Abdulmajid complete - Chapter 7
Abdulmajid complete Chapter 7: Abdulmajid complete Chapter 7. Murmushi tayi Mata " kada ki damu Besty is not so worst fa, nima I will be back soon inshaa…
4,456 words
Murmushi tayi Mata " kada ki damu Besty is not so worst fa, nima I will be back soon inshaa Allah " sannan ta wuce.
Duka sun tausaya mata ganin yadda ta rude har Yusuf ke tambayarta halan k'aninta ne, nan Sakina ta gayamishi a yaronta, ba k'aramin mamikine ya Kama shi ba danshi duk kallon budurwa yake mata ba Wanda zai ganta yace tanada aure hadda d'a, yace
"Amma fa bantaba tunanin matar aure bace, duk da kuwa naga tanada kamun kai".
"Hakane amma yanzu bata tare da mijin" nan dai Sakina ta bashi labarinta, sosai ya tausaya mata, hadda k'wallarsa, tare da sak'awa ransa wani tunani.
*life goes on......*
Kwana d'aya, sati, wata, shekara, haka shekaru keta tafiya a guje kamar ana kora su, zuwa yanzu Abdulrahim ya kammala karatunsa inda yake internship a nan Uduth, Asma'u kuwa tana rubuta final exam nata, soyayya suke gudanarwa cikin tsafta, dan sun dad'e da bayyanawa juna sirrin zuciyarsu, jira kawai suke Asma'u ta kammala karatunta su sanar da magabatansu, ayi taimaka a aurar dasu. Lol
Ayau ne ta kammala jarabawarta cikin nasara, kuma a yaune kowanne su ya shirya tsaf ya doshi familyn sa dan fallasa sirrin da ke ransa, dan cikar burin zukatansu, lokacin da Abdulrahim yaje da maganar gidansu Ard'o ya goyamasa baya d'ari bisa d'ari, dan yasan d'ansa bazai zabo abinda zai cutar dashi ba, dan haka ya bashi tabbacin a satin zasuje har shi A Argungu domin ganawa da iyayenta.
Tashin hankali Wanda ba'a sa mishi rana, ai Iya Hari dukane kawai bata mishi ba, amma ta inda take shiga ba tanan take fita ba, tas tayi masa ta kuma tabbatar masa baida matar aure inba Saude ba, dan bai isa ya banna mata lokaci a banza ba dole ya Aureta(Niko nace kamar shi yace ta zauna).
B'angaren Ameena na kuwa ta kammala karatunta cikin nasara, harta anshi resi d'in ta, Abdool kuwa an girma dan yanzu yakai shekara 5 yana nursery 2 a Emirate dake garin Argungu, gashi da k'ok'ari sosai sai dan Neman wayo da surutu har tsoro yakeba Ameena idan ya fad'i wata magana kamar wani Babba, Niko ya had'u da Asma'u aifa shikenan d'an biyemasa takeyi suyi tayi, itadai Ameena kallo kawai nata tana mamakin wannan shak'uwa dake tsakaninsu.....
Asma'u yayarta ta fara sanar ma soyayyarta da Abdulrahim, Ameena tayi farinciki da jin k'anwar tata ta had'u da *muradin ranta* (maman ussey), amma saida tayi Mata mitar k'in fad'a mata tun farkon soyayyar sai yanzu take gayamata, hak'uri ta bata tare da had'e hannayenta biyu guri d'aya.
Dukan wasa takai mata tare da Kama hannayenta ta maida ita kan bed "ki rage zurfin ciki kanwata kada ya cutar dake wata rana"
Tana dariya tace "yes Aunty ur wish...." Dariya sukayi baki d'aya dai shigowar Abdool shima ya dane gado tare da kamu rungume Asma'u tayi tare da jan guntun hancinsa tace..
"Clever boy kasan me akewa dariya ne hala?"
"Yes tunda Aunty da Mami na dariya nasan suna farinciki ne.." Nan dariyar sukayi gaba d'aya suna mamakin wayo irin na yaron...
Ameena nace taje ta sanar da Babban su game da maganar Asma'u, har da maganan zuwan su Ard'o dan Abdulrahim ya kirata ya gayamata suna zuwa cikin satin.
B'ata rai taga Baban nasu yayi yace ta kira Asma'u, jiki sanyaye ta fita, tare suka dawo.
Asma'u ya kira sunanta cikin kaushin murya, bai jira amsawarta ba yaci gaba da magana.
"Yayarki tazo min da zancen yaron da kike so, yanzu abunda ya faru da 'yar uwarki bai zama izina gareki ba, har kike tunanin Auren 'yan jahar Sakkwato, to bama wannan ba na Riga mun gama magana da Malam Musa zamu had'aku Aure da d'an wajensa Mustapha" tunda ya fara magana Kanta na k'asa haka itama Ameena, harda hawayenta jin anyi mata fami akan ciwon ta.
Sannan yaci gaba "dan haka inaso ki kira wannan yaron ki gayamishi karma yazo da iyayensa dan an Riga anyi miki miji, kinji ko?" Kai ta girgiza masa alaman eh.
"Yawwa kuje Allah yayi muku Albarka" Ameen suka ansa sannan suka wuce, bayan fitarsu inna dake zaune tunda aka fara maganar bata ce komai ba.
"Amma Alhaji kana gani anyiwa yarinyar nan ad......." Katsesa yayi.
"Ya isa Habeeba wannan ba huruminki bane" shiru tayi da bakinta tare da fadin "Allah ya kyauta"...
K'arshen tashin Asma'u ta shiga, rabuwa da masoyi da rana tsaka siddin akwai wahala, sai dai ya zama wajibi gareta tabi umarnin babanta, Ameena da itama d'aure kawai take amma k'anwar tata ta bata tausayi tasan zafin rabuwa, dafata tayi tana tare da k'arfafa mata guiwa(dan uwa rabin jiki, Allah ya barmu da yan uwanmu).
Wayarta ta d'akko ta kirasa amma ina bata zuwa saboda matsalar network, ko ranar da ya kirata saida yaje kan titi dan basuda network cikin gari, haka taita kira tak'i shiga, tsawon kwanaki uku amma ba labari, ana hudun kuma tace bama zata kira ba.
Ard'o kuma duk bala'inda iya Hari yi yayi kamar bai san tanayi ba, Sam bai yarda da tarbiyar Saude ba, kuma bazaiyima danshi auren dole ba, haka suka shirya tsaf shida Malam Garba da k'annensa guda biyu sai Abdulrahim suka doshi hanyar Argungu ba tare da sanin Iya Hari ba, Abdulrahim yaso ya kira Asma'u ya gayamata sai kuma yace kawai bari ya bata surprise.
Basu sha wahala ba gurin gane gidan dan sunbi kwatancen da Asma'u tayi, har k'ofar gida suka isa da motar da yake ta Abdulrahim CE, sunyi sa'a sun samu Baba k'ofar gida tarba ta karamci yayi musu, kamar yasan da zuwansu bayan sun gaisa sukayi mishi bayanin meke tafe dasu, mamaki ya kashe shi wato shi yarinyar zata renawa hankali, tambayan Abdulrahim yayi akan bata kirasa ta gayamai komai ba yace eh bata kirasa ba(kusrensa bai fad'a masa sunada matsalar network ba).
Gyaran murya yayi Sam bai nuna musu b'acin ransa ba "ah naji mi a tahe daku, idan a shirye kuke bani da buk'atar komai daga gareku sadaki kawai zaku bani a d'aure Auren yanzu" cikin mamaki suka shiga kallon juna kamar 'yarda aka gaji da ita.
Kamar yasan me sukewa mamaki yace "ko d'aya ban gajia da ita ba saidai ta zabi abinda takeso dan haka shi za'ayi Mata, kuma in Baku taho da niyyan aure ba to Ku tashi Ku tafi abinku, amma kai kar in sake ji ko ganin kafarka a gidana ko ka kira yata, ka fita hanyar ta gaba d'aya" ya fad'a tare da nuna Abdulrahim.
Duk ya k'ara d'aure musu kai, haka malam Garba ya Zare dubu 20 ya bashi ansa yayi tare da mik'ewa 10 ya d'auka na Sadaki 2 na goro, ya maida musu da saura, cikin k'ank'anin lokaci sai gashi da goro da wasu mutane nan take akayi Addu'a aka d'aura Aure, duk wannan bidirin da ake cikin gida basusan meke faruwa ba sun dai San yayi bak'i amma basusan su waye ba.
Nan yace su jira ya fito musu da Amaryarsu su wuce da ita, sudai kallonsa kawai suke mamakin duniya ya ishesu Abu kamar tatsuniya, ciki ya shiga tare da d'aure fuska tamau ya fara kwalawa Asma'u kira kamar hauka.
A tare suka fito ita Mama Ameena suma cikin mamakin kiran.
"Asma'u ungu wannan" ya mik'a mata kud'in, ansa tayi jiki a sab'ule.
"Sadakinki na inaso ki shiga ciki ki d'auko mayafinki Angonki na waje yana jiranki, saidai inaso ki sani tunda kin zabi Abdulrahim akanmu to daga yau bamu bake, baki sammu ba haka muma bamu sanki, kada ki kuskura kiyi tunanin mu ko tunanin tahowa inda muke, mun yafe masa ke har lahira" ba Asma'u kad'ai ba har Mama da Ameena saida kalamansa suka girgiza su, sai yanzu ta gane kuskuren ta na rashin fad'a mishi, ita kuma taki fad'i gudun matsala, Ashe hakan babbar matsala zai haifar mata.
Cikin sheshshekar kuka ta isa gabansa ta duka da duka gwuiwarta, bakin ta na rawa "Baba don....." Katseta yayi
"Kul kada ki yadda kice komai kiyi kawai yadda nicce miki" rik'e mishi kafafu tayi tana gunshekar kuka, Ameena kukan take haka Mama, Don tafi kowa sanin halin mijinta idan ransa ya b'aci Sam bayaji baya gani, zuciyarsa rufewa take.
Ameena ma ta bud'e baki zatayi magana ya hanata, haka Asma'u ta rarrafa inda Mama ta rungume ta itama Ameena zuwa tayi ta rungume su, suna haka saiga Mansur ya d'auko Abdool daga school, a cikin wanga yanayi suka isko su ga Baba tsaye sai huci yake.
Da gudu Abdool ya yaje ya rungume su shima yana kuka
"Mama kukan mi kukayi, Aunty kema kuka na kikayi, Mami kema" yana tambayan su yana yi shima gwanin tausayi.
Baba ganin zuciyarsa naso ta karaya yasa ya shiga sa kanshi ya d'akko mata hijab d'inta, ya saka mata ya jata, su mama na riketa suna magiya suna komai a banza, Mansur shima tuni hawaye suka wanke mishi fuska, Abdool shima rike ta yayi GAM.
"Baba ina zaka kai Aunty?"
"Abdulmajeed, Aunty bata buk'atar Ku, zan kaita inda wad'anda take buk'ata" ya fad'a tare da banbareshi ya mik'a ma Ameena, sannan yayi waje da Asma'u, Abdool sai kuka yake yana kiran "Aunty" amma Sam bata bai saura ra ba, haka magiyar su Mama suna kika duk bai saurara ba.
Yana fita bai zame ko'ina ba, sai cikin motar ya turata tare da basu Umarnin su wuce, anan su Ard'o suka fahimci da matsala, suka shiga bashi hak'uri akan ya tsaya a sananta, amma Sam yak'i sauran su, saima kashedi da yaka k'ara yi na karta sake ta tako kafarta gurin su, tare sa gayamusu ya yafe musu ita har lahira, ganin ransa ya gama b'aci yasa suka rubuta no- da garinda Suke idan ya wuce dan Allah ya kirasu, sannan sukaje mota suka tafi...
Asma'u na ganin an tada mota ta k'ara rushewa da wani irin matsanancin kuka................
🤦🏽♀🙆🏾🙆🏾
_Masoyan Abdulmajeed INA alfahari daku aduk inda kuke, pls kuci gaba da karfafa mini #ILVMNM❤guys# keep fallowing_
💄Meryerm Abdool💄 [8/9, 6:17 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
*Yakai d'an Adam meye tak'amarka/ki, meye alfaharin da kake/kike, meye fad'in ran naki/ka, meye d'agawar taki/ki, keda/kaida farkonka/ki ya kasance k'azantaccin ruwa, tsakiyarki/ki fitsari da kashi, k'arshenki/ka abincin tsutsa, mushe to meye abun jinkai da nuna isa.*
Nasiha ce👌🏻
_bazan gaji da gode muku ba, a zahirin gaskiya kune ni haka nice Ku, sai daku zanyi rubutu wato masoyana masu bani k'arfin gwiwa akan rubutuna, ina alfahari daku, ina rokon Allah yaci gaba da bani damar da zan rubuta abinda zai sakaku nishadi ya kuma amfanar da Ku, #heart u ❤ guys# ina k'aunarku a duk inda kuke #double love😍#_
📝 *Episode* 116-120
Tunda suka d'auki hanya, take kuka bil hakk'i da gaskiya, kuka take mai tab'a zuciyar mai sauraro, suma mutane cikin motar duk zuciyoyinsu a tsince suke, tausayin yarinyar ya lullub'e musu zuciya, shiru kake ji ba abinda ke tashi sai sautin kukanta, ba Wanda yayi yunk'urin dakatar da ita dan wani lokaci kuka rahama kana jin sauk'i a ranka, sanda tayi mai isarta, sannan ta tsagaita, hakan yasa Ard'o fara bata baki.
"Kiyi hakur'i 'yata duk da bansan ainihin abin da kikayima mahaifinki ba, yayi miki wanga hukunci, a gaskiya hukuncin yayi tsauri, saidai ki Sani su iyaye komai suka yima d'ansu to ya zama dole yayi hak'uri dasu kuma yayi musu biyayya mudin baici karo da Umarnin ubangiji ba, saboda sun riga sun gama dashi tunda suka haifesa, inaso ki rik'eni a matsayin mahaifi a gareki ni kuma nayi miki alkawarin zan zamo uba a gareki, kuma bawai ina nufin kibar iyayenki ba aa sunanan a iyayenki ba Wanda ya isa ya maye gurbinsu a gareki, kuma inaso ki d'age da Addu'a Allah ya sassauto zuciyar mahaifinki ya yafe miki kuma ya nemeki, muma zamu tayaki da Addu'a inshaa Allah".
Sosai taji dad'in maganar Ard'o, hakan yasa hankalinta yad'an kwanta, ganin tayi sa'ar suruki na gari, cikin nutsuwa ta gayamusu abinda ya faru, sun jinjina abun a ransu tare da gayamusu kuskurensu daga ita har Abdulrahim d'in, sannan kowa ya bata baki da kalamai masu dad'i, tare da gaya mata ta d'aukeshi a matsayin k'addararta domin rabon ayi auren ne yasa hakan ta faru, tare da sanya ma Auren Albarka, Abdulrahim dake jan motar shima jiki a sanyaye duk sonsa da Asma'u baiso Auren su ya kasance haka ba, amma ba yadda zasuyi dama tun ran gini tun ran zane sai fatar Allah yasan hakan shine mafi Alkhairi a garesu, Ard'o ko tuni yaji yarinyar ta kwanta masa a rai da alama zatayi hak'uri, haka dai suka doshi kilgori kowa da abinda yake sak'awa a ransa, kowa zuciyarsa ba dad'i......
***********************
Baba kuwa yana ganin sunja mota ya buga babbar rigarsa yayi cikin gida, anan ya jefar da takardar da suka bashi nan iska yayi gaba da ita, yanda ya barsu haka ya samesu suna kuka, kallonsu yayi cikin b'acin rai yace.
"Yanzu kunaga banyi muku dai2 ba ko? Baku dubi irin abin yarinyar tayi ba, ta nuna bata buk'atar mu a rayuwarta ta zabi wad'anda takeso amma Ku duk Baku gani ba, to bari kuji duk Wanda ya yadda ya kusanceta koda hanyar bani bashi, kuma ban yafema koda kuwa keda kike uwarta ne" ya fad'a cikin b'acin rai tare da nuna Inna, sannan ya buga rigarsa yayi waje.
Bai zame ko'ina ba sai gidan aminin nasa Malam Musa, dan gayama abin ya faru da Kansa kada yaji a wani gu, yayi sa'a kuwa ya samesa bayan sun gaisa ne yake bashi labarin abinda ya faru tare da bashi hak'uri.
"Kai amma Abu baiyi kyau ba, dama ko bakazo ba inada niyyan zuwa akan maganan, dama na samu Mustapha da maganan to shine yace shi gaskiya yana wacce yakeso abar zancen kawai, to shine naso inzo in fad'a maka sai kuma ban samu zuwa ba har ka taho.
Tsananin mamaki da imani ne yayi mishi yawa, yama k'asa magana lallai kowa ya daka ta mutane toya rasa turmin daka nashi, saida sukayi da mutumin nan komai lafia amma yanzu yace ba haka ba, shiya salawantar tashi 'yar akan farinciki wasu, yayin shi kuma ya bawa d'an shi abinda yakeso, nan take nadama ta rufesa lokaci na farko d'aya yi tir da (zuciya irin tasa na Ayusher).
"Alh, Abubakar bakace komi" boye damuwarsa yayi tare dayin murmushi yake Wanda yafi kuka ciwo "ba komai Alhaji Allah ya kyauta, sai anjima" ya tashi ya wuce ba tare dayace komai ba...
Gida kuma bayan fitar baba zaune saukai jugum suna jajanta wannan Abu d'aya samesu, wannan shine ga duka ka kuma tsunka jaka, Abdool Ameena takai d'aki Wanda yayi bacci sai ajiyan heart yake, sannan ta dawo inda Mama suna tattauna wad'annan ibtila'i dake bibiyarsu a d'an tsakanin, lallai Allah shike jarabtar bawansa suna fatar su zamo cikin masu cinye ta, Ameena gani take tafi kowa ganin rayuwa, Asma'un da ta rage mata mai bata shawara sa d'auke mata kewa gashi k'addara tazo ta rabasu, yanzu ma ta ina zasu samu labarin Asma'un bayan ko waya batada ita yanzu, dan daga ita sai kayan jikinta tabar gidan komai bata d'auka, gashi ta manta sunan garin dan tabbas ta fad'a Mata amma bazata iya tunawa ba, ko wacce irin rayuwa zatayi a gidan Aurenta a wannan yanayi sa taje musu zasu karb'eta kosu wulak'anta ta? Nan tayi saurin nema mata sauk'i gurin Allah, haka suka wuni gidan ba dad'i kowa sai jimami yake.
_such is life_
Baba kuwa k'asa komawa gida yayi bayan yazo gaf k'ofar gidan ya dudduba kozai ga wannan takardar amma ina bata ba labarin ta, jin yayi komai baya mishi dad'i, sai gashi hadda k'wallarsa sam baiyima Asma'u adalci ba, yafi kowa sanin biyayya irin ta 'ya'yansa amma ya rufe idonsa, lallai zuciya mugun nama CE, kowa ya biye mata zata kaishi ta baro ne, lallai kowa yahau dokin fushi k'arshen sa nadama ne (yana daga cikin karantarwar manzo S.A.W idan kana cikin fushi kada kayi magana sannan kada ka yanke hukunci cikin fushi dan k'arshen sa dana sani ne) Allah yasa mudace.
Sai dare ya samu sukunin komawa gida, shima jiki ba k'wari ya shiga, kamar yadda Inna ta saba tarbonsa haka ta tarbesa ba tare data nuna mai komai ba, kamar ba abinda ya faru, k'ara jinjina hak'uri irin na Inna yayi sau da yawa yakan tauye mata hakki shikansa ya sani amma bata taba nuna mishi damuwar, lallai mace tagari ni'imace(haka yake duniya d'an jin dad'i ce amma mafi jin dad'in ta Wanda ya dace da mace ta gari).
Haka suma su Ameena sukazo suka gaishe shi kamar yadda suka saba, zasu tashi yace su tsaya yanada magana, ayan da yayi maganan cikin taushin murya, abun har mamaki ya basu, nan dai ya labarta musu yadda sukayi da Abokin nasa, tare da nuna musu nadamarsa.
"Alhaji ka dad'e kana tauyeni sau da yawa kana maida damuwar kowa ba damuwa, damuwarka kad'ai kake dauka damuwa, kama rayuwa da fushi kana yankewa mutane cikin fushi, to yanzu gashi wagari ya waya, ka salwantar mana da yarinyar akan son ran wasu, me kayi kenan" Inna ta gayamai magana cikin nutsuwa.
"Baba shiyasa ake son bawa mutum uziri a rayuwa, lokacin da ka shigo nida Asma'u munaso muyi maka bayani amma haka rufe ido kak'i bamu dama" nan ta basu labarin abinda ya faru a lokacin da Asma'u ta kira Abdulrahim" Amma kayi hak'uri In na fad'i ba dai-dai ba".
"To kaji ma abinda ya faru ko amma saboda rashin bata uzirunka a rayuwa kak'i sauraren kowa".
Shiru baba yayi nadama na k'ara lullub'esa, duk abinda suka fada gaskiya ba karya, sai hango lokacin da Asma'u take rik'e mishi kafa takeyi amma yayi biris yak'i saurarenta, tuni tausayinta ya kamashi lallai baiyi Mata adalci ba.
Hak'uri ya basu tare da tabbacin inshaa Allah zai nemota duk inda take.
Kwana ki sun shura watanni sun wuce kullum Baba yawon Sokoto da garuruwanta saidai kuma ba'a dace ba, ganin abin yayi yawa duk ya dami Kansa yasa Mama cewa.
"Ka hak'ura da yawon nan haka idan da rabon mu gaba zaka ganta ta kawo Kanta har gida, idan kuma babu rabo zafin nema bazai kawo samu ba, hakan ya hak'ura dole tare da bibiyarta da Addu'ar fatan Alkhairi aduk inda take.
Ameena kuwa zuwa yanzu zaman gida ya gama isanta gaba d'aya saukinta ma tana teaching da Baba ya samo mata yanzu tsawon shekara biyar kenan da rabuwarsu gashi duk masu zuwa sun d'auke kafarsa, a halin yanzu ba abinda takeso irin tayi aure shine akwai kwanciyar hankalinta (dan Mace komai kamewarta, idan batada aure to mutuncinta ragaggene a idon mutane, balle kuma wad'anda suka d'auki zawarci a lasisin iskanci suka samu tunda yanzu su zawarane ba namijin da zai Aure yace yana Neman budurci, to ai ba anan gizon yake saka ba, walla d more kikayi zina kina bazawara bakida wani hukunci daya wuce a jefeki, ba riba kenan, a tunani zawarci wata damace da mace zata K'ara sanin rayuwa, ta kuma gyara halayenta, kowanne aure yanada sila a rabuwarsa saiki duba meya kashe miki aure dan gyarawa gaba, bawai ki lalace ba, Allah yasa mudace) ayuwar zawarci rayuwace mai cike sa kalubale da tashin hankali, zaman gida ya gama isarta yau idan mace takai munzali tofa da batayi Aure ba, zaman sai kasance gashi nan dai na ganin laifi ne keda iyayenki, shiyasa Ameena ta damu sosai da rashin Auren, sai ba yadda zatayi dan tasan komai lokaci ne.
Yau kamar kullum Mansur ne yaje ya d'auko Abdool daga school, da gudu ya shigo yana murna "Mami kinga Nina yi na d'aya" ya fad'a yana nuna mata result d'in da gift d'inta aka bashi.
"Iyye yaron Inna kaifa akwai rashin ji amma akwai k'ok'ari" Jan tayi zuwa jikinta tana duba idonsa "waini kam idon nan naka Abdool anya lafia ko?" Inna dake fitowa tace "me idon yayi?"
"Kiga farin yana surkawa da pink," duba idon Inna "tabbas ya kamata kuje asibiti" shikam sai k'ok'arin nunama inna report sheet yake, ba abinda ya damesa....
Likitan ya tabbatar musu ba wata babbar matsala bace, ciwon a jininsa yake so yayi inherited ne saidai ya kamata a nema mishi medical saboda idon yayi lasting, sai yanzu Ameena ta tuna tana ganin idon Auwal suna irin hakanan sometimes, no wonder shiyasa yake amfani da glass always Ashe medical ne.
**************
Har k'ofar gida suka sauke malam Garba da k'annin Ard'o sannan suka isa gida suma.
Da kallon mamaki iya Hari ta bisu sannan tace "malam ina kuka shige tun safe, wagga kuma fa?"
"Ai dai kin kawo tabarma tukun" tabarma tasa Shatu ta kawo tare da shimfida sannan ta kawo musu ruwa.
Zama sukayi sannan Baba yace Asma'u tasha ruwa ba musu tasha, guri ya nunawa Hari da tayi musu tsaye k'erere tana musu kallon dibar arziki, tuni jikin Asma'u yayi sanyi.
Zama tayi sannan Ard'o ya gayamata dukkan abinda ya faru, mik'ewa tayi cike da gatsali.
"Mi wagga uwar mata"................
💄 Meryerm Abdool💄 [8/11, 3:14 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬 🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na 💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers* P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
*All thankful and praises be to Almighty Allah, d one who give me chance to live and make Muslim in Muslim ummah without my knowledge,🙏🏻 Patience is a key 2 every success in life, everything come to he/she who have patient and wait in everything in life, may Allah give us d heart of patient👏🏽*
```Alhamdulillah, mashaa Allah, after long journey and go up and down crossing over many obstacles finally I get it, I mean my NCE result, I wish my self, big success in every stage i go, thank you Allah for every blessing upon to me hidden one and d one that appear``` 👏🏽
📝 *Episode* 121--126
"Mi! Wagga uwar Mata? Hehehe ah dole daga zuwa gaisuwar iyaye da nema, a baku aure baki d'aya, yo dama daga ganin wannan kasan neman kai ake da ita, an tsofe gida ba mashinshini yo ai dole, tab wayaga akwala" sannan ta juya ga Abdulrahim tare da nuna shi da yatsa.
"Tir! Amma ka bani kunya, dama akan wannan mai bak'ar huska da bak'ar kamane yassa kak'i 'yar uwarka, yo Allah na tuba wannan ai sa'a tace, to nidai bani cikin wannan kwaba taku ehe" ta k'ara sa tare da hararan Ard'o.
"Ke! Hari ashe dama haukarki da rashin hankalinki yakai har haka, ashe baki da imani bansani ba, yanzu da ace cikin d'iyanki ne hakan ta faru dasu zakiji dad'i?"
"Aa Malam yada kiramin rashin hankali da hauka daga fad'ar gaskiya? Kuma ni d'iyana tuff! Tohe musu mugun yawu, nidai nace bana cikin wannan auren, kuma ban d'auka a sirika ba ehe" tana gama fad'i ta wuce tana gunguni.
Girgiza kai Ard'o yayi "Allah ya shiryeki" sannan ya dubi Asma'u wacce tunda Hari ta fara tu'annatinta kanta ke k'asa tana zubar da hawaye zuciyarta sai zafi take Mata "inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un, Allahumma ajirni fi musibatih wa'akhlilni khairun minha, oh ni Asma'u tawa kalar jarabawar kenan, ya Allah ka bani ikon cinyeta...."
"Kiyi hak'uri 'yata Kada kalamanta su dameki, kamar yadda na gayamiki zan rik'e kamar 'ya'yana, kada ki damu ba abinda zai faru sai Alkhairi" sannan ya dubi Shatu wacce duk jikinta yayi sanyi abinda uwar tasu tayi sam baiyi Mata dad'i ba, ita bataga aibun Asma'u ba, dan daga gani tafi Saude nesa, ita dama can Saude bata yi Mata, wannan saidai Lanti da suke k'awance kullum suna tare, tasan Idan taji itama sai tayi tata haukan(dake anyima Lantanar aure).
"Aisha kai matar yayanki wancen d'akin, su fara zama can kafin a Gina mata na, ni zan koma d'akin zaure" (d'akin sa ne da Abdulrahim gina mishi bada dad'ewa ba).
"Muje Aunty" mik'ewa tayi ba musu ta bita, daga Leda sai katifa, kujerar roba sai kwaba da littafan musulunci ke cikin d'akin, zama tayi gefen katifar, ita kuma Shatu ta zauna k'asan Leda "Aunty don Allah kiyi hak'uri da abinda iya tayi miki, haka take komu data haifa yimana take yi".
Murmushi yak'e ta k'irk'iro " ba komai k'anwarta ai nima uwace a gareni kada ki damu" jinjina kai Shatu tayi "lallai yaya yayi dacen mata, duk wannan abun da iya tayi mata" ta fad'a cikin ranta, ita kam Wallahi ta kwanta mata a rai, nan tayi ta mata fira dan ta kwantar mata da hankali.
"Modibbo kaje ka rarrashi matar ka, ni zan fita na samo mata abinda zataci" yace ma Abdulrahim da yayi sugum tsabar kunya da bak'in ciki abinda uwar sa tayi.
"Baffa Aida ka Bari naje, ka huta kaima" .
Murmushi Ard'o yayi "kaidai kayi yadda nicce kawai" tare da ficewa daga gidan, shima tashi yayi ya shiga d'akin, shigarsa yasa Shatu yi mata sallama ta fita.
Zama yayi daf da ita tare da ciremata hijab jikinsa ya janyota yana d'an bubbuga mata baya Alaman rarrashi, cikin muryan rad'a ya fara mata magana "kada ki damu matata koda duka duniya zata taru ta k'iki nikam ina tare dake, bazan taba barin ki cikin kad'aici ba, zan game miki bango abin jinginawa" haka yayi ta rarrashinta da tsadaddin kalamansa na k'auna, ita kuma tai lahu a jikinsa tana saurarensa yayinda wasu kasu na damuwarta suka tafi ( hmmm k'auna kenan Allah ya had'a kowa da masoyinsa na gaskiya Ameen).
**************
B'angaren Yusuf kuwa tun ranar da Sakina ta bashi labarin Ameenah yaji wani irin tausayi da k'aunarta sun k'ara lullub'esa danshi tun ranar da ya fara ganinta a school d'in, yaji ta kwanta masa komai nata burgeshi yake musamman natsuwarta, saidai bai San ta inda zai fara ba, dan iya sananinsa da ita bai tab'a ganinta da ta kebe da namiji ba, sai shi shima d'in da sunan karatune kuma tare da Sakina, gashi shiba ya tab'a soyayya ba balle yace yasan yadda sai samota barin abin a ransa yayi kawai, saidai daga ranar kullum cikin tambayanta Abdool yake yana lafia, haka zai sayo kayan wasa dana kwalama ya bata ta kai mishi, koya kirata a waya yace ta bawa Abdool suyi hira, yaita yi masa shirme yana biye masa, ita abun har dariya Suke bata wai friends ne, dama ance mai da wawa hakan yasa ta sakance dashi wani lokaci sai sake-sake zuciyarta ke Mata game dashi saidai nan da nan take saurin ka yima Kanta fad'a akan bama zai yuyu ba.
Ko bayan kammala karatunsu zumunci bai yanke ba, yakan kira ko ita ta kira lokaci zuwa lokaci, ko lokacin da akayi Auren Sakina yaje Bk dan kawai ya had'u da Ameena danshi asalin d'an Koko-besse(local government ne a Kebbi) ne karatu ya kaishi Argungu.