Kenza eBookz

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 90

A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 90

A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 90: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 90. ****** ********* ****** Bayan Nafisa ta tashi yana falon zaune…

4,614 words

****** ********* ****** Bayan Nafisa ta tashi yana falon zaune ganin shi yasata mikewa zaune yace har kin gama barcin ke nan tace tana mikewa zaune wallahi fa yaya. Yace haba Nafisa ya kamata ace yanzu kin wa kanki fada fa gaskiya baki kyauta wa iyayen mu musan man ma Umma da take mace tana zama dake a gida ko yaushe. Shiru tayi tare da dukar da kan ta kasa yace lokaci yayi nafisa da zaki bar wanan harkan haka duk da nasan abune mai wuyan bari amma don Allah kiyi kokari ki dan rage wasu daga cikin halaiyar ki don Allah dai ba don niba Nafisa. Abin mamaki sai gata kawai tana hawaye tace wallahi yaya nima kaina ban san may ke kaini sha ba ko naso na bari sai naji kwata kwata bazan iya ba. Lokacin nafito falon ganin suna magana yasa na juya zan koma ciki sai yace No dawo ki zauna aikema maganan ya shafe ki tunda ya shafe ta. Tace wallahi yaya ni ina ganin Alhakin kune da maji ne ya sauka aikaina dakin mu don irin mugun abinda Umma da mama suke shuka maku kullun tun ina karama nakejin irin tugun da suke kullawa akan maji da ku. Dariya yayi yace kai haba Nafisa ai shi zama kishi ina ganin haka yake sai ta share hawayen tace yaya bazaka gane bane wallahi. Amma nasan ko nayi rantsuwa ban kaffara don su Umma ne suka sa kayin shaye shaye a baya. Na fadawa umma su bari kada Allah yajerabesu watara tundai ina suna zagin ka da mashayi dan maye mukan mata magana ni da yaya sagir amma umma bataji. Munafukan ga mama bata bari umma tabar aikin ta yaya yaya kake ganin zan iya dainawa idan su basu daina sheri ba. Tace umma tana sakaci da yawa tana yarda da mama asiya batan cewa muguwa bace ta karshe har yanzu bawai sun dai jifan ku bane fa. Allah daine ke kare ku kawai amma kai kan ka da,wuya in ka daina sha yanzun haka? Da sauri na dago kai ina kallon shi sai naga yai murmushi kawai yace Nafisa koma maynene ki sa a ranki cewa zaki daina sai kikaga kin daina din. Ki samu miji kiyi aure koma may nene kike so ni nai maki alkawari zan sai maki duk lokacin da kika tashi aure. Kai ta kifa tafara wani irin kuka take nima bansan lokacin da na fashe da kuka ba shima dai ina ganin kukan yakeyi a lokacin yadda na ga ya dukar da kan shi kasa. Can ya mike ya shige dakin shi ya bar munan muna kuka tai matukar bani tausayi namike zuwa inda take na dafata. Duk da nima kukan nakeyi amma sai na dafata ina bata hakkuri kawai sosai nake mata nasiha har nagama batace min kalla ba nace tazo tashiga tai wanka ko zataji dadin jikin ta. Ta kalle ni da mamaki tace Bintu ke baki kyamanane yadda sauran yan gidan mu ke yi min yanzu nace kyama kuma anty akan may zan kyamace ki kina da cutane ko may. Tace har fa ciwon aids mama Asiya da yaya Ahmad ke fadin ina dashi yanzun haka kallon mai cutar aids wasu mutane ke min. Nikuma wallahi komai mayena ban bari mutum ya shige ni baida roba a jikin shi. Ban san lokacin da na runtse idona ba danaji abinda tace min ba kunya take fada min tana amfani da maza haka. Dakina nakaita tai wanka na bata wani dogon riga na mai kyau tasaka muka dawo falo nan muka samu yaya yace tazo ya sauke ta gida don can zai tafi yanzu. Tare sukafita da ita tana min godiya nace haba anty aiyiwa kaine tausayin ta yai matukar kamani sosai. A hanya ma sosai yaya yaita mata nasiha ya na kwantar mata da hankali na ta natsu ta daina wanan harka baida amfani don babban illa da cikas yake kawowa mutum a rayuwan shi. Sai yamma ya dawo yake ce min tafiyan shi yana nan yace ko bazan iya zama ni kadai bane yaiwa Inna magana maman su Bashar a turo min daya daga cikin yan matan ta nace a,a zan iya zama mana yaya. Ai yanzun na saba da gidan ban jin tsoron komai kuma kamar baya yai min sallama bayan ya shirya ya wuce Abuja .

ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,

IDAN KUMA KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA NA BARKI GA ALLAH YAR UWA,,,,

Zama muke na zaman kwari tsakanina da Amira don iyanzu takai ni inda bani son mukai tun farko da ita. Ina zaune a dakina naui zugun ina tunanen irin wanan halin takuran da Amira take kawo min har a cikin gidana. Sai hakkuri nake tayi ina hadiyewa don ban son mahaifiyar su su sami labarin halin da muke aciki. Amma ranan da maryam tazo gurina ta fahinci akwai matsala a zaman mu da Amira. Gaba maryam ta sakani sa tambaya iri nata har dai na warware mata duk irin zaman da mukeyi da kawayen ta da take kwaso wa su zo su dinga min abu isa isa a tsakar gidana. Rayuwan maryam yai matukar baci tamike tana fadin wallahi sai tayiwa Amira magana Amma na sha gaban ta na bata hakkuri tare da fadin idan Allah ya yarda ni da kaina zan dauki mataki a kan ta. A kwana atashi ba wuya a gurin Allah sai ga shi yai har wata daya da kwana goma sha da tafiyan yaya sadauki. Munan da Anty Amira muna ta kwamawa a cikin gidan don gaba daya yanzu na fitar da tsoron ta ko shakka da kawaicin ta da na ke ji da farko . Karatuna nake don yanzu exam mukeyi hutu zamu fara next week banda wani lokaci sosai na kaina a gida gaba daya.

Tsaye yake idanuwan shi suna a lumshe dan murmushi ne ya sake don tuno da yanayin Fatima, da murmushin ta da take a boye tsiwanta da fushin ta da takeyi a lokaci daya , Sai dai kuma duk karancin shwkarun Fatima hangen nesa ta da kyakyawan zuciyan ta da manufan ta akan kowa haka halitta ne a gare ta. Yana gyara tsayuwan shi yake cewa Fatima ke ba diyan masu hali ba amma kuma kina da,diyauci irin na masu halarci. Su iso Lagos da yamma don ta nan jirgin su ya sauka Nigeria a gurin su basu dauki tafiya a bakin komai ba don haka ya tsaya yai clearing din kayan shi da ya shigo dasu. A lokacin mun kammala exam na dawo gida satin nan ba fita duk wani motsi na da,wani taku na yana kan idon Amira da ta saka min ido a agidan. A kullun tunanenta shine yadda zata kawo was Fatima cikas din rayuwa ta hanata jin da dadin rayuwa a gidan Sadauki. Don ita Amira a watau ta sune yan uwanshi na jikin shi sune ya kamata suci arzikin shi fiye da,wata mace can da tashigo da sunan zaman auren sai su mamaye komai na miji ya zama na au suda yan uwan su kawai. Shiko miji da dangin shi sai yadda akayi dasu kawai a gidan sun zama yan bi ke nan a dinga juya su yadda rai yaso, Hakan ke matukar bankan ta mata rai ita bata kaunan ace dan uwanta sai wata ta bata doka akan shi Amira na cikin irin jinsin mutanen dake adawa da matan yan uwan su maza a duniya. So take sai yadda tayi da shi da matar shi sai dai ta dinga bada commad ana bi kawai shine zaman lafiyan kowa da ita don bakin ran ta da yai yawa. Takan ce dan uwa dai dan uwan tane babu mai raba shi da ita don a tare aka gan su don haka sai dai mace ta kare kutin gwilar ta tabar da dan uwan ta saboda babu wanda zai kawo wani shamaki a tsakanin su. Haka mukai ta zama da ita a cikin fitina da gori habaici bakar magan cika baki sai dai wanda ba bu shi don duk nagani ga Amira lokaci guda. Gashi kuma yadda take samun, gashin kanta yanzu a gidan namu tayi kiba tai fari ta kara dan girma da ita.

****** ********* ****** Suna zaune falo da kawayen tabar gazan ta wai su wayayyu su salma kubura da Fauziya sai jin motsin turo kofan shigowa falon gidan sukaji. Idanuwan su na kan kofan don suga mai shigowa falon a lokacin don yanzu sha daya saura na safe muke ciki. Cikin mamaki Amira tace yayana dama yau zaka dawo ashe bai amsa mata ba sai bin falon yake da kallo cikin mamaki bayan ya gama kallon fuskoki wa yanda ke zaune a falon lokacin. Daya bayan daya yake kallon su har ya kai karshe Fatima bata falon. Hakan yasa shi wuce wa direct dakina yagani don sai yaji zuciyar shi tana mashi wani irin kuna a lokaci guda. Yana bude kofan zaune nake na sallamay sallah walha, ina dan jan tasbaha bayana yana jingine da fadon dakin Jin an turo min kofa yasani saurin dago kai ina kallon kofan dakin wanda nagani a tsaye ya harde hannayen shi guri guda yana min murmushi yasani saurin dan sakin murmushi tare da yunkurawa in tashi. Na nufoshi a a cikin fara,a ina cewa sannu da zuwa yaya yaya hanya ya can ? Murmushi yayi tare da,ware hannayen shi na sheko da dan gudu na na shige ciki ya mayar da hannayen shi ya rufe ni dasu . Sai da muka dan dauki lokaci a haka muna shan dumin junan namu ne yake cewa cikin wata irin shakkakiyar murya su waye nagani a falo kuma a ina suka fito hakane da au kuma ? Nai dan murmushi tare da dan dago kaina daga jikin shi nace ban san da ga ina suke ma amma kullun dasu muke wuni a gidan nan sai dai na girka na basu idan kuma sun gama na kwashe na gyara gida idan da duk ya baci. Yace a bisa ga umurnin wa hakan ke faruwa min a gida ban sani ba nace umurnin second command ne Anty Amira don haka sai ka tambaye ta bayanin komai. Ina rike a hannun shi yaja hannuna zuwa falon muna shiga suna ganin mu suka sauri dawo da hankalin su a gare mu irin yadda suka gan mu a tafe ne ya kara daure masu kan su. Zama mukayi a saman kujera daya nidashi ya dago fuskan shi dake a daure yana fadin wa yan nan kuma fa daga ina suke ne haka ? Shiru babu wanda ya amsa ya dago kan ahi yana kallon inda nake yake yana cewa nace su wayen haka kuma don ban san su ba. Nace ka tambayi anty Amira don tare na gan su dasu kuma ta fada min sunfini daraja a gidan nan kaga ni dole sai dai na bisu don yan uwankane na ji aiko. Sai dana fadi haka ya dago kai ya kalli inda Amira take zaune wani irin haushin ta ne da kiyayyan ta ya darsu a zuciyar shi a lokaci guda. Yace su waye haka kika tara min a gidana sai cewa tayi yaya sadauki salma ce fa diyar gidan baba prof da take mutuwan son ka wace nasha fada maka zancen ta tana karatu a london yanzu itama tagama ne ta dawo gida. Wani mugun kallo ne ya watso mata yace kina da hankali kuwa Amira look kwashe min wanan mugun tarkacen da kika tara min a gida don yanzu na gama sanin inda kika dosa. Salma da ta zage akan ta aamu shiga tunda ta samu kaunar shi nason ta sai yadda tayi dasu. Dalilin ma da aka kitsa ke nan su dinga zuwa gidan don ta san halina da kuma yadda zata saba da gidan kafin ta shigo. Haba UF inji salma data mike tsaye tace kaima kasan da ina son ka shi yasa kaga har nazo gidan ka kawai . Amma daba, son ka nakeyi mai zai kawo ni wanan nan gidan nazo na zauna har wanan yar matsiyatan daka aje tace zata kawo muna raini kawai. Don mun sauki cups din amfanin ka ta kama muna haushi ai badon Amira da ta dauki mataki a kanta ba da na so na gwada mata koni wacece. Wani irin kallon mamaki kawai yake masu take idanuwan shi suka rikide zuwa ja kamar gauta a lokaci daya. Yace cikin wani irin murya please get out in my house before i take a desition on you. No no UF kada kace zakai min haka please already mun riga mun gama maganan nan da kai ko. Tazo har inda mukw a tsaye tana cewa tare da nuna ni da hannun ta wa an yar kauyen matar taka bata dace dakai ba don tafi dace wa da masu gadin ka kawai. Fauuuu muka ji kara mari tace ido rufe maza su kwashe subar mai gida mara sa kunya fitsararu ko mata sun kare a duniya mai zaiyi da ita mace da taje london ta gama watse wanta zai dauko ya kawo wa kanshi fitina a gida . Tas yai masu suka fice simi simi da kunya wai su tantire sai gashi su hadu da wanda ya fisu iya fitsara yai masu tas gaban matar shi. Wanan karon tare da tsaraban ahi ya shigo gari don koda su salma zasu wuce wata hilux data kwaso mai kaya daga airport tana sauke kayan a kofan gidan mu. Ana shigo da kayan ciki yai tsaye yace Amira tafito ta wuce zuwa gida sai ya zo zai nemai ta a gida. Aiko Amira ta ce yaya may kake nufi korana zakayi don munafukar matar ka tai muna hadi a gurin ka hau kazauna akai. Babu inda zan tafi sai ka bude kayan nan a gabana kowa ya gani haka wancan karon nazo nai zaman banza komai baka ba.u ba yadda ka saba ta kwashe takai kauye inda,ba,a san darajan su ba ma. Amira waiko anya kanki daya kuwa, ina dai gani kanki ba guda bane kawai don hakan da kikeyi abin naki ya zarce sanina gaskiya. To bazan bude ba kuma maza ki kwaso kayan ki tun ban bata maki rai ba a gidan nan. Idan Fatima ta kwashe abina nakine ta kwasa ko nawa ina ruwan ki da kayana Amira Fatima matatace ko kina da abinda zakiyi kan zaman ta matata. Yaya ta furta tana mashi kallin mamaki tace kan Bintu kake fada min haka yaya Bintu fa Bintu dai. Yace Idan na kara jin kin kira Fatima da Bintun nan da kuke kiranta dashi don rainin wayo wallahi sai kinyi mamakina Amira fito kawai ki tafi gida zan zo zamu hadu agidan ai. Haka yai mata kora na kaskanci kan abinda tai min wanda tun yana can Bashar ya fada mashi komai duk irin halin da muke ciki da Amira a gidan, da bayana ranshi yai matukar baci shine ya zo muna a bazata batare da ya fadawa kowa zuwan shi ba. Wanka ya shiga don ya rage gajiyan jikin shi ina kitchen ina hada mashi abinda zaici na juya zuwa dakin na shi inda na samu ya fito daga wanka na yana saka kaya a jikin shi. Jin motsin shigowa yasa shi dan juyowa yana kallo na tare da sake murshi a fuskan shi. Yace batare da ya dago kan shi gare ni ba mai yasa kika boye min halin da kuke ciki a gidan nan da Amira. May yasa tun wancan zaman baki fada min ga irin rayuwan da kukayi da ita a gidan nan ba. May yasa ki ka bari Amira ta tara yan iska suna wullakanta min ke ne haka a cikin gidana. Ya dan dago kai kamar a fusace yake magana yace may yasa zaki boye min irin wana mugun halin da Amira taita gwada maki. Nace yaya Anty fa yar uwatace komai tai min kanta taima bawai, ni kadai tai wa ba don wata rana zai bata mata rai yadda tai min din. Nace yaya duk abinda Anty ke min a saboda kaine don taga ban cancanci na aure ka ba saboda matsayina bailai na hakan ba. Sau dayawa nakan rasa laifin may nai wa anty Amira take min haka yanzu , sai da ta fada min akan gangancin da nayi na auren ka yasa take min wanan halin. Hawaye ya gangaro min a fuskana nace yaya sadauki nasan nayi gangancin auren da matsayina baikai gare shi ba. Haka kuma wanan ba shine irin rayuwan da ya dace dani bayar tallakawa kamata bata dace da irin ku diyan masu kudi da matsayi ba a duniya. Ya sadauki kaima kanka kasani bankai matsayin da za,ace ka aure ni ba kasani ba irina ce ta dace dakai ba a gidan nan kamar yadda anty Amira ke fada min nima yanzu nasan gaskiya take fadi don ban kai matsayin hakan ba a gare ku. Yaya kayi yadda yan uwanka da masoyan ka ke son ganin ka tare da,diyan attajirai irin ku masu matsayi a duniya bani yar takawan kauye ba Fatima. Ba so tsakanina da kai sai zumunci na wa yanda suka tashi a daki daya irin na yan uwantaka kawai. Kamata yayi ace na auri maigadin gidan ku ko wani dan aikin gidan ku wanda baida matsayi irina. Sai faman kallona yakeyi kamar talabijin da mamaki ya lura ina a cikin damuwa da kuncin rayuwa mai yawa don bai taba ganina acikin irin wanan yanayin ba haka. Sai na fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciya a lokaci guda na durkushe a bakin gadon shi ina rusa kuka. Cikin kuka nace Allah kadai da mama suka san dalilin wanan hadin da sukai muna. Amma da zaka daure ka auri wacce tafi dacewa da zama a matsayin matar ka hakan zai matukar saka anty Amira farinciki a rayuwan ta. Hankalin shi yai matular tashi a lokaci guda yace tabbas Allah ba zai yafe min ba Fatima tunda nine yakamata na daukakaki a idanuwan mutanen duniya tun farko Fatima amma na kasa yin hakan. Matsalar duk nawane da na kasa fitowa fili na nuna cewa ina matukar son matata batare da duniya na mata kallon wacce aka tilsata min da ita ba. Dole ne komai yacanza daga gareni yadda kowa zai iya fahintar Fatima ta wuce yadda suke tsanmani a gurina. Ahankali ya tako zuwa inda nake a tsugun ne ina kuka shima ji yake kamar ya fashe da kuka a lokacin. Ya dago ni tare da kokarin mikar dani tsaye ya rigumay ni zuwa jikin shi muka zauna saman baki gadon shi a hakan. Yace Fatima ki kwantar da hankalin ki ki saurare ni dagani har ke zan iya ce hada mu akayi amma kuma ba bisa kuskure ba. Maji ta fahinci kiyayyan mu ba kiyayya bace illa kainace mai wani sabon launi ta hango abinda mu bazamu ita hango aa kan mu bane a lokacin. Fatima komai nawa ya canza a rayuwana adan zaman nan da mukayi dake tunane yanayi da komai nawa yanzu ya canza min a dan lokaci guda. Don haka ki fitar da zance su Amirah da wanan salman a ranki ,kimai da al,amarinki ga ubangiji don shi yafi mu sanin me ke boye yafi kowa sanin abinda bamu sani ba gaba dayan mu. Sannan ina son ki saka a ranki daga yau ni Umar faruq sanda ina sonki Fatima, ina kuma kaunar ki fiye da tsanmanin ki Fatima ke alheri ce babba a gare don ko nina tabbatar da hakan da kaina. Ina maki so na hakkika Fatima wanda ban taba tsanmani akwai wata mace bayan uwata da zanyi wa wanan irin son ba a duniyan nan. Ni Umar Faruq nai alkawari har ga Allah zan rike amnan da mahaifana danaki suka bani akanki zan . Zan taimakawa rayuwan ki naga kinyi abinda kikayi niyaryi, zan taimaka maki tako wace hanya inga burin ki yacika akomai. Ki sani yaya sadaukin ki nai maki alkawari Fatima muddin muna a raye insha Allahu zan maki komai don wanan Umar din zuciyar shi da gangan jikin shi wanan kirjin da kike son kwanci akan sa duk nakine ke kadai Fatima zarah,. A kullun zaki kwanta akansa kuma zan share maki hawayen ki harta inda baki zata ba Fatima. Fatima muddin ina a raye duk abin kike so shi zan maki don haka ki share hawayenki Umar nakine ba wani wanda zai shiga rayuwanki ni da ke , sannu a hankali muddin ni mijin kine kina a matsayin matata zakiga gurinki suna cika daya bayan daya. Yana dan buga min baya yake fadin Sadauki nakine zan maki duk maganin matsalolin ki don zan share maki hawayen ki. A hankali na dago kaina na kara shigewa cikin jikin shi ina fadin cikin kuka nagode yaya sadauki Allah yabar min kai a rayuwana yabamu hakkurin zama da junan mu. Yace Amin Fatima nima nagode Fatima da kika fahince ni a cikin sauki tashi muje ki bani abinci naci yunwa nake ji banci komai ba tun jiya dasafe don kawai nazo naci girki yar matata naji dadi. Murmushi nayi tare da mikewa ina gaba yana bina a baya mukaje falon sai da ya zauna na zuba mai abincin ya fara ci. Mikewa nayi na fara gyaran falon da suka bata kaca kaca wanda a kullun sai nayi gyaran shi fiye da sau uku suna batawa. Yana cin abinci yana kallona a fakaice yana tinanen ashe zancen da bashar ke fada mai Fatman shi ta koma kamar boya a gidan kan abinda Amira ke fada mai. Bayan na saka kamshi ko ina yafito neat ya mike ya dawo saman kujera yana waya. Daki na shiga na kara wanka na gyara jikina tas nafito falon ina kamshi inda yake zaune na nufa da hannu yai min nuni da nazo saman kujeran da yake a kai na zauna. A hankali yakai hannun shi saman jikina yana waya yana wasa da part din jikina a hankali. Yana gama wayan yake cewa idan kin huta zuwa dare ki bude kayan nan da nazo da su, naki ne sunfi yawa daga ciki sauran zaki iya zabawa maryam da Amira sai kuma wanda kika so aba. Nace mai mama fa yace atamfar Holland ce sunan nan zaki gan su kema ki zaba tunda naga kina son su sosai amma ki min dinki da zai fitar min da suran ki a fili. Nace kai haba yaya abinda ake fadakar da mutane ba,a son anayin su yanzu yace ba ani zaki sawa ba ko wani ne zakiyiwa kwalliya bani ba. Nace an gama yaya indon wannan ne kawai mikewa nayi na shiga fitar da kayan ina matukar yaba yadda ya iya zaben kaya haka kamar mace. Gaba daya gidan su sai dana fitar wa kowa da nashi kaso har yaran mummy da suke kanana sai da suka samu tsaraba haka yasani fahintar tafiyan da yayi akwai sa,a sosai a cikin shi ke nan don haka yakeyi duk yai tafiyan da yayo nasara zamu sha tsaraba masu tsada muma a gidan. Ranan kan naji jiki a gurin yaya sai dai daurewan danayi kawai don iyan zu na fara sabawa da halin shi ko. Da safe bayan mun karya ne yafita zuwa kai tsaraba gida bayan na rubutawa kowa suna a nashi yadda zai gane. Ranan kowa ya fahinci na fara jan ragamar aure na a gidan sadauki don ganin kayan kowa da sunan shi a jiki. Dakin su Umma cewa mama Asiya tayi waiko kin gane cewa wanan yarinyar itace ta zabawa kowa kayan nan don ga suna kowa a jikin su . Rukaiyya ta tare su da cewa amma kuma mama ai atamfan duk suna da matukar kyau wallahi don ni sun bani shawa,awa sosai wallahi. Ke rufa wa mutane baki ke may kika sani ba sai tazabi na iyayyen ta yafi kyau ba ta bamu matasa kyau. Kai haba mama wallahi haka baida kyau fa ina laifin Fatima gida su yaya ko tsuki sun taba kawo maku ne yakamata ku daina irin wanan halin wallahi inji yaya Sagir. To sannu uban mu inji Umma yan uwan naka zakaiwa gori kuma don bakin kwadayi. Mashayi dai ne ba wata tsiya ba can don har yanzu ba fasawa yayi ba ai tana cikin fadin haka sukaji hayaniya daga tsakar gida. Nafisa ce tayo mugun sha take ta watsar da duk abinda tagani a waje da sauri suka fito hardasu mama dake dakin su cikin tashin hankali. Ga kayan jikin ta yai futu futu sai ashar take zubawa tana fafin nagane duk munafukaine gidan nan don babu wanda ke sona. Sai kuma tasa wani ihu kamar wata yar daji da taje farauta tace yau zan ci kazar uban duk wanda ke gidan nan munafukan banza xa wofi kawai. Kuke nan kullun ku shige daki kuna kulla yadda zaku kashe UF ko wooo UF ko yafi karfin ku wallahi sai UF up up UF buga muje yayana ikon Allah . Umma tafito rai a bace ta nufe ta tana fafin Nafisa abin naki kuma ya koma haukane ko may . Tace Umma ni kika ceqa ma haukaciya yau ko zan gwada mamu ni ma ma mahaukaciyace a gidan nan saiko ta dauko tabaryan dake yashe a tsakar gida tayo kan Umma gadan gadan dashi. Ganin da gaske zata rotsawa umma ne yasa umma juyawa da gudu saiko ta fadi kasa ku caaa gap da ta rotsa mata Sagir dake daki yafito jin yadda kowa ke ihu yayo kanta yakai mata shuri sai da ta fadi kasa takife bakinta ya fashe. Kara dagowa tayi tana fafin wallahi yau sai na kashe ka gidan nan ni zaka daka haka ? Nan ya samay ta yai ta jibga saida aka tare shi ganin haka yaran mummy suka sa ihu maji ta jasu zuwa dakin ta taboye su a ciki. Yaran duk sun tsorace Umma tayi tayi ta tashi abu yaki kafa ya rike mata ashe tayi targade ne ba,a sani ba. Ganin haka yaran ta suka saka ihu suna kuka neman taimako ga uwar su. Mama Asiya ta bugawa Maigidansu waya yazo gida ba lafiya suna tare da sadauki dayaje gurin shi kasuwa. Tare suka iso gidan cikin rudewa gashi an taru akan umma sai hawaye take tanaji kamar zata mutu. Mummy ma dawowan ta ke nan ta samu wanan tashin hankalin daukan mama akayi dakyat zuwa asibiti sadauki da sagir da mama. Yaran mummy suka fito dakin a tsorace suna ganin uwar su sukayo kanta suna kuka. Ta rugumay su tana fafin yau kuma wanan iftila,in ne yazo muna agida haka kai Allah ya kyauta kawai. Nafisa na cikin dakin uwarta sai ashar take ta zubawa da tonon asiri wa uwar ta. Alhaji yana tsayevsai zufabke karyo mashi na tashin hankali mama da mummy suka nufe shi suna cewa yashiga ciki ya zauna kada kuma yajawa kan shi matsala. Sai wani lokaci aka dawo da Umma duk ta jirkita ga uban bandejin da aka lailaiye mata kafa dashi. Baba najin muryan su sun dawo yafito da sauri yace Atika kada ki shiga min gida dauki mahaukaciyar yar ki kubar min gidana. Cikin yashin hankali aka shiga bashi hakkuri amma ina ya hau baji alokacin da kyat sadauki dasu mama suka samu ya koma dakin shi. Umma tace tana kuka ai dama nasan shetine wallahi sai Allah ya isar muna duk wanda keda hannu cikin lalata min rayuwan yata. Kai kaji kuma wani wauta wa zai tsa yiwa Nafisa wani sihiri kuma ga abin kwarai ba ai masu ba sai wanan barkatatan taki. Haba hjy kubura a dai bar zancen ai Allah ba azzalumin kowa bane duk mai wa wani sheri ai zai girbi abinshi tun anan duniya don Allah bai barin bashi yanzu.

Readers Also Read