Kenza eBookz

Abdulmajid complete - Chapter 18

Abdulmajid complete - Chapter 18

Abdulmajid complete Chapter 18: Abdulmajid complete Chapter 18. Alh Sada ma yazo yaga 'ya'yan nasa tare da basu kyauta mai tsoka, su Amal duk sun zo sai…

4,498 words

Alh Sada ma yazo yaga 'ya'yan nasa tare da basu kyauta mai tsoka, su Amal duk sun zo sai tarairayar yaran ake feeding kawai ke had'a su da Ramlah, Nihal, sadee, Amal kullum asibiti suke wuni sai dare ga kuma nurses masu kula dasu na musamman, ga uban gayyar shima yana kusa, satinsu d'aya aka sallamesu.

Abdool an gyara gida a tunanin sa can zasu wuce sai jin yayi Mami tace gidanta zasu nuna ba halin musawa duk da ransa baiso ba, dan har yanzu Mami bata huce dashi a ganin ai wauta ce ba rudu ba.

Nihal sai kullum suna gidan Mami sai dare Hakeem ke zuwa ya d'auketa da sassafe ya sauketa Sadee ma hakan ce, nan fa Ramlah ta samu bakinta sai tsiya take zuba musu don kowacce na d'auke da cikinta sai kwad'ayi suke zubawa Amal ma an kusa amarcewa.

Inna da Mami sun dage da gyaran Ramlah gyara na musamman irin na 'yan Sokoto Ard'o ma ya Aiko da sako, Abdool ko gida bayason komawa saboda gidan ba dad'i, yasan ko yace ya dawo Mami ba zata bari ba sai wani kaffa-kaffa take da Ramlah Sam bata barinsa zama gurinta.

Ranar suna anyi shagali wai barinyi shiru dai amma kuma dai kunsan ba dama Sa biyu da rago shida aka yanka, kaya kuwa kamar wani mahaukaci kowane jariri da nashi set, itama mai jego tasha kaya hadda kyautar mota k'arama irin ta mata k'irar Mercedes ash color.

Biki yayi biki can na hango 'yan *Abdulmajid fans* a gaban kasko my parrot an tattare zani ana gyaran hanji, mom zee sai k'ok'arin gyara wuta tace Aysha na zuba mai a kasko maman khady sai yankan nama ake ana aikawa baki anga banza ta fad'i, lubna ba sauk'i anata shan fanta, dear na Raheenat sai cin rengem ake ana korawa da coke su maman Nana, Aziza, zuzu, zee mai Kano, maryam cool sai hadije yawu ake anji hanji ya fara k'amshi, nace oh Abdulmajid fans kwad'ayi sun kama hanji sai aiki suke masa ba sassauta to kudai ragewa dotana kada Ku cinye gaba d'aya. Lol.

Yara sunci *Abdullah, Abdurrahman, Amatullah, Amaturrahman* Allah ya raya akan sunnah yasa mahaddata Qur'an ne.

Dangi kowa ya taka rawar gani yayi bajinta sun suna 'yan hud'u 'yan gatane gaba da baya, anyi suna lafia an watse lafia, Allah ya raya yaba mai jego lafiar shayarwa...........

*Remgem ren gemgem shinkafa da dad'i wlh tanada dad'i* 💃🏻💃🏻😋😜

💄Meryerm Abdool💄 [10/13, 9:20 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM* *#IG PML WRITERS* *#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035* *#http://maryamsbello.blogspot.com*

*_Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a garesa yana cewa "ba zaku shiga aljannah ba har sai kunyi imani, ba zakuyi imani ba harsai kunso junanku, in baku labarin ta yaya zakuso junanku? To Ku yad'a sallama a tsakaninku_*👌🏻

*_Assalamu Alaikum warahmatullah wa barakatuhu ya ihwatih fil Islam* 🙋🏾

📝 *Episode* 246--250

Abdool ya shiga busy saboda shirye-shiryen bud'e hospital nasa da sukeyi bai zaunu ba, wata rana ma through out day su Ramlah ba zasu ganshi ba saidai waya kawai, Mami kam ta dage da gyara 'yar tata,tuni na hau sheki fatarta tayi smooth tayi k'iba abinta, yan 4 sunyi bulbul dasu a dan Ramlah akwai kyawun Mama ga kuma sinadarai da madara da Abdool ya kawo musu wand'anda zasu k'ara musu lafia da kuzari, junior kullum yana mak'ale da Maa d'insa, Inna da Nany ne iyayen renon su Amatullah su Husna ma muddin suna gida suma suna tare dasu.

Bukin bud'e hospital aka gudanar Inda ya samu halartar mai girma governor na Kaduna State da k'ungiyar likitoci ta kaduna state misnistan lafia, asibitin ta samu karbesu gun k'usosin Gwannati, sannan ta cika duk wasu sharudda na asibiti mai zaman kanta, duba da yadda aka zuba kayan aiki na zamani wad'anda a yanzu ba'a cika samun a kowacce hospitals ba, an nashi number yabo tare da jinjina masa akan namijin k'ok'arin da yayi akan hospital d'in tare da jawabin yabo da mai girma governor yayi tare da Jan hankali up coming Dr dayin koyi da Matashin Dr Inda yace idan ana samun iri-irensu masu kishin k'asa to tabbas za'ayi nasara sosai a fannin lafia kuma za'a yak'i cututtuka da dama tun anan gida Nigeria basai an fita zuwa k'asashen wasu ba, haka dai kowa ya tofa albarkacin bakinsa tare da mik'a kambun girma ga iyayensa a matsayin su na wad'anda suka ginashi suka tallafa masa ta hanyar taimakonsa da bashi ilimi mai kyau har yakai wannan mataki, Aka kuma ja hankali iyaye akan suyi koyi da iyayen Dr Abdool su dage akan ilimin 'ya'yansu both islam and western dan shine kad'ai gatan da zakayi ma d'an ka a rayuwa saboda ilimi shine gishirin zaman duniya.

Mami dake gefe sai murmushi take tana jin dad'in ganin wannan rana da Allah ya nuna musu Abdool ya zama wani Abu a rayuwa har ana buga misali dashi wannan kad'ai ya isheta farinciki, Alhaji Sada hadda kwallarsa ta farinciki ina ma Auwal na kusa yaga wannan abin farinciki, Ramlah ma ji take kamar ta tashi sama dan farinciki tanaji tafi kowa sa'ar miji a rayuwa, ganin yan mata sai pics sukema Abdool yasa tasha kunu ta had'a rai ganin my parrot ta dage ta zak'alk'ale ita da my Aysha, Abdool kuwa idonsa na Kanta ganin yadda tasha kunu yasan labarin yasa sai jifarta da murmushi yake sannan yak'i kula kowa duk nacin Hafsi saida ta sarara masa, dan yak'i basu fuska, wow kawai 'yan matan gurin ke fad'i sunaji inama wannan young Dr mallakinsu ne.

Gurin dinner da akaje Ramlah na mak'ale Dr ko kunyar Mami bataji idonta ya rufe da kishi, sunkuyawa Abdool yayi Dai2 kunnenta "Haba baby irin wannan rikon ai sai ki kashemin kasuwa" harara ta watsa masa tare da kwab'e fuska tana d'an dukan k'irjinsa cike da tab'ara, nan fa masu camera suka shiga basu pics dan sun burge ba kad'an ba wasu sai fad'i suke "wow perfect match" tuni jikin wasu yayi sanyi ganin madarar k'auna a fili, Mami sai murmushi take tana k'ara godewa Allah, su sadee, Nihal duk ana gurin ana aikin na kwad'ayi. Lol

Taron yayi perfect anan aka bashi lasisi na tabbacin Asibitin sa ta samu k'arbuwa 100%, taro ya watse kowa na farinciki da murna, Abdulmajid fans baki kamar ya yage dan murna sun cika burgamensu da kayan mak'ulashe(oh wad'anda mutanen burinsu baza ta fad'i kawai subi takai) lol.

***************

Watan su Ramlah d'aya Abdool ya fara k'orafin su dawo, gaba Mami ta saka shi ta mishi tass tace suda komawa sai sun k'ara 2 months kuma da ta k'are wanka zasuje can kilgori suga halin da ake ciki dan baffa ne da kansa ya buk'aci haka, Ba yadda ya iya Ya hak'ura saidai idan Mami batanan yakan zagaya gurin Ramlah tayi masa 'yan dubaru dan tasan kalar mijin nata, duk iya nacin sa bata yadda anje can.....ba, kullum da rigima suke rabuwa dan idan ya aza mata daru ji take kamar ta bashi ta huta amma idan ta tuna da gargad'in Mami saita fasa, fushi yahau da ita ya daina kulata iyakarsa parlour idan yazo ya nan yake zama da yaran sa, haka yai fushin har ya gaji, lokacin ne tafiyarsu ta tashi gashi yayi dai2 da auren Amal kwanansu 3 a Sokoto suka sha biki sannan suka wuce kilgori...

*************

Tunda suka shigo cikin garin take binsa da kallo tsawon shekarun da ta d'auka bata ba a samu wani dogon canji a ciki ba kusan ma yananan yadda yake saidai abinda ba'a rasa ba, tsayuwar su k'ofar gidan ne ya k'ara tsananta bugun k'irjinta da Ard'o sukaci k'aro a k'ofar gidan, washe baki yayi yana musu sannan da isowa sannan yayi musu jagora zuwa ciki.

Gidan ma na nan yadda yake ba canji, k'ark'ashin bishiyar tsakar gidan ta hango Gwaggo Shatu tana yima wacce ke kwance jagab an lullub'e kusan rabin jikinta basa hango fuskarta, mahucin Shatu ta aje tare da tasowa tana musu sannu da zuwa fusksrta cike da tambaya dan itakam bata ganesu ba "sannu Gwaggo mun sameku lafia?" Ramlah tace, bud'e baki Shatu tayi tare da nunata da yatsa "Laure keta? Keta(kece) kika bacemin gaba dai ban ganeki ba" tace tana rungumeta "nice Gwaggo ya bayan rabuwa yasu Salmanu sun girma ko?" Tace suna k'arasawa gindin bishiyar da sauri Shatu ta d'auko sabuwar tabarma ta shimfid'a musu tare da kawo musu ruwan Randa masu sanyi "su Salmanu sun zama samari, wad'annan ne jikokin nawa?" Tace tana zama tare da k'ara gaisawa dasu Mami da inna da Nihal sai kuma nany, dake inna bata koma ba sai yanzu ta biyosu su daga nan su isa can.

Murmushi kawai Ramlah tayi, sai Mami ce ta amsa mata sannan tace "ya mai jikin ko tana ciki ne" dan Sam bata kula da ita ba.

"To alhmdllh ta samu sauk'i, ai gatanan ta samu yin bacci" tace tare da nuna musu ita, idon Ramlah ne ya sauka kan Iya Hari dake kwance kamar tsumma duk da dama can bamai jiki bace amma kam ta k'ara lalacewa ta yankwane ta tsofe sosai, nan take zuciyarta ta tsinke cikin sasarfa ta isa gareta tare da sakin kuka Mara sauti ta d'ora hannunta kan nata, rike hannun tayi gam tana fad'in "Laure ce dan Allah ku kawo min Laure mu gana"cikin muryan tsananin ciwo, cikin tausayawa tace "Iya nice...nice Laure iya" da sauri Iya Hari ta bud'e idonta tana son tashi amma ina ba dama.

Rik'e ta sosai tayi tare da gyara filo ta d'agota, still tana rik'e da hannunta gam "Laure kega yadda Allah ya hitar miki hakkinki gareni ko? Kega yadda nik koma ko?" Tace tana yaye zanin da ke rufe a jikinta, wani irin wari ne ya doki hancinta Ramlah ga k'afafun ba kyan gani duk sun kumbura ga tab'o a wasu guraren sai kuda ke bi.

Lokacin su Abdool suka shigo shida Ard'o da Hakeem " Laure banyi miki adalci ba keda uwayenki ban ba Modibbo hakkinsa ba na cutadda Asma'u sannan nabi ki da cuta kema gashi Allah ya nunamin iko nai...".

"Duniya kenan ka bita sannu ma ya kak k'are balle kayi garaje, kuma shi zakaran da Allah ya nuhwa da cara ko ana muzuru ko ana shaho sai yayi, wanga ya isheki darasi kisan duniya tafi bagaruwa iya jima" Ard'o ya fad'a hankali kwance.

"Wlh hakanan na Malam na yadda nabi Allah na kurena " Iya Hari tace tana kuka nan ta shiga basu labarin yadda ta cutar da Ramlah da iyayenta har zuwa zuwanta Inda boka da yadda ta had'u da Jauro ta k'ara sa "wlh sharrin shed'an na da son zucciya gashi sun kaini sun baro, Lanti da ni d'auka a matsayin d'iya gashi ta watsar dani bayan ada da ita mukayin komi ina ganin ita kanaso na bata tarbiya ta Ashe na dab'a ma cikina wuk'a na ban Sani ba gashi taje taba d'iyanta irin tarbiyar da nibbata, nidai kaico dani nayi hasara, dan Allah Laure ki taimaka ki yafemin ko zan samu sassauci daga ubangiji na" ta fad'a cikin matsanancin kuka mai ban tausayi.

Ko kai waye kaga Hari a wannan halin dole ka tausaya mata, duk ta k'ashe musu jiki, cikin sheshekar kuka Ramlah tace "ban tab'a rikeki a raina ba Iya, na yafemiki tuni, kullum babbar burina Allah yasa ki gane gaskiya, nagode wa Allah daya sa kika dawo hanya Allah ya yafe mana baki d'aya".

Cikin kuka ta shiga Neman gafarsu Inna duk sukace sun yafe sannan ta juya ga Ard'o " Hari kinyi abubuwa da dama saidai nikam ban tab'a rikeki a raina ba, kullum fatana ki gane gaskiya ko a haka aka tsaya nasan kega yadda duniya tace koda wannan azabar dake tare dake aka barki ga hasarar dukiya da kikayi Allah yasa wannan turbar shiriyarki"..

Sun jima suna jimamin abun, Abdool yana girmama abin wato ita duniya muddin kana cikinta zaka abubuwan mamaki, Al'ajabi, zalinci, cutarwa, cin amana da abun tausayi dana dariya, amma muddin bakabi hanyar koyar war Manzo S.A.W sai kayi dana sani a rayuwa, (Allah ka bamu ikon bin dai2 da aikata dai2).

Duba Hari yayi anan ya gane kafafun sun rub'e dole saidai a yankesu, nan suka k'ara shiga tashin Hankali, ana haka saiga Lanti ta shigo gidan tana ihu da kururuwa ta zube anan tana fad'a musu ga gawar Jauro nan da hinde an kawo wai ashe suna can tare birni suna bushasha da kud'in iya Hari da wad'anda Hinde ke karuwanci tana samowa shine sun samu matsala sun fito suna bala'i har bakin titi babbar mota ta kwashesu ba Wanda ya shura a cikin su.

Shine mijinta ya dankara mata kashi ya sakota saki uku yana fad'in ta cuceshi duk ita ta lalata masa d'iya, bud'ar bakin Ard'o sai cewa yayi "kega shuke- shuken ki ko Hari sai girba kikai da hannunki" fashe tayi da wani kuka mai cike da nadama, itama Lanti kukan take tana nadamar biyewa mahaifiyar tata musamman da taga yadda Allah yayi da Ramlah sai rok'on gafararta suke, tace ita bata rik'e kowa a rai ba.

Delu k'awar Ramlah tanajin labarin zuwan Ramlah tayi ma gidan Ard'o tsinke sai tayi da gaske sannan ta gane aminiyar tata "Laure keta kid dawo baturiya haka, ai in bisa hanya munka had'u aradu ban ganeki" delu ta fad'a tana zare ido.

"Kai Delu har yanzu kina nan baki canza ba ya bayan rabuwa" Nan suka shiga gaisawa da firar yaushe rabo, tana ta zuba mata godiya dan duk zuwan da Ard'o zaiyi sai bada tsaraba an kawo mata.

Anan suka kwana washe gari suka wuce Argungu Abdool yace su zama cikin shiri dan tare zasu koma ayima iya Hari Aiki dan kada k'afar ta janyo wata Marsala.......

💄Meryerm Abdool💄 [10/20, 4:55 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Real Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM* *#IG PML WRITERS* *#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035* *#http://maryamsbello.blogspot.com*

```An karb'o daga Baban Abdullah, Nu'umanu d'an Bashir (R.D) yace "naji Manzon Allah (S.A.W) yana cewa " hak'ik'a halal a bayyane take haka ma haram a bayyane take, saidai a tsakaninsu akwai wani al'amari mai rikitarwa Wanda kad'an daga cikin mutane suka sanshi, duk wanda ya kiyaye shubuha(rikitaccen al'amarin da ke tsakanin halal da Haram) hak'ik'a ya kiyaye addininsa da mutuncinsa, duk Wanda ya fad'a a shubuha hak'ik'a ya fad'a a haram, kamar makiyayi da yake ciwo a iyaka ya kusa ya ketare iyakarsa, Ku saurara! Kowane mai mulki yana da iyakarsa, Ku saurara! Iyakar Allah shine ababen da ya haramta, Ku saurara! A cikin jiki akwai wata tsoka idan ta gyaru dukkanin jiki ya gyaru, idan ta b'aci dukkanin jiki ya b'aci, Ku saurara! Itace ``` *zuciya*

_Bukhari da Muslim suka ruwaito shi(arba'una hadith)_

*ya Allah ka azurtamu da zuciyar musulunci* 👏🏽

📝 *Episode* 251-255

Ziyara sukayi sosai a Argungu, gidan k'awayen Mami dana Asma'u, b'angaren Inna duk sunje, da sukaje gidan Firdausi suka had'u da Ameena sai hirar tuna baya suke, gashi yau sune iyaye hadda jikoki rayuwa kenan, yau da gobe ta wuce wasa, kullum ganin Firdausi na tunawa Ameena da Auwal, gashi shiru har yanzu ba labari ko a raye ko a mace allahu a'alam, sunje har Besse daga nan suke wuce mungadi inda Sakina, tayi farincikin ganin su sosai itama ta tara nata iyali hadda jikoki, nan suka shiga tuna baya rayuwar C'O'E barkwancin Yusuf da irin yadda yake assisting nasu, ita tasan tayi rashi Mara adadi ta rasa Auwal a karon farko tazo ta rasa Asma'u da mijinta, sai uwa uba jigon rayuwar ta Yusuf yanzu kam mutuwar iyayenta da 'ya'yanta kad'ai ne zatace batasan d'acinsa ba amma ai taga mutuwa mai shiga rai (Allah yayima dukkanin musulmi rahama ya kyautata tamu bayan tasu)

Sunje birnin lafia gurin dangin Baba, cike da kayan tsaraba kamar yadda suka saba, sai kunya da nadamar abinda sukayiwa Abubakar sukeyi dan sun san kaf dangin yanzu da bazar Abubakar suke taka wa, shi d'in da suka wulakanta gashi ya zame musu haske a family, ya zamo zakaran gwajin dafi, shiyasa ba'a yiwa d'a da dukiya k'eta dan bakasan Wanda zai amfana dashi ba, d'ana kowane.

Tuni su Inna sun tare sabon gidansu dake Shagari Quarters, ganin zamani ne irin mai kyau d'in nan Sosai fa, Wanda Ameena, Asma'u, Mansur suka had'u suka Gina, abinda yasa nasaka Asma'u saboda gadonta hadda shi aka hada akayi ginin da sunan ta, Mansur ma yanzu harka ta bud'e dan ya samu aiki a Navy, so yanzu familyn Abubakar sunfi k'arfin a kirasu talakawa, hakan baisa musu girman kai ko k'yamatar talaka ba face wata hanya ta taimako data bud'e musu dan sun dage gurin taimaka yan uwa da gajiyayyu(abinda ya yakama ta ko wane mai hali yayi kenan ba gina manyan gidaje a koma Abuja a lafe ba, dan sadaka haske ce gobe k'iyama, Allah ka wada tamu da halal ka bamu ikon ciyar dashi ga bayinka dominka ya Allah).

************

Su iya Hari an isa Kaduna cikin yardar Allah, akayi mata aiki, dan Dr Abdool yana da k'wararrun likitoci da suka shafi kowanne b'angare ga ingantattun kayan aiki, cikin nasara aka yanke k'afafun tare da yi mata na roba, aikin da ya d'aukesu sati d'aya, anyi aiki successfully, Iya Hari sai kuka take tana nadama abinda ta shuka a rayuwar ta ga Ramlah data wulakanta ta d'oketa a banza ta zamo silar samun lafiyar ta duk da tasamu ciwon ne a gurin cutar da ita amma ta yafe mata har da kuma taimaka mata, lallai d'an hakin da ka rena shike tsole naka ido, kuma hak'uri jigon rayuwa ne, gashi Ramlah tayi hak'uri da cutarwar Iya Hari a gareta gashi Allah ya d'aukaka ya bata komai da ake nema a rayuwa saidai godiya da hamdala ga ubangiji kawai da Neman gafararsa.

Duk da yanayin da suka shigo garin na tsananin ciwon iya Hari hakan bai hana su bawa idanun su hakkinsa ba lallai garin dad'i na nesa haka kawai su Shatu ke fad'i a ransu basu k'ara tsurewa da lamarin ba saida suka isa gidan Mami k'amshin nan daddad'a da furannin ke fitarwa da iskar ni'ima dake gidan as usual, nan fa a shiga bawa ido abinci, suna girmama Allah, ashe Laure tana cikin aljannar duniya, da aka kawo musu better sukaci nan santi ya tashi Anji girki.

Da sukaje asibiti nan ma k'auyenci tsabage suka baje abinsu wai asibiti kaman gidan wani sarki ba doyi ba komai sai k'amshi da sanyin A.C dake kad'asu a haka sukata baje gidadan cinsu har akayi aikin aka kammala, bayan ta warware sosai aka shiga dasu zaga gari kusan tashi zaucewa sukayi hadda su Iya Hari sai wasar baki ake kamar gonar auduga, banki, hanci, ido sai kallo suke, wuni sukayi zungur sunje malls, da parks sosai sun cire kwarkwatar ido, anci ansha.

Adan watan da sukayi sun murmure sosai musamman Shatu tayi ja sosai tayi jiki Ashe duk wahala ce ta lalata ta, sosai suke kama da Ramlah d'an kammaninta d'aya da marigayi Abdulrahim, Iya Hari ma da Lanti sun murmure abinsu sunyi kumari da haske, saidai har yanzu sun k'asa sakewa dasu Mami suna ganin kamar suna kallonsu da cutarwar da sukayi wa Laure, duk da Mami na iya k'ok'arin ta gurin jansu a jiki, itama dai Ramlah kullum tana tare dasu, su kuma sun dage da renon su Amatullah.

Watansu Ramlah 2 amma har yanzu shiru Mami tak'i bashi matarsa tun yana ma Ramlah naci har ya gaji ya saka mata ido ga gidan a cike ba damar ya samu ya keb'e da ita, ko gidan yaje yace tazo ta kawo mai Abu a d'akin sa, cewa tace ai haihuwa d'aya horon abin..ba abinda zai kai k'afarta ya sakeyi mata wani cikin, shi dariya ma ta basa wato har yanzu akwai sauran k'uruciya tattare da Ramlah, wato ma a d'akin sa ne, takeyin cikin tun da anyi na farko.

Mami ya samu da maganar komawarsu Ramlah, b'ata rai tayi ta shiga balbale sa da fad'a tace ba zata koma ba sai yaran ta sunyi k'wari tukun, ganin ta ko'ina ba nasara yasa ya shirya nashi plan, Mami kuwa bayan tafiyarsa tace ma Ramlah ta fara shirye-shiryen komawa dam tasan halin d'an nata zai iya k'ara wata tabargazar dan idanunsa sun riga da sun soye tuni, yanzu Sam baya kunyarta Indai akan Ramlah ne.

Washe gari da wuri ya shigo a parlour ya samu su iya Hari suna ta faman kallo, gasu Abdool a hannunsu, gaisawa sukayi cikin sakin fuska, sannan yayi wa su Amatu wasa da sai b'angalar baki suke suna dariya Sam basu da matsala indai tumbinsu ya d'auka, junior rik'e a hannunsa yana masa surutun nasa daya iya, tambayan Mami yayi suka gayamasa tana ciki.

Mami na zaune gefen gado tana yiwa Ramlah bayanin kayan dake hannunta ita kuwa tana tsaye gun sif tana gyarawa Mami kayanta duk a kunyace take da bayanin da Mami ke mata, da eh kawai take binta shima can ciki ta maida hankalinta ga aikin da take.

Turo k'ofar yayi tare da sallama a bakinsa a tare suka amsa masa, zama yayi kan sofa yana gaida Mami, amsawa tayi tana tambayan sa aiki, gaidashi Ramlah tayi tana satar kallon sa dan ba k'aramin kyau yayi mata ba a Cikin k'ananan kayan da ya saka jean blue da shirt yellow mai dogon hannu an rubuta i'm d prince a gaban rigar da bakin penti sai zuba k'amshi yake.

Ko inda take bai kalla ba ya amsa gaisuwar tata ba yabo ba fallasa, shiru ne ya ratsa na d'an lokaci dan Mami ta aje kayan da takewa Ramlah bayani ta d'auko wata jarida tana dubawa, ita kuma Ramlah sai aikin gabanta take.

"Um Mami dama magana ce dani".

"ina jinka" tace a tak'aice ba tare data d'ago ba.

"Am dama Aure nakeso na k'ara am.." Sai yayi shiru.

Smiling tayi tare da kallon na d'an lokaci "to ai ba matsala sai kayi magana da Alhaji ko 'Yar inace yarinyar?" Ta fad'a cikin kwanciyar hankali, shiru yayi kansa k'asa "oh God I totally fail" ya fad'a a ransa, a fili kuwa yace "anan take Kaduna" a nashi tunanin idan yace haka Mami fad'a zatayi sannan ta bashi Ramlah cikin lokaci.

Ramlah Kuwa jinin jikinta ne ya daina aiki na d'an dak'ik'u, yadda maganar ta daki zuciyarta, k'arfin halin tattaro nutsuwarta tayi zuciyarta sai suya take tuni k'walla ya cika mata idanu, ji take kamar taje ta rungume shi tace ya fasa Neman auren su wuce gida Indai akan tak'i komawa ne.

"Ok ka samu Alhaji kuyi magana sai ayi bincike ko?" Mami ta katse musu tunani "tom" yace tare da mik'ewa yana kallon inda Ramlah take dan ya ga yanayin ta, ganin sai aikinta take kamar bataji me yace ba yasa jikinsa k'ara yin sanyi a sukwane ya fice.

"Ki kwantar da hankalinki kinji dota, ruba ce kawai yake ba wani Aure da zaiyi" sunne kai kawai Ramlah tayi tana murmushi, itama Mami murmushin tayi sannan ta fice zuwa parlour gurinsu iya Hari.

Bayanin komawar Ramlah tayi musu tace su shirya zasu rakata gidanta da anjima da dare, sannan ta basu labarin bazanar Abdool, cewa iya Hari tayi "kema dai Hajia ke rik'e mai mata da yawa ai dole yayi muku barazana kinsan yaran yanzu babu hank'uri" dariya sukayi gaba d'aya.

*************

8:00pm su Iya Hari suka kai Ramlah gidanta bayan Mami tasa an tsantsara mata Jan lalle da kitsonta mai kyau, ga gyaran jiki tasha sai shek'i take, susucewa su Shatu sukayi da ganin gidan Ramlah ashe na Mami nafila ne ga farilla anan, Dak'yar Mami ta tattarasu suka wuce sunata santin gidan.

Yara biyu Mami ta samo mata dan tayata renon yaran, nan suka shiga k'yalk'yale gidan da kimtsa sa, duk da dama a tsare yake dan Abdool akwai tsafta da k'amk'ami kullum cikin gyaran gidan yake, Nihal ma an kawo jiki dama tasan da dawowar dan tun rana Ramlah tayi mata waya dan kullum cikin damunta take yaushe zata dawo, zaman kad'aici ya isheta gashi Hakeem ya daina kaita gidan kullum yace bai son ana wahalar masa da baby da yawon hanya, abincin da ta shirya musu ta kawo musu nan ta bige da hira sai 9 ta koma kada Hakeem ya shigo bai sameta ba dan Ramlah tace kar ta gaya masa dawowarsu dan tasan tsaf zai iya tuntub'ar Abdool da maganar gashi surprise takeson bashi.

Sai 10:00pm ya shigo gidan dan a gajiye yake lilis yasha aiki, ko gidan Mami bai samu ya koma ba duba yaran sa, dan yanzu yayi giving up ya barsu in an gama ja masa rai ai ta dawo.

Tun a harabar gidan ya fara cin karo da daddad'an k'amshi, saida ya lumshe ido daya shiga parlour saboda yadda sanyin A'C ya had'e da wani tattausan k'amshi bai gama mamaki ba saida ya hango dinning d'auke da kulolin abinci aiko shawara bai tsaya ba ya haye ya kwashi gara, shi a tunanin sa Nihal ce da yake tana da spare ke na gidan kuma takan shigo tayi masa gyara girki kam kullum zata kawo mishi duk da kullum yake ci ba, wani sa'in da yaci a gidan Mami shikenan dan Sam bayacin abincin kasuwa k'yamarsa yake.

Saida yaji dai2 sannan ya wuce d'akin sa yayi wanka tare da shirya wa Cikin kayan baccinsa, parlour ya dawo dan rufe k'ofa, motsi ya ringa shi a part d'in Ramlah, rufo k'ofar yayi sannan ya nufi part d'in.

A parlour ya samu mai renon su Abdool tana bawa Amaturrahman madara, kallon mamaki ya bita dashi, ita kuma saurin sunkuyar da kanta tayi tana kwasar gaisuwa amsawa yayi tare da tambayan Mamansu bayan ya Amshi Amatu data koma bacci, "tana ciki" ta bashi amsa, wucewa yayi ita kuma ta wuce d'akin da aka keb'e musu.

Zaune take gefen gado tana feeding din Abdullah tasha kwalliya cikin wata fitinanniyar half sleepy gown Brown my santsi shara-shara sai k'amshi take zubawa, tsaye yayi ya jingina da k'ofar ya kafeta da kallon fitina.

D'ago wa tayi tare da sakar mai k'ayataccen smiling hadda kashe masa ido d'aya, da sassarfa ya isa gareta tare da kwantar Amatu gefe, matseta yayi yana hararanta matsa Maman yayi yana kallon ta " zaka sa ya kware ka tayar mana da rigima" tace Cikin slow voice nata.

Bai amsa mata ba sai d'aukesa da yayi daga kan cinyarta, ya aje shi gefe shima, sannan yayi mata mugun matsa har saida kashinta ya koka, d'an k'ara ta saki tana 'yarfe hannu tare da turo baki gaba.

Kama lip d'in yayi cike da zalama ya shiga totsar su da sauri-sauri da wasa da duga sassan jikinta cikin zafi-zafi, ganin abin nasa bana wasa bane yasa ta turesa tare da zame jikinta tana maida numfashi tare da nuna masa yaran dan har junior na kan gadon.

"Ina sauran?"ya fad'a cikin maye, idonsa sun canja launi, " suna gun masu renon su"

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull