A mafarki nasanta book 1 mallakin fa'eeh - Chapter 13
A mafarki nasanta book 1 mallakin fa'eeh Chapter 13: A mafarki nasanta book 1 mallakin fa'eeh Chapter 13. Sallamar da akayi A dayan b'angaren ce ya amsa…
3,370 words
Sallamar da akayi A dayan b'angaren ce ya amsa yana sakin murmushi,Unni yakike?ya gida?'sunan da aj ya furtane yasanya gaban Dr.Ammar fad'uwa idanu ya tsurawa Aj dake wayarsa da unni a tsanake cikin girmamawa cikin ladabi.A d'ayan b'angaren Unni ta tambayi Aj ya aiki ? bayan ta amsa masa duka gaisuwarsa,Alhmdllh ta furta ya furta yana mai sake fad'in Unni ai yanzu haka ma muna hospital d'in yau bamu tashi da wuri ba...
Ohk tau Allah yataimaka"ta furta masa,A hankali ta furta" Nur na kusa"ehh ya bata amsa atakaice yana mai d'aga idanunsa ya kalli Dr. Ammar da ya tsuramasa idanunsa masu kaifi Ba ko kyaftawa tunda yaji sunan Unni ya fito bakin dr aj gaban shi ke k'ara faduwa.
Unni ce ta juye harshen ta a yaren fulatanci,tana tambayarsa har yanzu Ammar yana nan kan bakansa ne?bazai karb'i sarautar ba,fahimtar da yayi bata son Dr Ammar d'in yagane zancen da suke yi yasanya sa shima chanja shima zuwa fulatanci,dan duk sun san Dr.Ammar baijin sa tun suna yara akayi koya musu yaren inji kakarsu Ammie gimbiya fatima,wanda itama ga mijinta margayi sarki Hamza ta iya sa da kuma kawar tata HAjiya,har ya" yan ta ma,shi yak'i maida hankali ya iya ne shiyasa bai iya yaren ba.
"Amsawa unni yayi da tabbas dai kam Unni yana nan kan bakansa,Unni bata nuna komai ba duk da amsar tasa tad'anji ba dadi ganin kafiyar yaron nata duk da tasan baizubar bane haka mahaifinsa yake da kafiya.furta masa tayi " kyalesa kar ka k'ara masa maganar komai yazo karshe in sha Allah.Sosai Aj yayi mamkin sosai da jin maganar da unni tayi dakuma rashin nuna damuwa da batayi ba kamar sauran lokutta,sai dai bai tambaye ta dalili ba saboda yanajin nauyin ya yar ta mahaifiyarsa fiye da mahaifiyartasa.Tambayar da ta masa ce ta katse tunanin zucin nasa"•••••••••
Ranar nace ka kirani inkazama less busy Amma Aminullah shiru babu kiranka,da yake haka take kiransa some times itada Sarki Ali ko son,shiru yayi na rashin gaskiya dan tabbas yana sane yak'i kiran nata gudun tambayoyin nata game da Dr.Ammar d'in akan rigimarsa da mahaifinsa,saboda kuma bayaso ya rik'a yawan yiwa Ammar maganar dan duk lokacinda ya masa magaanar sai yaga damuwa karara akan fuskar d'an uwannasa shikuma hakanne bayaso duk da yasan cewa yana cikin damuwar da shi kansa bazai iya boyeta ba a wasu lokuttan ba duk da jarumtar da yakeyi,shiyasa tun ranar da suka fito meeting d'in bai kirata ba,A yanzu ma koda yad'aga kiran yana d'ar darr ne a zuciyarsa duk da yasan unni mace ce marar daukar zafi,sai kuma yaji akasin Abunda yake tunani,yazata yaga ta nuna damuwa ko b'acin rai ko tayi fushi ma dasu.
A hankali ya furtama sorry unni kinsan aikin namu ne,shiyasa bansamu na kiraki ba,Murmushi kad'ai Unni tayi dan tasan tabbas gan gan yaki kiran nata domin baison takurawa AMmar d'in dan tana basa umurni ya tambayesa in yajanye domin ita ko takirasa shiru yake mata,DA kuma yarika convincing nasa har yajanye ra'ayinsa duk da tassan abu ne mai wuya.Shima Aj murmushin kad'ai yayi
dan yagane dalilin murmushin na unni akan maganarsa.
°©•••••••••••••••••••••©°
Bayan minti biyu dukkaninsu suka yi shiru,Unni ce ta takatse shirun nasu ta hanyar tambayarsa game da mafarkin da Ammar yasabayi tun yana k'arami wanda anyi neman taimako akai Amma ba,a dace ba kusan shekara ishirin da yan kai.
Amsa mata yayi da ehh yanayi Unni ma a wasu lokuttan kad'ai dan yasan Ammar bazai masa karyaba in yayi saboda shak'uwar dake tsakaninsu.
labarin last mafarkinn nasa yabata wanda ya banbanta da saura duk a harshenn na fulatanci suke maganar.
Ta B'angaren Ammar ido kad'ai ne ya zubama Aj din dan dukkanin abunda suke fad'a baya fahimtar komai inbanda gaisuwar daga cikin yaren,kuma tabbas yaji ajikinsa duk akansa ne suke magana sai dai bai gane kan zancenba,A hankali Ya lumshe idanunsa tare budesu wadanda suka d'an sauya daga farin madararsu yanayin nasa kamar mai jin bacci wanda haka kawai yake jin kasala na saukarmasa ta rashiin dalili.
'Ta B'angaren Unni ta razana sosai da jin labarin mafarkin da dr Ammar yayi,sosai hankalinta yatashi,Kwantar mata hankali Aj Yayi yana furta "unni karki manta fa ba duka mafarki yake zama gaskiya ba agaremu, Annabin mu muhammad saw shine kad'ai wanda yakeyin mafarki kuma ya tabbata dan haka karkisa damuwa dan sun furta zasu dawo kansa bashi ke nuna ko suwaye zasuyi nasara akansa ba Unni kawai kisanya duka wannan mafarkin nasa amizaninb sharrin shaid'an (la'anannen Allah) ba abunda zai iya zama gaske ba,sannann UNNI Addu'o'in ku natare damu mezaisa ki razana,ayanzu ya mayarda maganar sa da hausa inda duk maganar da sukeyi yanaji rad'am akunnensa.
Ajiyar zuciya Unni ta sauke abangaren ta cikin jin dadin furucin na dr aj wanda yasanyata jin sanyi aranta. wanda akullum take k'ara jin sa kamar ma ita ta sunb'ulosa duniya saboda kusan halinsu guda da aj a tabangaren iya sarrafa zance na fahimta da nutsuwa, Ahankali ta furta hakane son muna kai kam addu,a kuma kudage da Addu,a kaji,kai yad'aga mata inda takara furta Allah ya muku Albarka yakare gabanku da bayanku,Ameeen ya amsa mata cikin jin dadi har tamasa sallama Aj yamaza yatare ta daga shirin yanke kiran Unni pls karki sanarwa da kowa harda Abbah,in sha Allah ta furta suna yanke kiran.
Ajiyar zuciya kad'ai yake saukewa a jere cikin kara lumshe idanunsa kansa ya dafe jin yana juyamasa kad'an,A hankali ya bud'esu tar yakoma a mazauninsa daga d'an tsayen da yake tun dazu wanda su bakomai bane agaresu yin irin wannna tsayin saboda yanayin aikinsu na likitota.
Idanunnsa yak'ara lumshewa dasuka k'ara yin d'an jaaa na damuwa
Mafarkin nasa ne yadawo masa akai bayan zaman nasa wanda maganar da yaji aj nayi ce tak'ara dawo masa dashi sabo duk da yana ransa ne har yanzu baisan meyasa yake jin kashe yarinyar da akayi a mafarkin nasa ba yake jinsa har cikin ransa idan ya tuna da sun kashe masa ita jiyake kamar ya yi ta yin kukan da babu mai iya rarrashinsa,tambayar kansa yayi wai dagaske ne kwa?sun kashe masa dream girl d'insa,kansa ya girgiza da karfi yana furta nooo baki mutu ba Cikin d'aga murya irin tsawa d'in nan ta rashin tabbas Kan abu....
©°••••••••••••••••••••••••••••••°©
Ikon Allah kad'ai Aj ke kallo dan Shi Al amarin Ammar nabashi mamaki anya kuwa ba aljana ce ta Auresa ba ko ta shiga jikinsa take zomasa a mafarki kamar yadda su unni suka zata abaya sai dai duk iya binciken da manyan malammai sukayi masa ta hanyar yimasa rak'iya babu alamar hakan atare dashi.
Kuma yanaji ajikinsa kamar ma soyayya yakeyi da aljanar ko sonta yakeyi .Dan tabbas Alamu ya fara nuna son yarinyar yakeyi inma ba soyayya sukeyi din ba,domin ba tun yauba yana ganin wasu alamu agaresa duk da bai tabbatar ba.
Kallon Ammar yakeyi kallo na tausayi da mamaki,ganin kallon da yakemasa shima bayan bud'e idanun nasa da ke
a lumshe jin yayi sub'util kalam,yasan kallo ne yake masa na tuhuma duk da yafi hango tausayin sa acikin idanun na d'an uwansa,maganar da ke zuciyarsa ta fito fili yasan cewa sai Aj ya tuhumesa shikuma hakanne bayaso,kauda kansa gefe yayi daga kallon da sukeyi wa juna shida aj d'in yana mai tsuke d'an karamin bakinsa kar Dr .aj yaga damar sa har iya yimasa wata magana kan zancen.
Dr.Aj k'aramar dariya yayi duk da ya fahimci Ammar d'in sai yayi kamar bai gane nufinsa ba,A hankali Aj yadan duk'o da kansa yana mai furta masa anya kuwa ba son wannan aljanar kakeyi ba domin Kuwa nikam nafi tunanin ALJANA CE (oum Amjad) yakai k'arshen maganar tasa yana sakin karamar dariya,Dasauri Ammar yad'ago Dara Daran idanunsa yana sakarwa Aj wani irin kallo da idanunsa da suka kara girma kallo ne wanda sai da Aj yaja baya,shima yana kallon Ammar d'in da mamaki take zuciyarsa ta kara tabbatarwa da aljanace Ammar din yake tare da ita.
Ran Ammar ya b'ace sosai matuka wanda har sai da labbansa suka kara yin jan wahala na taunar da suka sha sanadin bacin ran da yasame sa na furucin Aj,Huci yake fitar wa mai zafi wanda shikansa aj sai da yayi danasanin maganar yakara yadda tabbas aljanace ke tare da Ammar d'in shiyasa yake wulakanta ire irensu dr malini.
Bayan kamar minti shida yafara sauka daga fushinsa A hankali ya bud'e bakinsa da kyar kamar wanda bayason yin maganar ya furtawa aj "yanzu nizaka had'a da aljannu halittar da muke neman tsari daga gareta,kuma wannnan baiwar Allahn itace Aljanar dude harararsa yayi yana furta kuma ni ba sonta nakeyi ba kawai dai inajin badadi ne sannan ita ba aljana bace then karka kara kiranta da aljana pls mutunce itama kamar kai inada yakinin tabbas mutunce duk da bansan sunantaba har yanzu bansan a ina take ba.
Kallonsa kawai Aj keyi baki asake,Addu,a kad'ai yayi aransa Allah yabawa Ammar lafiya,domin shi gani yake wannan Abu bana hankali bane.
Aiko insunje Nigeria zai sanarwa su Unni aljannu nan kamar ya kamata kara dubashi agani,anema masa magani kar abun yak'arayin girma ganin irin bacin ran da Ammar ya shiga kan furucinsa.kai kawai yak'ara kad'awa yana mai furta ohk!nagane,Amma fa dude kabani tsoro wannnan fushi haka daga kawai na furta Al......Dr Ammar murmushin da baiyi niyyar fitomasa ba yasaki jin aj yayi furucin Aljanna yakasa idasawa kenan bazai k'ara furta masa hakan ba,har ransa yaji dad'i yadda d'an uwan nasa yake gudun b'acin ransa tun kuwa suna kanana.
Aj wanda yayi shiru jin zai kara sub'util kalami ya furta baki yabawa Ammar hakuri sannann ya kara furta"nasan kaji wayar damukayi da Unni har naroketa karta sanarwa da sarki gudun fad'awa tashin hankalinsa"kallonsa kawai Dr Ammar keyi bece dashi komai ba.
Dr aj samun kansa kawai yayi shima dayin murmushi,ganin yadda yake ta kallonsa kamar wata sabuwar halitta.
Hadadden Rolex din dake daure akan tsintsiyar yakalla ganin lokacin sallar azahar yagabato yasanyasa mikewa dukkanninsu suka dauro alwallah suna dan gabatar da sallar alokacin ta.
*NIGERIA*
*ZAMFARA GUSAU*
Uwar ranar da ake kwatsawa ce ta ruwa tasanya dukkanin wani mai abun nawa yake gaggawa ya is a gida don ganin hadarin da had'u lokaci d'aya gudun shan kashin ruwa musamman masu babura.
Baba Adee ne ke ta k'ok'arin barin babban fuel station na nnpc bayan yasha man da zai kaisa garinsu Bungud'u,mashin d'insa ne d'ai daga cikin dankara dankaran motocin dake shigowa a gidan man ne,ya buge mashin d'in na Baba Adee sanadin shigar da sukayi ba dai dai ba.
Fadawan dake cikin motar ne suka fito dasauri suka rik'a masa mashin d'in nasa suna masa sannu tare da duba lafiyar mashin d'in NASA dan tabbatar lafiyar sa suna kara basa hakuri kan d'an karamin had'arin da ya auku sanadinsu,shiko yana furta musu bakomai cikin dattako.
A lokacin ne kyakkyawan dattijon dake cikin motar da duk tafi daukar hankali tafi sauran kyau kirar range rover fara tass new design yasauke glass a hankali dan son yin magana da Wanda accident din ya so faruwa kansa dan yabashi taimako a lokaci nne shikuma Baba Adee ya juyo A hankali daniyar duba bayansa yadda zai fita batare da ya buge wani ba da mashin d'in sa sai yayi dai dai da d'ago kan maimartaba sarki Aliyu Murai da ya sauke glass d'insa gabansa ne yayi mummunar fad'uwa ganin Wanda yahad'a ido dashi sak k'anensa Abdul rashid,sai dai d'an yanayin manyan taka dake tare dashi bakamar lokacin da yana saurayi ba. Wanda har yau basu San meyafaru dashi ba,sai dai kawai anwayi gari da rashinsa anyi nemansa ba,agansa ba.
Sarki Ali kuwa ido yasakar masa ganin bai nuna alamar cewa yagane saba,sai abun yabashi mamaki da alajabi Wanda har yasanya sa tunanin anya shine kuwa shine,kodai bashi bane mai kama dashi ne ,har Baba Adee yayi wucewarsa baisani ba da d'aya daga cikin fadawansa ya furta Allah yataimake sarki shin ko kasan wannan bawan Allah ne sai dai kuma gashi har ya wuce ai,sai lokacin ne hankalinsa yadawo kansa cikin tashi hankali bafaden ne cikin rashin hango tashin hankalinda sarki Ali yashiga ya furta Allah ya taimake ka har ma kama kuke dashi fa,Amma sai dai shi farar Fata ne duk da zafin ranar da ya d'an k'onasa a na hango farinsa....
Ganin samu da rashin da yake shirin yi alokaci d'aya duk da baya da tabbacin cewa shi din ne,Umurni yabawa d'ai daga cikin fadawansa cikin gaggawa da subi mutumin daya fita yanzu Wanda suka buge wa mashin,dasauri suka ja motar d'aya suka bisa.
💫A MAFARKI NASANTA💫
In my dream I know her
By
Pha'eezah Almustapha
Daga Alkalamin✍️✍️
💫Fa'eeh BG💫
Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔
------------------------------------------------------------------
--------------------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCITION📚🖊️*
*💫P.E.W.A💫*
*Home of perfect essential writer's together we stand🤝*
*ESSENTIAL WRITER'S📚🖊*
*Pen🖊️*is migthier than the sword *🗡️*
*Free*📙
EPISODE1️⃣
PAGE3️⃣3️⃣
TYPING📲📲📲
°©•••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••°©
Fitowa motocin sukayi daga gidan man suka parker a gefe gwanin burgewa dama mota biyar ce d'aya tabi mashin d'in Baba Adee,Bayan kamar mintuna goma sai gasu sundawo,sunyi rashin sa,ar ganinsa,sarki Ali Bayan dawowarsu da wannnan mummunan labari labari hankalinsa yak'ara tashi sosai sun sanar masa wata mota ce ta tsaya ta shiga gabansu kuma sai ta lalace,....maimaraba sarki Ali baice musu komai ba face umurtarsu dayin reverse sukama hanyar Gida ( fada).
Abunda yafaru Alokacin da Baba Adee yake tafiyar sa hankali cikin rashin kwanciyar hankali ganin hadarin da ya had'u yana so ya isa gida lafiya batare da yasha kashin ruwa ba... sai dai kuma baima lura da motar da ke bibiyarsa Abaya ba, kuma Alokacin da suka bi bayansa kad'an saboda d'an cunkosan da akasamu sai dai suna hangosa kad'an yana tafiyarsa akan babur d'in kasancewar sa bama gudu da abun hawa bane,wata katuwar mota ce jif bak'a wulik mai tinted glass tashiga gaban motar fadawan atsiyace,wanda dukkaninsu sai da suka razana yadda motar ta kutso agabansu bayan barin guraren da cunkuso yake,abun haushi kuma wanda ke cikin motar ne yak'i fitowa duk da jin k'arar horn d'in da fadawan ke ta sakar masa,d'ai daga cikin fadawan ya fito cikin yanayin masifa yana kwankwasa gilas d'in motar,A hankali glass din motar yake zugewa izuwa k'asa wata matashiyar kyakkyawar budurwa ce da taji bleaching ta bayyana a driver seat d'in wanda da alama ita kad'ai ce acikin motar yanayin ta kamar arazane Amma bai hana ta taunar cingum d'inta ba.
'Magana bafaden yayi cikin nuna bacin ransa"meyasa zaki tare muna hanya kinsan aikin da ke gaban mu ne,Alamun kuka ta fara cikin kissa tana furta masa motar ce fa ta kucce mata kuma she try to control it but takasa sannan ta daura da basa hakuri,sannann kuma yanzu taki tashi ma,Cikin d'an yanayin gamsuwa bafaden ya furta bakomai yan mata amma akara kulawa da irin gudun sa za'ayi domin mafi yawancin haka mota ta kufcewa mutun to ta iya yuyuwa mugun gudu yakeyi da ita ko kuma d'an koyo ne,kai ta d'aga masa cikin kara yimasa godiya,tana mai kara gwada tada motar da farko bata tashi ba na biyu ma sai a na uku ta tashi cikin murna tad'ago tana ma bafaden murmushi da yabata umurnin ta tada motar akaro na biyu taga ko zata tashi,Hannu tad'aga masa cikin sakin fuska sannan ta fisgi motar tana yin gaba abunta,suma fadawan da basu fahimci komai ba suka juya ganin tabbasa Baba Adee ya kubce masa basu ga ko ku'rar sa ba Yasa suka koma gurin sarki domin isarda sako...
©°•••••••••••••••••••••••••••••••°©
Gudu motar tayi kamar na barin Duniya sai gata a wani tangamemen gida,Bayan wangale mata k'aton gate d'in inda ta shiga aguje suna parker motar a inda yadace maimakon mace ta fito sai wani saurayi ne yafito a driver seat din wanda daga ninsa dai kaga d'an hau,dariya kad'ai yake tik'a yana furta ashe dai lawisa zaki iya sana'ar film wannan acting haka kinga yadda kikayi kuwa wallahi kad'an yarage dariya ta tafito fili a bayan nan da nake kwance. budurwar da naji ankira lawisa ce ta fito a extra seat itama tana ta tik'ar dariya harda rik'e ciki ashe ma itace budurwar da tashiga gaban motar fadawan sarki...
💫FA'EEH BG💫
FIRST LADY🙌
"Muryar tace take tashi tana furta kace kaso katona mana asiri jimmy sugane da gan gan muka shiga gabansu takai k'arshen maganar tana dariya,tak'ara furta jimmy Amma fa nima naso in d'an kwafsa dan namance kwata kwata inbar taunar cingum dinan tana mai kara yin wani k'aton kwai da cingum d'in,dasauri saurayin da aka kira jimmy ya furta wallahi kuwa taunar cingum d'in nan naki yaso yabadamu dan naga kamar bafaden nan yana miki wani kallo duk da nasan bai fahimci komai ba,dariya tayi tana furta yau da aikin mu baiyi kyau ba da oga ya hana muna na sharholiyar mu na kusan sati gashi yau muna da party a club takare maganar da shewa hannayen su suka bige irin na jin dadin nan.
'Jimmy ne yak'ara furta a wanchan karon makinsan anso samun matsala da sai sunga juna tun lokacin,kuma kinsan oga yace da sunyi magana shikenan komai zai lalace shiyasa ma nakara sanya su gaja su su kara saka mana ido kan wanchan tsohon,dana rasa dalilin da yasanya oga bai bada damar akashe masa shi ba na rasa dalilin da yasanya yasa ake kular masa da shiga da ficen tsohon cikin garin nan,duk da ni bazan iya wannan kasadar ba....
Firar su suka cigaba dayi suna lakkame da juna har suka shiga kofar Babban shigarsu su acikin tangamemen falon tabani damar kare musu kallo,lawisa dai irin karuwan nan ne masu lasisi dan tundaga shigar jikinta zaka gane hakan yadda kana nan kayan jikinta sukayi tieting din ta babu inda ba,a gani najikinta abun ba kyan gani,ga uban attach da zuba akanta da nail zago zago kamar wata horanya farace tass kalar farin bleaching,shima jimmy dai da ka gansa kaga d'an wanka ne kuma rikakken d'an shaye shaye bakinsa yayi bak'i alamar shan taba da sauran kayan maye tundaga yanain maganar sa zaka gane,shikam dai bak'ar fata ne irin tamu bakamar lawisa mai bleaching ba.
Su lawisa anji kunya💁 domin ba,a godewa Allah ba shine aka koma neman kyaun kanti🙅.
*gareku "yan matan mu kuji tsoron Allah kudaina fita tsirara kuna sakin siffar jikinku ga mutanen kan hanya,domin kuwa Allah yatanadar da azaba mai tsanani ga masu irin wannan shiga,Dan Allah arage yin irin kayan nan masu matse jiki,iyaye kuma hakkin ku ne ku hana ya yanku saka irin wannan sutura domin ko zunubi suka samu a danaku kason indai dasanin ku suka sanya,teloli kuma kuji tsoron Allah kudaina yiwa yayan mutane dinkin da kuka san bazaku iya barin ya yanku da k'annenku..Allah yasa mudace yakare mu daga sharrrin shaid'an dana zuciya *🙏🙏
©°•••••••••••••••••••••••••°©
Hayaak'i ne ya turnek'e falon inda nakai duba na a tsakiyar falon inda na hangi jimmy da lawisa manne da juna,Ance mannau😁Nida cingum..
suna zukar shisha hankalinsu kwance,hannu jimmy d'aya akan kirjin lawisa daya kuma rik'e da tiyo mai kyau nashisha,kar'ar wayar sa ce dake a hannun kujera yasanyasa cire hannun nasa akirjin lawisa yana duba mai kiran nasa sunan oga yabayya akan screen dinsa dasauri yayi picking call yana karawa akunnensa,A ad'ayan bangaren oganne yake furta jimmy inata kiranku shiru inji in aiki yayi kyau,cikin muryar maye maye jimmy ya furta ya oga na ka kwantar da hankalinka ai kasan ko yaushe mune da nasara indai tawanann fannin ne yakai karshen magaanar cikin sakin dariyarsu irin ta yan hau,A bangaren oga shima dariyar yayi yana furta nakasa zaama tun d'azu yanzu hankali na yakwanta domin tin lokacin da yashigo akasanar mini yakara furta kace yau akwai party kenan aikin ku na kyau zakuji alert din miliyan biyar yanzu yanzu shewa jimmy yakeyi lawisa na tayasa da duk taji komai tare da furta godiya mukeyi oga sannan suka datse kiran,dasauri lawisa ta mike cikin farinciki ta kwaso kwalaben giya dake kan dinning ta tile agabansu da kwayoyin maye,
*SAY NO TO DRUGS ABUSE🚭🚭
.*YAN UWA MUGUJI TA AMMALI DA MIYAGUN KWAYOYI DOMIN ILLANE GA RAYUWARMU*💡💡
A hankali suke bin kwalaben da'i dai suna shanyewa tare da kora wasu kwayun da ga su ga kamar ko kyan kallo baabu,take dukkaninsu suka sake rikicewa kai yad'au chaji kamar wasu mahaukata haka suka kara had'ewa da juna suka fara masha'ar su da suka saba cikin maye kamar wasu dabbobi
( wal iya zubillah )Nidai ganin haka yasa na fece kar inyi mugun gani.
Allah kashirya muna zuri'ar mu🙏