan malalata yaushe ma,suka,iya,gyarawa Maji guri yai kyau balle na,wani. Da,sauri zuciyar shi da,tafara tunane tabashi amsa,da,fadin ba,aikin kowa,bane sai wanan yar kauyen ta Maji. Bakowa zai iya wanan aikin haka,ba,sai ita wata irin yarinyace bata jin ciwon jikin ta ita aiki bai isanta ko yaushe a,tsaye take ita. Nan dai har barci ya dauke shi inda bai farka,ba,sai da yamma lis don gajiyan da,ya,debo. A,tare ya hada,sallah dake kan shi yayi ya,zauna gurin har lokacin da,aka,fara kiran sallah magariba,ya,wuce masallaci akai jam,i dashi. Yaushe rabon shi da,yin haka,mutumin da komai nashi a,tsabare yake abinshi bai shiga mutane kamar mugu yake ko yaushe, sai yawan nisanta kanshi da mutane yakeyi. Tun a masallaci suka hadu da mahaifin shi ba karamin dadi yaji ba na ganin Sadauki a jam,i tashin farko da,dawowan shi. Sama sama suka gaisa da mahaifin nashi don akwai mutane da yawa lokacin. Yai matukar manakin yadda mutane ke kokarin gaisawa dashi yau sabanin da can baya da mutum zai wuce ya,wuce abinshi ba mai gaida wani cikin su. Shi girman kai mutane kuma suna kyamar dabian shi da ya tsira acikin al,umma. Ana idar da,sallah direct cikin gida ya,shiga gurin mahaifiyar shi don bai gaji da jin dadin ganin ta,da,yayi don dan,kwana biyun da,sukayi basu tare a lokacin yasan dadin Maji sosai gare shi. Ashe ma yawan fadan dayake ganin tana mashi wani babban gata ne gareshi. Don zaman ta kusa dashi yafi rashin ta a kusa dashi ko yaushe. Yana shiga falin duk suna zaune ga dan busashen falon nasu kamar kullun suna hira. Sannu da dawowa suke mashi gaba dayan su a cikin murna kamar su lashe shi don jin shi da,suke ajiki ranan. Cikin harshen turanci yake ce masu daidai lokacin da yake zama kai I miss you people fa. Ina yawan tuna ku ina can ko wani lokaci wallahi, Yace ina Maji take ? Tana part din Baba tana hada mashi abinci yace ok yau itace da duty ke nan ? Maryam ta bashi amsa da eh, Zaunawa yayi dakyau yace Amirah may aka dafa ne da,daren nan ? Amirah ta bashi amsa da tuwon semo da miyar kubewa danya. Jeki kawo min na dan ci na fita,na,samo maku dan wani abin sha kafin dare yayi. Maryam mai kwadai tasa ihun kai canji yaya wallahi har naji dadi har cikin raina, Yace common see yo mai kwadan tsiya kawai tace ba haka na,bane bakaji har gori ake muna wai mu saidai abamu abamu kullun. Wallahi wanan abin ya dade yana,bata min rai bafa rokon su muke ba kuma,da kudin mahaifin mu ake saye amma,don diyan sune a,kasuwa shine ake wa Maji gori da mu. Bintu da,taga basu da niyar bashi abinci ta mike taje ta hado mashi takawo mashi don dama zaune take gefe tana sauraren su. Ga abincin yana kallo ya tasa a gaban shi amma maganan da maryam tayi ya hana,shi cin abincin. Yasan daga shi har yan kannen shi biyu ba karamin hakkuri sukayi ba agidan nasu. Don sun taso suna ganin kalubali rayuwan iri, irin tun suna yara har yanzu da,suka mallaki hankalin su. Shikan shi ada can baya kafin ya fara dan shaye shaye yana kokarin dan dauke masu wanan nauyi. Amma tunda yafara shaye shaye komai ya,dagule mashi a lokaci guda. Shi kan shi ba zai iya cewa ga dalilin da yasa ya tsiri yin shaye shaye ba,a rayuwan shi. Haka kawai ya,wayii gari yaji yana,da ra,ayin yin haka a,ran shi. Tunanen shi ya katse ne don jin muryan maji da yayi a gaban shi tana cewa may kuma ya faru ka,tasa tuwo a gaba kana tunane, Ko baka iya cin abincin mune yanzu ka koyo cin dankunun mutanen kasar ghana. Murmushi ya dan sake a gefen fuskan shi wanda sai ka kula zaka gane murmushine yayi haka. Maji takara tanbayan shi komay yasa may shi taga yana tunane haka karo na biyu, duk yan uwan dake surutu basu kula da,damuwar da ya shiga ba. Yace wallahi ba komai Maji gajiya ce kawai danayi yasani yin shiru haka. Ya jawo kwanon abincin a gaban shi yafara diba a hankali a cikin plate din dake gaban shi. Kadan yadan tsakula ya ture plate din yana fadin ya koshi da abincin. Maji tace amma sai ina ganin kamar ba gajiya yasa kaki cin abincin ba dai, ai gajiya bai hana cin abinci tunda har naga kayi wanka ko? Ya mike a lokaci daya bayan ya wanke hannu yana cewa bari na,dan fita na,dawo yanzu. Da,sauri maryam tace tau yaya adawo lafiya cikin gidimi. Maji tace dakata ina zaka bakaje ka gaisa da mahaifin ku ba daya dawo duk da yace min kun hadu a massalaci dazun. Yace Maji da nace saida safe kafin yafita naje mu gaisa da shi da kyau nai mashi bayanin komai. Daga inda maryam take tace shine daidai Maji bari ya fita yadawo din kawai da,safe suga juna da,Baba din. Akwai dai abinda kuka,kulla nake gani kukuka,sani koma may ye ai ta juya zuwa cikin dakin ta. Bayan wani dan tsawon lokaci ya,dawo da ledoji irin na super market manya har guda uku a hannin shi. Da murna suka tare shi suna karban ledejin maji dake fitowa daga daki tana fadin Fatima don Allah kada ki gaji kinji dauko min abinci naci nima. Zataci gaba da magana sai ganin abinda ke wakana falon nata tayi, takai idon ta ga ledojin da su Amira ke budewa. Drinks ne snacks, su apple da nama gudan mai yawa na rago da kaza gassashe. Take kamshi ya,gahraye falon nata a lokaci guda sai faman binsu da kallon mamaki takeyi daya bayan daya. Bintu da ta riga tamike take cewa a hankali Mama na debo maki abincin ne? Yace ke bar abincin nan dauko mata plate kawai ki zuba mata wanan taci tasha drinks din. Cikin mamaki maji takai zaunr a saman dayan kujeran ta tana cewa haba Sadauki kai da ya kamata kai tanadi shine zaka biyewa wa yan nan makwadaitan ka,fara almubazaranci da kudi haka. Murmushi kawai yayi azuciyar shi yace mamana bakiga komai ba ma tukun ai. Amma a fili cewa yayi ai maji wanan bai hana ai tanadi don su wa naje wasan badon ku ba aci kawai bai sa ya kare ai. To amma sadauki kana dai jin har an fara min gori yaddackaje fa haka ka dawo wa mutane tsula dakai. Maji kada ki damu da zancen su wanan magana da sukeyi takine a gare mu yanzu. Bintu tana kawo plate din tamikawa Amira dake ta faman bude kayan, inda Amira ta dago kai tama cewa maji may zan yago makine daga ciki? Dakuwa Maji tamika mata tana fadin ungo naki nan ta juya inda Sadauki yake zaune tana fadin kada ka biyewa wayan nan yan kwaden don basu san ciwon kasu ba,su ba abindake ran su sai kwadayi. Kai tanadi ga dan abinda kake samu don gaba nada yawa don kaine muke gani wani gin shikin mu gidan nan. Maji kada kiji komai kuci kawai ai don hakane na,sayo maku din don naga kunci kun sha daga gareni nima. Komai da ya,sayo saida Amirata sawa Maji inda shima sadauki ta zuba mai a cikin dayan plate din. Ta juya inda Bintu take makure tana cewa bisimillah mana zo muci ko,? Maryam data fara kaiwa abaki tace ,a,a bazataci ba kin san ita akwaita da filanci ai. Shigowan yaron Asiya da,aka turo don yafa may suke a dakin saboda dariyan su da akeji, Amma sai ya fake da yazo gayar da yayan sune da dawowa. Maji tace Amira ta diban mashi inda ta yaga mai rabin kaza guda da yan sauran tarkace tabashi yafita. Maryam tace munafuki gulma dama tazo yi ba duk gaisuwa yakawo shi ba fa. Kai ke kan maryam wallahi ki rafe yawan zargi ina laifin shi yadawo yahi dan uwa yadawo yazo ya gaidashi. Kila ba inji Amira maji tace ku dai kuka sani don bakujin magana. Bintu dai na gefe tun da ta dauka saudaya,sai faman taunan shi take ta kasa hadewa duka.

ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,

A LOKACIN MU KE,,,,

Bai yarda ya,fita daga gida sai yai wanka ya gyara jikin shi kamar yadda yaji ana yabon shi da tsabta ko yaushe, Yanzu yana ciniki fiye da farko a baya don ko bai sayar ba mutanen gurin zasu saye na karshe suce zasuyi amfani dashi da dare dashi, don da dare ana wuyan samun pure water. Haka yasa yaron ya kara kwantar da hankalin shi da mutanen gurin da yake zaman don yanzu duk sun saba dashi ko sosai sun kuma yarda dashi yaron nada kirki yana da,wayo, Don duk inda suka aike shi da gudu zai tafi kuma bai bata ranshi. Ya kai yanzu taban da ake aiken shi saye ya canza sallo don dai shi bai san wani irin taba bane shidai a ganin shi ai duk taba tabane. Amma sai dai yasan wanan yafi wanda yake sayo masu don sai anyi warning din shi akan ya boye idan an bashi kuma idan ya sayo kada ya,basu infront of mitune yai hiding din shi. Haka ko yake ko wani irin sako zai bayar in secret zai ba mutum abin shi. Duk hiran da matasan zasuyi a kan idon shi ne cikin kunnen shi yake shiga. Akwai wani wanda idan ya sai ruwan shi ko nawa ne canji zaice ya bashi kawai bai karban canji gurin yaron. Haka yasa Aliyu har Allah Allah yake yafita tallah koda lokacin fitan nashi baiyi ba. Suma gurin da ya tun karo zaka ji suna smally ya iso ke nan yaro kana wanka,fa. Shiko yarinta sai yaji kan shi ya,fashe yana mai jin dadi yana kokarin yin wasa da su don sun saba dashi ko. Nan za,a fara smally sayo min sigari zo ka sayo min abinci tsalaken titi da dai sauran su. Irin haka,watarana yazo sayen sigari sai ga wani abokin mahaifin shi yace ,a,a Aliyu wa ya aiko sayen sigari kuma? Yace wani mutum ne a van tsalaken titi ya aiko ni aka mika mai yatafi, sai mutumin yake fadin kai amma gaskiya haka bai dace ba a aiko karamin yaro sayen irin wanan abin baidace ba da karamin yaro. Mai shagon yace aiko kullun sai yazo ya,saye kashi da kashi ake aiko shi ni nazata ma ko mahaifin shine ke aiko shi saya. Ina mahaifin shi ai bawan Allah ne, ina mutumin nan mai dako a bakin kasuwa mai wuce wa tunda safe yana fitowa kwanan can na malam sale. Mai shago yace nagane shi dan shine ashe yace wallahi dan shine kai wanan mutumin ai ba ruwan shi wallahi. Mut8m ya hadu da mijin maria yake fada mai abinda yagani da idon shi a kan yaron shi. Bai ji dadin zancen ba, nan ya koma gida da fada anyi sa,a ya samu Aliyu a gida nan ya haushi da fada harda dukan shi sai da yayi ranan kuma yai mai fada daga ranan duk wanda ya tareshi ya aikeshi sayen taba yace Baban shi ya hanashi zuwa. Washe gari da,aka ake shi yake fada masu cewa, an fadawa Baban shi yana zuwa sayen taba harda dukan shi akayi kan hakan. Kai mutane dai wallahi muna fukai ne yanzu har mahaifin ka,saida ya,samu wanan dan labarin kamar wani abin sheri can. Nan suka,bada shawaran ya canza shago kawai inda baza,a sani ba yana zuwa.

****** ********* ****** Tun dawowan su ka fara karo da kwalayen da akai amfani dasu a dakin Maji na kayan da aka haka, duk da an kwashe anzubar da saura ga kuma shirgin kayan da aka fitar a inda suka barsu dazun. Yaran su ne suke fada masu cewa yau basu nan an sha aiki a dakin Maji don an gyara mata dakin ta kamar na amarya. Mama Asiya bata yarda ba saida ta shiga hardakin don ganewa idon ta abinda yaran ke fada masu. Tun daga labulen falon tafara shock don bata ma taba ganin su ba da idon ta gidan kowa ba. Kujerin da tai tozali dazune suka saka gaban ta wani irin faduwa, don tasan bana kasar nan bane da ganin su. Juyawa tayi don babu kowa a falon bata tsaya ba sai dakin Umma wadda itama shigowan ta gidan ke nan a lokacin. Yaya waiko kinga abinda idona yau yaganan min may kuma kika gani zaune takai tafara lissafawa Umma abinda tagani da idon ta. Amma sai Umma bata dauki abin da muhinmanci ba ta zaci kawai idon Asiya ya rufe ne har take dada abinda akasa don ina zasu samu kudin irin abinda take fadin tagani a dakin Maijidda. Maji da ta idar da adduoin ta da mika godiyan ta da neman tsari a gurin Allah tafito don yi masu sannu da zuwa. Don kullun suka dawo dama sai tai masu sannu da dawowa bata gajiya duk da gwatsaleta da watarana sukeyi. Har ta juya sai kuma ta tsaya tana cewa yaya baku nan fa abin arziki yau ya samay ni don dan ki ya sayo min kayan daki da kudin da ya samu. Wani dan nawa Umma ta tambaya a gwatsale cikin basar wa maji tai murmushi tace dan ki sadauki mana. Umm,uummm, dakin dai Maijidda tunda gashi uwarshi ya sani inda danane ai da ni zaiwa. Tace idan kin huta sai kije ki gani ki samin albarka a ciki, ta juya ta fita zuaa gaida mama Asiya . Itama ta fada mata yau abin arziki ya samay ta daga dan ta tazo tagani don Allah. Nani kawai tace ba wani adfuan alheri akan wanda yayi din dama ita da tasamu din. Hjy kubura dai dama sai yamma lis take shigowa gidan kullun koda kuwa sun tashi daga gurin aiki ne bata dawowa sai ta gama gantalin ta take shigowa gidan da yaran ta a gala baice da yunwa. Maji tana shiga daki tafara cirewa kowa tsaraban shi kamar yadda suka tsara ita da diyan ta. Matan gidan dai sun samu turamay yan ghana masu kyau da tsada turmi biyu, biyu sai yaran su maza bandir din shadda kowan su koda kuwa yaro karamine, Yan matan kuma dogayen riguna da turamay suma aka basu, masu kyau sosai. Nan gida ya kaure da surutu kowa da abinda yake fadi inda babu wanda yazo godiya cikin su sai yaran ne duk wanda akabawa zai zo yayi godiya da jin dadi masu bakin hali irin na uwayen sune basu shigo ba. Hjy kubura da aka kai mata sakon cikin mamaki tace sadauki fa ya kawo muna wanan haka don harda kwallon da danta yaba da soko saida aka sayo mashi Bata san da zancen gyaran dakin ba saida ta shiga taga ikon Allah dare daya Allah ya kai su gaba haka. Tace may nake gani haka hjy maijidda kice min ci gaba yazo ke nan nan ta shiga sauran dakunan tana kallo tana kada kan ta cikin mamaki don bata taba zaton haka ba. Falo ta dawo tana fadin kai Maijidda kin ko tambayi yaron nan akan kwallo ne ya samu wanan kudin haka? An fa kashe kudi yakai miliyan biyu a nan ma kawai fa tanayi tana kara latsa kujerun don jin kwalitin su. Tace ina dan nawa yake sarki yan kwallo ke nan ace mutum shigan farko ya dawo da haka. Sai bayan ta mike take cewa ja iri yako tafi da dabun da nai mashi na tafiyan kuwa. Maji tace ai yace yaji dadin danbun sosai shi uake ci ma a can yasha ruwa kawai don bai saba da irin abincin su ba sosai ,a lai kan naga alama.ai. Tafita tana tunanen hitan su da yan office din su dazu da safe da suke cewa ashe dan kwallon gidan ku yadawo tace cikin tabe baki yadawa yadda yatafi shiririce mana. Wanan dan iska wani tsiya dama zai tsinanowa mutane a can ban da tambadan daya saba nasan ya tafi yana shaye shayen shi sun koro shi. Sai dayan dake rubutu take cewa ,a,a nifa naji kanina na fadin shine ma yazo na farko don ya samo kudi sosai wallahi. Ba gaskiya bane wallahi yadda yaje haka ya dawo tsiya tsiya dashi wallahi don ina ga baiko maganin sisi ma. Don ya samu wani abu da naji ko gurin Alhaji ne ko inga suna facaka ko ba abinda ya tsinano. Sai daya tace balle ma mashayi kafin fa suyi sai an bincike su agani idan kana shaye shaye basu yarda ka buga kwallo yanzu. Balle ma bai samo komai ba suna dai ganin hakane tunda ya tafi har wani kasa yin wasa. Sai gashi ta dawo gida ta samu zancen abokiyar aikin ta ashe gaskiya ne ke nan boyon kurwa yai masu dama. Maji dai ta rakata da harara tana fadin muguwa aniyar ki tabiki dakin ki munafuka yar sheri, Allah ya shirye ki kawai. Maji tace wa Amira gobe ina son a kwashe tsofin kayan nan akai wa mai masa gidan ta ita ma,ta canza. Nan Bintu tafara murna tana godiya kafin hjy masa tazo tayi mai karfi da bakin ta. Sai da yamma da Alhaji yadawo ya samu wanan labarin gurin mama Asiya da ta fara tsegunta mashi ciki tsigar gulma. Yace masha Allahu kai amma ko naiwa maijidda murna haihuwa ta fara rana ke nan yau Allah ya amsa mata adduan ta . Sai ga maji da nashi tsaraban shaddoji da su turare masu tsada ta zube mashi su a gefen kujeran da yake zaune. Ya kalleta cikin murmushi yana fadin yanzu Asiya take fada min abin arzikin da ya samay ki ashe sadauki ya fara fitar da uwarshi. Maji tai murmushi tace kai haba Alhaji kai kuma da kanka zakai min sheri kuma. Suna cikin magana sai ga hjy Bintu dauke da tsaraban ta dana yaran ta tana ta faman washe baki tana fadin ga abin arzikin da mutanen ghana suka kawo muna. Yace mata nima kinga ga nawa nan yanzu aka kawo min shi ko dubawa ban gama ba. Mama Asiya mai girki tashigo ganin kayan hjy Kubura dana yaran ta yasa take kallo don taga sun fi yawa ga idon ta. Nan take cewa hmm muma fa anbamu har yaran nan gaba dayan mu gidan. Masha Allahu inji Alhajin ya fadi yana mai kai ruwa a bakin shi yace haka ake son samu idan ka samu kowa ma yasan kasamu cikin yan uwan ka. Yana gama cin abinci ya nufi dakin Maji don yaga abinda ake ta faman zuzutawa, Yako gani kuma yai murna da farin ciki sosai sai faman sawa dan shi albarka yakeyi. Bayan fitan su Amira tace ikon Allah yau Baba ne da kan shi kewa yaya sadauki wanan adduan haka. Amma da can an zuga shi a kan shi sai faman cin mutunci da tonon asiri yakewa mutane a tsakar gida. Maji take ce mata wanan ai haka yake duk uwa mai haihuwa sai ta samu bacin ran mahaifi akan dan ta watarana. Don duk abinda yayi mara kyau laifin uwa ne maikyaune na uba ni dai na godewa Allah daya takaita min wanan bakin cikin da wuri. Maryam dake kunna tv take cewa amma ai basu daina kiran shi da sunan mashayi ko? Don ko dazun naji Umma tana fadin wai tsaraban yan shaye shaye suka samu take fadawa yaya Imirana da ya shigo. Ba sai ta dawo dashi ba tunda bata son kayan mashayi da aka bata maganan banza kawai. Maji dai shiru tayi batace masu uffan ba har suka gaji sukai shiru. Da safe ne sadauki yaba mahaifin shi check din kudi yace yana so ya fara noma dashi ko za,a samu anan ma din Bayan Alhaji ya karbi kudin yaga yawan su yake cewa sadauki duk wanan kudin haka akan kwallone kawai ka samay su. Ya dan dukar da kan shi a kasa yace Baba a nan na samay su don ma ban yarda bane da,har wasu club sun so su sayeni amma,nace masu a,a subarni cikin club dina kawai har gaba. Ikon Allah ashe Alhaji Sani gaskiya yake fada min cewa idan nai hakkuri Allah yasa maka hannu watarana sai na dara akan kwallon ka. Murmushi kawai sadauki yayi ba cewa mahaifin nashi komai ba yana fita hjy kubura tana shigowa suka gaisa dashi ya fita. Alhaji ke ce mata kingani ikon Allah kudi sadauki ya kawo min wai na fara noma dashi. Maimakon yaji tayi murna yadda ya zata sai ji yayi tace Alhji adai binciki a gani wanan harkan amma abin yai yawa wallahi. Ya juyo cikin mamaki yana kallonta yake cewa ban gane hausan ki ba fa kubura. Tace ni gani nayi kamar wanan kudin sunyi yawa ace duk a saboda kwallo aka samo su haka gaskiya abincika dai aji. Yace to kina ganin kamar da akwai wata a kasa ke nan ko ya tambaye ta don son jin may zatace. Tace gaskiya kasan halin dan yau fa kada ya yaudare ku da,wasan kwallo ya fada wani harka na tir da Allah waddai. Cikin mamakin jin abinda ta fadi yace assha kubura ban zaci jin wanan magana daga bakin kiba wallahi. Sai lokacin ta tuna tayi barambarama fa don mahaifi mahaifine ai,da sauri ta gyara zancen tana cewa a,a ba wani abu nake nufi ba kasan halin dan yau ne shi yasa na ce a dai bincika kawai ba wani abu ba. Nan dai taita kamay kamay ta tafita shi dai yana jin ta kawai baice mata komai. Kwana biyu sai gashi zance na yawo a gari da unguwa wai ya samu kudi ba,a san inda yasamo ba sai facali yake iyayyen shi suna jin dadi. Wasu suce wai ba kwallo aka dauke shi ba zuwa akayi dasu suka fita da kwaya kasan waje shine aka fake da kwallo kafa. Maji dai da zancen yazo kunnen ta da farko ta so tayar da hankalin ta don sai da ta tsure sadauki a dakin ta take tambayan shi gaskiyan zancen abinda taji. Murmushi shi na rabin fuska kawai yayi mata yace haba Maji idan wani ya fadi an yarda aike bai kamata ki yarda da wanan zancen ba don kin fi kowa sanin halina. Ban son raini da wullakanci shiya sa na roki Allah yai min mafita na dogara da kaina. Nan dai hankalin ta ya kwanta tace koma,waye yai muna wanan sherin mun barshi da Allah shikw nan. Takara ja mashi kunne akan ya futar da ita da yan uwan shi daga kunyan duniya don mutane yanzu ake kiwo ba dabbobi ba. Bata hakkura ba ranan da take da girki ma saida ta samu maigidan su da wanan zancen. Yace au kema ashe zancen yazo kunnen ki amma ya kamata ace kin san halin abinda kika haifa. Ni ban ji ko dar ba akan maganan nasan kawai hassada ne irin ta mutanen yanzu kawai. Amma ai watarana gaskiya zatai halin ta don shi kwallo ba,sanar boye bace duniya tana sanin mutum a lokaci guda. Ki dai yi mashi fada yai tanadi kada yaga kudi suna shigo mashi haka dayawa lokaci guda yace zai bullo da shashanci cikin rayuwan shi. Haka yasa tattara zancen ta watsar tabar masu hassada akan danta suna zuba mashi taki.

Readers Also Read