A lokacin muke by zainab i makawa - Chapter 98
A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 98: A lokacin muke by zainab i makawa Chapter 98. ****** ********* ****** A gurin da zanga likita ma sai dana dan…
3,370 words
****** ********* ****** A gurin da zanga likita ma sai dana dan kwanta kafin shiga ya kawo kaina banda kuzari sai yawan jin kasala dake damuna ko ruwa nasha sai na fitar dashi san nan naji shakat a raina. Nan yakira wayana nace gamu asibiti muna jiran layi yazo kan mu ne. Yace wai may ke damun ki ne Fatima haka ? Na lumshe idanuwa na nace ban sanni ba yaya komai naci dai sai na amaye shi kuma banjin kuzari a jikina ina dai ganin maleria ne yai min yawa a jikina. Yace bari a shiga gurin likita muji may ke damun ki haka kilama ruwan kauyen ku ne bai karbe ki ba kike wanan wahala haka ? Mun shiga gurin likita yai min yan tambayoyi irin nasu ina bashi amsa can dai yajefo min tambaya yaushe rabona da period ne ? Gabana ya fadi sai lokacin na tuna zancen wani period can nace gaskiya ina ganin kamar yakai kusan three month yanzu sai dai koda nake gida ai nakan yi irin haka din. Test akai min cikine dani har wata uku da kwana takwas nan dai suka rubuta min magani tare da,son na samu hutu don nayi weak da yawa. Kunyane ya rufe ni da akewa yaya bashar din bayani tun nan yaya bashar yake min congrats. Muna fitowa wayan sadauki na shigo mashi yace wai may ake cikine kunga likitan. Yace eh mungan shi gashi mun fito zan da tsaya na sai mata magani ne mu koma gida. Yace may sukace yake damun ta yace may ko zasuce banda cutar daka zubawa yar mutane mugu kawai. Gaban sadauki ya fadi shidai yasan baida wani cuta a tare dashi asalima shiba mane min mata bane balle. Yace for god sake may ya samu fatima din Bashar wani cuta ke gare ni da zan zubawa Fatima shi ? Yace kaiko keda cuta gatan kana kayan shi cikin wando kullun kana durawa yar mutane wahala. Nan yake ta tsokanar shi har yagane ciki yake nufi ke gare ni yace don Allah da gaske kake yi ko shirmay ka bashar ? Lokacin yake shigowa mota yake ce min karbi wayan maryam ki fada mai da kanki tunda ni ya mayar dani makaryaci yanzu. Kuma ka shirya tukwaici na wallahi don wanan ba karamin albishir bane nai maka. Yamiko min wayan yace ga fitinanen mijinki kiyi mashi bayani da kanki ko zai yarda murmushi kawai nayi mashi. Na dauki wayan cikin sanyin murya nake cewa hello yaya. Bai amsa ba sai cewa yayi wai wanan munafikin maganar gaskita yake fada min ko wasa yakeyi nace uhumm kawai tare da murmushi na mikawa yaya bashar wayan shi. Nan sukaci gaba do zolayan kan su har muka isa gida yaiwa iya bayani kan ance ana son in samu hutu sosai don haka kada ta bari inyi aikin komai please. Barci ne ya dauke ni mai nauyi ban falka ba sai misalin karfe takwas na dare koshi amai din ne ya tayar dani a lokacin. Sai dana natsu na jawo wayana kirane ciki barkatai na mutane nashi yafi yawa amma. Ban kirashi ba don yanzu ko hayani kwarai ban so sosai na shiga whastff nan naga yayi posting din suraitai barkatai na farin ciki. Ban dade ba nafita na kwanta sai ga Iyya tashigo dakin take min yaya jiki nace mata naji sauki sosai. Tai min tayin abinci nace tea nake so na ruwan liptop kawai ba madara ba sugar tace ikon Allah shi ta hado min na zuba zuma ciki dan kadan nasha shine har naji dan dadin bakina nai sallah na kara kwantawa. Da safe kiran mama ne ya tayar dani daga barcin tace Fatima ashe kin dawo kuma ba lafiya nai dan muushi nace wallahi mama. To yaya jikin da sauki yanzu ko nace naji sauki sosai mama tace shima yace insha Allahu yau zai dawo zuwa yamma don yana abuja babu jirgin safe yau. Nace Allah yakawo shi lafita tace amin ki kula da kanki kinji Fatima Allah ya inganta banyi magana ba don kunya. Falo na fito na samu Iyya da Saade azaune suka gaishe ni tare da min Allah ya sauwaka. Can nace Iyya afito da tsaraban nan kiraba abawa mutane nasu tace to nace man shanu da nama akai wasu mama shi idan kin dibi naki tunda munan akwai nama su zai masu a.fani suna da yawa can nasa ta diban ma anty maryam nata da Inna mama bashar kwai nace akaiwa mummy ta soyawa yaran ta. Yadda nace haka iya tayi kayan miyane kawai tabar muna don muna da bukatan su sosai. Iyya ce da kanta takaiwa kowa nashi mama tai matukar jin dadin yadda nayi don Iyya ta labarta mata komai kwai danace akawo wa yaran mummy da kwakwamayti ya matukar burgeta har mummy din suka ce suma suna nan shigowa su gaidani. Nan mama ta debarwa ko wani daki ta aika masu tana fadin ga tsaraban Fatima nan da ta dawo dashi suka karba suna gyatsire fuska kuma suka shiga ci.
****** ********* ****** Bayan sallah azahar mama da mummy suka shigo tun a kofa mummy take fadin ina yake tun bai fito ba na kwali kan na yana wahalar min da yarinyana haka ? Kunya naji sosai na dan dukar da kaina,a kwance suka samay ni saman dogon kujera na mike da kyat muka gaisa dasu nan mummy take fadin tun da dare sadauki yakirani yake fada min ai ban san lokacin da nai ihu ba har Alhaji saida yafito. Mama tace kai in ma ba abin kurciya ba yaya mutum zaiyi ciki har wata uku ba,a sani ba tun fa tafiyan su ke nan ta dawo da cikin nan amma haukan shi bai bari ya sani ba. Taron dai kurciyane hajiya inbashi ba ai ko ita zata gane tana da ciki a jikin ta ma kawai dai duk kan su kurciya yana cin su ne. Mummy tace mazajen ki na gaishe ki sunce sunga tsaraba sun gode sunace suna murna wai yayan su ya samu baby Banan da haukan ta wai nazo da ita ta dauki baby. Murmushi nayi nace lah mummy shine baku zo min da ita ba tace ban iya kiriniyan ta barta can suzo idan yayan su yadawo yakai su yawo ai yasaba da kwaram din su shi. Mama tace a,a Sa,adatu din ke nan ai ni dani kuka ba ita ta debe min kewan ku wallahi gata kamar ku daya wallahi nace mama ai munfi kama ko da Asmau sosai idan kingata kaman mu yayi yawa tana can mun barta tana kuka wai ita ma sai tazo mukai mata wayo nace zanzo na dauke ta daga baya yanzun ba wuri. Amma ko Fatima baki kyauta ba kikabar min Asmaun nawa kaunata ce ina ji da ita duk cikin kanne na wallahi. Bari ya dawo ai zan sashi ya tura azo min da ita tunda ku baku son zama da ita nan. Naji dadin jin haka kuma haka nake so don ina son yaran su fito suyi karatu itama mama ta dan huta yawan iyali. Idan kuma ta zauna gurin mama zata sha dadi sosai a gurin ta don mama uwace bata fada ba. Basu wani dade ba sukai muna sallama suka tafi akabarni da Iyya da Sa,ade a gida musa ya fita abin shi. Sai da dare ya shigo garin ina,falo kwance na dunkule yashigo gidan Sa,ade naji tana mashi sannu da zuwa don tare muke zaune Iyya tana kitchen. Yashigo idanuwan shi na akaina har ya karo inda nake kwance ina kokarin mikewa zaune daga kwancen da nake. Yace No don Alla kwanta abinki yazo ya zauna bakin kujeran da nake kwance haka yasa Sa,ade mikewa ta nufi kitchen gurin iya tana fada mata dawowan shi. Ya dan kai hannu shi a saman wuyana yana tabawa a hankali yaji ba zafi sosai yace how the you feel now ? Nace a hankali da sauki ya daga hannuwana ya rike a cikin nashi gama yace I dont know what to say but nagode Fatima na gode kwarai da wanan babban kyauta da kikai min. Na lumshe idanuwa na a hankali tare da kwantar da kaina ga jikin shi nace yaya I miss you. Yai dan murmushi ya shafi fuskana yace kina hakan da fa fushi nake dake da kikaje kika zauna da ciwo a kauye kamar wacce bata san zafin kanta ba. Amma yanzu kin wanke kanki ko gare ni komai ya,wuce ko yake cewa yanzun may kike ji kuma ne wai ? Nace ba komai yaya bandai jin karfin jikina ne kawai sosai kamar farko yace ina zakiji dadin jikin ki kina haka Allah dai ya rabaku lafiya kawai. Wanka ya,shiga yafito ya dawo falo inda muke don ni na kasa tashi ma,a lokacin sabada jiri dana ke ji. Da dare ma dai haka muka kwana dole washe gari aka sa min ruwa don amai yai min yawa sosai. Wani irin ciki ne wanan kuma bai bani wahala ba da farko sai yanzu gashi yana son kawo min cikas ga karatuna. Haka nake daurewa na je lectures na dawo gida a,wahalce yau ciwo gobe lafiya.
****** ********* ****** Wasa wasa baba sani ya saka sadauki a gaba da zancen Rahama duk da mama tace bata yarda ba ita. Ido da ido sukayi da baba Sani take fada mashi indai ita ta haifi sadauki wallahi ba,a auren nan sai dai in bayan ranta za,ayi shi. Tace yanzu kasan suna da zumunci kamanta lokacin da kaiwa mutane cin mutunci kace dan shaye shaye ne shi baka aura mashi yar ka naje cikin dangina na nema mashi. To na nema mashi din kuma yanzun sai hassada da kyashi ya biyo baya nace ba ayin auren idan kuma ka isa sai ayi mu gani. Yace ke wallahi hauwa baki isa ki raba muna zumuncin ba sai dai ki mutu amma sai anyi wanan auren muddin ina raye kuwa . Mama tace to ayi mugani idan kaika haifa min dan dakace na bari ya baci da shaye shaye saboda sakaci na a baya. Sai da baba ya tsawa ta masu yace subar zancen zai yi tunane yaga mai yadace yasan maji na da gaskiya kuma baitaba ganin ta rufe ido tayi sa,insa da wani ba haka sai ranan. Takira sadauki tun a waya ta falfalleshi so sai har hankalin shi ya daga tace katatake mutanen da basu kaunar ka da alheri su shiga cikin jikin ka. Yar matar ka kuna zaune lafiya za,a shigo a tarwatsa maku farincikin ku da tsagumi yace wallahi maji ni wanan magana ma bai gabana don na riga na fada mai gaskiya ko. Ana haka ma tafiya wasan su ya taso ban tashi ji ba sai bayan tafiyan shi da Nafisa tazo take ce min . Ke ashe wanan munafukan wai yanzun kuma yayana suke so ya auri Rahama bayan sun gama ciwa mutane mutunci. Gaba na ya fadi nace wata Rahama kuma ? Nan dai tabani labarin abinda ya faru da Baba Sani da mama ranan a gidan su tace wallahi maji tabani sha,awa yanda ta mayar mai da amsa son ranta. Munafukin mutum ne fa tare suke makircin su dasu Umma kullun akan yayana ko yanzun ma kila wani makirci ne suka kulla suke son ayi hadin. Duk da hankalina ya tashi ban nuna mata ba sai cewan da nayi kai anty baba kikecewa muna fuki kuma ? Au ke baki san munafuki bane dama mugune wallahi duk shi ya cinyewa baba kudin shi haka suke so kuma yanzu su shigawa yaya su cuce shi shida yaya Imirana kuma fa duk su Umma ke turasu don basu da tausayi dakika gan su nan. Tausayi tabani nan ta kwanta tai barci ta tashi tace tana son shan tea ni da kaina ba hado mata tea din da nai mata hadin da bata sani ba acikin shi. Tana gama sha tace zata tafi nakawo alheri dana saba mata idan tazo nabata dubu biyar da su man shafa da turare tai min godiya ta tafi nace Allah yasa a dace . Aiko da dare tafara gala baita hankalin uwar ta yai matukar tashi sosai a ka kwasheta sai asibiti ranan can aka kwana da ita hankali a tashe. Sai da tai kwana biyar tana abu guda a asibiti aka gaji aka sallamota. Ko yaushe muna makale da waya da yaya muna hira akan dai zancen ciki yake min surutun shi sai nagaji nace zan kwanta. Da safe ma,shi zai kirani ya tayar dani yana min yaya jikin haka na zan shirya na tafi makaranta da alolayi . Ranan nakewa maryam magana kan zancen Rahama tai mamaki inda na samu labari tunda mama tace kada abaru na san zancen ina cikin lalura haka. Ban fada mata inda naji ba sai dai cewa danayi ni ba wai shigowan ta nakewa tsoro ba wullakanci nake gudu tunda ita yar gida ce ni bare. Tace yar gidan wa Fatima don Allah ki daina kiran kan ki da bare a cikin mu please. Tace balle ma may yaya zaiyi da,wata Rahama can bakiga yadda takoma bane yanzu fa yan wahala wai harda ranon anko sukeyi fa. Nan naji hankalina yai matukar tashi sosai ranan har saida jikina ya tashi cikin dare dole aka kaini asibiti a can na kwana kwanana biyu Allah ya taimakeni anyi hutu sai mama tace a wuto dani gidan ta tunda dai jikin yakiya kuma shi bai gari. Daga ni har Iyya da Sa,ade muka koma gurin mama can gidan su amma ina matular jin jiki. Maryam ke fadawa mijinta har da zancen Rahama da nasawa raina ke kara damuna. Yakira sadauki ya fada mashi suna kashe waya sai ga kiran shi yake cewa uban wa ya fada maki zan auri wata Rahana can da zaki tayar da hankalin ki haka kina batun kashe kanki Fatima ? Murmushi nayi nace haba yaya akan Rahama zan kashe kaina don may zanyi kishin yar uwar ka ce fa ba,a aure ka aure ni ni ? Yace waya fada maki auren Rahama zanyi ne wai Rahama may ce ni bata ko a cikin lissafina wallahi. Sai da ya gama fadan shi yake tambayan jikina nace mai naji sauki yace kina cin abinci kuwa nace eh mama tana saka ni gaba na sha koko. Yace kokon may kuma can Fatima koko abinci ne da zakice kina cin abinci. Zan wa maji magana ta saka ki gaba sai kin dinga cin abinci sosai na dan marauraice nace ko naci wallahi bai zama a cikina wahala kuma yake sakani. Ya kashe wayan nace namiji ke nan kamar badashi ake wanan zancen ba ji wau Rahaman may can kamar ba a baya sun sha soyayya tare ba. Yadda ma nake jin labari duk abinda ya samu su yake kaiwa ita da uwarta shi yasa bai kawowa maji komai a lokacin. Amma da suka tashi bashi baya suka rufe ido sukai mashi cin mutunci ta uwa ta uba. Baba da kan shi yake zuwa har dakin maji da safe ya duba lafiyata wanan abin yana matukar ciwa su Umma da mama rai sosai. Sunyi gulma har sun gaji sun kyale shi suna zunde wai don ina matar dan son shi ne yake min haka. Ya bugo min waya muna zaune da mama da Iyya yake ce min gashi wani shago yazo shopping din kayan jarirai wani iri zai zabo antambaye shi yace a bari ya tambaya. Sai naji yace Fatima mace ce ko namiji a cikin ki innalillahi na furta da sauri suka kallo ni mama taju tsoro ta karbi wayan a hannu na lokacin da ya kara tambaya yana cewa fada min mana please. Mace ne ko namiji ba ance kuna ganewa ba idan mace tana da ciki don in san wanda za zaba. Mama tace to mara kunya ita ba irin ka bane mara ta ido kai kasan wanan ita batasan shi ba kada Allah yasa ka sayo din insai tafada maka abinda ta kumsa. Kaida kaicikin bakasan ko wani iri bane ka saka mata a cikin sai itace zata sani mara hankali kawai. Amira da ke zaune ko kallo bamu ishe ta ba tai tsuki tace maji tambaya fa kawai yakeyi killa yana son sayo kayane a can. Shidai yana jin fadan mama ya kashe wayan yana dariya kawai. Wani irin mahaukacin sayayya yayi kamar bai san zafin kudi ba yadda ya kashe su akan kayan baby kawai. Har su kayan wasan yara saida ya sayo sukekuna da gadaje ya hada da kayan uwar jego gaba daya, ya sako su a jirgi kaya guda dasu. Sai da dare ya kirani yana cewa watau dazun kika hadani da maji ko don kina muguwa na dauka abin siri ne tsakani dake amma kika mika mata waya don keta. Nace to naga sune manya su suka san abinda ya dacs asaya shiyasa nabata wayan ta fada maka abindake cikin. Kai dan kwallo dai bai jin wahalan kashin kudi kodan samun shi sukeyi any howa balle shi dayake ya,shara dan kwallon duniya ne shi yanzu kasa kasa ana hayan shi ya buga masu wasa. Don nan yanzu sun dauko sheri wa yaran musulman mu sai su hana su buga masu wasa idan za,a tafi. Haka yasa yanzu yai watsi da yan Nigeria yake bugawa wasu kashe she sai daga baya kuma suke son wai ya dawo masu yanzu ya dinga buga masu. Amma shima yaja masu aji ayace yabarsu can inda yake sunfi sanin darajan su suna biyan su da tsada fiye da nan da,ake masu kyat. Yayi kudii fiye da tsanmani don dai yana,bogon kurwa ne ba,a gane yawan kudin shi sai wanda yasan kan abin. Yana can yana gina gida a abuja wani irin maithigh house na gani na fada ba wanda ya sani sai yaya bashar da Baba kawai da mama. Don gudun yan baki irin su Umma don gujewa sherin su da munafunci don zasu iyacyin komai suga bayan shi. Zaman mu gurin mama yakaiwa Anty Amira ko ina don yadda mama take ririta sai take jin haushin hakan a ranta. Cewa takeyi wai shagwabane nakeyi ba wani ciwo dake damuna don dai naga kawai ana kulla min ne. Sai ranan da dare fever ya rufe ni sosai taga an rufa min bargo amma jikina sai shocking yake ina rawan sanyi Shine washegari har na samu sannunta take min yaya jiki yaya Sagir ne ya kai mu asibiti ni da mommy muka tafi akece wa fever ne na masu ciki yakamani. Kila sauro ya cije ni ne sadauki yana ji yaturo bashar a gyara AC a canza fanka a saka neat a window mama da kofa. Amira tace lalai ashe abin nayi ne wai duk a bintu ake wanan abin haka wani aiki kan sai malam. Ina jin ta nai murmushi nace lalai kam malam yai aiki saura biya tace Allah dai na ganin ki wallahi idan ma daure min dan uwa kukayi ke da mai masa dama ta iya bakar shige shige ai wa mutane balle nata. Nace ai wanda tayi ma saka ta akayi tayi din ba yinkan ta bane tayi don haka ashe masu ahige shige suna da yawa. Aiko tace wai na zage ta nai mata cin mutumci nan tafara min masifa mama tashigo tasamu tana min zari tace a,a ashe rashin tausayin naki yakai haka yarinya bata da lafiya mijin ta bai gari kice zakiyi mata rashin mutunci. Ke na gaji da wanan bakin halin naki wallahi Amira nan gidan su Bintu ne tunda gidan mijin tane kema kije ki nemi uwar mijin ki can ku karata can da ita. Amma baki zuwa ki saka min yarinya haka a gaba bata da lafiya kin isheta da masifan tsiya haka. Haka taita tunzura ta kwashi fushin ta tashige daki itama maji tafice zuwa waje. Iyan Rabi tace kinyi daidai wallahi wanan yarinyar kamar ba hajiya ta haifeta ba wallahi mugun halinta yayi yawa Allah. Nace haka take ita bara da,son jama,a yaniyin take tunda tace kai dan Allah wallahi dai halinta baiyi ba. Mutum bai da lafiya ace kuma bakai mashi sannu ba sai bakar yadiya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU [16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,
IDAN KUMA KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH,,,