A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 49
A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 49: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 49. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi…
3,541 words
ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKK8N WASU PLEASE,,,,,,
A LOKACIN MU KE,,,,,,,,,,,
An sallamo mu daga asibiti bayan gwaje gwajen da akayi kan mama an tabbatar da ta samu lafiya yanzu sosai, Sai dai likita ya kara jaddada muna cewa a guje bata mata rayuwanta, wanan kalamin na likita a gaban kowa akayi shi. Duk yaran mama suna kusa haka yaya sadauki yakoso su zuwa gida motat tashi bata daukan mu duka don haka ni da maryam muka hawo Nepep zuwa gida da sauran kayan mu. A kofan gida muna sauka na hango yaya Imirana da wata yarinya yar makwabtar mu ya rike mata hannu yana wasa da ita. Kawar da kaina nayi tankatmr ban ganshi ba amma da yake baida zuciya muna kawowa kusa sai cewa yayi adon gari kun dawo. Yaya mune kuma adon gari yau inji maryam yai dariya yace inbada abinki maryam ai yan mata adon gari ne ko? Wanan yarinyar da Maji zata ban ita aida na more wallahi ta juya tana wa Bintu yace ita fa. Ai babban adon garice wanan tun dai in ta samu guri zakiga ta baje ne kwana biyi lokacin caji ya fara daukan ta. Nace ba adon gari ba adon dawa mara mutunci kawai, maryam tace ke Bintu yayan nawa kike zagi a gabana yanzu zamuyi fada kuwa. Ban tsaya basu amsa ba na kwashi kaya zuwa cikin gida, ban san yana tsaye ba jikin motanshi sai da nazo shigewa na gan shi a tsaye ya sha bakin glass a idon shi. Ni dai na,shige yabini da harara kawai, tun kan nashigo nake jin hayaniyan yan gidan ga kida na tashi dakin Umma. Haka yasani sanin Nafisa tana gida a lokacin don idan tana na zakaji sauti yana tashi a dakin su. Na samu su mama da gwagona zaune a falo nan na zube kayan suna min kun iso nace eh. Nazauna ina cewa wai Allah mun gode ma, jiki dan tafiyan nan kikewa wai inji Amirah. Kafin nai magana cikin muryan mara lafiya mama tace tunda baki san kwana rayen da takeyi akaina ba ai zaki fada mata hakan. Amirah tace cikin make murya maji tare fa muke kwana da Bintu don dai na daina kwana biyu kawai. Kudai kuka sani ace uwar mutum na asibiti amma ku har kunji dadin kwana a gida. Ashe badon Allah ya kawomin wanan yarinyar ba sai dai na karata can ni kadai. Gwagona tace a,a haba hjy ai bazasuyi haka don dai sunga ita din tana masu kara ne kada su raina mata shiyasa. Mai masa bari yaran nan ban san irin su ba kodan sunga su kadaine min suke min wanan halin ban sani ba. Amirah ta tashi tashige daki tai fushi da maganan mama, nice ma na tashi nabi bayan ta har zan shiga gwagona ke cewa dawo mana ki kwashe kayan zuwa ciki kada a barsu nan watse. Maji tace ai kinga abinda nake fadi din waya fara dawowa cikin su ba ita ba amma batai azancin ta kwashe ba. Suna ganin abinda sauran yaran gidan keyi sun zaci alheri ne basu san cewa suma gidan wani zasuba. Idan kaje gidan mutane kace kai baka iya motsa jikinka kai komai sai dai ai maka aiko akwai aiki babba. Da sannu za,a koya masu tunda basu saba da hakan ba tun farko amma ai zasuyi insha Allahu . Allah dai ya kyauta mai masa yaran nan halin su sai su wallahi basu san ciwon kan su ba. Koma irin yadda ake min a gidan su baya damun su dawasu ne ai basai an fada masu abinda zasuyi ba wanda ya dace. Kiyi hakkuri hajiya kowa da ir8n halin shi amma bari zasuyi idan ana lurar dasu. Na samu Amira a daki tana, waya nashigo dakin , tabini da kallo tace yanzu duk kokarin da nake wai maji bata gani. Nace Anty uwa uwace duk abinda suka,fada muna gyara ne a garemu mu godewa Allah da ya barmu dasu a raye. Wanda baida uwa fa a duniya bai kuma damai kwabamashi fa. For god sake may ye banyi a gidan nan ne wai amma kulun maji tace banyi daidai ba. Fadan iyayye fa takine gare mu anty tun da tace haka yanzu da ta dawo gida sai ki matsa ki kula da ita yadda zata ji dadin ki. Kallo na tayi kamar zatai magana sai kuma tai shiru kawai nikan na koma dakin mu na,shiga wanka don duk warin asibiti nake jin ina yi a jikina. Bayan nafito ne na tara duk kayan da mukai amfani dashi asibiti na wanke su tas sannan nadawo falo na zauna sai naga Amirah tafito. Taje gurin mama tace a kawo maki abinci ki dan ci ko da kadan ne maji don rana yayi lokacin shan maganin ki ya kusa. Uwar taji dadin haka sosai don ta kasa boye farincikin ta tace tau akawo min Amirah. Ta hado ta kawo mata har gaban ta tare da ruwa da maganin gaba daya. Maji tace mata na gode Allah yai maku albarka da haka kuke min wa zaiji mu daku. Gwagona tace tau gashi dai uwata ta gyara yanzu ai shiya fadan yake da dadi ga yaro don ya gyara kuskuren shi. Tajuya inda nake tana cewa ke kuma Bintu wallahi ki bar yi wa maji komai daga yau kibarni ni zan mata. Maryam tace wallahi saidai a raba amma ban yarda nima ai ina son albarkan . Nan dai aka wasance zance ana dariya tajuyo tana daga min gira alaman godiya nima hannu na daga mata alaman komai ya wuce.
****** ********* ****** Kabir yazo duban jikin maji da ya shigo kauyen su kamar yadda ya saba duk karshen wata da yake zuwa. Kabir ya iso gidan namu amma bai shiga ciki ba, ya tsaya daga kofan gida inda ya zauna cikin motar shi. Yana saye da kananan kaya amma dinkin shadda ce akai mashi karamin dinki dashi. Sai kamshin turare yakeyi ajikin shi yai matukar kyau dashi sai annuri yake . Waya ya buga min cewa gashi ya iso a kofan gidan da nai mashi kwatance. Na fito acikin hijjab dina duk da nasha kwaliya daga ciki amma na rufe jikina da hijjab. Waya yake amma hankalin shi yana a kaina yana kallon yadda nake takona ina dan waige don ban sheda motar shi ba da yazo da ita. Saida yai min horn nagane cewa shine acan gefe daya zaune cikin motar shi. Ina isowa inda yake ya kashe wayan shi yana min wani kallo can kasan idon shi. Na dan duka kadan ina cewa barka da isowa ya hanya ya mutanen gida suke? Yace duk suna lafiya suna gaida ke amma uwargida tace tana fushi dake wai baki taba kiranta kun gaisa ba. Nayi murmushi gami da cewa karufa min asiri don Allah, yaya ina ni ina kiran ta tace banda kunya. Yace aiko gara ki daina jin komai don Haulatu tace bata dauke ki kishiya ba a matsayin yar uwa da kuka fito shiya daya ta dauke ki. Nai murmushi kawai tare da cewa Allah sarki aiko na gode Allah ya bamu hakkurin zama da junan mu. Ya amsa cikin jin dadi da fadin amin my love, har kin sa naji wani sanyi a,raina da na ga wanan gidan da kike har na fara fargaban kada wani ya kwace min ke anan. Nace haba yayana ai kyau alkawari cikawa da bazanyi ba tun farko baxaka ga ma fuskana ba ai har mukai haka dakai. Yace nako gode da,wanan karamawan da akai mun yanzun hankalina ya kwanta sosai da jin kala man ki. Nan muka dan dauki lokacin muna hira dashi sai dariya yake bani na yadda zamu zauna a gidan shi. Tun daga nesa na hango motar shi tafe da karfi yazo ya park dan nesa kadan damu. Tun karyo kwanan shi ya hango su mamaki yake irin yadda ya hangota tana dariya abinda bai taba ganin tanayi ba a rayuwan ta. Kallon wanda suke tare yake inda yaga maishi ai ba yaro bane ya ma girmi duk yan gidan su balle shi. Amma shine wanan yarinyar ta tsaya haka har take wasan baki a gaban shi koma may wanan zai iya fadawa budurwa har taji dadi haka. Ko dai dama da wanan tsohon take waya tana wani kashe murya a gaban mutane ba kunya saboda wanan tsamuraren mutumin. Wani ir8n haushi da takaicin yarinyar ne da baitaba jin irin shi ba ya kama shi. Ya fito daga motan shi lokacin Kabir ke tambayana waye shi nace mashi yayanane na nan gidan. Don haka yafuto suka gaisa sama sama dashi kamar mai sauri ya shige abinshi tare da gaura marfin motar shi. Kabir ya juyo inda nake yace tau ikon Allah nace rabu dashi haka yake hutsune dama shi baida mutunci. Dakin shi yanufa yana jin wani gumin bacin rai yana fetso mashi ya bude dakin shi ya shige hakana. Mun dan kara dauka lokaci yai min sallama tare da mika sakon shi gurin mamana da bata da lafiya. Nan yake ce min shi abinda yakawo ma yaji kunya don wanan gidan abin yai kadan wallahi. Cikin mamaki nace haba aiba komai wake raina alheri sai mara godiyan Allah kawai. Nan nasamo yara suka shiga dashi nace sukai dakin maman UF don sunfi gane ma hakan. Mukai sallama yatafi sai banji dadin hakan ba don ban so mu rabi dashi ba don jin dadin dan kasancewar mu na dan lokaci a tare. Har na shigo gida yana tsaye a kofan shi kamar may waya take yaji zuciyar shi na azazzalar shi tankat ya shake a lokacin. Can kuma yai tsuki yace ina ma ruwana da yar iska komay zatayi taje tayi mana may ye hadina da itama dahar na damu kaina. Sai zuwa dan wani lokaci ya shigo gidan inda ya samu kayan da Kabir ya kawo muna a falon mama. Ya shigo wani iri dashi idon shi akan kayan duk da kayan ba laifi amma sai yaga ai duk komatsen banza ne kawai. Ya samu guri ya zauna yana fadin wanan kayan kuma fa haka? Amirah tace surukin kane yazo yaya mai neman Bintu shi yazo yakawo wa Maji na dubiya da Allah sawaka. Ance mai mu bamu iya saye ne sai ya kwaso muna wani tarkace haka ba kyau gani. Ko an fada mai mu makwadaita,,,,, Kai don Allah ya isa kai wani irin suruki ne kuma maimakon kasa albarka sai kuma ka fara fadin maganan banza kawai don Allah kwashe min su zuwa ciki kinji maryam. Maryam ta mike tana fadin ai yaya an fara kawo maku tarkace ke nan tun da maji ta tara zuka zukan yan mata haka har uku a dakin ta. Amirah tace wanan kan nima nawa yana tafe sai aka sa dariya kawai gaba daya maji tace Allah kawo shi lafiya mugani ni dai naga ta ya ta saura naku din. Wallahi Maji kina bata yaran nan haka fa na hango wanan yarinyar a,waje da wani tsoho tana wani washe baki kamar taga wani saurayin kwarai gaban ta. Daga inda nake ciki ciki nace kai kaga tsoho nikan bai min tsufa ba wallahi ai aure ba inda baikai mace. Maji tace wallahi ke dai ya ta ai in an kwana biyu zan fadawa babaku don yasani kada yaga kina tsayi dashi kofan gida yazana,min matsala. Cikin hasala yace may kikace banji ba fadi mana naji ya fifito da idon shi waje. Maji tace kai ban fason hauka ko kuma kayo shaye shayen nakane zaka sauke muna hauka anan. Mikewa yayi tare da kutawa yace wallahi maji duk ke kesa yarinyar nan tana rena mutane bata jin tsoron kowa a gidan nan. Na,sa ubana sai kai min fada ko in ba a zo neman su ba kai za,abarwa su kaita kallon su ko yaya. Ya fita yana fada ba maijin abinda yake fadi muka kwashe da dariya kawai Amira na cewa ni wallahi yaya mamaki yake bani Allah. Kamar Bintu za,ace wai bata isa aje saurayi ba yanzu sai yaushe ko ni Allah yaba maiso yanzu ai fiya da haka zanyi mai. To Allah dai ya kawo wa kowa na alheri ke kuma Fatima sai aita hakuri kuma a kama kai don mazan yanzu sai a hankali.
****** ********* ****** Muna zaune da yamma ranan mukaji sallama wasu mata sai da suka fara shiga gur8n su Umma an dauki lokaci sai gasu sun shigo gurin maji sun zo gaida ita. Nan dai suka fara gaisawa suna mata yaya jiki sai mai dan shekaru a cikin su ke cewa wallahi lokacin da kika kwanta asibiti Alhaji baya gari sai jiya ya dawo. Shine yau mukace zamu zo nan gida mu gaidake yaya kika kara ji ya kuma katfin jikin naki ? Maji tace Alhamdullahi na samu sauki ke nan sai matar tace ai halin dan yau inkace zaka sashi a ranka sai ka mutu ga banza su basu damu ba. Tau anyi wani abin ne kuma hjy Saude? Maji ta tambaye ta tace ba ance zancen yaron nan kika sa a ranki har yakai ki ga son kamuwa da ciwon zuciya ba? Inna lillahi haka kuma kukaji to Allah ya sauwaka ni dai na san zazzabi nayi mai karfi . Sai suka kama kallon junan su cikin mamaki sai ga hjy Kubura ta shigo dakin tana cewa a,a hjy saude yanzu nafito wanka yara kece min kun shigo ai. Kunzo gaida hjy ne gata nan tasha allurai ta farfado kin san maleria yanzu baijin magani kadan sai da ya kaita kwance wallahi kin san bana ana sauro da yawa ita kuma sai tace bata shiga net bata son kuma hayakin coil. Matar tace muko yanzu ake ce muna,wai ciwon zuciya ne ya kamata kan zance Faruk . Kai ina kuma kuka samu wanan labarin haka mutum kan abin tsoro ne wallahi zazzabi tayi nima har gurin likitan nake yake min bayani. Allah dai ya sauwa inji dayar matar da batai magana ba tun shigowan su tace ai yanzu da abu ya samay ka magana ya samu ke nan dada . Aishine inji hjy kubura ta fara tafiya sai tace a,a sarakuwa na ashe kuna gida anyi hutu ke nan ko? Matar tace ai suna gida anyi hutu har sun kusa komawa ma. Ince dai kinga dan nawa ko yafitane hjy maijjida tana kallon maji don son bayani maji dai murmushi tai mata kawai bace komai ba. Duk hiran su a kunne mu yake muna can zaune daga bayan su sai lokacin na fahinci budurwan sadauki ne tazo gaidashi. Ni dai bari nasa akirashi ku gaisa tunda kun shigo don nasan kila yana gida naga motar shi dan shigo gida dazun. Uwar yaran tace wai wa Faruk, kai hjy kubura kina dai zance wallahi. Basu jima ba suka mike suna cewa zasu tafi nabi yarinyar da kallo gajera ce sosai baka bata da haske amma tana da kyauta gaskiya. A rai na nace shine har yake kiran wata yar kauye gatashi wata irin cus da ita sai gajirta. Har kofa maji taraka su duk da suna cewa ta barshi yarinyar ta juyo tana cewa su maryam bye bye da dan daga hannu. Suna fita maryam tace kinga mai dogon rigan nan pink ita ce zata auri yaya sadauki tun suna yara aka hadasu diyar kanin baban mune suma ana cikin gari suke da zama suna tudun wada ne su uguwar su baban mune can. Maji ta dawo daga rakiyan su take cewa kai matan gidan nan basu barin halin su. Yanzu don sheri su hjy Saude zasu fadawa wai saboda sadauki ne na kwanta ciwo wai ciwon zuciya don hana ruwa gudu kawai. Amirah tace ba kowa zai fade shi ba sai mama Asiya don itace yar bakin ciki nidai inajin su imani duk ya kashe . Wai haka kishi yake ne kaitawa dan uwanka zagon kasa da hassada a fili haka haba jama,a wanan wani irin sheri ne kuma. Ka zauna gaban surukan mutun harda sarakuwa kuna sukan mutun haka haba dai duniya. Nan kuma muka fara zancen hjy kubura mama tace ni ko ba komai ai hjy kubura tana min ta wani guri. Amirah tace namay maji jifa wai har gurin likita taje tambayan shi da gulma. Daga inda nake nace kaman nasan haka tunda mukaje na roki likita ya boye muna wanan magana. Ke din Bintu nace wallahi anty tace kinji ba aiko da yanzu an yada shi kashi kashi ko. Hayaniya mukaji daga cikin gida bul su maryam suka fita don saurare wai ashe hjy kubura ce tafito tsakar gida tana fadin munafuki dai baiji dadi ba,wallahi. Yanzu don bata zama shine ake wani fadawa mutane arasa ma inda za,ai gulma wai sai gurin sarakan mutum ace wai surikin su ya haddasawa uwarshi ciwon zuciya. Sai ga umma dunkul dunkul tafito tana cewa in ma gulmace mu muka fada masu haka. Karya ne muka fadi ba shine yajawo mata wanan matsalan ba don bakin shaye shayen shi daya sawa kan shi da rana tsaka. To an fadi din ko akwai abinda zakiyi ke ma nan daban ne baki fadi ne maye baki fadi gurin aikin ku akan shi. Ko k8n zaci bamuji ne sai anzi gida don makirci ki nuna ke tasuce, don kilibibi kawai an fadi din may zakuyi. Haba nan sukai tawa kan su tonon asiri har saida Amirah ta kira mahaifin su yazo ya samay su. Ran shi a bace ya samay su da fada yana cewa kun daiji kunya wallahi yau may yarinyar nan hawau ta tare maku a gidan ita da yaranta. Kullun cikin bakin cikin ta kuke da hassada baku gajiyane wai ku, wallahi duk abinda ke gudana a gidan nan nadani ido kawai na samaku don ta Allah bata mutum ba. Ni sadauki dana ne ko wani hali yashiga ban gydun shi don ba,a canzawa tuwo suna. Kuma ku sani babu wace ta wuce kaddara a cikin ku don haka kowa tashiga hankalita. Inba lalacewa ba yaushe za,aji wanan mugun labarin a bakin ku koda kuwa hakan ya zama gaskiya ne ma. Yanzu inma hakane har zaku iya tonawa yar uwarku asiri a hakan may zaku gane gurin tonawa cikin ku asiri. Umma tace ni banga wani abi gaddama ba agurin nan duk garin nan waye bai san abinda yakeyi ba da har za,a tsaya ana tayar da jijiyoyin wuya hakane wai. Yace oho haka kikace tace dama hakan ne don kai baka son gaskiya shine zakazo kana son danne gaskiya. Kafin mu mu fada masu ma ai suma sun sani ba abakin mu suka fara ji ba tunda in yai bakin shaye shayen a can kan titi yake tanbelen shi. Duk wanan rigiman da akeyi akan idon sadaukine wanda ya dawo gida a lokacin don yai shirin fita gurin wasa. Alhaji yace sai kuci gaba da fadi shege ya fasa indai hakane sai kafara fita kayi shela a waje kafin kazo gurin mu. Nan kowa ya watse yabar gurin suna ci gaba da yada bakaken maganganun su a dakunan su. Bai fasa shigowa gidan ba sai dai bakin ciki ya hana shi yin magana duk ran shi a bace yake yai murtuk da fuskan shi. Ya samu guri ya zauna tare da dafe kan shi gwanin ban tausayi, Amira ce matace mai takawo mai abincine yace No kibarshi kawai Amirah. Ya mike yafita daga dakin don baiga fuska ba gurin mahaifiyar su. Batai magana ba sai ajiyan zuciyar datakeyi kawai, ganin zata sa damuwa nake cewa. Inda daji bai gama cin wuta ba aiba ai wa kututure barka don kowa na da "ya"ya ai, balle mutum yaji dadin zagin nawani. Amira tace ai shine ai Allah ba azzalumin kowa bane yana sama yana kallon kowa. Nace ai shine mudai kullun fatan mu Allah yada ya daina kuma ma ai ya daina zancen su daine kawai. Sai lokacin maji tai magana tace anya Fatima kada fa kiyi shedan zur waya fada maki ya daina? Nace mama da,bai daina,ba ai baki ganin shi haka normal kullun nifa munyi magana dashi asibiti. Da sauri suka kallo ni maryam tace ke Bintu kikai magana da yaya sadauki din nace wallahi ko Allah. Tace cabdijam lalai Bintu kin kai wallahi kikace mashi may nace wanan kuma ai siri ne anty maryam. Amma wallahi ku yarda dani insha Allahu yaya ya daina shan wanan abin saidai ban sani ba ko ya daina kwatakwata, ne Amma gaskiya da,wuya kuma dai kan adai gidan nan ko garin nan akaracewa wai yasha wani abin maye. Da sauri maji tace Allah dai yasa Fatima Allah yasa hakan ne wallahi ta fadin cikin ban tausayi, Nace insha Allahu mama don na yarda da maganan shi zai daina ne din ko kuma ma ya daina kawai za,ace ma. Maji tace Fatima ke alheri ce sosai a gare kuma ke wata haske da Allah ya jefo min cikin diyana. Tunda kikace haka wallahi Allah na yarda da zancen ki don na karanci halinki ko Shima dai din da gaske wallahi naga canji sosai a gare shi don banga alaman wanan shadin ba duk kwanakin nan. Maryam kan sai mamakina takeyi tana matsa min wai sai na fada mata yadda mukayi nace ki bari inyadawo ki tambaye shi anty amma ni ba,ajin mutuwan sarki a bakina wallahi.