Kenza eBookz

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 78

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 78

A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 78: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 78. Tun da safe na na shirya komai nawa ina jiran ace nafito ne…

2,987 words

Tun da safe na na shirya komai nawa ina jiran ace nafito ne kawai, a lokacin don ko karyawa ban yi ranan. Ina nan zaune a takure maryam ta shigo dakin tana cewa a,a matar yaya ba dai har kin shirya ba kamar mai gudun mu kuma ? Hararan ta nayi idanuwa na sun dan ciko da hawaye a lokacin cikin murya mai kama da ta shagwaba nace haba dai anty maryam. Nice kuma matan yaya don Allah dai ki bari mana please wallahi kina kara tayar min da hankali Allah. Dariya ta kwashe dashi tace au to yanzu kuma may ya rage maryam ai kin zama matan yaya ko shafawa kawai ya rage insha Allahu. Abinci mama ta aiko min ni da maryam din wai mu karya da taimakon ta na samu har na dan kurba ruwan shayi a cikina. Ina nan ina zaman jira ina saye cikin wasu lace brown color sai duwatsun da akai mai ado dashi don nafi son dinkin riga da zani a rayuwana. Tun lokacin da naji wa,azin mace ta rasu an rasa zani a cikin kayan ta da za,a yafa mata zuwa makabarta nake jin tsoron dinka skirt sosai, ina dinkawa amma ba ko yaushe ba. Mama ta shigo dakin guri na muna zaune saman gado da maryam take ce min Fatima har kin shirya ne? Maryam tace ai tuni da anbi ta nata ma ai da yanzu mai kaita ya dawo ko tundazu. Murmushi mama tayi tace ai yau insha Allahu kuna zuwa ba fashi sai dai ban son ki kwashi kaya da yawa tunda kwana biyu kawai zakiyi a can. Nace cikin yar muryana kala hudu kawai na dauka mama tace yayi kyau haka sai ki hada duk wani abinda kike so anjima su hajiya lami zasu kai sauran kayan ki can gidan ina son naga kafin buki ya kankama na gama da komai naku ko. Mama koran mu ma ake kenan inji maryam tace ai muna tare balle ku da zaku zauna kusan uguwa daya da junan ku ai ba a rabu ba. Da sauri na kalli maryam tace nima haka naji ana fadi wai nesan gidan baikai gida goma ba a tsakani. Tace mama amma dai Bintu idan an dawo sai andawo da ita ta nan kafi a wuce ko? Tace sosai ma kuwa tare da masu zuwa daurin aure fa zasu dawo kuma kinga su nasu can da safe ne goma na safe za,a daura naku kuma sai da rana karfe biyu na rana. Don haka tana nan gida za, a daura naku ai insha Allahu, ko akwai wani magana kuma ? Maryam tace a,a shike nan ai dama ina ce ko shike nan daga yau dai mun rabu ke nan. Kun rabu mana tunda kowa zata kama dakin ta ku barni da wanan mara hankali muyi ta fama da ita. Mama tace bari na fita kinji Fatima na aika akira min sadauki naji yaya zancen tafiyan naku kada ai rana ba,a tafi ba kuma. Yana daki kwance yaji wayan mama ya shigo mashi ya dauka a kasale yana fadin salamu Alaikum. Ta amsa mashi yadda ya dace tace baka shigo ka karya ba mana tin dazun ga wanan yarinyar Fatima kuma zancen tafiyan ta fa may ka shirya akai? Yace maji bazan iya shigowa gidan nan ba yanzu don mata sunyi yawa wallahi, dariya yaba mama tace to ai duk uwayen kane a dakin zallan mu kawai. Yace No maji gaskiya ba zan iya shigowa ba saboda yawa ba zan sake ba anan. Tace ko abada akawo maka dakin ka ne yace shike nan maji hakan yayi. Sai da aka shirya komai na karyawan mama tace nazo na kaiwa sadauki breakfast din shi yana dakin shi. Wani irin faduwan gabane ya kamani amma dai haka na dake na fita da kayan a hannuna. Ina fita na samu Abdul dan wurin mama Asiya zai fita na bashi nace don Allah ya kaiwa yaya sadauki. Yace kai amma dai ke Bintun nan ke da mijin ki kuma kice baki iya kai mashi abin karyawa da kanki. Na dan marairaice nace yi hakkuri yaya Abdul bashi kadai bane a dakin shiyasa nake jin kunya. Yana min sheri ya karbi kayan ya shige mai dashi ina ganin ya shiga na juya cikin gida da sauri na. Abdul na shiga ya samay shi a kwace ya fara gauda shi tare da aje mai kayan abincin yace kai amma dai Bintu shine tace min wai tana jin kunya bakai kadai bane a dakin bazata iya shigowa ba don Allah na taimaka na kawo ma ashe wayo tai min ke nan. Murmushi yayan nashi yayi yace kyale yar kauye bata son shigowa ne tai maka haka . Yace ai zamu hadu da ita ne sai na rama nima har yakai kofa zai fita yajuya yana cewa yauwa yaya UF dama ina son ka bamu kudi zanyi party da kuma ball na mu yan unguwa akan auren ka. Yace kai Abdul party may kuma kawai da ka share da zancen wani party can ni kaga ba wani shirin da naiwa wanan auren. Kai yaya auren da muke son aji labarin shi a gari zakace haka auren ka ne fa na farko yaya muka gaskiya zamu cashe sosai ne wallahi. Sadauki ya mike zaune tare da jawo kulan abinci a gaban shi yace ka bari karfe biyar sai na ganka ba shi ke nan ba. Yana cin abinci yana tunanen rainin wayyo irin nawa common abinci da zan kawo mai wai bazan iya ba sai na bayar akawo mai. Kuma yasan da wani manufa maji tace ni na kawo mai abincin da kaina. Yai tsuki tare da fadi a fili yar kauyen banza kawai wai a haka zan zauna da ita kuma. Kiran wayan maji yayi tace maji yaron da kika ba abinci ya kawo min bai kawo min ruwun sha ba fa. Tace yaro kuma ba Fatima nace ta kawo maka ba yace ni Abdul ne ya kawo min abinci yanzu. Murmushi mama tayi tace kai Fatima wanan kunyane wai ko tsoro har yanzu ? Kaga abinda nake fada maka gashi ka saka tsoron ka a ranta tun yanzu yaushe zata sake dakai kana mata mugun ta haka. Tana gama waya ta nufi dakin mu ina kwance na kifa cikina a saman filo naji tana fadin Fatima yayan ku yace baki kai mai ruwan sha ba fa. Kara faduwan gaba naji na dai ansa a fili da to mama ina mikewa zaune kamar da gaske. Har tajuya tace ki tabbatar kece kika kai mai ruwan da kanki don in akwai maganan da zakuyi kafin ki tafi kan bukin ki sani. Kunya ya kamani na sanin da mama tayi bani ce nakai mai abinci ba kamar yadda ta umurce ni. Dogon hijjab dina na saka tare da daukan ruwa a jug na nufi dakin sai faduwa gabana ke yi a lokacin don nasan cewa zan samo wani sabon bacin rai ke nan kuma again. Dan sallama na tsaya daga kofan dakin inayi cikin yar muryana yagane nice sarai sai yaki karbawa. Na kara dan daga murya da sallaman naji yace please kada ki cika min kunne da wanan muryan naki kamar na munafukai don Allah. Jin haka na sa kai cikin dakin yana kwace rigigin gine daga shi sai dan wando three quarter a jikin shi da yar singileti. Na kai ruwan inda naga kayan abincin farko suke na aje tare da juyawa zan fita daga daki. Naji yace manya kawai watau sai da kika nace sai kin aure ni ko don bakin jaraban ki da nacin tsiya. To ki saurara sai ki shirya zama da U F don baki san koni wane ba da baki yarda da wanan bakin hadin auren ba. Murmushi nayi nace niko nasan ko waye mijina fiye da kowa don ni san akwai aiki ja a gabana na sharan amai da fitsri irin ta mashaya. What ya yunkuro kafin na karasa fita ya cafko hijjab dina ta baya sai naji gaban ya shake ni sosai, na sa kara da dan karfi ya karasa riko min kai tare da rufe min baki yana fadin . Ashe ke yar karamar yar iska ce tukun may zaisa ki gudu tunda kin isa nine mai amai da fitsari ko? Nace baka taba min bane karya nai maka idan ka manta aini ban manta da hakan ba, kaga nafi kowa sanin halinka ke nan. Yanzu abinda yarage min na goge na kwashe idan kuma nayi arziki baka hada min da kashi ba ai na gode Allah. Wani irin shaka da karfin shi yakai min sai da idanuwana suka fifito waje kwala kwala kaman zan somay. Yana fadin zaki ci uban ki kuwa inkince ke yar iska ce don zaki dan dani wahalan ki a gidan. Yace good haka ma nake so gara ki shiga shegiya na gasa maki kwakwa ga hannun ki, kagin na wullakantaki na mayar dake karamar bazawara gidan nan. Nace shine dama sauki na in har kai min haka da sauri ka ceci rayuwana don, zaman kaddara dama kawai zanyi da kai. Yakai wa kaina bugu da karfi sai da na gwauro da bango idona ya kawo hawaye nace dama duk matar mashayi wanan ne sakamakon ta ai duka da zagi da cin zarafi banyi mamakin haka ba don na shiryi taron irin wanan ddaga gare ka tun tuni. Akan mama zan iya hakkuri da duk wani cin zarafin da zakai min matsawon hakan zai mata dadi a ran ta. Don nasan darajan mama nasan kimar mata a rayuwana kuma ban manta da irin halarcin da tai min ba a baya. Don haka kaga tunda wanan ne kadai hayan da take ganin zan iya saka mata da alherin da tai, min ashirye nake da na rugumi duk wani kaddaran da zan tunkara a gidan ka. Fita min daga daki yar kauyen banza kawai mara tarbiya wace bata san komai ba sai rashin kunya. Nace nagode na gyara hijjab dina na fito daga dakin, idona taff da hawaye, sai da na saita kaina na shiga cikin gida. Dakin mu na koma na kwatan ina tunanen makomar wanan auren da ake shirin kullawa a tsakanin mu a haka. Ni dake fanin da safe zamu tafi sai gamu sai sha biyu da rabi na rana muka bar sokoto zuwa kauyen mu. Tare da rakiyan yan uwan mama da suka zo daga Niger state gurin buki sai kawaye na muyi yan layin mune kuma school din mu daya dasu tun secondary school muke tare dasu. Mun samu gidan mu ya cika makil da yan uwa da abokan arziki, da suka zo gurin buki nai matukar mamaki yadda na samu an gyara gidan mu a lokaci guda haka. Dakin da zamu zauna an saka katifa maya guda biyu a cikin shi, nan muka sauka bakin da muka zo dasu basu dade ba suka koma don akwai event din da za,ayi na matar Ahmad gidan su suna son zuwa. Sai bayan mun hutane nake jin wai mamana tana gari ta zo amma tana gidan su. Da yamma aka sakani lalai kamar yadda al,ada yake a garin mu nan aka shiga shagalin buki, sai abinci ake ta faman tukawa na farar shinkafa. Muma munzo da kayan cima da abokaina zasuyi amfani dashi a garin don haka ba sha wani wahala ba sosai. Sai da safe naje gaida mahaifina yake ce min Fatima Bintu kinzo kin samu alherin da mutanen arzikin nan sukai muna a gida nan ko? Alhaji ya aiko daga can birni an gyara muna guri don baki masu zuwa daurin aure sai kuma jiya gashi da safe kafin ku iso anzo da abinci da katifo wai daga marikiyar taki ta aiko dashi. Nace an gode Baba ya ce tau Fatima sai dai ban tsanmanin zamu kara samun lokaci irin haka dake ba. Abinda nake son ki sani shine shi zaman aure dan hakkuri ne don yanzu so ya kare a tsakanin ku sai hakkuri. Yi nayi bari na bari inji manya sai a zauna lafiya, kin dai san ance mijinki mutum mutane ne gashi kuma dan gidan yawa. Don haka ki zauna da kowa da halin ki duk da nasan ki amma ki kara da hakkuri Fatima, shi hakkuri baya karewa fa musulmi. Duk da a hasashe na ina fanin kaman wanan aure aure ne na hadin iyayye a tsakanin ku dashi halinki shiya ha har suka kwaidaitu da son zaman ki da dan su. Don haka ki kara wani saman wanda suka sanki dashi sai kiga akarshe ke ce da riban hakkuri. Take naji idona ya ciko da hawaye har na kasa control din su sai da suka zubo min nan dai baba yaita min nasiha akan hakkuri da zamantakewan aure da kuma sabon rayuwan da zan shiga ciki. Mukai sallama dashi yana ta saka min albarka tare da fatan samun zuria dayyaba. Yinin ranan haka nayi shi a kwace babu walwala tare da ni ga mutane sai masha,an da sukeyi kawai. Da dare gwagona mai masa tazo tace nazo mu tafi gidan su mahaifiya na don ko can akwai yan uwa da suka zo buki. Mun shiga gidan mutane sai jin dadin gani sukeyi suna ga amarya tazo gaida ku. Nan muka shiga gaisawa da mutanen da na dade banga wasu ba sai ranan. Sai wani lokaci na samu kebewa da mahaifiyana a wani daki dagani sai ita muka zauna a dakin. Tace tau yarinyar ga gashi dai Allah yayi zaki aure yanzu don Allah idan kin je kiyi hakkuri da sabon rayuwan da zaki tsunta a sabon gidan ki. Ance zo mu zauna zo mu saba ne sai dai mu mata da hakkuri aka san mu dan namu yafi na maza don mune a kasa garesu. Kina dai ganin irin rayuwan da nake ciki ba sai na fada maki ba kin san hakkuri nake dashi don da ban hakkuri da tuni nabar gidan nan na,watsar da yaran nan. Amma sai naga idan na fita na barsu dawa kuma zasu zauna har ya basu tarbiyan da nake son su samu saboda kinga shi wanan ba irin naki mahaifin bane. Ina jin haka sai wani irin kuka mai karfi yazo min don tausayin mama na dani kaina. Da kyat ta dan lalashe ni na sasauta cikin kuka nace mama ina ganin kusan rayuwa guda Allah ya jefo muna na aure. Don kinga shima din mashayi ne ne kaman baban su musa sai dai dan banbancin su kadan ne don akwai wayewa a cikin nashi. Mama bana son shi na tsane shi natsane shi a rayuwa na amma sai gashi magaifiyan shi ta nemi alfarma a guri na akan na rufa mata asiri na aure shi. Mama may zanyi da mutumin da bayaji tsoron sabawa Allah bai dauki sabawa Allah a bakin komai ba. Mama don mahaifiyan sadauki zanyi wanan auren don ba zan iya mussa mata fa bukatan taba a gare ni. Mama ta katse ni tace amma kin bani kunya wallahi yarinyar ga ina iliminki da tarbiyan ki ya shiga da har kike ganin ba zaki iya taimakawa hajiya ba yau. Tace da kikaga hjy ta zaboki a cikin dubu ta bukaci ki auri dan ta kina zaton don kyau kine ko arzikin ki ko wani abu can. Tayi hakane don tana hasashe watakila tagare ki zata samu nasaran raba dan ta da waban halaiyar tashi. Bafa don bata sonki ne tace ki auri dan ta ba suna da kudin da zasu aura mao duk macen da yake so a duniyan nan. Amma kikaga ta nace akan sai dai ke din take so ki zauna dashi, nasan kuma tai hakane don tana ganin ke ce kila zaki iya kawo karshen wahalan nashi. Shi fa hanyan sabon Allah shiga rai ke gare shi sosai, daga lokacin da akace wanan abin baida kyau haramun ne, sai kiji zuciyar mutum na tura shi aikata shi a ko wani lokaci. Shiyasa akace an zagaye wuta da abin sha,awa wanda zuciya ke so, an kuma zagaye aljanna da abubuwan ki wanda zuciya bata so. Don hakane duk wanda ya kama hanyar aljanna zai ta haduwa da abubuwan da zuciya bata so, haka kuma shi wanda ya kama hanyan wuta zai hadu da abubuwan da zuciya ke so. Shiyasa akace daga cikin hakkurin da ake son mutum yayi shine harda biyayya ga Allah da manzon sa dama magabatan mutum da kuma hakkurin gujewa sabon Allah. Hana zuciya aika ta sabon da ya ginu a kanta farat daya abu ne mai wahala so sai sai mai hakkuri. Idan kana da hakkuri zaka iya jure jawo hankalin mai yawan sabon Allah sannu a hankali ta yawan nasiha da lurar da mutum illar abinda take aikatawa. Uwa uba kuma addu,a da nasiha ga mutum har Allah ya bada sa,a ya bari ko ya rage. Yin fushi da mutum ko kaurace mashi baya hana mutum sabawa Allah sai dai ma ya kara kangarewa kawai. Amma jan mutum zuwa jikin ka shike sa mutum ya rage watarana har ya tuba ya daina gaba daya. Don haka ita hajiya taga cewa, kece kadai zaki iya taimaka mata gurin wanan yakin. Don haka yaki babba a gaban ki yar ba don hajiya ta dora maki nauyi mai girman dauka gare ki. Fushi zagi gori da kawar da kai ga abinda yake aikatawa yanzu ba naki bane yar baba. Don haka wani kawar da kan ki gare shi ko ki kyamace shi ba naki bane yanzu. Don idan kinyi haka tankar kin kara tura shi ga halaiyar da yakeyi ne na kyamata da uwarshi bata son ganin shi a ciki. Hajiya ta wuce ki watsar mata da bukatan ta gare ki, sai dai ki kara runguma kawai da hannu bibiyu. Zata ci gaba da magana gwagona ta leko tana cewa fito mana Bintu, dare fa ta soma kin san ba wuta garin. Haka yasa nai sallama da mahaifiya na tana ta jero min addua irin da yadace duk uwa taiwa yar ta da zata dakin auren ta.

Readers Also Read