Abdulmajid complete - Chapter 15
Abdulmajid complete Chapter 15: Abdulmajid complete Chapter 15. Haka akaci gaba da jinyarta harta murmure ba tare da Mami da Nihal sun fahimci komai ba,…
4,463 words
Haka akaci gaba da jinyarta harta murmure ba tare da Mami da Nihal sun fahimci komai ba, hadda Sadee tazo dubiya nan take fad'a musu exam d'insu ta fito kuma sunyi passing d'an ta dubo musu, murna sosai sukeyi sun kuwa zuwa jami'a nan take gayamusu kuma an saka ranar bikinta da Uncle lukman kuma ya amince mata karatu bayan aurensu, nan ma murna sukayi sosai da jin labarin, nan suka d'auko chapter Nihal sukayi ta mata tsiya saura ita Yaya Hakeem yayi sauri asha biki, itama Ramlah suka shigo nata wai Dr Majeed shima yayi sauri a tare su dagargaji biki.
Yak'e Kawai take musu amma yanzu bata son ana ko maganar Aure a gabanta dan ta tsorata da lamarin...
Yanzu ta daina shigar k'ananun kaya saidai native kawai, ta daina zama koda parlour ne, balle kuma maganan zuwa d'akin Abdool ko hanyar d'akin batasan gani, ta daina ansa wayarsa haka zaita kira da turo text duk bata kulasa tun ranar ta d'auke wuta tun yana dauk'ar abin wasa har ya fahimci ita fa da gaske ne, duk ta toshe wata hanya da zata had'asu bata fita saita tabbatar baya gidan, haka da taga lokacin dawowarsa yayi zata shige ciki.
Wannan hukuncin ba k'aramin galabaitar da jiki da zuciyar Abdool yake ba, don ganinta dai yana sanyaya masa rayuwa, gashi yanzu ganinta nason yafi k'arfinsa, shi dama ba zuwa d'akin su yake any how ba kamar ita, zai iya k'irge shigarsa d'akin, dama ciwonta ke kaishi tau ta warke, ba wata hanya zuwa, ya jigata iya jigata da hukuncin nata.
Mami ma saida ta tambayeta ko sunyi fad'a da yayan nata ne tace ba komai, batasan damunta ta kyaleta, shima data tambayesa ba komai yace, haka ta zuba musa ido tasan da wani Abu kam a k'asa.
Nihal tambayan da take mata kenan, ansar dayace ba komai, sannan ga canjin da take gani gareta ta daina k'iriniya da surutun nan any how ka English wears ta fake gefe ta daina sakawa, "uhm nidai gaskiya sister ban yadda ba da wata amma in tayi tsami maji" tun junior na damunta suje d'akin paa har ya daina saidai yaje shi d'aya...
Yaune ake kawo kawo kayan Nihal,Wanda yayi dai2 da 2week da faruwar abin, gida ya cika da mutane, Nihal tun safe tabar gidan ba yadda batayi da Ramlah suje tare ba, amma tace ba Inda zataje haka ta kyaleta ta tafi..
'Yan kwanakin jin ta take, gatanan dai ba komai baya mata dad'i daurewa kawai takeyi, kwance take d'aki surutun mutanen ne ya isheta gasu junior sai k'iriniya suke shida su Husna, tashi tayi ta wuce garden, bakin k'oramar taje tana shakar k'amshin furannin tare da wasa da ruwan da hannayenta..
Kamar an jefosa ya shigo garden d'in, shima dawowarsa kenan daga hospital, fresh up kawai yayi tare da sauya kaya zuwa k'ananun kaya sai zuba k'amshi yake.
Kamar a mafarki ya hangota gurin k'oramar ta shagala da wasa da ruwa, sanye take da atampa riga da Zane ne sun yi mata kyau, gani yayi ya k'ara masa kyau fiye da tunani.
Da sand'a ya isa, Inda take ta bayanta yaje tare rungume ta, wani numfashi ya sauke da k'arfi Wanda ke nuna dinbin missing nata da yayi, ko ba'a fad'a tasan waye dan k'amshin turarensa na Amir ud ya sanar da ita, cike da masifa ta juyo dan sauke masa idonsu ne ya gauraya lokaci d'aya wani shock ya ziyarcesu, samun kanta tayi da yin shiru, jikinta kawai ta fizge ta fice da sauri daga garden d'in.
Sororo yayi yana binta da kallon mamaki, "shin gaske ne abinda na hango tattare da yarinyar nan? Tab idan ko hakane da hidden thing must be out soon" ya fad'a a ransa, a fili kuwa yace "hmm nawawoo there ris d fire on d mountain oo" smiling Yayi tare da shafo k'eyarsa sannan ya zube kan resting chair dake gun yana jin farinciki a ransa duk da yasan da rigima gaba k'adan.
Anyi komai daya dace, Inda suka tsaida ranar 4 months masu zuwa, haka tsaron ya watse kowa fuskarsa d'auke da farinciki, a ranar mutanen Besse suka wuce suma dai abin yayi musu sai fatar Alkhairi...
Ramlatun baffa fa jiki yak'i lafia yau ciwo gobe lafia, tun tana d'aurewa tana yi a tsaitsaye, har ya kaita kwance, ga ganin jiki ko a zaune take, ga zazzabi da amai ga rashin cin abinci, sai ramewa take a tsaye tak'i bari kowa ya sani, Mami tayi juyin duniya tace ita qlau take..
Ranar ko jikin yayi nauyi ko waje takasa tun abin safe tana dunk'ule a d'aki har 2:00, ba yanda Nihal batayi da ita ta tashi tasha koda tea amma tak'i ga juniour shima nanik'e da ita yak'i tashi shima, yana jiyan Maa, saida Mami ta dawo da office ta matsa mata dak'ar tasha tea kad'an shima tana gama sha ta Amayar hankalin Mami ya tashi, kallon tayi dakyau take a ranta ta zargi wani Abu, saurin basar wa tayi tace "is not possible" Abdool ta kira a waya ta gayamasa bata da lafia yazo ya dubata, yace to gashinan, haka suka zauna har dare babu shi.
Ranta ne ya b'aci da tasan ba zaizo ba aida asibiti zata kaita tun dazun, ganin jikin da sauk'i yasa ta bari har gobe idan baizo ba, da gangan ya k'irk'iri kwanan hospital, sai kiran Mami yayi wai uzirine ya rik'e sa patient aka kawo emergency a can ma zai kwana.
"To" kawai ta ansa.
Da sassafe ta nufi wata private ta kusa dasu da Ramlah, Cikin karamci suka karbesu dake abokin Abdool ne mai hospital d'in, bayan gwaje-gwaje aka kawo result, kallon Mami doctor Ubaid yayi da murmushi a fuskarsa yace "Mama ai k'anwar tamu Nada Aure ko?"
Da d'an sakin fuska Mami tace "baka ganeta ba ai amaryar kuce".
K'ara fad'ad'a murmushi fuskarsa yayi" kai wlh ban ganeta Sam, da yake gani daya nayi mata a bikin marigayiya" sannan yace.
"Madallah Aure yayi albarka 'Yar reno ta zama Uwar reno kenan" ya fad'a yana dariya tare da mik'awa Mami result d'in........
*****************
Wasu Matasa ne sukaje jeji don dibar icce, anan suka hango mutum kwance cikin jini, da gudu suka koma Cikin gari suka fad'a.
A tare suka dawo da Ard'o da sauran dattijawan garin, suna zuwa wa zasu gani inba Hari ba, mamaki ne ya hana Ard'o magana shidai basai ma da fitar ta, ko daga INA take oh.
Ranga-ranga suka kwasheta gida aka wuce da ita amma abin takaici Lanti da Hinde na gidan suka k'i wanke mata zawon sai Shatu aka kira tayi mata, sannan suka kwasheta sai asibiti har lokacin bata farfad'o ba, Shatu sai kuka take ganin mahaifiyarta Cikin mummunan hali, sabanin Lanti dasai muzurai take idonta ko gezau.......
_Fatar Alkhairi gareku iyaye na gari abin alfahari, Alkhairin Allah ya cimmaku aduk Inda kuke#double love# ❤❤❤_
💄Meryerm Abdool💄 [9/25, 2:18 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM* *#IG PML WRITERS* *#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035* *#http://maryamsbello.blogspot.com*
```Daga Aisha uwar mummunai (R.D) tace: Manzon Allah (S.A.W) yace "idan kika ga iska(guguwa) ya taso kuce, ya Allah ina neman Alkhairinta da Alkhairin da ke cikinta, da kuma Alkhairin da take tafe dashi, sannan ina neman tsarinka daga sharrinta da sharrin cikinta da kuma Sharrin da take tafe dashi.```
(Hakkun mubeen)👌🏻
_💋💋jinjina zuwa gareku, Fatyy Azland, Mom sultan, MSB(sakwara), Mrs fawwaz, Sadnas, sadnaf, Suhana, fannah, first lady, husna, sweery, fashuna and rest gaisuwa ta musamman my berries👌🏻😍_
Namecy na tafi ta kowa (Maryam y Zango) a kullum kina raina💋💋
📝 *Episode* 211--215
Ware takardar Mami tayi, bayanai sun nuna tana d'auke da cikin 3weeks, Mamaki ne ya kama Mami Ashe dai abinda take hangowa a idon Ramlah shidin ne, "to yaushe hakan ta faru?" Tunani ta shiga, "okey wato ranar da yace ta zame kenan, kai yaran yanzu bata ido, tunda yace na bashi ita nace ba yanzu ba, shine ya nunamin iyaka, to ai yanzu yazo gatanan can su k'ara sa" duk Cikin ranta take maganar, amma a kasan ranta tayi farinciki da cikin saidai bataso ya faru kafin tariya ba, duk da tana da tabbacin Abdool bazai juyawa Ramlah baya ba, hasalima sonta ne yaja faruwar lamarin.
Murmushi tayi tare da kallon Dr Ubaid "mashaa Allah, Allah ya inganta".
Shima smiling yayi " Ameen Mama, amma Dr Majeed baya gari ne ko?"
"Aa yana nan hospital dai ya kwana shiyasa muka zonan kawai" ta fahimci so yake yasan meya hana ya dubata da kansa, tunda b'angaren sa ne.
"OK, bari nayi saurin kiransa na bashi albishir" murmushi kawai Mami tayi, sai yanzu ta gane dalilin sa na rashin zuwa wato yasan meyake damunta, kwafa tayi a ranta alaman zasu had'u.
Magunguna ya basu yace ayi amfani dasu kafin Dr Majeed ya k'ara dubata, Ramlah dai zaune kawai take kamar mutum mutumi duk an sakata a duhu, ta k'asa gane komai, sallama sukayi masa sannan suka wuce, biye take da Mami jikinta duk sanyi ganin kallon tuhuma da Mami ke aika mata.
Bayan sun shiga mota ne Mami ta mik'a mata result d'in, hantar cikinta saida ta kad'a tare da zaro ido, sai hawaye sharr "wlh Mami ba lai....." Katseta tayi.
"I know ba laifinki bane, amma meyasa bakk gayamin gaskiyar abinda ya faru ba? Kodai baki d'aukeni a matsayin Asma'u ba?" Mami ta fad'a Cikin d'aure fuska.
Girgiza kai ta shiga kamar k'adangarwa sai hawaye ta k'asa magana, Aida nauyi ta tunkareta da wannan zancen koda Asma'un ce raye ba zata iya gaya mata ba".
"Na fahimceki yi shiru, share hawayen ki kinji" Mami tace da sigar lallashi, sannan tayiwa motar key.
Life kanta tayi a cinyarta tana kuka mara sauti "shikenan Yaya Abdool ya wargaje min rayuwa, yanzu shikenan, irin abinda ya faru da Larai ne zai faru dani, na shiga uku" wata 'yar kauyensu ce bayan an d'aura mata Aure ba tare ba mijin yayi mata ciki, aiko akayi ta rikici daga k'arshe ya saketa yace ba cikinsa bane.
Itama tunanin ta haka Abdool zaiyi mata, k'ara rushewa da kuka tayi na tausayawa kanta, yanzu shikenan idan Mami ta yadda Kilgori zata koma gurin Iya Hari "oh dota meye na kuka? Wipe ur tires zanyi maganin abin kinyi" Mami ta katseta jin sautin kukanta.
Tissue da Mami ta ta mik'a mata ta k'arba ba musu ta share hawayen, saidai ranta a jagule yake, lumewa tayi akan seat tare da lumshe ido, tunani barkatai takeyi, na neman Mafita.
Mami da kanta da had'a mata soft breakfast ta sakata gaba sanda taci sannan ta bata magani tanasha ba dad'ewa bacci ya d'auke ta nan parlour kan 2seat, jin saukar numfashinta ne ya tabbatar wa Mami tayi bacci, mik'ewa tayi bayan ta gyara mata kwanciyar.
Nihal ce ta fito "Mami kun dawo, meke damunta? Sisto ya jikin?" Ta fad'a a tare tana k'ok'arin tab'a jikinta.
"Karki tasheta mana yanzu ta samu bacci" Mami tace, sannan tace "ina junior?" Yana ciki yayi bacci " ta ansa.
Shigewa d'aki tayi ba tare data k'ara magana ba, wayar ta, ta janyo ta kira k'awarta bayan ta Zaune kan sofa, bayan sun gaisa "furnitures nakeso ayimin oda designers a satin nan Hajia in da hali" banji abinda k'awar ta fad'a ba.
"Uhum kedai bari, 'yata ce zata tare kuma Cikin satinnan nakeso ayi tariyar".
"Ada kenan, ai Abdool ya b'ata komai, ciki fa yayi mata dan ya nunan iyakata, nidai ayi k'ok'ari ayi komai in time ta tare kawai su barni na huta nima, koma kawai ki sayo komai biyu na had'a hadda na nihal ayi zuwa d'aya" ta sake ansata
Dariya itama tayi "to ai yaran yanzu sun shafawa idonsu toka ba kunya" sannan sukayi sallama, saida k'awar tata ta bata shawaran ta bashi matarsa tun da ya nuna buk'atar ta tace Aa sai sun shiga jami'a to ai ga digiri nan an samar mata Inji kawar.
**************
Yanke shawarar yaje gida kawai yaga halin da tace ciki, ba wani boyo a yanzu kam tunda Allah ya tonasa, koma ya fad'i ko kar ya fad'a bayyana kansa zaiyi, tare da Hakeem suka taho dan yace zai biya yaga sweetyn sa, Abdool sai tsiya yake masa wai baya kunyar sa a matsayin sa na sirikinsa, dariya kawai yayi yace ba wannan kuma, nan dai sukayi ta zolayar juna kamar yadda suka saba.
Nihal da har yanzu tana parlour tana jinya, itama har yanzu bata farka ba da yake harda maisa bacci a maganin, gashi tasha kuka, sai bacci take, ga hawaye sun bushe a idon, ita Nihal a nata tunanin zafin ciwo ne ya sakata hawaye.
Tsayuwar motarsu ce, tasa Nihal shigewa d'aki, dan tasan tare da Hakeem dayake ya gayama ta zuwan, da sallama suka shigo yana ganinta kwance a parlour tare k'ofa yayi wai saidai Hakeem ya tsaya daga waje Nihal ta iskoshi can amma bazai kallar masa mata ba.
"Dad'in ta dai nima inada matar ko?"
"Bamu shaida ba, kanada jingina dai" ya fad'a yana dariya.
"Zaku shaida ne very soon, kai kanka ka sani"
"Tau naji tafi dai" ya turasa baya, girgiza kawai Hakeem yayi yana fad'in "zaka zo hannu zan rama nima" yace yana wucewa farfajiyan gidan, shi kuma ciki ya shige yana dariya "koka rame ba"
Sunkuyawa yayi tare da pecking goshinta, yana kallon ta da murmushi a fuskarsa, tayi wani fayau da ita ta k'ara haske, ga hawaye kwance a fuskarta, alaman kuka tayi kafin tayi baccin, tausayinta ne yaji yasan idan aka bibiya shine silar kukan, k'ara sunkuyawa yayi da niyyan lashe hawayen, dai2 fitowa Nihal cikin kwalliyar ta ta zuwa gurin Hakeem.
Fuskewa yayi, ita kuma ta sunkuyar da kai tare da gaidashi d'akin Mami ta wuce dan gayama ta zuwan Hakeem, shi kuma d'an siririn tsaki yaja "mutum ba damar ya sake da iyalinsa, gaskiya ya kamata mu tare hakanan" part nasa ya wuce, wanka yayi tare da sauya kaya, sannan ya fito dan shiga inda Mami.
Still bacci kawai take shaka abinta "aifa kin samu aikinyi baccin masu ciki" yace yana smiling, sannan ya shiga d'akin Mami da sallama.
Ciki ta ansa mishi fuska tamke, zama yayi a darare kan sofa, yana gaida ita "lafia" ta ansa a tak'aice, tare da mik'a masa takardar .
Shiru yayi kansa k'asa bayan yaga abinda takardar ta k'unsa Wanda already yasan dashi "sannu ko Abdool aikin ka yayi perfect" Mami tace ba tare data kallesa ba, still shiru yayi dan bai da bakin magana.
Jin shiru baice komai ba ta shiga surfa masa "wato tunda ban amince, sai kayi mai gaba d'aya ko? Yanzu ka kyauta kenan, duk da addini bai hana kaba amma ai yaci Karo da al'adar bahaushe ko? Yanzu kai fisabilillah idan akayi wa 'yarka haka zakaji dad'i eye?"
"Yanzu da ace ba gida d'aya kuke rayuwa ba, kuma ba jininka bace? Saika iskota har gidansu kayi mata cikin?" Nan fa taita mishi inda take shiga ba nan take fita ba, shiru yayi mata har saida ta sauke aya sannan ya shiga bata hak'uri
"Ba wani hak'uri ai, kaje kayi gyaran gidan ka k'arshen satinnan zata tare, ina shikenan ko?"
Hak'uri kawai yake bata, Sam baiyi tunanin lamarin zaiyi zafi haka ba, ya d'auka rigimar iya ta Ramlah ce, shi baiga abin fad'a ba, tunda dai sunnah ce yayi ba zina ba, akan wata al'ada can daban za'a damu, ai kowa yasan matarsa ce, kamar yadda Cikin ma nasane kuma ta hanyar halal, baiga abin damuwa dan miji ya kusanci matarsa kawai dan bata tare ba.
Kuma ai ko meye ita taja, tunda ita ke shigar da ke tayar masa da hankali kuma har d'aki take iskoshi fa tana kusantansa ai yayi k'ok'ari ma, a nashi ganin, kuma ai zaifi dad'in fad'a ace yayima matarsa ciki before ta tare da ace yayi zina da wata daban.
Sai bayan ya fita ne ya bawa Mami tausayi, tasan yanayin d'anta sarai mabuk'aci ne, ga shigar k'ananun kaya dasu Ramlah keyi Wanda saida yayi magana akan hakan tace ai ba laifi ne, laifin ba nasa shi d'aya bane hadda su, but still dole ta nuna b'acin ranta dan siyama Ramlah mutunci gareshi, amma ba laifi a Cikin haka a musulunci saidai al'adar bahaushe (mata iyayen kariyar al'ada).
Koda ya fito bata a parlour, ta tashi taji jikin da d'an sauk'i shine tai ciki dan watsa ruwa, wucewa yana tunanin ita kuma koda wace rigimar zata zo masa.
Murmushi yayi "unborn ka taimakamin daka zo gashi za'a bani matata cikin sauk'i, love u much 'yar baffa iyayen rigima"................
_kuyi hak'uri waya tace sai a slow matsala tace bani, Hocking take inna dad'e INA typing_
*love u guys buhut- buhut kunsan kanku😜 yes u!💋😍 #one love # all of u* 👌🏻
💄Meryerm Abdool💄 [9/26, 5:39 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM* *#IG PML WRITERS* *#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035* *#http://maryamsbello.blogspot.com*
```Daga Baban Darda'i (R.D) yace, Manzon Allah (S.A.W) yace:- Duk Wanda ya k'are mutuncin d'an uwansa, Allah zai k'are fuskarsa daga wuta ranar alk'iyama.
Ma'ana Wanda ya tsare mutuncin d'an uwansa, ya rufa masa asiri, ya boye miyagun dabi'unsa shima Allah zai k'are sa daga wutarsa.
Kenan rufawa d'an uwanka musulmi asiri koda ka kamashi miyagun ayyuka wajibine ka boye su, sannan ka naima masa shiriya gurin Allah a maimakon ka fallasa shi, Allah yasa mu gyara``` 👏🏽
Tunatarwa ce👌🏻
📝 *Episode* 216--220
Tsaye take gaban mirror daga ita sai k'aramin towel tana busar da gashinta da hand dryer, bayan ta gama ne ta shafa mayuka akan ta kama da ribbon, kallon kanta tayi ta mirror tare da d'ora hannu kan mararta "yanzu da gaske cikine dani?" Tace tana b'ata fuska da turo lip gaba, kamar mai shirin yin kuka "oh yanzu mai zan gayama su Besty idan suka gane, wayyo yaya ka cuceni Allah..... Shiru tayi jin an turo k'ofar tare da juyawa dan ganin mai waye.
Tsaye yayi b'akin k'ofar, yana binta da mayataccen kallon, smiling kwance a fuskarsa, tsuke baki tayi tare da d'aure fuska taci gaba da Shafa man ta, smiling yayi mai sauti tare da takowa zuwa inda take, rungume ta yayi ta baya tare da d'aura hannunsa kan mararta, kansa bisa kafad'arta.
Turashi ta shiga yi ba tare da tace komai ba, amma ko motsi baiyi ba saboda rik'on da yayi mata bana wasa bane, ganin ta k'asa kwatar kanta ne yasa ta fashe masa da kuka Wanda da gani na renin hankali ne.
Sakinta yayi tare da janta zuwa bed, zaro ido tayi sannan ta shiga turasa, sakinta yayi yana 'yar dariyar tsokana sannan ya rad'a mata a kunne " me haka baby na, lafiyar unborn d'ina, bafa abinda kike nufi bane, idan kuma Shi kikeso to sai muje d'akina, kinga da junior anan" ya fad'a cike da tsokana.
Wani takaici ne ya turnuk'eta ta k'ara bud'e baki "ka tafi Allah ko in tada junior ya ganka, kuma Allah dole ka zubar min da Cikin nan ko naje a zubar dashi haka kawai sai a ganni da ciki ba tare dana tare ba, kuma bazan yadda na haifesa yayon fitsari ya kamani a banza ba" har ya juya zai fita, yana dariya sai ya jiyo furucinta na k'arshe, tsayawa yayi cak tare juyowa fuskar murtuk'e yayi kanta gadan-gadan.
Baya ta rink'a yi cike da tsoro ganin yanayin fuskarsa, saida ta manne da sofa sannan ta dafe kanta da hannayenta, tana jiran abinda zai mata, shiru bataji komai ba, d'agowa tayi ta gansa tsaye idonsa sunyi ja.
Nunata yayi da yatsa "ke ashe mahaukaciya ce ban sani ba, to duk Wanda zai ganki da ciki shiya dad'e bai canyeki ba, da yake nina kiraki d'akin har nayi miki Cikin, to bari kiji ba yawon fitsari ba, ko yoyon kashi zakiyi sai kin haifesa tunda dan sunna ne ba zina ba, naga alaman kin renani tunda kinga gadon bacci na ba, to mu zuba nidake" sannan ya fice Cikin b'acin rai.
Tunda ya fara balbaleta ta rufe ido jikinta sai rawa yake dan bata tab'a ganin b'acin ransa kamar haka ba, iya sanin ta dashi, duk'ewa tayi k'asa tana rusar kuka lallai wannan shine a dakeka a hanaka kuka, kukanta ya tayar da junior shima ya tashi yana tayata.
A dole ta daina kukan ta d'auke sa tare dayi mishi wanka, shiryashi tayi itama ta shirya sannan ta wuce parlour dashi dan bashi abinci amma duk ranta a jagule yake tama rasa wane tunani zatayi, anan taci karo da Nihal ta dawo tare dasu Husna da driver ya d'auko daga school.
"Sisto kin tashi ya k'arfin jikin, wai meke damunki ne?" Ta jero mata tambayoyin same time, yake kawai tayi mata "uhm Malaria ce fa, na samu sauk'i sosai" sannan ta sauke junior ta rungume su Husna dake mata sannu tana tambayan su school.
"Allah k'ara sauk'i sis, barin shiga na fito" Nihal tace tana shigewa ciki.
"Ok" tace tare da shigewa kitchen...
Safa da marwa kawai yake tsakiyar d'akin, ransa a b'ace "lallai yarinyar nan ta gama renani at all, ni zata gayawa zata zubarmin da gudan jinjna? Lallai dole na jingine sonta a gefe na koyamata hankali, dan naga kanta na rawa, Amma zanyi maganin abin"........
*****************
Gaba d'aya ya watsar da lamarin Ramlah gefe, duk da yanda ruhi, zuciya gangar jiki suke son kasanewa da ita, a ganinsa hakan zaisa ta shiga taitayinta, bai cika zama gida ba yanzu inya fita tun safe sai dare kuma, yafi maida hankali akan gyaran gidan kamar yadda Mami ta umurcesa, duk da ba wani gyara ne sosai ba, amma kullum yana gurin ana k'alk'ale-k'alk'ale kunsan Drs komai nasu unique ne, yau ma office d'in Hakeem yaje tare da damunsa ya tashi ya rakasa ya dubo aikin da ya bayar ayi masa.
" wai kam wannan gyaran gidan na meye ne? Naga dai tare zakuyi tariyar nan da bikinmu gaba d'aya, kuma still have time"
Dariya yayi "naka wasa, ada kenan, aini a satinnan zamu tare"
"Bansan da wannan ba, kode ka k'asa jurewa ne da jiran 'yar renon taka zakayi mata k'anwa" Hakeem ya fad'a cike da zolaya.
" 'yar reno ai ta dawo Uwar reno kuma yanzu, saidai kace Maman Unborn " ya bashi amsa Cikin seriousness.
Cikin mamaki Hakeem ya kallesa, ganin iya gaskiyarsa ne yasa yakai masa duka yana dariya "amma dai wallahi bakayi ba, yanzu saida ka lalube yarinyar nan ka lallab'a kayi mata ciki, amma dai anji kunya".
" dalla matsa can mutum da matarsa zakace naji kunya, ni kaga tashi muje ayi a gama gyaran nan dan nafison ta tare da wuri kasan eh..yane..eh" ya fad'a yana dariya tare da kanne ido daya.
"Kai kam Allah shiryamin kawai zance, yaro dakai sai jarabar tsiya" Hakeem ya fad'a yana hararansa tare da mik'ewa suka fice.
B'angaren Mami sai shirye-shirye take, kullum bata nan bata can anata hada-hada, ta kira ta gayama su Inna maganar tariyar haka Ard'o ma ta kirasa, saidai yace bazai samu zuwa ba, zaidai aiko da sak'o, har gidan Zainab ta kira kuma sun ce zasuzo ai an zama d'aya, wata 'yar sakkwato Mami ta d'auko take gyara Ramlah ciki da waje tasan yanayin d'an nata saida gyara.
Ita dai Ramlah batasan ma'anar gyaran ba, sai ta d'auka ko don tana da ciki ake mata gyaran, to amma saboda me bata da Amsa dole ta kama bakinta, itama Nihal da batasan wainar da ake toyawa ba danko labarin Cikin bata bale tasan na tariya data tambayi Ramlah cewa tayi itama bata sani ba wlh, bata hak'ura ba ta tambayi Mami, harara ta rakata da ita tace meye nata inta sani dole ta kama kanta.
Sai a bakin Hakeem takejin komai aiko jiki na rawa ta fesawa Sadee M bash, da sauran k'awayensu na jiki, nan suka had'u sukazo suka yima Ramlah caaa da masifa da tsiya irin ta 'yan mate, hadda fad'in ashe taje garin....shine bata gayamusu ba, to ta basu labarin ya abin yake..
Banza tayi dasu ita abinda ya dameta ya isheta ga Mami tace ta shirya k'arshen sati zata tare, tasan tata tazo k'arshe idan ta shiga hannun yayan nata, gashi ta daina ganinsa ya daina shiga sabgarta, alaman fushi yake da ita saboda yasan ya gama da ita shida laifi shida mata fushi.
************
Gidan Mami ya cika da jama'a da yake ita mutuniyar mutane ce, kamar wani biki ake ba tariya ba, Maman Zee ma ta iso da kanwarta Amal da yake itama tayi graduation itama tare dasu Ramlah, sun ji dad'in ganin junior Cikin kulawa kowa nan nan yake dashi musamman Ramlah Wanda hakan ke nuna musu baya cikin tsangwama, Inna 'yar tsohuwa ma sunzo ita da matar Uncle Mansur, sai tsiya takema ma Ramlah wai Amarya zata tare da d'an kunshi sudai kam anyi mara kunyan yara, Abdool ma tayi masa, amma shikam saidai ya bata amsa yace su ai 'yan zamani ne ba irinsu ba k'auyawa.
Ard'o ya aiko tsumi da sauran kayan gyaran amare yace zaizo daga baya in an kwana biyu yaga gidansu, ranar Asabar aka gudanar da walima anan gidan Mami inda su Nihal da M bash suka taka rawar gani, anyi rabon kayayyaki Wanda duk sune suka d'auki nauyin yi hadda Amal, Amarsu ansha kyau, gyara tasha har ta gaji, ansha Kitso da kunshi Wanda duk akan dole tayi su dan itakam a firgice take, lafewa kawai tayi tana yak'e, da daddare bayan tasha nasiha sosai daga iyayen nata, sai kuka take dak'ar aka rabasu da Junior ta dage tare zasuje saida Mami ta amsheshi Wanda shima sai kukan yake yana kiran "Maa" Inna, da Sauran k'awayen Mami ne matar Uncle Mansur sai su Nihal sukayi rakiyar amarya zuwa tamfatsetsen gidanta dake unguwar Dosa, fad'in kyawun gidan ma bannan lokaci ne, just guest friends. Lol.
Su Nihal sai zagawa gidan suke suna ta santinsa, daga nan suka tsere, dama su Inna sun dad'e da wucewa, Nihal tana tsoron yayan nata dan tun rana ya kirata yace ba wani siyan baki da za'ayi kada ta yadda ya samesu a gidan..
Ramlah sai shafawa tayi taji basu, zagaya gidan tayi, "mashaa Allah" kawai take fad'a da tsarin gidan yayi mata sosai kamar tsarin larabawa komai neat ba hayaniya da yawa ga furanni ta ko'ina sai K'amshi ke tashi gidan dai yayi ba k'arya.
Toilet ta zarce nan ma tasha kallo, kafin tayi wanka tare da d'auro alwala, shirinta tayi kamar yadda ta saba, sannan tabi lafiyar bed dama a gajiye take libis, bacci ne mai cike da dad'i ya d'auke ta.
Abdool ma daga bakin k'ofa ya dakatar da abokansa yace ba wani sayen baki da za'ayi kuma nasihar sun gode, nan suka kansa da zolaya da tsiya yace yadai ji.