A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 97
A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 97: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 97. ****** ********* ****** Mun sauka a China inda na kara tsinkewa…
2,818 words
****** ********* ****** Mun sauka a China inda na kara tsinkewa yaya ke nan irin abokan da nagan shi da su can har sun so sufi na saudiya ma don ko a can naga yadda yake hurda da yaran masu kudin kasan ga kyautan dana samu har tsoro abin ya bani. Mun tafi wani katafaren hotel mai shigen tsawo da kyawo sosai kauyanci kan wallahi nayi shi sosai na lumshe idanuwa na daga inda muke zaune a bayan mota nace Alhamdullahi Ala Kulli Halin. Yace jawoni yace may kikace Fatima nace godiya nake mikawa ga uban gijina da ya nufe ni da hakan . Tsayawa bada labarin hotel din zai bata muna lokaci amma gaskiya nasha kallo Allah ya horewa mijin kowa yakaita kashen duniya tai kallon abin mamaki a can. Munga karamawan ta ban girma a gurin abokan shi na can nikan sai faman godiya nake ga Allah da ya daukaka min rayuwana haka. Ina rungumay a jikin shi muka bar gurin haraban hotel din zuwa masaukin mu a tare muka zube agado dashi. Na lumshe idanuwa na tare da ajiyan zuciya yace yaya akayi ne Fatiman yaya ? Nace ni may ma zance yaya dariya naji yayi yace kice kina son U F dinki sosai Fatima . Ki dinga gyara min kanki ina kallo ko yaushe gadona yazama ready ba sai na nema ba abani idan kin min haka kin gama min komai Fatima a rayuwana. Murmushi nayi nace ai baka da matsalar haka din ko yanzu yaya . Yace umm haka din ne amma ba sosai yadda nake so a raina na ba jinayi ya shiga zuge min zif din rigar dake jikina a hankali tare da fada min wasu kalamai da bazan iya fadin su ba anan. Nace ko wanka ba zamuyi ba yau kuma yace wanda mukayi kafin mu fita may mukaci dashi kada fa ki manta honey moon dina nake yanzu. Rugumashi nayi nace ai kayi abinka tin a gidan ka na sokoto sai dai ka dora inda ka tsaya kawai. Yace hakan za,ayi ranan kan nafitar da duk wani kunyan shi a idanuwana na nuna mashi nifa ba yar kauyen da yake kirana da ita bace. Rayuwa sosai na jin dadi mukayi da yaya a kasan China satin mu biyu a can ya sanya hannun jari a kamfanin yin karafuna da yake son yi a sokoto. Mun dan kara kwanaki muka wuce har Hong Kong nasha mamaki sosai yadda yaya yasan kasashen duniya haka da mutane kuma cikin yan shekarun kwallon shi. Daga karshe muka dira a Dubai a lokacin banda matsalan komai a raina ban da na tuhumar ko yaya yabai daina sha ba har yanzun . Don wanan irin mutanen da naga yana hurda dasu haka dole ne idan mutum.baikai zuciyar shi nesa ba ya yi aikin sabawa Allah. Amma sai naga shi akan ibada baida wasa ko kada ko wani kasa yana da time din sallah su ko baya gida zai bugo min waya yace lokacin sallah yayi na tashi nai sallah. A kasan Dubai kan kamar a gida Nigeria muke don yan Nigeria dake kasan maza da mata gasu nan manya da yara kana gani. Nan naga matan manyan kasan mu yadda suke hurda da matasa ko ina zai tafi tare muke zuwa yana nuna masu ni a matsayin matar shi. Mutane da yawa suna cewa basu taba tsanmanin yai aure ba ma a rayuwan shi don basu ji ba ana fadin zancen auren shi akasa ba. Akwai wata hjy wai shi take so ranan da ta ganmu mun fito gurin wani shakatawa sai da ta girgiza da ganin mu. Nagane hakan a fuskanta tun da muka hadu gasu su uku hamshakai sai wani shakiyancin duniya sukeyi wai su karuwai. Bayan mun rabu dasu ne naso na tambaye shi ko su waye su amma sai kawai na basar da zancen su. Shi da kan shi naji taja tsaki yace rabu da mahaukaciya wai a haka sona takeyi bata san ni ba irin shashan matasan nan bane masu kwadayin tsofin mata ba. Ni yanzu ko budurwa bata gabana balle wata tsuhuwar kwama can na banza. Har Lindan shi sai da muka hadu da ita a Dubai wai tazo tare da mahaufin ta wani business nace tir da kafurci ta sa ni dan skirt dan mitsitsi iya cinyar ta kawai duk komai nata a fili. Ita kanta Linda ranan da ta ganni sai da ta girgiza sosai don yadda taga nai mata kyau ga dress din jikina ya karbe ni nan tasan dole ne U F ya manta da wata Linda can. Tasan lalai yanzu Fatima ta sace zuciyar U F din ta don babu ta inda za a kwata mu da ita gashi kuma addinin mu daya dashi gamu yan uwa kishi ya rufe ta taji kawai tasakawa ranta hakkuri ga tunanen zai dawo gare ta wata rana. Daga ita har mahaifinta da muka hadu wanda yasab soyayyan su da yaya sai da suka bimu da wani irin kallo . Mahaifin Linda yake tambayan wanan ce matar shi daya aura din linda tace ita ce dadd. Yace so young pretty how are you tare da mika min hannun shi na girgiza kaina nace mashi dai yana lafiya tare da tambayan family din shi. Yaji dadi yai murmushi yace sorry na manta addinin ku ya hana hakan nan ya shiga muna murnan aure ya dafa yaya yana cewa kinga shi nan ki rike mijin ki da kyau don mijin ki big man ne sosai yana cikin lokacin shi. Dariya mukayi a tare har dan dimple dina ya dan lutsa kadan . Linda taja tsuki tace ai dole ne UF ya rikice dadd a kan wanan karamar yarinyar ji yadda ya mayar da ita kamar wata queen can . Ta juya tabar gurin ya ce don't mind her she is jealous of you taga kin fita komai baby ki rike mijin ki kinji yarinya. Nai mashi godiya ya bani kyautan wasu irin mahaukatan kudi kamar bau san zafin su ba. A mota hanyan mu na dawowa ne na ciro kudin ina bawa yaya yace na may ye fa nakine fa kece akabawa don haka kibar abinki gurin ki. Tsaraba kan nasha shi gurin yaya don bai bari na kashe koda kwandala ba daga cikin kyautan da nake samu. Mun baro kasan mun dawo gida Nigeria don hutuna da ya kare ba don yaya yaso yakare din ba don bai gama morewa ba can. Sai da mukai kwana uku a Abuja san nan muka ahugo jirgi zuwa sokoto birnin shehu cikin jin dadi da walwala muka iso gidan mu. Nai mamaki kwarai yadda muka samu yan uwa sun cika muna gida gurin taron mu. Anty maryam na ganina lokacin cikin ta ya tsufa sosai ya kara girma tazama wata mama da ita. Muka rugumay juna muna murna daganawan mu again ta sake ni tace wai ko Fatima don Alkah kece haka kodai yaya yakaiki cikin injin ne please. Na dan shafo cikin ta nace masha Allah ubangiji ya raba lafiya ya bamu mai albarka. Nan muka samu yan uwa sun cika falon sai faman sanu suke muna kowa kallon mamaki yake min don ganin yadda gaba daya na sauya na koma,wata yar larabawa dani abu ga dana,asalin buzaye. Mun samu a girka abinci kala kala wanda nasan aikin maryam ce haka na. Ban lura da Anty Amira a falon ba sai da naji yace mata haba sweet sister ba ko gaisuwa ne ? Sai lokacin na dago na dubi inda yake kallo tana zaune ta yi irin zaman dacta saba yi ta dunkule saman kujera sai chatting takeyi abinta. Ashe tun shigowan mu ta daga kai ta kalle mu taji wani abu ya tsaya mata arai irin yadda gaba daya taga na koma wata matar manya ko diyar manya can dani sai kamshi da annuri ke tashi gare ni. Gani cikin wani irin dogon riga kore yaji duwatsu tun daga sama har kasan shi hannayen rigan shara shara na yafa mayafin rigan a kaina ina rataye da jakka ja da takalma mai duwatsu kamar na rigan. Ga yan uwan su sai haba haba sukeyi dani mu kamar sunga wata basarkiya can daban. Haushi ya kumay ta tace wai wanan Bintun kauyen ne yau ta murje ta zama haka da ita kai kai maji why please maji taja wani dogon tsuki tamike tana fadin ita zata tafi gida ke nan. Nace a,a haba Anty Amira yanzun nan da shigowan mu hatta hausana ya sake ba sakwatancin nan sosai a cikin shi . Tace a,wulakance wani abun kuma zan tsaya nai maki bayan naga kun sauka lafiya ko so kike na tsaye ina,fadanci a kanki kuma ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,
IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YABI MUNA HAKKIN MU AKAN KI,
Yana isa zuwa yamma ya bar garin ya wuce zuwa lagos inda zai tafi ghana daga can gurin business din shi. Yana can ya bugo min washegari lokacin na tashi nai wanka ina shiryawa wayan shi yashigo na dauka tare da gaidashi yake tambayana jikin yayi sauki ko nace na samu lafiya sosai. Dama ai idan na shiga mota ne kawai nai tafiya mai nisa nake jin haka. Mundayi hira yana tambayana mutanen gida nace duk suna lafiya yace nagaida su nai mai Allah ya tsare yaba da sa,an tafiya muka kashe waya. Sai dana shirya ne mama tashigo dakin tana ce min karyawa fa nace mata da,dai akwai dumamay tuwo ne shi nake son ci. Tuwon aka dumamon an saka mai man shanu shi na danci kadan still ina jin tashin zuciya har lokacin. Nan mama take tambayana yaya za,ayi da kayan da mukazo dashi nace a fitar wa Baba na da nasu sai su raba sauran amma sabulu da clean abawa makwabtan su. Yadda nace haka mamana tai rabo na adalci don har na Baba na yafi yawa sai da nazo nagani nace a,a daidai za,a raba ita dashi. Mutanen da aka kai ma tsaraba sukai tashigo yi muna sannu da zuwa naji dadin yadda mutane sukai ta nuna min karamci haka. Ice dake gidan mama a karkashin shi muka mayar gurin zaman mu ni da iya sai dare muke shiga daki don rana haka na wuni kwance rijib ba lafiya. Iya ta matsa wai na fadawa maigida banda lafiya asan abin yi nace mata haka nakeyi dama idan nai tafiya. Sai mama ne da iya dake taya ta aiki suke ta faman kai kawo a tsakar gida kawuna yazo amsa kiran mamana da ta aika tana neman shi. Nan suka kebe tai mashi bayanin komai kuma ta kawo kudin aikin ta damka mashi don shi a garin yake zaune dama gurin shi tazo har mijinta ya ganta ya aureta. Sun gana da maigidan mama da kawu yace aiba matsala wanan taimako ne ai akai mashi da yamma kuwa sai ga masu aiki sun shigo gidan suka fara awon yadda za,a fitar da plan din ginan. Dakuna guda biyu na mama ciki da falo dayan kuma single ne sai wasu biyu a gefe daya su ma sai na samari washe gari yan aiki suka fara aiki akan idona akafara komai ga katan aiki kawu har ya sawo an fara aiyuka ko. Da dare daga ni sai mama na a daki Iyya na waje kwance wai zafi take ji. Nace mama dama ina son mu samu lokaci in fada maki wani magani da aka anso muna naba yaya yasha wanda ina gani shine sanadin barin shan abin maye da yakeyi. Nan dai nai mata bayani da kuma garin don ba nisa tace tagane mutumin ai dan uwan mahaifina ne tace insha Allahu zatayi kokari taje gurin shi. Muna cikin hirane yaya sadauki ya kirani muka gaisa yana jin murya na yace Fatima na amsa may ke damun ki nace may kagani ne yace you sound like baki da lafiya na kakaro murmushi nace daga barci na tashi yanzu barci na somayi kata dani. Ina ganin bai yarda ba sai naji yace humm kawai yace ina mama nace gata tare dani barin bata ku gaisa dama tana son maka godiya. Yace No No godiyan may kuma don nayi wa mamana alheri haba kada ma ki bata idan hakane kice ina gaida ita nace to ya kashe wayan. Koda ya kashe wayan hankalin shi bai kwanta ba yadda yaji muryana sai hankalin shi yai matukar tashi. Amma kuma baida yadda zaiyi tunda nace mai lafiya nake da ance sokoto nake da ya zo gobe gobe taga yanayin da nake ciki. Dole jiki ya matsa min ban samu tafiya ba ranan da muka ce zamu tafi sai da dare ya samu time ya bugo min waya yana tambayana mun sauka lafiya da kyat nake magana don da zazzabi na wuni. Yake tambayana ko mun sauka lafiya yaya baba nace cikin karfin hali ban samu wucewa ba yau yaya. Ya rage fara,anshi yana tambayan saboda may nai mai shiru yace baki da lafiya ko Fatima ? Shine kika shige kauye kika zauna da ciwo yana cin ki ajiki haka. Watau ke kin samu su mama kin manta da lafiyan ki ko ? Na rasa abinda zance sai da ya kara tambayana may ke damun ki ne ma wai ? Na rasa abinda zance mai sai can nace zazzabine amma naji sauki shine mama tace na bari sai gobe mu tafi idan na kara jin sauki. Yace a zaune zaki ji sauki bakiga likita ba ko may nace nasha magani ai na samu sauki yace ina Iyya take ne wai nace tafita. Yace gobe goben nan ki koma sokoto zan ma bashar magana yazo ya kaiki asibiti idan kun isa kafin na iso. Gabana yai matukar faduwa gashi banje gurin babana ba kuma yasan munzo. Na marairaice nace don Allah yaya kayi hakkuri naje gurin baba nai kwana daya jibi sai na karasa gida. Bai jira may zance ba ya katse layin bayan dan tsokin da yaja. Mama dake zaune gefe na takale ni a tsorace tace so yake ki koma gida baki isa can ba ? Na bata fuska tare da jan tsuki nace wai haka yake nufi ni kuma ba zan koma ba banje gurin baba tunda ba bari yake nazo ba. Tace a,a yar baba kirashi ki roke shi idan ya yarda sai ki karasa gurin su idan kuma yace lalai sai ki koma gobe din sai ku shirya ku koma din. Na dai daga wayan badon naso ba ga mama ta tsareni da ido na kirashi na zaci ba zai daga wayan ba dana kira. Amma sai naga ya dauka yace yaya akayi kuma ? A hankali na ce mai kayi hakkuri yaya don Allah naje gurin baba gobe nai kwana daya sai na dawo kada yace ko gudun shi na soma yi na rike uwata. Yace as you wish ai jikin ki ne nace kadai yi hakkuri please gobe da safe zamu karasa can mu kwana da safe sai mu taso. Yace na fada maki da kun kwana daya ki dawo gida kije asibiti aduba lafiyan ki nace insha Allahu jibi da safe zamu taso da yarda ubangiji. Yace is ok Allah ya sauwaka nace nagode muka kashe wayan mama tace ai kinga haka yafi da ran shi ya baci yakawo ki cikin dadin rai kuma akoma ana haka baiyi ba gaskiya. Nai mamaki irin tsaraban da mama ta hada muna mu tafi dashi wai kaji, man shanu fura da nono kwakwamayti kuka daddawa da kuli kuli da kwanzabbi mai yawa. Mijin mama ma yabani mamaki rago yasa akayanka aka,soya shi sai da ya cika bucket din penti yace nashi tsaraban ke na da mazzakwaila mai yawa. Tun da safe mukai masu sallama na wuto da kauna ta Sa,ade muka bar Asma,u tana kuka nai mata alkawari itama zan dawo in dauke ta ai tai makaranta haka yasa tai shiru. Sai kauyen mu nan na samu baba bai gida da farko kamar mama tabawa bazata karbe mu ba amma tana ganin an fara jido kaya ana shigowa dashi tafara washe bakin ta tana cewa sai yau Hjy maryam tun fa shekaran jiya akace muna kina Rabah. Nai dariya nace wallahi mama munje daniyar nai kwana biyu nazo nan nakarasa kwana uku sai ga ciwo ya rike ni acan. Tace assha subahanallahi inji da sauki dai ko nace naji sauki mama. Nan muka basu tsaranan su na aika,wa kakanina da nasu sukai ta godiya. Da baba yadawo shima na bashi nashi sakon yai ta saka albarka kwanan mu daya tunda safe muka kama hanya sai sokoto. Rijibb na iso garin na kwanta bamu jima dashigowa ba wayan yaya ya shigo yana cewa yaya kun taso ko nace gani dakina kwance yace ki shirya bashar yazo yanzu kuje asibiti. Ba adade ba bashar yazo muka wuce asibiti ganin likita duk a lokacin na jigaye na wahala sosai.