A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 86
A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 86: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 86. Tun ranan da wanan abin ya shiga a tsakanin mu na kasa sakin…
3,133 words
Tun ranan da wanan abin ya shiga a tsakanin mu na kasa sakin jikina a gidan. Ban yarda mu hadu da yaya sadauki ko da a falo ne ganin na dan samu sauki yau natshi tunda safe ina son shiga school kasancewa monday ce yau din. Tsaye nake a bakin zinc na kitchen ina dauraye kayan da akai amfani dashi daren jiya. Ga kuma girkin dana dora ina sauri ingamawa kada na makara ko ya futo yasamay ni ban fita ba. Jin kaman mutum tsaye a bayana yasani sauri juyowa ina kallon kofa shigowa kitchen din, . Gaba nane yai mugun faduwa da ganin shi yana tsaye ya saka hannayen shi biyu ya raba kofan tsakiya jikin saye da kayan exercise din shi sunyi matukar yi mashi kyau a jikin shi. Dan daburcewa nayi daganin shi bansan lokacin da nakai kasa ba a tsorace ina cewa ina kwana yaya. Bai amsa ba,sai karasa shigowa daga cikin kitchen din da yayi gaba daya ina durkushe. Tsayawa yayi tare da jingina jikin shi da bayan inda nake tsaye da farko yace wa kike boyewa kwana biyu a gidan nan. Mikewa nayi don ganin bazai amsa min ga tambayan da ya jefo min kuma lokaci guda. Fuskewa nayi nace may zan boyewa kuma ni don banda lafiya ne kawai. Murmushi yayi yace may yasamay ki baki da lafiya kuma? Turo baki nayi na karasa dauraye plate din dake a hannuna, na juya ji nayi ya finciko ni tabaya na. Tsoro ne ta kamani jikina ya dauki rawa a lokaci guda don balain tsoron shi nake ji yanzu . Idanuwa na a runtse tare da sauraren abin da zai biyo bayan rikon da yai min a lokacin. Hannuwan shi naji saukan su a saman kirjina tare da rankofo kan shi a daidai wuyana a hankali. Yana fadin abinda kike min rowan su ke nan gasu yau na kama su a hannuna. Idona na ritse gam don jin abinda yaya ke min wanda ban taba ma kawo tunen hakan ba a tsakanin mu. Cikin wata yar murya nace da kyat don darajan Allah yaya kadai na wanan abin please ? Don Allah ka bari kada musa ya shigo ya samay mu a haka please. Murmushi yayi yace idan yashigo and so what bada matata ya ganin ba. Kara rintse idanuwa na nayi cikin rashin fahintar abinda yake min a lokaci zafi ne ko haushi ko ko dadi. Da karfi na zille daga jikin shi na koma gefe ina mai da numfashi kaina a duke. Murmushin keta yai min yana cewa matsoraciya kawai yau ina bakin naki yashiga kuma mai fadar bakat magana. Idona da yakawo hawaye na dago kai nace don wanan cin zalin da ka dauko yi min a gidan nan bashi zai sabakina ya mutu ba ai mugu kawai mai ruwa biyu. Murmushi yayi ganin da nayi ya juyo kamar zai yo kaina na zille akasa tare da kare fuskana da hanaye na sai naji yai dariya yace ashe bake bace ? Har ya kao kofa ya juyo ya tsaya yace, kuma idan na kara shigo na samu kin boye zakiga abinda zan maki gidan nan. Yana fita na sauke ajiyan zuciya tare da mikewa na karasa abinda nakeyi ina yi ina kwallon kofa kada ya dawo again. Sauri sauri nagama komai tare da shiryawa zuwa school don lokacin har dining sai dana hada komai na fito a cikin hijjab dina kamar kullun. Naso nafita batare da na,sallamay shi ba sai naga rashin dacewan hakan gareni don haka na nufi dakin nashi. A hankali na tura kofan daki da yar sallama a bakina, yana kwance saman gadon shi yai rigingine fuskan shi na kallon ruffing din dakin nashi. Daga kofa na tsaya ina fadin zan tafi school, sai na dawo. Da kyat ya iya dago kanshi idanuwan shi kamar yafara barci ne a hakan. Kallo na yayi tun daga samana har kasa na sai ya mayar da kan shi yana fadin akwai mai a motan, nan kuwa nace ranan da na fita last akwai mai a cikin sa sai dai ban sanar ma yau din nan ba. Mikewa naga yayi ba tare da yai min magana ba yafita a dakin nima bayan shi nabi muka fita a tare dashi . Motan ya bude ya shiga ya tayar da ita ya dan dade a cikin ta yana service din motan ina tsaye daga gefe ina kallon shi. Yafito daga cikin motan bayan ya gama warming dinta tare da ce min sai kin dawo ya juya ya shige gida. Mun hadu maryam a school duk yadda taso ta zolaye ni taji yadda muka kwasa da yaya sam naki bada fuskan yin haka. Dole ta gaji ta kyale ni muka canza hira kan hiran matar yaya Ahmad da akace sunyi fada har da buge buge har gurin yan sanda sukaje. Amma kuma sun dawo anshirya kamar basuyi ba nace ai dama irin su irin matan nan yan duniya ne daidai dasu. Tace ita kuma matar yaya Imirana ance kazama ce kumai tana dan kurba syrup akai akai, Sai dana gama saurare nace wai ubangiji Allah ya kyauta kawai zamuce ga al,amarin don yanzu abubuwa daban daban lokacin nan da muke cikin ta. Ba mu dawo gida ba sai yamma lis after six na shigo gidan agajiye dani daki na shiga na cire hijjab dina na fito kitchen don dora girkin dare. Misa ne yashigo yana ce min sannu da dawowa yace yanzun ko yaya ya bargidan nan yana tambayan baki dawo ba. Nace may zan mashi idan na dawo din sallon son yaiwa mutum muguntan shi dayasaba kawai. Kai haba anty yayane kuma mugu ni dai wallahi yana bani shawa wallahi don ba ruwan shi rayuwan shi akwai sauki sosai. Murmushi nayi a fili a zuciyata nace baka san komai ba yaro da baka fadi hakan ba. A gurguje na hada girki na koma dakin shi dake a hargitse na gyara mashi tare da wanko bayi na feshe ko ina da kamshi nafito nazo na samu shikafan dana dora ya tsane na tuka tare da kwashewa. Kafin a gama kiran magariba na gama hada komai na shige dakina wanka nayi tare da dauro alwala nafito. Ban daga ba sai da nai sallah ishai na fito tare da kara feshe falon mu da kamshi kafin ya shigo gidan. Na koma na zauna tare gyara jikina wani riga da wando na saka daga cikin kayan lefe suke English wear ne na gyara gashina da ribon jelae shi ya sako a baya. Dan karamin gyale na yafa ga kaina na fito falo na samu musa ya shigo nace mai ya dibi abinci yaci dare ya soma yi. Ya dabe ya dawo inda muke zaune ya faracin abincin muna hiran mu ta zumunci labarin rayuwan garin sokoto da ya gani yake bani ina dariya. Haka yasa bamuji shigowan shi ba sai ganin shi mukayi har ya kawo tsakar falon. Sannu da dawowa muka fara mashi ya amsa tare da zubewa saman kujera da alaman daga gurin wasan su na ball ya fito a lokacin. Sai ya kasance shigan da nayi na takura da zama falon dan wani kallon da naga yai min ya wani lumshe idanuwan shi. Can ya bude bakin shi da kyat yace musa ina gani gobe zaka wuce school don an gama maka shirin komai ko. Daga ni har musa dago kai mukayi muna kallon shi a cikin kasala yake maganan shi yace. Ban san ko akwai wani abinda zaka bukata ba kaje cikin buth din motana ka kwaso abinda akasoyo ma ka gani idan akwai abinda zaku kara sai ku duba ku gani. Mikewa musa yayi yafita yabar abincin don dauki sai lokacin na dago kai na kalle shi ya rike goshin shi da hannun shi daya nace yaya mungode Allah ya saka da ,,,,,, Hannu ya daga min yace is ok please nima ai kanina ne musa. Kara cewa angode bai yi magana ba sai mikewan da yayi ya bar falon tunawa nayi ban hada mai ruwan wanka ba a lokaci da sauri na mike nabi bayan shi. Na samay shi a tsaye yana kokarin cire kayan jikin shi sallama nayi na shigo ya bini da kallo kawai. Bathroom na shige tare da joner mashi heater ruwan zafin da zai yi wanka dashi. Nafito bayan na matsa mai su maclean da subulun da zai bukata na aje mai a gefe nafito din. Nazo zan wuce yana daure da towel iya kugun shi da sauri zan wuce naji ya finciko ni zuwa jikin shi. Yar kara nayi nace cikin wata irin murya wayyo yaya please kayi hakkuri don Allah matse ni yayi gam yana kokarin hada bakin shi da nawa. Sai kokarin zillewa nake don gaba daya balain tsoron shi yanzu ya cika min zuciya na don bangane wannan son yawan hada jikin shi da yake son yi dani ba akoda yaushe. Sosai ya tsayar dani sai tsotson bakina yake cikin wani irin sallo da shi yasan irin shi. Kafafuwa na ne naji basu dauka na a lokacin gashi ya cika min baki da harshen shi ban iya maganan komai a lokacin jikina sai kyarma yake min. Shi kan shi yaga dama ya sake ni tare da bina da shu,umin dariya yace zamu hadu dake ai matsoraciya kawai. Sai dana sai ta kaina a tsaye inda nake tare da bin bayan shi da zai shige bathroom. Lokacin ne na kara sheda girman jikin yaya sadauki sosai ashe karfafan mutum ne haka ban sani ba. Na samu musa a falon ya kwaso kaya gasu nan birjit a gaban shi. Jakkuna na kaya guda biyu na hango sai na karasa gurin yace anty kinga abinda yaya ya sayo min haka. Nan muka shigo budewa daga kaya sawa takalma uniform sai kayan abinci na gwagwani da na sha su madara da sauran abubuwan sha. Kallon kayan nake cikin mamaki don ba karamin kudi ne aka kashe ba gurin sayayyan wanan kayan masu yawa haka su bucket da kulan da zai ci abinci duk an sayo mashi man shafi su maclean da sabulun wanki dana wanka da turare. Musa yace kai yaya I love you wallahi ban ma san irin godiyan da zan mashi ba idan yafito wallahi. Murmushi nayi kawai naji dadi kwarai a raina don nuna kaunan da yayi wa dan kanina haka. Can yafito cikin wasu yan kananan kaya a jikin shi rigan mai dan karamin hannu iya hammata sai wando three quater da yasa fari kal dashi sai kamshi ke tashi a jikin shi. Direct dining erea ya nufa hakan yasa na mike na nufi gurin tare da daukan flask na fara zuba mai tuwon shikafa fara da miyan water leaf yaji agushi sosai da nama. Dan kadan na tsakurawa kaina a plate a shiririce nake ci inda ya zauna ya kwashi abincin shi sosai. Sau biyu yake cin abinci a wuni da safe idan ya karya sai kuma da dare wani lokaci kuma fruits salad kawai zai sha yakan ce wai ina son dirka mai abinci yaci yai kiba kwana biyu ya kasa yin wasan shi. Waya yake yi yana kallon yadda nake wasa da abincin dake gabana duk da rashin yawan da baida shi. Da ido yai min magana alaman maza na cinye shi na make kafada na alaman banyi, sai dai ban daina cin da nakeyi ba a yangance. Mikewa nayi tsam na fara kwasan kayan zuwa kitchen ban fito ba sai da na tsaya na wanke kayan don na rage yawan aikina da safe. Na dawo nasamay shi da musa yana gwada mai wasu takardu a hannun shi ashe takardan addmition ne na makaran tan da zai tafi. Zama nayi a gefe daya ina satan kallon su duk da hankalina yana gurin tv dake aiki a lokacin. Musa ya tatara kayan shi ya kwasa cikin jin dadi zuwa dakin shi tare da muna sai da safe nasan zai tafi yyakara baje kayan ne yasake kallon su a tsanake. Shiru falon yayi ba wanda ke magana a cikin mu sai tv dake aiki shi kadai ana ta watsa turanci ganin ankirashi a wayan hankalin shi ya dauke yasa ni mikewa nabar falon. Bathroom na shiga da niyan nakewa sai naga kawai nai wanka na ji dadin kwanciya kawai nafito na dan shafa mai laushi tare da saka yar rigar barci na dana feshe da turare, light pink mai dagwari biyu sai dai iya cinya ya tsaya min rigar. Ina zaune saman gado naji ya turo kofan daki sai dai ya sauya kayan jikin shi saye yake da wani wando mai laushi iya gwaiwan shi kamar three quarter da rigan shi mai kama da dinkin banga na maza. Sau daya na daga kai na na kalle shi na dukar da kai kasa inda nake zaune a dan stoll din mirror yazo ya zauna tare tare da kura min ido. Muryan shi naji yana fadin tashi muje mu kwanta tunda ke baki san abinda ya dace mace taiwa mijin ta ba sai an fada maki. Na dan bata fuska tare da turo bakina nace ni anan zan kwanta murmushi naji yayi tare da riko min hannuwa na ya mikar dani tsaye. Look at me yace, sai na dan dago kaina kadan na kalle shi amma ban iya jure kallon shi ido da ido dole na dukar da kan nawa, kasa. Yace daga yau ban son sai na kara biyu ki a dakin ki don ko zo guri na ke baki san right din ki ba ne a gare ni. To bari kiji bazan biya kudin sadaki na ya tafi a banza ba ni ina gabas kina yanma kudi nabiya dole kuma a bani hakkina. Jin abinda yace yasa ni watso mashi harara au harara na ma ki keyi ko ba biya nayi ba ne ? Cak ya daukeni kamar ya dauki babyn roba sai dakin shi ya dire ni saman gadon shi yana cewa this where you support to belong every night. Rankwafo wa yayi tare da raba hannaye shi yasani tsakiyan shi kokari yake sai mun hada ido dashi amma na kasa lumshe idanuwa na nayi. Yayin da naji yafara canza min sallon wasan shi a hankali yafara bin sassan jikina da wani irin romacig. Tun ina iya daurewa har na fara dan nishi, kadan kadan cikin neman agaji sosai yake gwada min wani irin mahaukacin kauna wanda ni kaina ban iya cewa ga inda nake a lokacin. Mun dauki tsawon lokaci dashi sai da ya gaji dan kan shi ya sarara min tare da rugumay ni a jikin shi yana sauke numfashi a hankali. Al,amarin yau da dan sauki bisa ga daren farkon mu dashi don banyi mugun jikita irin na wancan ranan ba. Gaba dayan mu shiru mukayi kowa da abinda yake sakawa a zuciyar shi a lokacin. Ni dai tunane nakeyi anya kuwa zan iya da yaya sadauki ashe mutum haka bai da tausayin mace ko kadan. Ko dai dama haka yake ne wai yana mu,amula da wasu matan ne acan baya. Da sauri nai istigifari don ance zato zunubi ne koda ya zama gaskiya don haka nai saurin janye wanan tunanen a raina. Shiko tunane yakeyi wai dama ashe abinda Bashar ke ta fihintar dashi ke nan akan mace. Tabas yanzu ya yarda da zancen bashar da yake cewa dan hakin daka raina shike tsone ma ido ashe ni,ima da baiwane tattare da wannan yar kara mar yarinyar da ya raina a idon shi. Bai tsan mani a rayuwa zaa samu mace haka mai tarin ni,ima da baiwa ba irin na Fatima ba yarinyar da bai taba samun wani jindadin rayuwa ba irin wanda yake tsinta yanzu a jikin Fatima ba. A hankali ya kai hannun shi saman kaina naji yana shafa a hankali ban san lokacin da na saukw wani irin ajiyan zuciya ba mai karfi. Ji nayi yakira sunana a hankali yana fadin FATIMA na amsa a hankali da fadin naam . Sai naji ya rugumay kamar wani zai kwace mashi ni a lokacin yace. Don Allah ina son kiyi hakkuri da halina kizama mai dauriya acikin duk wani al,amari na zaman takewan mu nidake. Idan har kin min haka kin gama min komai bazan taba son na samu matsala ba daidai da rana daya da mahaifiya na koke don rayuwa a yanzu akwai akasi a cikin shi kala da kala. Shiru nayi ina sauraren shi, yayin da idanuwana suka ciko da hawaye wanda ba zan iya fadin ga dalilin zubowan su ba a gare ni. Kukane ya kubuce min jin yadda nake kuka yasa shi kara manna jikin shi sosai da nawa shi bai lalashe ni ba kuma bai iya furta komai ba . A haka barci ya daukeni ban san manayi barci ba sai dai dana falko nagani a saman chest din shi kwance nayi filo dashi. Gyara kwanciya na nayi dakyau abinda yasa shi dan motsawa ke nan ya kara jawoni zuwa jikin shi. Da safe da kyat na mike na nufi dakina can na gasa,jikina sosai da,ruwa masu zafi haka yasa na dan samu saukin ciwon jikin da nake ji dana tashi. Nai matukar mamaki kwarai da naga yaya yana sallah jam,i bai wuce shi duk asubahi sai naji fitan daga gidan zuwa masallacin uguwan sallah. Ya dawo daga motsa jiki ya samay ni tsaye ina hada table din cin abinci a cikin kunyan abinda ya faru a tsakanin mu daren jiya yasani dukar da idanuwa nakd gaishe shi da kwana. Ya kara so tare da dan rike ni daga bayan na yana cewa, ke baki gaji bane har kika tashi ki aiki haka mai yawa? Kunyan shi nake ji ban yi magana ba sai dan murmusawan da nayi nace yanzu zakaci abinci ne? Ba abinci nake son ci ba ke dai nake so yanzu ya bani amsa fuskan shi a daure tamau kamar ba wani magana yayi ba a lokacin. Da sauri na kalli agogon ban gon dake falon sai na ji ya furzi iska yace zan makarar dake ke nan kike nufi ko? Ya juya ya fara tafiya yana ffadin ok a dawo lafiya sai dai kafin ki dawo zan kai musa school din su sai kuyi sallama dashi. Daga haka ya shige dakin shi ya barni gur8n tsaye koda na shirya nashiga yi mashi sallama na samu ya shiga wanka a lokacin. Don haka na cire mai kaya daga cikin wardrobe din shi haka zai sa yagane na shigo dakin na juya nafita da sauri don na kusa makara ranan. Bayan yafito kayan da ya samu na fitar ma saman gado don yasa yasa shi gane cewa na shigo dakin a lokacin sai daya gama shirin shi yafitone musa ke fada mashi nace na tafi don na makara yau. Yana gamawa dama musa duk ya kagu su wuce don haka,basu bata lokaci ba suka fita zuwa school din da za,a kai shi na kwana.