Kenza eBookz

Abdulmajid complete - Chapter 16

Abdulmajid complete - Chapter 16

Abdulmajid complete Chapter 16: Abdulmajid complete Chapter 16. D'akin sa ya fara shiga ya watsa ruwa tare da saka farar jalabiya, sannan ya nufi d'akin ta…

4,396 words

D'akin sa ya fara shiga ya watsa ruwa tare da saka farar jalabiya, sannan ya nufi d'akin ta da ledoji a hannun sa, jin ba'a amsa sallamarsa ba, yasa ya shiga kawai dan yasan ko taji tana iya kin amsawa saboda haukanta.

Kwance take sai sauke numfashi take Cikin nutsuwa alaman tana enjoying baccin nata.

Tsaye yayi kanta tare da hard'e hannayensa a k'irji, kallon yake kamar yau ya fara ganinta, tayi masa wani irin kyau ji yake kamar ya shige jikin jikinta yai ta romance nata, lips d'inta ya kalla da suka kara jajar dasu ganin sha'awa, har ya sunkuya sai kai mata kiss sai kuma ya fasa kada ya tasheta ya katse mata jin dad'i.

Ledojin ya aje kan d'an table dake gefen gadon tare da wuce wa, har ya kai k'ofa, ya tuna kila fa bataci komai ba, kitchen ya wuce ya d'auko plate da cup ya dawo, naman ya juye Wanda yasha kayan vegetable sai tururi yake, sannan ya tsiya ya mata juice d'in ya ije.

Gefen gadon ya zauna tare shafo fuskarta a hankali, motsi ta faraji jin ana Shafa ta ne yasa ta ware idonta tare da sauke su a kansa, tsuke fuskarta tayi, shima fuskarsa ba yabo ba fallasa yace.

"Tashi ga abinci nan ciki nasan da wuya idan kinci wani Abu, and banaso ana barmin baby na da junwa" yana gama fad'i ya tashi ya fice.

Da harara ta rakasa, tare da jan tsaki, nan idanunta sukayi tozali da plate d'in, wani yawu ta had'iye, Cikin yayi k'ugi jikinta har b'ari yake, abunka ga mai yaron ciki, da sauri ta sauko ta d'auki plate d'in ta baje k'asa ta shiga d'ibarsa........

_kowa yace shine tofa ba shine ba_ 🙄

💄Meryerm Abdool💄 [9/27, 8:01 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM* *#IG PML WRITERS* *#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035* *#http://maryamsbello.blogspot.com*

*_Annabi Muhammad S.A.W yana cewa "Ku kasance masu yawan tunawa da mai yanke jin dad'in rayuwa, mai rabaka da masoyinka da mahaifanka, kai dama duniya gaba d'aya wato MUTUWA. Yar uwa nidake dasu anya muna tunawa da ita a kowace rana? Muna sane da tana nan tana bibiyarmu ba makawa ba gudu ba tsira? To idan hakane mai muka tanadar ma wannan doguwar tafiya? Wane guzuri muke dashi a wannan tafiyar? Mu dage don lahira anan duniya ake nemanta, kuma mutuwa bata bada alert zuwa take bagatatan koka shirya ko baka shirya ba!🤷🏽‍♀ Allah ya bamu kyakkyawan k'arshe dan alfarmar rasulillah S.A.W_* 👏🏽👏🏽

Kud'in na daban ne a gareni

```Maryam Y Zango(Wanda yayi nisa) Raheenat Mahmoud(meye hujjarki) Fareedat sweery (yar sarki) muna zuba👀 Fashuna Salma Queen(momma)

Daduk sauran member of pure moment, Ku sani kuna wuta fa, kufa unique ne, just keep d fire burning #ana tare iya wuya#💋💋❤```

📝 *Episode* 221--225

Kiran farko na Asuba akan kunnenta, dama bata da nauyin bacci, ga kuma training d'in Iya Hari, a daddafe tayi alwala, dan da muguwar yunwa ta tashi jikinta har rawa yake kamar wacce tayi sati bata ci ba, har mamakin mugun cin nata take daya sameta a 2days d'in nan.

Koda Abdool ya shigo dan tayar da ita a dadduma ya sameta tana raka'atanil fajr, gaggauta fita yayi jin ana shirin tada sallah.

Tana kammala wa ko addu'ar kirki batayi ba, ta kwab'e hijab d'in tare da janyo sauran kazar data rage, ba maganan d'umamawa haka tahau ci, saida ta cinye tas, ta kora da juice d'in, ta dad'a da hollandia sannan taji dai2, ajiyar zuciya tayi kana ta d'auki Qur'an ta shiga karantawa.

K'arfe 6:00am ta gama karatun da azkar nata, mik'ewa tayi tare da d'aukar plate takai kitchen, wankesu tayi sannan ta share ko'ina tare da mopping, turare tayi nan take gidan ya d'au seti da k'amshi, to renon Iya Hari ce ba kyuya tana ganin ta cutar da ita, batasan taimakon ta tayi ba.

Saidai jin tayi turaren na haye mata kai, Allah yasa iya parlour ta saka bada bedrooms ba, d'akin ta ta shige tana toshe hanci ga zuciyarta sai tashi take kamar zatayi amai, aiko saida tayi sannan ta samu sassauci, saida ta dad'e zaune kafin ta iya gyara jikinta da wanka gaba d'aya.

Bayan ta gama shafe-shafenta, sip ta bud'e Tun k'asa har sama duk English wears tsaki taja tare da rufewa "nice zan K'ara saka wad'annan? God forbid" (d'iyar Baffa an tuba) lol.

D'ayan gefen ta bud'e nan taga su atampha, less, shadda da materials, wata super ta ciro blue and yellow, riga da siket ne ya zauna daram, tasan gun telansu akayi dama shike kai musu dinkin, bata d'aura d'an kwali ba, sarka ta saka 'yar simple me kyau, perfume ta d'auko dan fesawa tun kan ta fesa taji ya fara hau mata kai, dafe kai tayi tare aje turaren, hollandia ta k'ara sha sannan tasha maganin ta, da Mami tayi mata gargadi kula da shansa, bed ta koma tana game daga nan bacci yayi gaba da ita.

Saida gari yayi haske sannan ya dawo daga masjeed, direct d'akin sa ya wuce saboda a gajiye yake, duk kwanakin sunata hada-hada bai samun issheshen bacci, kwanciyar sa keda wuya bacci yayi gaba dashi shima mai cike da mafarkin 'yar rigimar tasa suna soyewa.....

**************

10:00am

Knocking ne ya tayar dashi, jiki a mace ya isa tare da tambayan waye, Nihal data shaka Dan sun dad'e wurin suna Knocking, jin muryan yayanta yasa ta waye tare da fad'in "mune" bud'e musu yayi sannan ya basu hanya, junior kuwa sai mak'ale sa yayi shi kuma ya daga shi sama suna dariya, gaidashi sukayi sannan suka aje basket d'in abincin akan dinning suna tambayan Ramlah.

"Tana ciki, and ki zubo min abincin nan, ki kawomin a d'aki" yace ma Nihal yana wucewa tare da junior.

"Kai waya gayamiki Amarya na baccin safe" Nihal tace tana Kai mata dun du a baya.

Bud'e ido tayi cike da masifa, sai taga ba Wanda take tunani bane, dariya suka sa mata Nihal da Amal, dan zaro ido tayi " yaushe kuka zo?"

"Ina zaki sani kuwa kina nan kina bacci, keda ya kamata ace kina parlour kina jiran isowar mu" Amal ta fad'a tana harara ta.

Dariya tayi "um kinga fa daga game ne, baccin ya sureni" tace tana sauke k'afafun ta k'asa, parlour suka wuce tana fad'in "me kuka zo mana dashi ni break fa ban had'a ba nayi baccin" d'an yunwa takeji sosai, dinning Nihal ta nuna mata tana mik'ewa zuwa kitchen dan d'auko plate dan zuba abincin da Abdool yace takai masa kada ta manta.

Gyara zama sukayi a parlon tare da jona kayan kallo, ganin Nihal ta d'auki hanya d'akin Abdool yasa tace "wai bani kika zubawa ba?" Harara ta balla mata "OK jirani nazo" tace tare da wucewa, dariya Amal tayi tace "um aunty barin zubo maki" ta mik'e zuwa kitchen...

Junior ne kad'ai kan sofa yana game da tab d'in Dadyn sa "son ina Dady?" Iya toilet " yace yana cikin bagwarar hausarsa, aje abincin tayi kan coffee table nashi, tana fad'in "wato ba zakaje Inda Maa dinka ba ko?" Tana k'ok'arin ficewa.

"Maa tana iya" ya fad'a yana aje tab d'in tare da biyota baya da gudu...

"Maa!" Ya fad'a da k'arfi, Ramlah dake zaune tana d'uri Amal sai dariya take mata, aje abincin tayi tana tare da ware hannu tana mishi murmushi.

"Son d'ina ni d'aya" ta fad'a bayan ya shige jikinta ta rungume sa "iyye yaron Maa ya kake"

Nan suka zauna sunata mata tsiya wai ba'asan Amarya da sakin ciki tana d'uri, jinsu kawai take, nan Sadee ta iso tare da wasu k'awayenta suka had'u sai tsiya suke mata, wai ta fad'a musu EDD dan kada ayi musu ba zata tunda anyi basu sani ba, banza tayi musu kamar bataji su ba, nan suka wuni har 6 sannan suka wuce bayan ta cikasu da kayan make up da English wears tare tace suje suyi ta sakawa itakam tayi retired sannan tace Sadee CE ta cuceta koma mai ya faru, dariya kawai suke mata, tace suyi dakyau yana zuwa Kansu, nan sukayi sallama da Amal dan gobe zasu koma, ba yadda batayi dasu su bar mata junior ba, sukace Aa sokoto za'aje dashi gobe tare dasu Amal, kuma ma Mami tace bata gama warwarewa ba balle ta iya d'aukar rigimarsa tadaiji da kanta..

Abdool kuma yana gama Karin ya shirya, ta k'ofar parlonsa ya wuce abinsa, bashi ya dawo ba sai after magrib, yau ma kazar ya k'ara kawo mata, saidai kowa jin k'amshi yake bamai kula wani.

Washe gari su Inna sukazo tare sukayi mata sallama, ta cikasu da tsaraba suma, sati Mami ta d'auka tana aiko musu abinci saida Ramlah ta tace ta daina kawo wa ta samu sauki zata iya yi sannan ta daina, komai tanayi a gidan kama da gyaran gidan, girki da sauran su, hadda maid Mami tace ta kawo mata tace aa, saidai ita da mai house d'inne kowa a sama magana ma sai a dole sukeyi, kowa d'akin sa yake kwana saidai hakan bai hanashi kula da duk wani motsinta ba,duk da zaman ba dad'i yake mishi ba dan gaskiya yayi missing nata d most, kusan kullum saita kira Amal ta had'a ta da junior sunyi waya, Inda hakan ba k'aramin dad'i yakewa iyayen Zee ba.

Ard'o ma suna waya akai akai, kullum maganar sa suna lafia dai ko to ta k'ara hak'uri yana nan zuwa....

****************

Wasa-wasa har sunyi month da tarewa ba wani ci gaba a zamansu shi yanaso yaga iya gudun ruwanta ne, itama zaman nasu na damunta dan kad'aici ba dad'i damar ta ma bata irin laulayin nan ci daine kamar gara, wayarta da kayan kallo ne abokan hirarta, anata ganin wulak'antata ne Abdool yayi saboda ya samu abinda yakeso daga gareta, bayan itace ta d'au zafi data ganshi zata wani d'aure fuska kamar taga abin k'i, amma kuma shi ta d'aura wa laifi.

Kullum zata kira Mami ko ita ta kirata, tana tambayan ta ba matsala tace ba komai, shima abinda yake gayamata kenan kullum inta tambayesa, kuma ko zuwa tayi basu bari ta gane komai.

Yau kam ya d'auki niyyan gyara zamansu dan ya fahimci in yabi ta tata saisu shekara ba ruwan ta, shiko ya gaji da zaman ga extra care da yakeson bata ita da unborn.

D'aure mad'aurin rigar baccin ta tayi tana k'ok'arin Sanya gashinta a net ya shigo, can ciki ta amsa sallamar kamar yadda ta saba, ba tare data juyo ba, dama normally duk dare zai shigo ya dubata kawai ya fice.

Zama yayi kan sofa, yana binta da kallo, itakam sai lamarin gabanta take, shiru ya ratsa su bamai magana na y'an sakwanni.

"Meye matsalarki da zama dani a yanzu?" Ya jefa mata tambayan.

Ba tare data juyo ba "babu" tace in short.

Smiling yayi yace "OK bakya k'auna tane?"

Wannan Karon saurin juyowa tayi tare kallon sa fuska d'aure "au nice ma bana k'aunarka?"

"Of course! Bakyasona, dan da ace kina sona danna kusanceki saboda kawai baki tare ba, ba zaki d'auki zafi haka, har da fad'in zaki zubar min da ciki imaging!"

Hawaye ta fara cikin k'unan rai ta fara magana "Yaya halin ko in kula da kake numanin ne k'auna, ko kuwa saboda ka sanni a 'ya mace kafin na tare gidan ka? Haka kayi ma Aunty Zainab, a gidan su kaje ka fara saninta kafin a kawo maka ita?"

Duk'ewa tayi gurin tana kuka "saini saboda kawai na damu dakai naje d'akin ka? Idan akayi ma 'yarka haka zakace so ne?"

Duk ya rikice ganin yadda take kuka akan wannan abun da bai isa ayi fad'a akansa ba, meye a ciki, tashi yayi ya taka zuwa Inda take tare da mik'ar da ita tsaye ya had'a ta da k'irjin sa, tura sa ta farayi, k'ara riketa yayi Sam baya son kukan nata, kuma ya shirya d'aukar duk laifin da zata d'ora masa, zai bata hak'uri dan dai a zauna lafia, tun ta d'auki abin da zafi.

"Saurareni Ramlah kinji, pls nutsu kiyi hak'uri na sani ban kyauta ba amma kiyi hak'uri kuma ki sani sonki ne ya kawo haka" ya fad'a da slow voice nasa.

Janye jikinta tayi ba tare datace komai ba, gefen bed ta zauna tana ci gaba da kukanta, binta yayi yana rarrashinta dan kukanta ba kad'an yake tab'a sa ba, "me kikeso nayi miki na goge laifina a gareki?"

Nan ma shiru tayi masa tanaci gaba da kukanta, sai rarrashinta yake amma tak'i kulasa, ita gani take dad'in bakine kawai yazo yayi mata dan wata buk'atar sa daya samu ya biya yaci gaba da sha mata omo.

"Aiba haka ka zauna da Aunty Zainab ba, zama kake tare da ita kana sake mata fuska, kana mata hira kana d'ebe mata kewa saboda takai mata budurcinta gidan ka, ni kuma daka amsa tun gida, ai ranar da aka kawo ni bakayi d'okina ba, hasalima had'e min fuska kayi tunda ka samu abinda kakeso dani tun gida, baka damu dani ba baka zama dani kaji damuwa ta, baka debemin kewa wannan duk son ne? Yanzu ma da abinda ya kawo ka shiyasa kakemin dad'in baki, daka samu ka watsar dani"

"Oh Allah" shine abinda ya fad'a, mezai gayama ta yadda dashi, shi baiyi hakan dan tozarci gareta ba, amma ta fahimceshi opposite, gashi ba ganin surutu ba, balle yai ta mata harta fahimceshi, Sam baison hayaniya duk ta birkita masa tunani.

"Ban iya tsari ba Ramlah, kamar yadda ban iya k'arya ba, a kanki na fara son mace, kuma banso wata bayanki ba kamar yadda nakeson ki, ki yadda dani, bazan tab'a wulak'antaki ba, kefa jinina ce, kuma matata pls believe me!"

Shiru tayi tabbas tasan bai iya k'arya ba kuma tasan yana sonta, to amma maganar baiso wata ba bayanta kamar yadda ya sota ne bata yadda dashi ba kuma zata k'arya ta shi akansa, don son da ya nunawa aunty Zainab yafi nata(ayya anaki ganin ba)

Jin tayi shiru yasa ya mik'e "ina zuwa yanzu" ya fad'a tare da fita, kiran Zainab da tayi ne ya tuna masa da sak'on da ta bayar ya bata, duk da baisan meke ciki ba, yaji ya kamata ya bata a yanzu, tunda dama cewa tayi idan sun tare.

Tana nan Inda ya barta, sunkuyawa yayi har sunajin numfashin juna "gashi Zainab tace na baki" ya mik'a mata takardar tare da zuba mata ido.

D'agowa tayi suna had'a ido tayi saurin d'auke nata, jiki a sanyaye ta amsa.

Ficewa yayi ita kuma ta warware takardar ta fara karantawa kamar haka...

_Zuwa gareki Aunty Nah kuma k'anwata Ramlah_...........

💄Meryerm Abdool💄 [9/29, 9:10 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM* *#IG PML WRITERS* *#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035* *#http://maryamsbello.blogspot.com*

*_Manzon Allah S.A.W yana cewa:- yake Fatima 'yar ma'aiki zan iya baki komai anan duniya, amma ki sani bazan iya amfanarki da komai lahira ba, aikinki ne kad'ai zai ceceki da rahamar ubangiji._*

_idan har Manzon Allah zai fad'i haka akan mafi soyuwa gareshi a cikin 'ya'yansa, to ina gamu gama garin mutane? Ina mai tak'ama da ilimi, arzikin, darajar, kimar, muk'amin babanta? Nasan dai tasan koda wasa ba zata kimantasa da fiyayyen halitta ba, to ko idan hakane mu sani iyayen mu ba zasu iya ceton mu da komai ba, aikinmu ne kad'ai zai cecemu, dan haka mu dage, mu gyara gobenmu, Alla yasa mudace da rahamarsa👏🏽_

📝 *Episode* 226--230

_"Ina rubuta miki wannan wasik'ar ne a dai2 lokacin da nake tunanin zanbar duniya, ina mai rokonki da had'a abinda zan haifa da sauran yaran da zaku haifa nan gaba, nasan zaki iya dan na yadda da kyakkyawar zuciyarki, sannan ina mai neman afuwarki akan kiyafe duka laifukan da nayi maki both known and unknown, by may size bakiyin komai ba face Alkhairi idan kinyi na yafe maki har ga Allah, a tare na sameki da Dr Majeed gashi zan barku tare dama Allah ya k'addara sai mun zauna ne a sanadin wannan d'an ko 'yar ubangiji yafimu sanin dalilin sa na tsara hakan wata kil yasan Dr bazai iya adalci a tsakaninmu ba idan kika tare duk da dimbin kyawun halinsa da adalcinsa, Ramlah yayanki Mutumin kirkine mai adalci duk da kin zama tauraruwa a cikin zuciyar sa bai hana ya bani wani fili a rayuwarsa ba ya bani kulawa da soyayya da mata dubu suka rasa a wannan zamanin yayi zaman Aure dani kamar yadda Manzon Allah S.A.W ya umurce mu bai tauye da komai ba, Ramlah bayan Mami ba abinda yayanki yakeso a rayuwa sama dake, duk wani motsi da bugun zuciyar sa dake yake yinsa, nasha jin kishinki lokuta da dama amma innayi tunani sai inga ba dai2 ne ba, saboda yayimin karamci bai kamata naji haushin Abu mafi soyuwa a garesa ba, wallahi Ramlah tun da nike a rayuwa ban tab'a ganin soyayya irin wacce yayanki ke miki ba ana yiwa wani ita, Ramlah kin dace da masoyi na gaskiya, ki daure ki nuna masa soyayya a zamanku ki tarairayesa da dukkan kulawa kiyi hak'uri da buk'atarsa ki d'aure ki jure inada tabbacin zakuyi zama mafi kyau a rayuwar aurenku, ina muku fatar Alkhairi a zamanku, ina rokon Allah ya kawar da fitina da shaidan a ciki, wishing d most blessing, peaceful marriage life"_

Ur sister Zainab Salis

Hawaye ne wani nabin wani ke sauka a idanunta, jimk'e takardar tayi da duka hannayenta biyu "nima nayi kishi dake sosai Aunty Zee, na d'auka kin kwace min Yaya Abdool ashe ba haka bane, na yafeki aunty Zee bakimin komai ba, kuma inshaa Allah, bazan tab'a banbamta junior da d'an da zan Haifa ba, ina sonsa sona gaske, Allah yakai haske k'abarinki, Allah ya sadamu a Aljannarsa mad'aukakiya don rahamarsa, missing u much Aunty Zee" duk Cikin kuka take maganar cike da nadamar abubuwan da tayi ma Dr Majeed, tasan komai ya faru laifin ta dan ita taja hankalinsa kuma tasan yaso ta tun kafin ta zama abarso, to yanzu ta ina zata fara bashi hak'uri?

Turo k'ofa akayi ganin tana hawaye yazo da sauri tare da rungume ta yana bubbuga bayanta, mamakine ya kamashi ganin bata tureshi ba saima k'ara lafewa da tayi a jikinsa, bai gama mamaki ba yaji ta zagayesa da duka hannayenta ta rungume shi.

"Pls yaya Sorry 4 everything I totally misunderstand u pls forgive me....!"

"Shitttt! U don't nothing wrong!" Ya katseta tare da d'ora yatsansa akan lip nata, bud'e baki tayi zatayi magana, kafin tace wani abu har had'e bakinsu guri d'aya, cikin wani irin salo yake kissing nata, itama ware wa tayi tana tayashi, sun kai 10mt haka, sannan ya fara zare bakinsa yana kallon ta k'asa-k'asa idanunsa sun canja launi zuwa ja, ita kuma sunkuyar da kanta tayi cike da kunya, mik'ar da ita yayi tare da d'aukar ta kamar wata baby doll, bai sauketa ko ina ba sai toilet, da kansa yayi mata alwala shima yayi sannan ya sake d'aukota direta yayi tare da shimfid'a musu darduma, sif ya bud'e ya d'auko mata zane da hijab, ita dai binsa kawai take da kallo, turare ya d'auko zai fesa "aa karka saka" tace, murmushi kawai yayi tare da mik'a mata, itama murmushin tayi masa Wanda rabon da yaga irinsa akan fuskarta har ya manta "nafayi sallah na" tace cikin siririyar muryarta.

Kashe mata ido d'aya yayi yana smiling "wannan special ce irin ta ma'aura wacce bamu samu damar yi ba zamuyi k'ara'i" turo baki tayi kamar wata yarinya, cikin wasa yasa yatsarsa ya buga bakin kad'an "common baby munada abubuwa a gabanmu masu yawa ga time na tafiya" d'aura zanin tayi tare da saka hijab d'in ba tare da tace komai ba.

Shigewa gaba yayi tare da jansu, raka'a 2 sukayi kamar yadda sunnah ta tanadar sannan ya dafa kanta ya shiga kwararo musu addu'a da harshen larabci da kuma hausa duka.

Saida yayi tsawon 30mnt yana addu'a, mik'ar da ita yayi sannan ya nad'e darduma tare da cire mata hijab da zanin ya ninke, gefen bed ya zaunar da ita sannan ya zauna shima, kama hannun ta yayi yace "nagode wa Allah daya nuna min wannan ranar da muka samu fahimta juna, zanyi marking nata cikin rana mai girma bayan first night namu, sannan nayi alk'awarin zan kula dake zan tarairayeka zan zamo hango abin jinginawarki zan kare mutuncinki zan rik'e amanar ki har abada, fatar zakiyi hak'uri dani da kuskurena idan nayi miki, ina mana fatar zaman lafia mai d'orewa".

Matse hannunsa tayi cikin nata " inshaa Allah zaka sameni mai biyayya a gareka, ta kowanne fanni zanyi iya k'ok'arina, Allah ya bamu Alkhairi mai dorewa a zamanmu"

Lumshe ido yayi wani dad'i na ratsashi yana feeling special, sannan yace "ameen uwargidana, one mnt" yace tare da mik'e wa yabar d'akin, plate ya dawo dashi a hannunsa, kayan cikine masu kyau a ciki da zafinsu sunji albasa, da tumatur da yaji sai k'amshi ke tashi, aiko d'iyar baffa tuni yawu ya tsinke, table ya janyo ya girke a gabanta tare da bud'e fridge d'inta ya d'auko fresh milk, stool din mirror ya janyo ya zaune yana fuskanta "bismilla" yace tare da d'aukar yanka d'aya zuwa bakinta, itama d'auka tayi ta bashi, a haka suka ciyar da juna cike da salon k'auna.

D'auke plate d'in yayi yakai kitchen ita kuma toilet ta shiga tayi brush, tare da hayewa kan bed, d'akin sa ya wuce yayi brush shima sannan ya dawo d'akin ta, kashe wutar yayi yabar deep one, sannan ya bita kan bed d'in, kusa da ita ya kwanta tare da leka fuskarta, likimo tayi yasani, murmushi yayi mai sauti tare da janyota zuwa jikinsa, anan suka shige wata duniya mai wuyar fassarawa romancing juna suke ba sassautawa duk da ranta fal tsoro, kasa daurewa tayi "pls yaya i'm scared kamin a sannu" Cikin kasalalliyar murya yace "feel free baby, ba zakiji zafi ba wannan Karon and zan biki a sannu ki saki jikinki kawai"....

***************

Tun daga ranar zaman lafia ya wanzu tsakaninsu, soyayya suke kamar su cinye juna, ga kulawa da tarairaya da take samu wurinsa kamar wata sarauniya, lallai a yanzu ta k'ara yadda da ba kowa a zuciyar Abdool sai ita natane ita kad'ai, komai tare sukeyi tun daga, kullum suna manne da juna suna soyewa, datayi d'an motsi kad'an " mene ne, meya faru, unborn ne ko" duk ya rikice yana tambayan ta, haka idan hospital yake yana mak'ale da waya suna hira har dawo gida, baya jin shakkar nuna mata soyayya a gaban kowa, ko gidan Mami sukaje bayajin kunyar nuna mata k'auna da tarairayar ta, sai ita yake bari da kunya.

Tuni suka dawo da junior gurin su Inda suke nan nan dashi, Ramlah kuwa ta had'a kiba abinta ta k'ara haske, Abdool sai tsokanarta yake wai ta zama Auntynsa yanzu tunda ta fishi kiba, had'e fuska take kamar yarinya inya tsokaneta, junior kuwa saidai yayi ta dariya yace Maa ta dawo yayinya.

*****************

Sanda Iya Hari ta farfad'o ba abinda take fad'i sai "kai mini rai Jauro karka kasheni" sai tambayan ta ake meya had'a ta da Jauro, meya kaita jeji amma ba amsa sai kuka take tana rokon Jauro yayi mata rai.

Tsawon watansu uku a asibiti sannan Ard'o yace a dawo gida tun da raunukan sunyi sauki ayi maganin kariyar na gargajia, abun tausayi iya Hari duk ta jeme ta lalace dama can ya muke muna 'yan sarki, kullum cikin kuka take tana fad'in a kira mata Ramlah, idan aka tambayeta me zata mata saidai tai ta kuka tana ita dai a kawo mata Laure, Hinde kuwa likkafa taci gaba dan yanzu tabar k'auyen gaba d'aya tabi wani saurayinta birni, wai iya Hari ta dameta da doyi a gida, da yake ba'ayi mata wanka saidai a goge mata jiki kawai Wanda shima Shatu CE keyi kullum tana gidan tun safe sai dare take komawa gidanta, da yake mijinta bai da matsala, Lanti kam sai tayi sati bata zo ba kuma ko zuwan tayi saidai ta kame gefe tana mata sannu ko Inda take bata zuwa wai d'oyi takeyi, kuma a dalilin ta tasa 'yarta ta gudu saboda azabar d'oyi.

Ard'o ma zuwa yanzu tausaya mata yake sosai ganin yadda duniya ta juye da ita (hmm duniya kenan tafi bagaruwa iya jima).

Gashi har yanzu tak'i fad'ar meya kaita jeji amma yafi kyautata zaton ba Alkhairi bane, ga shanunta ya Nema ya rasa anyi juyin duniya tak'i fad'in in da ta kaisu, kullum saidai kuka daga an tambayeta, yanaso yaje Kaduna yaga Ramlah saidai ciwon Hari ya hanashi tafiya gashi sai kashin kud'i ake amma kamar ana k'ara ma ciwon tak'i ne (to dama duniya imma shakiran ce ko imma kafura 🤷🏽‍♀) Allah yasa mudace......

Manage pls

_ina cikin damuwa ina Neman Addu'arku Friends😣_

💄Meryerm Abdool💄 [10/3, 10:53 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM* *#IG PML WRITERS* *#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035* *#http://maryamsbello.blogspot.com*

*_zuwa garemu writers, ban cire kaina ba, tambayace dani shin meyasa muke rubutu? Saboda samun fans masu zugamu suna cewa muci gaba da fire zasu bimu da fetur ko kuwa munayi ne saboda gyara? Bansan abinda ke ranku ba, amma abin da na sani shine kowace kalma da muka rubuta wallahi zamuyi bayani akanta a gaban ubangijinmu gobe k'iyama, shin muna tunanin idan muka doge da yadda muke rubutu a yanzu all about romancing sex, zamu tsira kuwa? Zamu iya hujja da rubutun mu gaban mahaliccin mu? As an advice we ar not too late even now, muyi k'ok'ari mu gyara mu, nidake dasu ana sabawa ubangiji dare da rana shi kuma mai gafara ne dare da rana muddin bawa yayi tuba mai kyau, so mu taimaki kanmu muyi amfani da basirar mu ta hanyar ceton al'umma daga wata musiba ba tsunduma su a ciki ba, idan har nayi/kikayi rubutu mai amfani koda mutum daya ya karanta ya amfana dake yafi mu rubuta barna mutum dubu su yaba mana, Wanda yabon iya Inda mukayi ne shikenan, ita kuwa azabar Allah tana can tana jiranmu a madakata, Allah yasa mu gane🤦🏽‍♀banyi dan cin zarafi ga kowa ba, duka nace so wacce ta tsargu ita taso ba ruwana.🙅🏿_*

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull