Abdulmajid complete - Chapter 8
Abdulmajid complete Chapter 8: Abdulmajid complete Chapter 8. B'angaren su Hajia kaltume kuwa tun suna saka ran dawowar Auwal shiru shekaru sun tafi ba…
4,404 words
B'angaren su Hajia kaltume kuwa tun suna saka ran dawowar Auwal shiru shekaru sun tafi ba labari hakan yasa suka fitar da rai, har anyi Auren Maryam da wani Dr, inda suka wuce Germany an turashi course, Ayuba ma ya k'ara Aure, yayi yayi da Rafia suje hospital amma tak'i tana tsoron tonon silili, Hajia kin amince tayi da Auren saboda kar abatama 'yar gaban goshinta, saida ya nace sannan ta yadda dan itama rashin haihuwa na damunta, saidai duk da haka Rafia CE ke mulkinta a gidan sai abinda tace.
_wannan kenan_
***************
Kawunnan Alhaji Abubakar sukazo daga k'auye sukayi masa tas wai ya maida d'iyansa d'iyan yahudawa, ita waccen saboda ta isa da Kanta tabi namiji ta barsu cewa da Asma'u (baki ke yanka wuya shiya kira ya fad'a musu) sannan ita kuma wanga shekararta nawa da rabuwa da mijinta ance karatu to ai tw gama, zaman me take idan ba tana bin maza ba, taya za'ace bata damu ba, cin mutunci dai inda Suke shiga banan Suke fita ba, kalamansu sun mugun b'ata ransa, amma ba yanda zaiyi iyayensa ne.
Bayan tafiyar su ya kira Ameena yace mata tayi k'ok'ari ta fitar da miji cikin masu sonta tayi Aure, amma cikin sanyi yayi Mata maganan dan shima tausayi take bashi, itakam ya zatayi bayan bamai zuwa inda take, da za'a bud'e ranta tafi son tayi Auren nan kota huta da surutun mutane, amma ya zatayi.
Cikin satin Alhaji Sada yazo dubasu shima dai maganar d'aya ce ta daure ta manta baya tayi Aure.
Kwance take kan gado tunanin abin duniya ya isheta, tana matuk'ar son aure dan itama ai rayuwa ce kuma matashiya mai cikakikiyar lafia, saidai tasan komai yanada lokaci da lokaci yayi ba makawa zatayi shi, tana rokon Allah, kuma tana da tabbacin zai ansa mata, ringing din wayarta ne ya dawo da ita daga duniyar tunani.
Sunan Yusuf ne ya bayyana kan screen sauke numfashi tayi sannan ta d'auka, bayan sun gaisa ya tambaya Abdool daya dad'e dayin bacci yake CE mata.
"Ameena wai yaushe ne zamuzo Argungu musha biki?"
A bazata taji tambayan shima kenan ya k'osa tayi Aure? Murmushin dole ta k'irk'iro "Umm Yusuf bada dad'ewa ba inshaa Allah"
Jin sukayi gaba d'aya kowa na sak'a Abu a ransa, shikam yau ya shirya fallasa sirrin ransa gareta kota amince ko tak'i, gyaran murya yayi "Ameena" ya kirata cikin wata irin murya "Na'am".
"Inaso kiyima magana ta kyakkyawar fahimta ki d'ora a mizani mai kyau," sannan yaja hanci "maganan gaskiya Ameena I'm deeply in love with u".
" what " shine abinda ta fad'a cikin firgice, tare da katse kiran.
Kanta ta dafe "lahaulah walakuwwati, meke shirin faruwa ne, kai never yaudara kawai zaiyi...." Karan shigowa message taji, bud'ewa tayi.
_"everyone is a someone dream, and ur a my dream, pls don close ur heart to d one that is in need of u, never say goodbye 2 ur lover accept it as destiny, as I said I really love u with one heart, don't let me go astray..!"_
Tana gama karantawa kiran sa na shigowa d'auka tayi ba tare da tayi magana ba "Haba Ameena ki yadda dani da soyayya ta nayi miki alkawarin bazan cutar da ke, zan rikeki Amana da zuciya d'aya pls Ameena ki yadda dani".
" taya Yusuf taya zakace ni, koma manta nifa bazawara ce, bazawarar ma mai d'a, kaifa saurayin da bai tab'a Aure ba, to taya hakan zata kasance?"
"Haba Ameena kada ki canja daga yadda ba sanki mana, nasan ke mai ilimi CE, fiyayyen halitta da wace Mata ya fara? Nina ganki a yadda kike nace ina sonki, saidai idan sonane bakyayi daban ne, amma kima var wancen maganar.
K'aryane ne tace batason Yusuf domin ya had'a komai daya cancanci aso namiji domin shi, to amma ya fa?.
" Koda zan amince mata saika je kayi magana da iyayenka idan sun amince maka, sannan zan amince ".
"Shikenan Ameena inshaa Allah, zanyi yadda kikeso, ki shafan kan Abdool, saida safe".
Wayar tabi da kallo, ita haka take ganin abun kamar almara, mik'ewa tayi ta d'auro alwala tahau dadduma tayi raka'a 2, sannan ta fara Addu'ar istikhara(Neman zabin Allah) kamar haka:-
_Allahumma inni astahiruka bi ilmika, wa'astagfiruka bik'udratika, wa'as'aluka min fadlikal azim, fa'innaka tak'dir wala ak'dir, wata'alam wala a'alam, wa anta allamul guyuwbu, in kunta ta'alamu anna hazal amru(saika fad'i buk'atar ka) khairun liy fiy deeniy wama'ashi wa'akibatu amri, fak'durhu liy wayassirhu liy summa barak liy fiyhi, wa'in kunta ta'alamu Anna hazal amru sharrun liy fih deeniy wama'ashi wa'ak'ibati amri, fasrifhu anni wasrifni anhu wak'dul liy khairan haisu kana summa raddani bihi._
Fassara
*ya Allah ina Neman zabinka domin iliminka, kuma ina Neman ka bani iko domin ikonka, kuma ina rok'onka daga falalarka mai girma, domin Kaine mai iko ni kuma bani da ikon, kuma kaine masani ni kuma bani da sani, kuma Kaine masanin abubuwan fake, Ya Allah! Idan kasan cewa wannan al'amari (ka ambaci buk'atar) Alkhairi ne a gareni cikin addinina da rayuwata da k'arshen al'amarina (wata rayuwar ) da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa, ka k'addara mini shi, kuma ka sauk'ak'e mini shi, sannan ka Albarka ce ni a cikinsa, kuma idan kasan wannan al'amari sharri ne, gareni a cikin, addinina da rayuwa da k'arshen al'amarina (a wata rayuwar) da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa, ka kawar da shi daga gareni, kuma ka kawar dani daga gareshi, ka k'addara mini Alkhairi a duk inda yake, ka kuma sani in yarda dashi*
(Cikin husnul Muslim take, yana da kyau komai bawa zai gabatar a rayuwa ya nemi zabin Allah a ciki. Allah yasa mudace)
Bayan ta kammala ta nad'e dadduma tare da kwantawa kan bed, tana tunanin wannan al'amarin,sannu a hankali natsuwa ta fara shigarta, a haka bacci mai dad'i yayi gaba da ita.................
_masoyana ina Neman addu'o'inku, I really in need of it👏🏽 ina muku fatar Alkhairi a duk inda kuke_
💄 Meryerm Abdool💄 [8/12, 6:07 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
🙏🏻 *From he we are, and 2 he we return, oh! Allah forgive our dead one, that find their self in absence of no one to pray 4 them, ya Allah have mercy on them, and make our dead day the day of happiness 2 us, ya Allah don't take our souls until urs happy with our souls ameen🙏🏻*
📝 *Episode* 126--130
Koda Yusuf ya jema iyayensa bai samu matsala da yake yayi dace da iyaye masu hangen nesa, sunce tunda shi yake sonta in har anyi bincike 'yar kirki ce to su basu da matsala, amma 'yan uwansa sunce sudai basu amince ya auri bazawara ba yana saurayi dashi, saida Baban yayi musu fad'a yace "meye naku a ciki tunda a hakan yakeson abarsa, kuma ma in banda abinku, fiyayyen halitta ma da bazawara ya fara, to meye dan yace zaiyi koyi dashi idan har ba zaku bashi k'warin gwuiwa ba bai kamata Ku hanashi dan haka kar in sake jin wani daga cikinku ya soki wannan tafiyar" da haka Baban ya kwabesu dole suka hak'ura badan ransu yaso ba.
Koda ya fad'ama Ameena tayi farinciki sosai a ranta amma bata wani nuna mishi cewa kawai tayi "to yayi" sauke numfashi yayi "Haka kawai zakice Ameena tah, kamar bakya farinciki".
" um inayi mana tome kakeso ince ne".
Smiling yayi kamar tana kallon sa harda lumshe ido " cewa ya kamata kiyi yaushe zaka turo my love".
Dariya zancensa ya bata dama tasan Yusuf da barkwanci kamar me "au dariya KO, ai gara ma ki gayama Baba dan kada ayi mai ba zata, dan bazan tsaya kallon ruwa ba kwado yazo yamin kafa" nan ma murmushi kawai tayi dama Ameena ba yawan surutu...
"Um nidai bana Abdool dan naga yau miskilancin ya motsa" nan ta ba Abdool sukayi ta fira kamar wani babba dama Abdool badai wayau ba, in yayi wata magana ka d'auka fad'a mishi akayi.
Malam Sa'id mahafin Yusuf yayi duk binciken da ya dace ya kuma tabbatar da Tarbiyar Ameena, hakan yasa ya gaya ma 'yan uwansa domin Suje su nema nasa auren.
Lokacin da Ameena taje ma su Baba da labarin sunyi farinciki Sosai dama babban burinsu kenan Ameena tayi aure, shima yayi nashi bincike kamar yadda addini ya tsara, hakan yasa saka shiga cikin maganar har an tsaida rana wata uku masu zuwa.
Suma su Yusuf ba wasu masu arziki bane akwai dai rufin asiri, nan family house d'insu, aka gyara wasu dak'una biyu aka maida mata room and parlour sai toilet, ba laifi zaman dai mutum d'aya a talauce ba sarauce ba.
Alhaji Sada ma da yaji maganan Auren yayi mata murna Sosai, kuma yace ko bayan tayi Aure Abdool zaici gaba da zama gurin su Mama, dan yasha alwashin saidai in Abdool ya girma yakai Kansa Sokoto da kansa tunda dai sun nuna basa ra'ayinsa har gara iyayensa maza suna zuwa dubashi sa'in sai kuma Maryam kafin tayi aure duk da Hajia ta hanata zuwa hakan bai hana in Alhaji zaije ba, ta bishi wani sa'in kuma ta bada Abubuwa akai masa.
Cikin ikon Allah Anyi Aure lafia cikin farinciki ranar Ameena tasha kukan rabuwa da iyayenta uwa uba kuma Abdool shima dai yasha naji kukan dakyar aka banbareshi jikinta, a son Yusuf ma yaso abasu shi amma Baba yace Aa a barshi nan yayi karatunsa lokacin yana 6years yana primary 1, haka dai Ameena ta tare cikin aminci a gidan Angonta Yusuf.
Farkon Auren ta had'u da kalubalen dangin miji haka zasuzo suna yad'a mata magana, da yake macece mai matuk'ar hak'uri hakan yasa sam bata nuna tamasan sunayi, Amma kam surukarta suna zaune lafia, yawan kyautata Mata da dawainiya da take Mata, haka zata saka Yusuf ya d'auko kayansu ita da Abbansa su had'u su wanke su goge, komai ta dafa da nasu, suma 'yan uwan nasa da yake yayin nashi Mata ne duka suna gidan mazajensu sai dai in sunzo, shine namiji babba sai k'annin sa, hakan yasa in sukazo tana yawan kyautata musu gada Sam batada rowa ko kyashi tuni suma ta saye zukatansu(dangin miji saida kyautata ake zama lafia note women).
Taci gaba da teaching d'inta dan an samo mata transfer haka tana business d'inta, shima dai Yusuf teaching yake yana kuma zama kasuwa inda mahaifinsa da haka suka rufama junansu asiri Sam bakajin Kansu, zaman k'auna da soyayya suke dan sai yanzu tasan lallai Yusuf son gaskiya yake mata, kullum cikin tattali da nuna mata k'auna yake, Sakina ma anzo bikin tayi murna sosai dama ta dad'e tana hango son Ameena a idon Yusuf.
Tana zuwa Argungu lokaci zuwa lokaci har yanzu dai ba labarin Asma'u abin kullum yana ranta "oh ina zamu ganki Asma'u, Allah ka bayyana mana ita ka tsareta a duk inda take" kullum shine Addu'arta, Abdool na zuwa mata idan anyi Hutu.
Shekararsu 2 da Aure Yusuf ya samu Aiki a NNPC KADUNA, ba k'aramin farinciki sukayi da cigaban da ya samesu ba, haka yaje yayi interview aka bashi upper, watansa uku sannan ya dawo, nan ya gayama iyayensa zai wuce da Ameena dan an bashi gida, nan sukaje Argungu sukayi musu sallama, nan ma Yusuf saida ya tada maganar son abasu Abdool, hak'uri Abba ya basu yace kada su katse mai karatu, hakan suka wuce badan ransu yaso ba, irin kulawarda Yusuf ke bama Abdool shiyasa Ameena k'ara sonsa da ganin girmansa, haka sukayi bankwana da yan uwa da abokan arziki suka lula garin gwamna...
_safe trip_ 🚗
~~~~~~~~~~~~
Lokacin da labarin Auren Abdulrahim ya bazu a k'auye Kilgore mutane sai tururuwa sukeyi gidan dan ganin amarya da 'yan gulma da 'yan ganin kwam, da masu yabawa da masu tsinewa, su Lanti anzo sai yatsine take dan Uwar ta kitsa mata tana yad'a bak'ak'en maganganu, Abdulrahim ko dayaji tass yayi Mata sannan yace karta k'ara zuwa gidan muddin ba abin kirki zai kawo ba, aiko iya Hari ina wuta in fad'a inda take shiga banan take fita ba, cin mutunci gaske tayi masa, wai karya kuskura ya takurawa 'yarta akan wannan korarriyar wanda iyayenta suka sallama, cin fuska dai sai Wanda ta manta, ranar Asma'u tasha kuka tare da kewar gidansu lallai kowa yabar gida ya barshi, gata ana mata gori ba yadda zatayi, hakan ya k'ara ba Lanti kwarin gwiwar yi Mata iskanci son ranta, saidai batayi in Abdulrahim nanan dan tana shakkarsa, Saude kam haukane kawai batayi ba, da taji Auren Abdulrahim haka tazo har gida tayima iya Hari rashin kunya, wai ai ita tayi mata alk'awari amma tsabar munafurci ta bari ya auri wata ba ita ba, itako Sam bataga laifinta ba saima hak'uri ta bata akan lallai zai aureta ta shigo ta biyo, tace Allah ya kiyaye ta zama ta biyu ta d'auki sauran wata, ta yafe, dama ba sonsa take ba sha'awa ce kawai.
Kamar yadda Ard'o yace haka kuwa akayi an Gina mata ciki da falo hadda bayan gida. Lol
Shanu biyu Ard'o ya Ware yayi Mata kayan d'aki a matsayin sa na uba gareta, an gyara d'aki ba laifi, nan kuma wani gorin ya tashi habaici kam tasha harta gode Allah, zuwa yanzu ta fara sabawa da cin mutuncin Iya Hari da Lanti, amma kullum abin na kona ranta bata dai yadda zatayi ne, ga uban aiki gidan da yanzu ya dawo Kanta, komai ita danma Shatu na kamata inba idon Iya Hari, dan tuni tayi Mata iyaka da Asma'u, in kaga Asma'u saika tausaya mata duk tayi baki ta rame danma ta Saba da aiki a gida da sai tafi wahala, Abdulrahim baida halin magana a balbaleshi da bala'i itama Asma'u tace ya dena magana kada ya had'u da fushin mahaifiyarsa tunda ita ta haifeshi ya zama wajibi yayi mata biyayya, Ard'o ma yayi fad'a harya gajia amma a banza da maganan sa da babu duk d'aya suka ha Hari, saidai in ya samu tanayi yace ta aje inya fita ace tazo tayi dan ubanta (oh Asma'u kina ganin rayuwa).
Sauk'inta Mijinta na tausasa mata da nuna mata k'auna, inta zauna sai taita tunani "wato mu haka tamu k'addarar take an jarabcemu da uwar miji, haka aunty Ameena tayi fama, ashe nata nafila ne, gwanda ita ina kusa kuma zata kira gida taji dad'i to nifa ba ko d'aya, yanzu ko sakina akayi INA zan nufa, ya Allah ka sassauto da zuciyar Baba yafemin ya mai domin da family i'm in need of them badly".
Ana hakane akayi posting nasu gurin service ita da Abdulrahim, ba state d'aya aka ajesu ba shi Katsina ita kuma Edo, hakan yasa yaje ya nemi alfarma aka maida ita Katsina, nan ma anyi rigima da Iya Hari wai ba inda zataje, k'aryane meyakai mace bautar k'asa, nan ma saida Ard'o yayi da gaske sannan ta Shafa musu lafia, zaman su Katsina zamane mai dimbin tarihi a cikin rayuwar Auren su dan sai a sannan ne suka samu nutsuwa, dama Dr gida ake bashi, so basuda matsala haka suka gudanar da service d'insu cikin kwanciyar hankali, ko marmarin dawowa basuyi,ranar da suka isa Abdulrahim ya sayomata waya nan ta kira numbobin gidansu amma ba wacce ke nan jikinta ya k'ara sanyi da d'auka kodan karta kirane yasa Baba sasu canja layuka(ba haka bane baraye suka kwase musu wayoyi dare d'aya) lokacin da suka gama zasu dawo kamar karsu dawo sukeji, haka sukayo tsaraba sosai suka dawo amma kam Asma'u ranta fal tsoro za'a koma 'yar gidan jiya.
Hakan ko takasance bayan dawowar su akaci gaba daga inda aka tsaya wannan karon hadda gorin rashin haihuwa ganin suna cikin shekara ta uku da Aure ba haihuwa, Abu dai kullum ba sauk'i sai abinda yayi gaba, gashi anyi Auren Shatu mai tausaya mata.
Cikin ikon Allah Abdulrahim ya samu aiki a uduth Sokoto hakan yasa Ard'o yace ya d'auki matarsa su koma can da zama, Iya Hari cewa tayi bak'in ciki ake mata tunda tana taya ta aiki, banza yayi da ita danya San Neman a tanka ne.
Haka suka tattara suka koma Sokoto, kuma Ard'o yayi Iya kashedin duk ta taka Sokoto bakin Aurenta, dole ta lahe dan tasan rabuwa da Ard'o babbar asarace gareta.
Suna shekara cikin ta 5 da Aure Asma'u ta samo ciki, fad'ar irin farinciki da sukayi ba'a ma magana, haka sukaci gaba da kula da cikinsu cikin so da k'auna har ya isa haihuwa inda Abdulrahim da Kansa ya anshi haihuwar zankad'ed'iyar 'yarsa me kama dashi, baki kamar gonar auduga, su Modibbo anyi 'ya, Ard'o yaje yazo dasu da sunan ayi mata wankan jego tunda haihuwar fari CE batasan makari ba, Amma abin takaici ko kallo basu ishi Iya Hari ba, anyi ba'ayi ba dai kenan dan komai Asma'u ce kema Kanta, da bata iya ba saidai ta rub'e anan, tayi kukan rashin 'yan uwanta harta gode Allah, lallai naka sai naka, da sunanan da bata wulak'anta ba, Abdulrahim ne ke kama Mata aiki sai kuwa Shatu idan tazo shima idon uwarta kamar ya tsiyaye gurin harara, Abdulrahim ko saidai tace shanyayye Mara tayi.
Haka sati ya zagayo ranar suna yarinya taci suna *Ramlah* rago biyu da sa aka yanka, Abdulrahim yayi k'ok'ari dan yayi musu komai na goyo tsadaddi Hari ko sai yad'a magana anyi Aure ba dangi haka suna ma, Abu sai kace mayya, ita Kanta Asma'u abun na matuk'ar damunta, dan Abdulrahim yasha cewa ta bari suje Argungu suba Baba hak'uri, sanin halin mahaifinta na kaifi yasa tace cewa Aa su jira dai(tab aiya canja duniya ta horashi) lol.
Tun kan suyi arba'in ganin wahala tayi ma Asma'u yawa, balle Abdulrahim ya kawo sai k'arshen sati yake zuwa yasa, ga dawainiyar kula da kai da jaririya gana gida yasa Ard'o yace ya d'auketa su wuce kawai, duk k'arshen sati Abdulrahim na zuwa duba iyayensa, idan Asma'u bata zo ya zama abun zagi idan taho ma aci Mata mutunci.
Abdulrahim arziki sai bud'ewa yake tana ganin haske saboda biyayyar iyaye da yake, ga kulawa da iyalinsa da yakeyi, har Saudiya ya biyama Ard'o da Iya Hari, amma Iya cewa tayi ya bata kud'in kawai (hasararriya Mara rabo) Ard'o kam ya k'ara tsorata da lamarin Hari, haka ta kashe su a banza.
~~~~~~~~~~
B'angaren Ameena da Yusuf kuma zaman su lafia lau gwanin sha'awa, kowa na kaffa,-kaffa da d'an uwansa, tare suka kowa makaranta inda take karantar Botany (ilimin tsirrai) sam rashin haihuwar bai tab'a dagama Yusuf hankali ba, shine ma mai kwantar Mata da hankali, idan tana nuna damuwarta, yace "haihuwa ta Allah ce idan sunada rabo zasu samu idan babu Abdool ya ishesu".
Suna shekara 4 da aure ta samu ciki, murna sosai sukayi da kyautar da Allah yayi musu, wata tara cip ta sunbulo 'yarta mai kama da Yusuf sak, a Besse suka koma akayi suna inda yarinya taci sunan mamar Yusuf Aisha suna kiranta Nihal, mutane Argungu anzo an kwashi shoki!
Musamman Abdool daya zama dan samari sai murna yaks yayi k'anwa.........
*lol every body a kame kam sabuwar rawa 🕴🏾🕴🏾🕴🏾🕴🏾*
_kuyi hak'uri Dani friends abubuwan ne da yawa #one love# 😍_
💄Meryerm Abdool💄
👌🏻😉 [8/16, 8:27 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
```Manzon Allah (S.A.W) yace ma wani yaro:- kayi bismillah(idan zakaci abinci) kaci da hanun damanka, kaci daga abinda ke gabanka.```
_Ladubba ne nacin abinci mu kiyaye sannan mu koyar da yaranmu_ Allah yasa mudace🙏🏻
*Ina mai farinciki da wannan Auren da kikayi Aunty Kausar (kausar M Hasan) Allah ya sanyawa aurenki Albarka tare da zuria dayyiba Ameen #HML💏*
_Ina mik'a ta'aziyya ga Feedo Deedo (marubuciyar mamata gimbiyata) akan rashin mahaifiyarta da tayi, Allah yayi mata rahama yasa mutuwa hutuce ameen, Ku kuma Allah ya Baku hak'urin rashin da kukayi👏🏽_
📝 *Episode* 131-135
Bayan sunyi Arba'in sukaje Argungu ganin gida da kai musu jaririyar su gani, lokacin da Ameena ta shiga d'akin su, nan taga wasu kayan Asma'u wad'anda ba'a kyautar ba, batasan lokacin da hawaye ya wanke mata fuska cikin jimami take magana "Asma'u kina ina? Tsawon shekara biyar kenan, Asma'u kina lafia kuwa? Kina cikin farinciki ko sab'anin haka, Asma'u kizo gida mu ganki wlh Baba Neman ki yake ruwa a jallo, pls Husnatah sisto na friend dita ever kizo garemu muma buk'atar ki" cikin kuka tace maganar gwanin tausayi, kullum safiyar duniya kira gida maganarta kenan Asma'u tazo, Mama dake tsaye bakin k'ofa rik'e da Nihal dake motsi alaman yunwa dan tunda suka zo take sharar bacci abinta, Abdool na kusa da ita sai kallon ta yake ya tab'a nan ya tab'a can yana matuk'ar son k'anwar tasa, ko yanzun ma Baba ne ya kirashi suka fita.
Itama hawaye take daga nan tsaye, ita ta haifesu gaba d'aya, amma tasan akwai shakuwa mai girma a tsakaninsu sau da yawa idan matsala ta taso a tsakaninsu suke maganceta ba tare da ta sani, saidai idan tafi k'arfin su suka kawo mata, to ya zasuyi k'addara ta riga fata, saidai su bita Addu'a Allah ya k'are ta aduk inda take ya dawo musu da ita lafia, share hawaye tayi kada ta rauna nata.
K'arasawa tayi ciki tare da kamata zuwa bakin gado, cikin muryan rarrashi da tace "Ameena kuka bazai dawo da Asma'u ba, Addu'ar mu kawai take nema, kiyi hak'uri ki daure ki daina kuka kiyi mata Addu'a" haka tayi ta rarrashinta daga k'arshe ta bata 'yarta data fara kuka tare da ficewa cikin sanyi, dan ganin Ameenan kad'ai tuna mata da Asma'unta yake yi.
*****************
Satinsu d'aya a Argungu sun zaga dangi sosai har birnin lafia sunje, gidan Firdausi duk taje, Abdool kuwa kullum yana rik'e da Nihal har goyata yakeyi Mama tayita zolayarsa, da sunan mati sai cewa yake ai k'anwarsa CE, a satin Yusuf yazo nan ya dage da rokon Baba ya basu Abdool su wuce dashi tunda ya k'are primary, ganin sun dage kuma yaga shima yaron yana buk'atar uwarsa a kusa dashi duk da suma ba abinda basa yi masa amma d'a sai uwarsa, kuma ya yaba yadda Yusuf d'in ya nuna kulawarsa akansa, yanada tabbacin zai rik'e sa da Amana, amma duk da haka saida ya kira Alhaji Sada ya shaida masa abin da sukazo dashi.
Kai tsaye Alhaji ya amince dan yasan waye Ameena yasan zata bashi tarbiyar da ya dace, shi kanshi yaron zaifi jin dad'i gashi ga uwarsa, nan Baba ya basu Abdool sunyi murna Sosai bakin Yusuf ya kasa rufuwa danshi harga Allah yana son Abdool yana jinshi a ranshi kamar yadda yakejin Nihal.
Ban kwana sukayi ma Argungu garin nabame kowa sarki, sannan suka wuce Besse anan ma sam dangin Yusuf basu nunawa Abdool wata fuska k'ama ko wulak'anci ba, Wanda hakan yayima Ameena dad'i sosai, daganan suka shirya tsaf suka lula Kaduna.....
Zamansu kaduna zamane mai cike da k'auna da kulawa da yaran su sosai Yusuf ke kula da Abdool kaman ma yafi sonsa akan Nihal, dan Ameena cewa take Nihal ce babynta shi kuma yaron Dady, tare suka zuwa masjeed kullum muddin yana gida, haka zai baje a parlour yana mishi lesson don tuni suka sakashi secondary wata private, muddin Yusuf na gida to yana tare da Abdool hakan ba k'aramin dad'i yakewa Ameena ba, hakan ya k'ara wanzar da zaman lafia a familyn.
Sannu a hankali rayuwa taci gaba da shurawa kwanaki na tafiya, Nihal nada four years Ameena ta k'ara haihuwa wannan karon twins ta haifa mace da namiji, nan Ameena ta roki Akan a sakama macen sunan Asma'u hakan kuwa akayi inda ake kiranta da Husna namijin kuwa Abduljabbar, zuwa yanzu Yusuf ya gina musu gidan Kansu a unguwar K/mashi inda Ameena ta k'awata gidan da kalolin furanni masu dad'in k'amshi ga kuma garden had'adde Wanda ya k'unshi kayan more rayuwa, kai da ka taho gidan ba tambaya kasan ka taho gidan miss Botany tun farfajiyar gidan zaka fahimci haka.
Abdool yana SS1 Nihal na nursery, tuni ya saba da saka medical d'insa inda a school d'insu wasu ke ganin jin kai ne da tsabar raini dan yaga yanada Brain yasa yake saka glass dan sauka haka kawai yake sakawa ganin yadda ya zauna mishi tsaf, Abdool ya taso yaro mai kuzari da sanin ciwon kai ga k'auna da yake nunawa kanninsa haka sai saka Nihal gaba yayi mata lesson in Dadynsu bayanan shi kuma inya dawo yayi mishi, shi har mamakin k'ok'arin Abdool yake yaro sai kace dan Jamia komai kana ana bud'e kwakwalwarsa ana zuba masa, ita ma dai Nihal Kanta naja ba laifi sai yake danganta hakan da ilimin Ameena, haka sukaci gaba da gudanar da Rayuwarsu cikin farinciki, sukanje Hutu lokaci zuwa lokaci haka Alhaji Sada na zuwa har Kaduna ya dubasu, yanajin dad'in yadda suke kula da Abdool, tuni Alhaji ya saba da Yusuf haka zasu zauna suyi ta hira in yazo dama ga Yusuf da barkwanci wuni guda kukayi a tare zaku Saba.
*****************
Ranar rabuwa ranar da zukata suka nisanta da juna ranar ruhi da gangar jiki suka shiga maraici ranar da mai rabawa ta raba, ranar da Yusuf yayi accident a hanyarsa ta dawowa Kaduna ya fito daga Besse anan on d sport wuyansa ya kare nan take ya ansa kiran maliccinsa, sai gawa su Ameena suka gani fad'in kalan tashin hankalinda suka shiga anan dan page d'in ga bazai ishemu ba, kowacce ta kwatanta da mijinta ne da babanta ne da d'anta ne da k'annin ta ko yayanta ne ya zataji haka suma Familyn Yusuf sukaji da rashin da ya sameso, a Besse aka wuce da gawar akan kayi komai daya dace da shari'ar sunnar Manzo S.A.W, ba'ayi wani zaman makoki ba, duba da yadda zaman ya koma zaman hira da tsegumi da cin shinkafa, Wanda ya mutu shiya mutu kawai sai kuwa na kusa dashi, da suke cikin jimami rashin sa, duk wannan abun Abdool baida labari dan lokacin yana ABU zariya inda yake matriculation, Wanda Yusuf ne da kanshi ya kaishi ya kuma zaba mishi medicine, ganin yanata kiran Dadyn nashi wayanshi bata zuwa yasa ya kira Maminsa, nan ta sheda mishi suna Besse ba charge a wayansa, sannan tace idan da chance ya samesu Bessen k'arshen sati, nan ya tambayeta lafia dai tace qlau ba komai, amma jikin na bashi ba lafia.
Lokacin da yazo ya samu abinda ya faru, yayi kukan rashin Dady dan sosai ya maye masa gurbin Auwal yanzu gashi ya tafi ya barsu.
(Duniya labari)