Abdulmajid complete - Chapter 19
Abdulmajid complete Chapter 19: Abdulmajid complete Chapter 19. "Jeki dawo dasu nan" girgiza masa kai tayi alaman Aa sannan ta zura dogon hijab, ta d'auki…
4,500 words
"Jeki dawo dasu nan" girgiza masa kai tayi alaman Aa sannan ta zura dogon hijab, ta d'auki yaran biyu ta fita dasu yasan me take nufi a can zasu kwana kenan, d'aukar junior yayi ya bita dashi, dama basa kwanciya da junior saidai in sun kammala .....abinsu suke dawowa dashi tasan yau mijin nata sai abinda hali yai kawai dan tasan yau zataci kwakwarta, (hattara iyaye Ku kad'aice yaranku koda jarirai ne bai kamata Ku tara kuna tare dasu ba, don ko jin numfashinku a garesu bala'i ne, Allah ya shirya mana zuria ameen.)
Saida ta shafesu da Addu'a sannan ta kashe musu wuta tare da ja musu k'ofa, a bakin k'ofar taci Karo da gogon nata, suntumar ta yayi kamar wata baby, muna zuwa k'ofa ya ballamin harara tare da tura kyaurensa ya barni anan ina cizon yatsa naso na d'auko muku Rahoto amma yau Abdool yace nahi(Aa).
Nan na rab'a a k'ofar ina jiran tsammani, can har bacci ya fara d'auka ta naji sai ihu Abdool ke tsundumawa, a firgice na tashi nima zan zunduma da gudu, muryan Ramlah na jiyo sannu-sannu tana magana, hakan yasa na nutsu na baza kunnena dan naji me take fad'a da kyau.
"Kada kajimin ciwo mana Yaya Bini a hankali" tace cike da shagwab'a.
"Um..aaa.. Sorry baby na ai ke d'in CE.."
"Wayyo Yaya kada fa ka sakeyimin wani ciki"
"Aa...bazan yi miki ba baby...
" toya maganar aurenka?"
"Wane auren kuma...ni ai duk maza nake kallon mata...ash.. Baby ke kad'ai ce fa......wayyo baby ina zaki kaini...wayyo! Wayyo!! Wayyo!!"......
🤣🤣🤣🤣 dariya tasa na k'asa ci gaba da d'auko rahoto, kuma Ku dara amma kad'an fa🙄😝
💄Meryerm Abdool💄 [10/20, 5:13 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Real Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM* *#IG PML WRITERS* *#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035* *#http://maryamsbello.blogspot.com*
```An karb'o daga Abdullahi d'an Abbas (R'D) yace "Manzon Allah(S.W.A) yace " idan d'ayanku ya mutu aka samu mutune arba'in muminai wad'anda basuyi shirka da Allah ba suka sallacesa to ana mishi kyakyawan zaton samun rahamar ubangiji ```
Hakkun mubeen
*Alhaji Waiman (Mukhtar) Allah yayi maka rahama yakai haske k'abarinka yasa mutuwa ta zamo Hutu a gareka kai da dukannin wand'anda suka rigamu ya Allah ka kyautata tamu bayan tasu ameen👏🏽*
📝 *Episode* 256-260
A week suka d'auka ana soyewa, Abdool duk ya susuce ya zama jela wa Ramlah duk inda tayi yana manne da ita, sambatun yau daban na gobe daban, tun Hakeem na mishi mita har gaji ya kyalesa, ganin za'a damesa da kira a waya yasa ya kashe wayoyin gaba d'aya har na Ramlah, sauk'in su yaransu basu da fitina sam kullum suna gurin maid nasu feeding kawai ke had'asu da Maman su, shima junior yana gurin k'anninsa kullum yana musu wasa, hakan yasa suka tare part d'in Abdool suna cin karen su ba babbaka, madarar k'auna ta ganta a gurin Abdool wacce ba algus ko kad'an a ciki, riritawa da tattali shine suka shiga bawa juna.
Dak'yar ta samu ta korasa ya koma bakin aiki ganin har gida ake iskoshi amma sai yace shi Amarci yakeyi a barshi ya huta, hadda dan tumbin Hutu ya ije ga wani fresh da sukayi fresh milk tayi aiki. Lol.
Ranar da ta samu ya fita ta d'auka wayarta ta kunna nan fa messages sukayi ta shigo mata na wad'anda sukayi ta Neman basu samu ba, dariya tayi ta tace "duk rigimar Yaya ce ta b'oye ni" sannan ta danna number Sadee rings 2 ta daga tana fad'in.
"Kaga Uwargida a gidan Dr wato shikenan sai mukaji shiru an shige anyi luf sai karb'ar upper ake" ta fad'a cike da shakiyanci.
"Ke Yar duniya baki yimin shi shiyasa naga kinzo min keda baki k'arbar Upper"
"Hehehe! Rufemi ki saya so kike nazo Dr ya harareni yasa na haihu ban shirya ba, banni na lallab'a da Uncle luku na har ki sarara da karb'ar upper d'in"
"Wlh kedai Besty anyi shu'umar mace kin zugani kin koma gefe kina dariya wlh duk kin lalatamu nida sisto".
" wai 'Yar air kina chan kina shan dad'in ki, zakizo kimin burga, wai ya maganar amaryarki?"
Dariyar ta sheke da ita sanda tayi mai isarta tace "ai tun ranar da muka koma aka rufe wannan babin".
" kai besty kema fa silent killer ce a wannan fannin, anya ba so kike kifi malamar taki ba" tace tana dariya
"Cap aike besty k'arshe ce adaiyi shiru kawai, wai yaushe zaki b'ullo ne?"
"Hhhhhh! Kinsan ko akwai sababbin darasi kuyi ready keda Nihal ina nan b'ullowa Akwai chapter". " sadee fire sai kinzo muna tsumayenki, kink'i sarara wa Uncle duk da tutsetsen cikin ki"
"Kai ai ba daga k'afa......'" Hakan sukayi ta rahar su tsawon lokaci....
Watan su Iya Hari 2 a Kd sukayi shirin tafiya dan ta samu sauk'i sosai, kuma Ard'o ya matsa su koma hakanan yace dawainiyar tayi yawa, dan shi sati d'aya kawai yayi ya koma saboda jagoranci dake kansa, dan tsawon tafiyarsa 2-3 days ne, wannan Karon ne kawai yayi sati koshi dan ayi aikin yana nan ne kuma anayi ya juya ya koma yace yabar gari sakaka kar wani Abu ya faru kuma bashi nan(jagoranci Abu ne mai girma da nauyi Wanda ya zama dole ga shugaba ya kiyaye domin amanace a hannunsa wacce za'a tambayesa yanda ya gudanar da shi).
Tsaraba sosai suka sha daga gurin su ki da suka je ma Ramlah sallama itama ta had'a musu kaya sosai, ga ingantattun magunguna da Abdool ya d'ora iya Hari akai, kuka Iya Hari ta fashe dashi tana nadamar bakin halin ta na baya, da tana da damar gogesa a rayuwa data goge shi dan kullum ta tuni sai tayi kuka da nadama Mara adadi(ki godewa Allah ke kin gane gaskiya kin shiryu tun anan duniya, wasu kam sai Allah kawai, Allah ya shirya mu akan tafarkin gaskiya mu doge a kansa har abada).
**********
Rayuwa mai cike da k'auna ma'auratan ke gudanar wa, Abdulmajid hospital ta samu d'aukaka sosai saboda kyawun niyya dake kunshe a zuciyarsa, ga sauk'i da ake samu akan komai ba lalle sai mai kud'i ke zuwa ba, ta zamo kamar government hospital yanda yake taimaka talaka da marasa gata Addu'o'insu yasa hospital d'in ta samu karb'uwa a fad'in Kaduna da zagaye a yan watannin da tayi da bud'ewa kowa Abdulmajid hospital kakeji a bakin mutane suna yabawa da kod'awa..
Ramlah tuni tayi mai da zancen karatunsu ganin anaso a shantake, aiko cikin satin ya kawo musu form guda uku ita da Nihal da Sadee, mass com Ramlah ta cike dan har yanzu tana nan akan burinta na son zama journalist, Nihal ta cike nursing, Sadee kuma Pure Biology amma sai bayan su nihal sun haihu zasu fara zuwa, dake Nihal ta shiga month nata sadee kuma next month, hakan yasa Abdool ya dage da koyawa Ramlah motarta dan su samu ta zuwa school, aiko in 2 week hannunta ya fad'a dan Ramlah akwai sauk'in kai....
Nihal ta haihu successful ta samu d'a namiji chaii! Su Hakeem an zama Dady murna bata fad'uwa, anyi shagali still dai ba'a bar Abdulmajid fans ba sun zo sun kwashi banza kamar yadda suka saba, Ramlah da Abdool sun taka rawar gani sosai haka Sadee da Uncle lukman ma ba'a barsu a baya inda yaro yaci sunan Abban Nihal Yusuf suna kiransa da Aabid, Allah ya yara Aabid akan sunnah.
After month itama Sadee ta sunkuto tata 'yar mai sunan Maman Uncle lukman Salma(ihsan) still dai aminan junan sun taka rawar gani haka yan cin banza basu fasa zuwa as always, lol
Sunyi resuming school da motar Ramlah suke tafiya sai su biya su d'auki Sadee dake ita bakin hanya take, wani zubin kuma mazajensu ke kaisu saidai su had'u anan aka k'ara dink'ewa duk da kowacce faculty nasu daban hakan bazai hana idan basu da lec ba su had'u su sha chapter, dan har yanzu bakin bai mutu yana nan musamman Sadee, a gidan Mami suke barin yaran da Masu renonsu su Abdullah anyi girma sosai inka d'auka saika nisa har sun fara rarrafe ko'ina zuwa suke da rarrafe b'anna kuwa ko burgu ya sarara musu shiyasa Mami ke ce musu burguna...
Sam karatu bai hanasu bawa mazajensu kyakkyawar kulawar da ta dace ba, a cewar su karatu baya haka aure kamar yadda aure baya hana karatu saima k'ara samun experience a kowane b'angaren dan sosai majazen su ke assist nasu a kan karatun su......
**********
Wani sanyin ni'ima ne yaji yana ratsa shi lallai yayi missing k'asarsa ta haihuwa na tsawon lokaci, yaga canji sosai da ci gaba a garin, adaidaita ya tara tare da gayamasa inda zai kaishi, dake gurin sananne ne nan take mai adaidaita yace ya San gun, shiga sukayi shida matashiyar yarinyar da ke tare dashi wacce kallo d'aya zakayi mata ka gane tana da jinsi da larabawa.
A dai2 get d'in mai adaidaita ya aje su, biyanshi yayi sannan suka sauko, tsaye yayi a gun yana bin gidan da kallo duk da canje-canje da gidan ya samu hakan bai hanashi gane sa ba, itama yarinyar rakub'ewa tayi gefen sa tana kalle-kalle ta ganta a wata k'asa ta daban wacce take da matukar banbanci da k'asar ta tana rik'e da luggage nasu.
Daga can nesa na hango wani mutum a keken guragu yana tunkaro inda wannan mutumin yake tsaye cike da mamaki a fuskarsa,yana fad'in "Alhmdllh" sai sauri yake dan yaga mutumin na k'ok'arin shigewa gidan ...
"Malam dan Allah tsaya" Kalmar da ta doki kunnensa kenan, dan tabbatar da dashi ake ya juyo.
Tozali da mutumin da yafi tsana a rayuwa wanda yayi silar tafiyar farincikinsa ya dasa masa bak'in ciki a rayuwa ne yasa ya tunkaro gurin sa gadan gadan fuskar nan kamar ta zaki, itama yarinyar ganin meke faruwa ne yasa ta saki jakar tare da bin bayan mutumin tana fad'in "Abi" dayin wani yare Wanda na fahimci larabcine.
Ko saurarenta baiyi ba ya isa ga mutumin tare da cafkar wuyar sa yana huci baiyi duba da halin nakasa da yake ciki ba.
Wawuyar matsa yayi ma mutumin a wuya tuni idanunsa suka firfito waje sunyi jajir sai kakari yake "saina kasheka azzalumi macuci mai raba sunnar manzo" shine Kalmar da ke fitowa daga bakinsa, shikam sai mutsu-mutsun kwantar kansa yake amma ina ko gezau bai ba.
Kuka yarinyar ta fashe dashi tana Jan hannun mahaifin nata "Aa Abi kada ka illatashi meyayi maka Abi ka barshi" tace fad'a Cikin kuka.
Sakinsa yayi da k'arfi tare da tura sa baya, Allah ya soshi badan kukan 'yarsa da yake matukar so ba da ba zai bar wannan azzalumin ba sai ya illatashi koya kasheshi, mugun kallo kawai yake binsa dashi.
Gurgun sai Sosa wuyar sa yake dayaji shaka ajali dak'yar ya daga keken ya sake hawa yace "na cancanci koma meye daga gareka amma dan Allah ka d'aure ka saurareni" yace, still da kallon yake binsa ba tare daya ce uffan ba.
"Nasan na zalince Ku kuma na dad'e ina Neman inda zan ganka na nemi gafararka kona samu sauk'in wannan bala'i da nike ciki, ba kai kad'ai na jefa a irin wannan halin ba hasalima Sana'a tace in bata aure a biyani, kaima ba haka kawai nayi maka haka sakani akayi inyi..."katsesa yayi da cewa "gayamin wane marar imani ne ya sakaka yimin wannan danyen aiki?"
Zaiyi magana sai wata mota ta tsaya a gabansu da mamaki na cikin motar ya fito baki bud'e ya nuna shi da yatsa baki na rawa yace "Auwal!"......
_gatan da zakuyimin d'aya ne masoyana ku nema min gafarar ubangiji dani daku gaba d'aya ya yafe mana kurakurai mu dan rahamarsa👏🏽_
💄Meryerm Abdool💄 [10/20, 5:27 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Real Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM* *#IG PML WRITERS* *#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035* *#http://maryamsbello.blogspot.com*
```An karb'o daga ka'abi d'an Iyadi (R.D) yace" Manzon Allah (S.A.W) yace "kowace Al'umma tana da fitinar ta, fitinar al'umma shine dukiya```
Sahihuh(hakkun mubeen)
*ya Allah kada ka jarabcemu da dukiyar da zata zamo fitina a garemu* 👏🏽
😍 _kun nunan cewa ko bani media kunayi dani, kun nunan ni yar gata ce a gareku💕 Ku sani Meryerm Abdool ma tana sonku sosai iya wuya ana irin mugun taren nan har abada🤝 Hafsat mai Sharif, Raheenat Mahmoud, Maryam Y Zango #ILVYSM 4rm d higher rank of my ❤#_
📝 *Episode* 261--265
"Yaya Rabi'u" shima ya fad'a yana kallon sa, k'arasowa Rabi'u yayi "Auwal dama kana raye a duniyar nan ka gujemu? Haba Auwal wannan wane irin hukunci ne kayi mana akan laifin da bamu aikata ba, haba Auwal! Haba! Yanzu dai mu shiga ciki wad'annan fa?" Ya nuna gurgun da yarinyar.
"Mu shiga ciki Yaya zakuji bayanin komai" tura gurgun Rabi'u yayi suka shiga ciki, direct part d'in Alhaji suka nufa, yana zaune kamar kullum kan kujerarsa carbi a hannun sa yana ja, sallama Rabi'u yayi tare da shiga.
Kasa k'ara sa amsa sallamar Alhaji yayi tare da mik'ewa tsaye yana nuna Auwal da yatsa cikin inna inna yace "Au..Auwalu kaine ko dai gizau kakemin kamar yadda ka saba"
Gabansa Auwal ya isa tare da sakin kuka "nine dai Auwalun ka Baba, dan Allah Baba ka gafarceni nasan nayi ba dai2 ba dan Allah kayimin afuwa Baba" yace cikin kuka tare da kama k'afafunsa.
"Alamdulillahillazih bi ni'imatih tatimmus salihat" shine Kalmar da Alhaji Sada keta maimaita wa, d'ago shi yayi tare da rungume shi tsam wani sanyi da rahama ce ta ratsa su irin ta uba da d'a, Rabi'u dake gefe sai murmushi yake, shikam gurgun sai kwalla yake yana kaico da rayuwar sa duk shine silar nisantar su, yarinyar kuwa sai kallon tsohon take ba tambaya tasan shine kakanta.
"Rabi'u kaje kayi sanarwar metting na gaggawa yanzu" Alhaji Sada ya fad'a.
Hajia Kaltume ce ta fara isowa parlon suman tsaye tayi tare da zaro ido tana nuna Auwal ta k'asa magana, duk Wanda ya shigo indai yasan Auwal turus yakeyi dan sun dad'e da cire tsammanin sake ganinsa, Maryam ma suna gari sunzo hakan yasa itama ta halarci taron da nata iyalan, wad'anda basu sanshi ba sai a labari duk dai sun ganshi wasu sun ganesa wasu kan basu gane ba, Rafi'a ce ta shigo last dan bata gida tana gurin shashancinta saida Rabi'u ya matsa sannan tazo, ganin Auwal bai wani d'aga mata hankali ba, sai bayan ta zauna idonta suka sauka akan gurgun, ki tayi kamar ta saki fitsari a gurin tsabar tsoro zaro ido tayi tuni ta fara gumi duk da sanyin Ac dake parlon, Ji take kamar ta zura a guje saidai ba damar haka.
Bayan an nutsu kowa ya hallara Alhaji yasa aka bud'e taro da Addu'a, sannan ya fara jawabi kamar haka "kamar yadda muka sani munyi rashi na d'aya daga Cikin 'ya'yan gidan nan tsawon shekaru 29 da suka wuce, wasu daga cikinmu sun sanshi wasu kuma basu sanshi ba sai a labari Wanda har mun cire rai da ganinsa, to Alhamdulillah a yau Allah Cikin ikonsa da ganin damarsa ya dawo mana da Auwalu cikin mu, Alhamdulillah Allah mun gode maka da wannan ni'imar da kayi mana ba tare da k'arfi ko dabarar mu ba" nan hayaniya ta tashi kowa yana fad'in Kalmar nuna farincikinsa game da dawowar Auwal, saida aka gama aka sake nutsuwa Alhaji yaci gaba.
"Kuma kowa nada labarin abinda ya faru dalilin da yasa Auwal ya tafi ya barmu duk da agaremu bai isa dalili akan tafiyarsa ba to shima dai ya gane bai kyauta ba ya kuma nemi afuwa akan hakan munsan wannan bazai wuce sharrin zuciya da shed'an ba, to kuma duk a lokaci d'aya Allah ya kawo mana warwara a cikin wannan lamarin ga Wanda ya zamo silar sabani tsakanin Auwal da Ameena yana ikirari da bakinsa sharri yayi ma Ameena sannan yace saka shi akayi dan haka waka a bakin mai ita tafi dad'i sai a bashi dama yayi mana bayani"
Nan fa kallo ya koma ga wannan gurgun kowa na jiran jin mai zai fad'a.
"Nidai sunana Saminu amma anfi sanina da Shago kashe aure, na samo wannan suna ne a dalilin sana'ata ta kashe aure duk yanda Aure yake muddin akazo gurina akace ana buk'atar mutuwarsa to zan kashesa muddin zan samu kud'i wannan itace Sana'a ta, na kashe aure Wanda ni kaina bansan adadin auren da na kashe ba, a haka ne waccen ta sameni tace zanyi mata aiki" ya nuna Rafia tare da koro musu bayani yadda sukayi da ita da yadda suka tsara komai har zuwa abinda ta bashi.
"Kai munafuki yaushe na tab'a ganinka ni bamma tab'a saninka a rayuwa ba, ni zakayiwa sharri" tashi tayi tana bobbotai da borin kunya, ba Wanda yace uffan sai ido da aka zuba mata, murmushi yayi "dama nasan za'ayi haka shiyasa na tanaji irin wannan ga duk Wanda nayiwa aiki" nan take ya danna wata mp sai muryanta Radau da yadda suka shirya komai.
Tass...kakeji hajia Kaltume ta wanke mata fuska da mari masu kyau "amma dai ke anyi tsinanniya, munafuka yanzu duk yanda na d'auke ki Ashe ke kurace da fuskar akuya kika nasa aka saki 'yar mutane, kikayi silar tafiyar d'ana da nake matuk'ar so, er banza Allah ya isa tsakanina dake" hajia Kaltume tace cikin kuka.
"Aa Kaltume mi a laifin Rafia bayan ke kika bata k'ofa da baki nuna k'iyayyar ki ga Ameena ba ya za'ayi Rafia ta samu hanyar yi musu wannan ta'adi ba, duk da bamu San hujjarta nayin hakan ba" Alhaji Sada yace, sanyi jikin Hajia Kaltume yayi tabbas tayi kuskure a baya na nuna tsanarta a fili ga talaka, amma tuni ta gane gaskiya dan miyagun halayen da Rafia ta b'ullo dasu na rashin tarbiya da musgunawa kowa na gidan, saidai ta riga ta makaro dan Alhaji ya fita batunta akan maganar Abdool da mahaifiyar sa baya fad'a mata komai game dasu gashi ya hana Abdool zuwa gaba d'aya.
Rafia sai raba ido take tana kyarma nan Rabi'u ya daka mata tsawa "meye dalilinki na wannan badak'alar?"
Cikin inna-inna da tsananin tsoro ta shiga gaya musu akan tana son ya auri k'anwarta ne sannan ta tsani Ameena saboda yanda Auwal ke nuna mata k'auna.... Ai bata k'ara sa bayani ba sai saukar naushi taji a baki, tare da rufeta da duka duk jikinta, sai ihu take zundumawa "Auwallu me kakeyi haka ka dawo hankalinka fa tsaketa" Alhaji yace cikin daga murya, saketa Auwal yayi tare da kama gefe yana huci "Alhaji daka barshi ya illata annoba guba, kije na sakeki saki uku kuma Allah ya isa da cutar damu da kikayi" Rabi'u yace.
"Kayimin dai2 Rabi'u" hajia Kaltume tace, hannu Rafia ta aza a ka tare da fashewa da kuka hadda ihunta dan tasan karyar ta ta gama k'arewa "dalla Malama fice mana a gida ko yanzu in karyaki anan" Sani yace yana binta da mugun kallo, dakar taja kafarta dan ba k'aramin duka tasha a hannun Auwal ba ga bakin ta daya fasa mata sai jini yake, nan fa kowa ya hau murna sun rabu da wahala dan a gidan ta addabi kowa, kowa sai fad'ar albarkacin bakinsa yakeyi, shidai Alhaji sai kallon su yakeyi, shiru ya biyo baya "Rabi'u me yasa ka yanke irin wannan hukuncin da Allah bayaso kai tsaye?"
"Kayi hak'uri Alhaji dole ce tasa dan Rafia tana cutar damu matuka" nan ya shiga zayyana musu yadda take shan kwayoyin rashin haihuwa har zuwa da tayi aka cire mata mahaifa da yanda take bin wasu mazaje, ba Wanda yayi mamaki a ciki dan sun san zata aikata abinda yafi wannan ma, nan dai aka shiga jajantawa kowa da San barka na rabuwa da Annoba, musamman Amaryar Rabi'u tafi kowa farinciki na rabuwa da sukayi da Rafia dan tana cin azaba a hannun ta.
"Kai kuma kaje Allah ya shiryeka" Alhaji Sada yace da gurgun".
"Alhaji na gane kuskure tuni, Allah bai bani bashi ba ya halakar duk k'azamar dukiyar da na Tara, kuma ya jarabceni da rashin k'afafu shi kad'ai ya isheni ishara" sannan ya gungura kekensa ya fice yana godiya, shiru ne ya ratsa kafin Alhaji yace.
"Tau inaso mu duka mu d'auki wannan al'amari a matsayin jarabawa daga Allah, Auwal kai kuma ina ka shige wannan tsawon lokaci ba tare daka waiwayemu ba, wannan yarinyar kuma wacce ce ita?" Alhaji sada ya fad'a, hankalin kowa anan ya dawo suna sauraron suji daga gareshi.
"Ameena sunan ta amma muna kiranta da meenal 'yata wacce taci sunan Ameena, bayan nabar nan direct Abuja na nufa bayan na share sati ina tunanin wace k'asa zan dosa dan na nisanta kaina da Ameena, daka k'arshe na yanke shawarar zuwa saudiya, zamana Saudiya bani aikin yi daya wuce zama a masallaci kullum ina can bacci kawai ke maidani gida, ganin guzurin hannuna ya d'auki hanyar k'arewa yasa na tuntub'i mak'ocina inaso zan fara Sana'a hakan kuwa akayi ya je dani kasuwa ya d'orani akan Sana'a, tun zuwana garin da malam Ikbal kad'ai nayi sabo wato wannan mak'ocin nawa, suna da matuk'ar kirki kullum zasu kawomin abincin safe rana dare basu gajia, sun jani a jiki sosai duk da ban tab'a gaya musu komai game dani ba, suna da 'ya d'aya wato Ahlam sannu a hankali sha kuwa ta shiga tsakanin mu, har takanzo ta gyaramin gida idan munje kasuwa, tana zuwa ta tayani hira a idan naje gidansu kullum taga tana ganina da foton Ameena da Abdool Dana Alhaji da Momy har dai ranar ta nuna tanason taji tarihina irin shakuwar mu tasa na k'asa b'oye mata labari na, Ahlam ta girgiza dajin labarina har da kukanta ta tausayamin, kullum bata da magana saita Abdool da Ameena irin k'aunar da take nunawa ga iyalina ne yasa na k'ara ganin kimar ta a zuciyata" nisawa yayi sannan yaci gaba.
" a haka shekaru suka ja har Ahlam ta kammala karatunta iyayenta suka bijiro mata da maganar Aure, haka Ahlam ta had'a Kai da fata tace idan bani ba ba zata auri kowa ba, tsananin k'aunar da iyayenta ke mata yasa suka amince da ta aureni d'in, bawai dan sunaso ba dan kowa yasan larabawa da nuna banbancin launin fata da tak'ama da nasaba, nidai bansan abinda ake ciki, sai kirana malam Ikbal yayi ya gayamin yadda sukayi da Ahlam, nan na gaya masa komai game dani kamar yadda na gayama Ahlam Ashe itama ta gaya musu jin banyi musu k'arya ba, yasa shima ya bada goyon baya, wannan shine silar aure na da Ahlam mutuncinta da kirkinta da kuma nuna damuwarta akan dukkanin al'amari na ne ya janyo mata k'auna ta, a haka muka zauna tsawon shekara 4 sannan Ahlam ta samu juna biyu, na bata dukkanin kulawa har lokacin haihuwar ta, ta haifo Ameena itace ta zabawa Meenal sunan Ameena, Meenal Nada shekara biyu ciwo ya kama Ahlam Wanda yayi sanadin rasuwarta, tun Ahlam na raye tayi tayi dani mu zo Nigeria, har Cikin raina inason zuwa saidai ina fargabar zuwa in samu labarin Ameena ta auri wani kuma inga inda muka rayu da Ameena amma yanzu babu ita, kullum kuna a raina musamman Abdool da bansan wace rayuwa yake ba, saidai na kasa zuwa, a haka naci gaba da renon Meenal shakuwa ce mai girma a tsakanina da ita, nina reneta da hannuna dan duk yada kamannin ta sukazo ta dawo inda suke k'i tayi ko kasuwa da ita nake zuwa muddin taje gidan kakanninta to tare dani ne"
"Har zuwa yanzu da Meenal keda shekaru sha shida bata yadda da kowa ba saini, ina yawan bata labaru game da gida hakan yasa tasan labaru game daku, kuma na koyar da ita Hausa tana jin Hausa saidai hausar tata kamar ta k'abila take don bataji ga kowa sai guna, a wannan lokacin ne gida ya dawo min a rayuwa kullum cikin mafarkin Abdool Nike yana kirana hakan ya tayar min da hankali naji dole sai na dawo gida hakan yasa naje ma su malam Ikbal da maganar tafiya ta sukace ba damuwa amma zanbar Meenal anan dan tana cire musu kewar tilon 'yarsu, ba musu nace na amince amma Meenal tayi fir tace kafarta kafata, haka suka hak'ura ba yadda suka iya amma sunce zasuzo daga baya" kallon iyayensa yayi "ina Neman gafararku iyayena akan barinku da nayi don Allah Ku yafemin"
"Mun yafeka Auwal kaima ka yafemin da abinda nayi maka kai da Ameena akan wani dalili nawa Mara asali da tushe, na gane kuskure na Alhaji dan Allah ka yafemin na tuba nabi Allah"
"Alhamdulillah nagode Allah daya ganar dake gaskiya, Allah zaki roka afuwa akan karan tsaye da kikayi akan dokarsa kin manta cewa shi yayi talaka da mai azziki ba tare daya nemi shawarar su akan kasancewarsu haka, sannan ki nemi yafiyar Ameena da Abdool akan hakkinsu da kika tauye Allah ya yafe mana baki d'aya" Ameen kowa ya amsa, kiran Meenal Alhaji yayi ya sanya mata albarka haka Hajia, nan yan uwa da iyayenta kowa ya shiga nuna mata so da gabatar da kansa a gareta.
"Alhaji ina labarin Ameena da Abdool?" Auwal ya tambaya.
Nan akayi zaman sabon labari, "Allah sarki Ameena ta, Abdool dina ya zama babban mutum harda iyali har haka, Baba ya kamata muje Kaduna a yau inaso inga Ameena da Abdulmajid" itama Hajia yanzu ba wad'anda takeson gani kamar su, haka Meenal tana cike da burin ganin takwarar ta da kuma tilon yayan nata, Alhaji cewa yayi su bari zuwa gobe sai suyi sammako suma sun d'an huta.
Da muradin ganin Ameenarsa da Abdool d'in sa, yayi farincikin jin Ameena bata da Aure yanzu kila rabon su sake zama ne.
***********
02:00pm
A garin Kaduna tayi musu, kasancewar Weekend ne, duk suna gidan Mami, k'ofar gidan suka tsaya, Hajia sai mamaki take yanzu Gidan Ameena ne nan lallai duk abinda ya baka tausayi wata rana sai ya baka tsoro, mota had'u suka ciko, waya Alhaji ya zaro tare da kiran Abdool, ring 2 ya d'aga yana fad'in "tsoho mai ran k'arfe yau soyayyar ta motsa ne" cike da zolaya.
Dariya Alhaji yayi "kamar kana kusa ko Likkita bokan turai, shiyasa ma gani k'ofar gida kazo kamin iso" dariya Abdool yayi shima.
"Banda zolaya fa Alhaji" ba zolaya fito ka gani".
"Saidai fa gani gidan Mami" ai tazo da sauk'i dan nima nan nake nufi ba dajin Ku ba"
"Naji dai ganin nan zuwa " kowa k'ofa ya zubawa ido don ganin fitowar Abdool da yake a hands free Alhaji saka wayar.
Auwal yafi kowa zakuwa son ganin gudan jinin nasa.
Fitowa yayi cikin tafiyar nan tasa ta mai nutsuwa, turus ya tsaya yana bin motocin dake gurin da kallon mamaki dan a zatonsa Alhaji kawai ne............
💄Meryerm Abdool💄 [10/23, 9:23 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Real Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM* *#IG PML WRITERS* *#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035* *#http://maryamsbello.blogspot.com*