Kenza eBookz

Abokin rayuwa by khadeeja candy - Chapter 43

Abokin rayuwa by khadeeja candy - Chapter 43

Abokin rayuwa by khadeeja candy Chapter 43: Abokin rayuwa by khadeeja candy Chapter 43. "Ni ma na yi marmarin ganinka, fatan kana lafiya"

3,315 words

"Ni ma na yi marmarin ganinka, fatan kana lafiya"

"Da sauki dai ina lafiya ga mutumen da uwarsa ke fushi da shi?"

Ya bude motar ya shiga baya Aliyu ma ya zagaya ya shiga baya, mutumen da suke tareda Turhan ya shiga front seat direba yaja motar suka fara tafiya, suna taba hira har suka isa gidan. Turhan da Aliyu a tare suka fito motar Aliyu ya wuce gaba ya shiga cikin falon Turhan na bayansa, Mai aikin Ammy ta amsa musu ta gaishesu, Aliyu ya karasa gurin da Ammy take zaune ya zube kasa yana gaisawa da ita Turhan ma ya karasa ya zauna kusa da Aliyu. Cikin murna da farinciki take kallon Aliyu.

"Madallah Aliyu ne a gidan na mu yau?"

"Ni ne Ammy ya jikin na ki"

"Jiki Alhamdulillah Aliyu ina samun sauki, ashe ka samu shigowa"

"Eh kin san daman na ce zan shigo na duba ki, sai gashi kuma wani uzurin ya taso aka yi daidai, a airport na hadu da Turhan ai sai muka zo tare"

"Maa Shaa Allah, haka fa ka fada min zaka zo ai ka huta baka tsaba alkawari uwarka ta yi farar haihuwa Aliyu"

Ammy ta fada har lokacin bata kalli inda Turhan yake ba. Turhan ya sauke kansa kasa yana jin wani iri, Aliyu ma ya ji babu dadi domin Ammy tana kokarin muzanta abokinsa ne a gabansa which it's not fair.

"Amman dai jikin da sauki sosai ko Ammy?"

"Na samu sauki Alhamdulillah, ai na ma fadawa abokinka ba sai ya zo ba, kawai be ji magana ta ba ne daman be saba ji ba"

"Haba Ammy taya baki da lafiya kuma ki ce kar ya zo? Ai ba zai yiyuwa ba, ke fa mahaifiyarsa ce Ammy ki rika duba wannan"

"Zuwansa ba zai rage ni da komai ba balle ya kara ni, rabin ciwon nan ba shi ne silarsa ba? idan ya zo ai ba da lafiya zai zo min ba, kuma ina da masu kula da ni nan yayan yan'uwa sun ce wadatar, idan za amin allura kullum sai Nurse ta zo, Likita kuma kullum yana zuwa duba ni, saboda na fada masa ni bana son asibiti ko da mutuwa ce a bar ni na mutu a gida, kaga shi kenan abokinka ya huta ba sai ya sake zuwa kasar nan ba sai yayi zamansa a can daman haka ubansa yake so"

Turhan ya kalleta felling hopeless cikin murya mai rauni ya ce.

"Wani dan kirki ne zai yi fatan mahaifiyarsa ta mutu ya huta? Ammy ya kike magana haka kamar mai magana da makiyinta? Danki ne fa ni jininki, na rasa ya zan yi na kawar da wannan bakin shatin dake a tsakaninmu, Ammy kina tunanin all this while abun nan dade yake min? Ko tafiya kika yi kika bar ni wannan abun ba zai barni na samu salama ba, Ammy ni ma ina cikin damuwa gaba daya yanzu bana jindadin rayuwar da nake, abun da a aikata kuskure ne kuma ni dan'adam ne aziji"

Ammy ta girgiza kai.

"Aa abun da ka aikata ganganci ne ba kuskure ba, da gangan ka aikata, saboda baka kallo da daraja irin ta uwa, kuma abun da ka yi min ai ka kyauta tun da ka samu tukuici, Allah ya maka albarka Turhan na gode"

Aliyu ya ce.

"Ammy ki yi hakuri dan Allah ki yafe masa abun nan ya wuce"

"Na yafe masa, amman wucewar wannan abun? Sai na koma ga Ubangijina, ni kadai na san me nake ji, yaron nan shi kadai Allah ya ba ni, idan kai ka manta mahaifiyarka ba zata manta ba Aliyu, irin fadi tashin da na yi akan na samu ganin yaron nan, na wahala a gidan mahaifinsa kuma na wahala kamin a bar shi ya zo gurina, na dauki yar mutane na aura masa da tunanin hakan zai saka na samu dana da zuri'arsa a kusa da ni, amman ya watsar ya karyata duk wata halayya tasa dana fadawa yarinyar nan, marainiya ba uwa ba uba, yanzu Allah kadai ya san halin da take ciki idan ma tana raye, bata da kowa sai Allah bata da wani wanda zai nemi ya san halin da take ciki tun da bata da dangi, yarinyar nan ta yarda da ni amman Turhan ya rusa duk wannan ya nuna ba ni da muhimmanci a garesa kamar yadda ubansa ya nuna min"

Ammy tana maganar hawaye ya sauko idonta, Turhan yayi kasa da kansa ya saka hannunsa ya rike goshinsa idonsa suka cika da hawaye, ba na tausayin Emily ba na bakinciki daya saka mahaifiyarsa har ta zubar da hawaye akansa gaban abokinsa.

"Wane irin muhimmanci Aisha take da shi a gurinki har haka Ammy? Da har zaki zubar da hawaye akan abun da ya faru?"

"Irin muhimmanci da baka da shi"

Ta amsa masa kai tsaye da kakkaurar murya.

"Indai saboda ni ka zo, toh ka hada kayanka ka koma bana bukata, ka bari idan na mutu sai ka zo jana'iza"

"Subhanallahi Subhanallahi"

Ya maimaita har sau uku sai Aliyu ya dafa shi.

"Turhan fita waje ka jira ni"

Ya tashi cikin wani irin yanayi na bakinciki da ya fice falon, sai da ya fita sannan Aliyu ya ce da Ammy.

"Ammy bana son na tunatar da ke abun da kika riga kika sani, na san kin so Emily da Turhan kin tsara zamansu, amman haka be samu ba baki tunanin wata su din ba alheri ba ne ga junansu? Kuma haka Allah ya tsara shi da ita babu dogon zama, kuma Ammy karki manta duk yadda zaki so Emily Turhan danki ne, na san be kyauta ba amman fushinki a kanki da damuwarki zai iya janyo masa matsala a rayuwa ko ba yanzu ba a nan gaba, kuma Ammy Turhan yayi nadama sosai yanzu haka zancen da yake min yana son ya saka kudi mai kauri akan nemo Emily, abun ya dame shi ma, ki yi hakuri Ammy"

Ammy ta yi murmushi.

"Allah ya maka albarka Aliyu, ka san muhimmanci uwa shiyasa ka fadi haka, tafi ka tafi na gode"

"Shi kenan Ammy Allah ya kara sauki ya baki lafiya"

"Ameen Allah ya maka barka"

Ya mata sallama ya fito falon a jikin motar da suka shigo ya samu Turhan ya jingina fuskarsa dauke da damuwa. Aliyu ya saka hannayensa aljihu yana sauke ajiyar zuciya ta dayan bangaren abokinsa ya ba shi tausayi, sai dai kuma idan ya tuna labarin da Emily ta ba shi sai ya ji kamar be tausaya masa ba.

"Turhan am sorry iyaye sai lallabawa"

"Haka take fada min maganganu marasa dadi a duk lokacin da na zo, kuma ta sani na yi iya kokarina gurin neman yarinyar nan, ban same ta ba toh ya zan yi? Kana jin tana fadin bata san halin da Aisha take ciki ba, ni kuma da nake cikin wannan halin bata jin tausayina na rasa ya zan yi"

"Da sannu komai zai zama daidai In Shaa Allah, wai taya ka yi Aisha ta subuce maka.?"

Madadin ya amsawa abokinsa sai ya ce

"Ita ma fa yarinyar ta jefa ni a matsala, miyasa ta amince da auren nan tun farko fisabilillahi"

"Allah ya kawo sauki, ni zan wuce abun da zan fada maka shi ne ka yi hakuri da mahaifiyarka kuma ka yi ta addu'a"

"In Shaa Allahu, ma gode Aliyu, bari na yi ma direban magana sai ya kaika gida"

Aliyu ya shiga motar Direban yaja shi zuwa gidansa, a mota Aliyu ya gwada kiran Number Emily ya jita a kashe sai ya aika mata sako.

"Are you okay?"

Domin ya san ya kamata ace ta kira shi bayan riskar sakonsa, and maganar Ammy ta taba shi na cewa bata da wanda zai damu ya san halin da take ciki tun da bata da kowa. Bayan direban ya aje shi ya juya shi kuma ya shiga gidan da yayi datti yana mamakin taya haka ta faru domin yana da mai gyara masa gidan every week. A falo ya samu Fatima na ta bachi har lokaci akan kujera hannu ya kai ya taba jikinta yana mamakin wane irin bachi ne take haka, sai ya ji shi da dan zafi kadan. Mai kula da harabar gidan ya shigo yana masa sannu da zuwa Aliyu ya amsa yana tambayar ina mai gyara gidan.

"Tun da ta tafi bata dawo ba, bata fada maka komai ba tace dai zata je ganin gida ta bada keys a aje maka"

Ya saka hannunsa aljihu ya ciro keys din ya bawa Aliyu da hannu biyu. Aliyu ya mika masa Atm dinsa ya fada masa code sannan ya fada masa inda zai tafi ya samo musu abinci mai kyau...

Sorry ku yi hak'uri gobe zan yi long page in Shaa Allahu. [7/2, 6:50 PM] 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆: 🍒 ABOKIN RAYUWA 🍒*

*© Khadeeja Candy*

Page 4️⃣5️⃣

Kamin yaron daya aika ya dawo Aliyu ya shiga ciki yayi wanka ya canja tufafi sannan ya dauki wayarsa ya kira Mama Barakat ya tambaya ko tana gida.

"Eh ina gida Aliyu ko ka shigo garin ne?"

"Eh na shigo kuma yau nake son na shigo gurinki saboda ina son komawa gobe kin san aikin na mu babu daga kafa"

"Haka ne to sai ka shigo"

Ya sauke kiran sannan ya fito falo yayi sallah yana sallamewa aka yi knocking, knocking din da ya tashi Fatima ta farka idonta har sun yi ja tsabar bachi, Aliyu ya karba ya rufe kofar.

"Yaushe muka zo nan?"

"Kina bachi little princess"

Ta yi mika

"Kai ka dauko ni?"

Ya risina inda take zaune yana kallonta da murmushi a fuskarsa.

"Eh kin tashi lafiya?"

Ta kalli falon.

"Nan gidanka ne?"

Ya daga mata kai.

"Ashe kana da wani gida Vito ma gida biyu yake da shi"

"Good taso ki wanke baki ki yi wanka sai ki ci abinci ki yi sallah"

Ta kalli shaddar dake jikinsa.

"Kai ka yi?"

"Eh"

Ya kama hannunta suka sauka tana fada masa kanta na ciwo, ya shiga da ita dakinsa ya nuna mata bandaki da yadda zata yi komai sannan ya fito ya dawo falon ya zauna yana taba wayarsa, har a lokacin sai da ya gwada kiran Number Emily ya ji ta a kashe. Yana ta nazarin abun da zai saka ta kashe wayarta kuma ta dauki lokaci har haka bata kira ba bayan sakon da ya tura mata, duniyar tunani ta dauko shi daga can bangaren Emily zuwa na Turhan idan ya ce be ji tausayin abokinsa ba yayi karya, ya san da zarar Emily ta bayyana a rayuwarsa komai zai zame masa daidai, sai dai kalamansa na dazun cewar da laifin Emily na amincewa ta aure shi ya sanyaya masa guiwa, jikinsa kuma yana ba shi cewar Emily ta yi gaskiya ko Ammy ta san da Fatima a matsayin jikarta abu ne mai wahala ta bar mata ita balle kuma Turhan, hakan ya saka shi ya ji lallai ya kamata ya bar garin Kaduna gobe gudun kar makamancin abun da ya faru a Airport ya sake faruwa, gashi kuma yana son ya san halin da Emily take ciki domin rashin samun wayarta da kuma maido masa da amsar sakonta ya saka shi a damuwa.

A tare suka ci abincin da Fatima tana ta fada masa mafarkin da ta yi, ya rigata koshi a dole ya jira sai da ta koshi ita ma sannan ya kwashe kayan ta bishi Kitchen tana kallo komai ta gani sai ta taba ta tambaya, ko ta fadi Momy na irinsa.

"Fatima Zaki iya zama a gidan nan ke kadai naje wani guri na dawo?"

Ta lake kafada

"Aa ba zan zauna nan ba, sai dai mu tafi tare"

"Ba zan dade ba kuma zan iya bar miki wayata ki yi game ki yi kallo"

"Duka na kalli komai na cikin wayar ni bana son zama"

Ya rasa ta ina zai fara rarrashinta ta zauna domin baya son tafiya da ita gidansu Kameela, na farko dai yana ganin hakan kamar cin fuska ne ga Kameela na biyu kuma iyayenta ma ba lallai su fahimce shi ba domin ko kowa be gane yar waye ba Kameela zata gane kuma karamin aikinta ne ta fallasa shi a gabansu. Ya mika mata dayar wayar da ita ya fi aiki da ita ya dauki wanda ya bata dazun ya saka aljihunsa.

"Wannan baki san me ke ciki ba, na kunna data zaki iya duba duk abun da kike so a YouTube ki kalli cartoon kuma ki sauke duk game da kike so, Momy ki na na san zata kira ta wannan wayar idan ta kira sai ku yi magana kamin na dawo?"

Ya karba ba dan ranta ya so ba, can ta kalli hotonsa dana Kameela dake makalle a falon.

"Waye wannan?"

"Matata ce"

Aiko take ta hade girar kasa da ta sama ya nukokoce kai.

"Ba zan zauna ba, so you have a wife"

"Yes Baby"

"I hate you"

Yayi murmushi

"I know I'm sorry, Bari na tafi na siyo miki chocolate da ice cream kinji?"

Sam ta ki yarda gaba daya mood dinta ya canja daya fada mata yana da mata, ita a tunaninta idan suka saba da shi zata iya dawowa gidansa ita da Emily su bar gidan Vito, amman tun da har yana da mata ai ba wannan damar.

"She's ugly"

"No she's not"

Ya amsa yana dariya.

"I want my momy"

"Bari na tafi na dawo sai na kaiki gurinta"

Daker ya samu ta yarda ta zauna sannan ya dauki dayan key din motarsa ya fice, daga gidan be zame ko'ina sai family house din su Kameela, a bangaren Mama Barakat ya faka ya fito yana tunanin ya kamata ace ya riko musu wani abu, gashi babu enough cash a aljihunsa, sai dai kuma babu yadda ya iya domin ya riga ya zo dama ace be zo ba ne sai ya tsaya ya nema.

Haka dai ya aje komai ya shiga bangaren da sallama, yaranta suka amsa masa suka gaishe shi sannan suka kawo masa drink da abincin, suka fice daga falon cike da tarbiya, babu jimawa Mama Barakat ta sauko sanye da wani lace mai tsada irin na su na yarbawa domin zama a cikin hausawa da kuma auren bahaushe be saka ta jefar da al'adarta ba, yaranta ma yawanci da yaren yarbanci take musu magana shiyasa duk sun iya yaren.

"Maraba maraba da Aliyu"

Ya sauka daga kan kujera ya zauna kasa saboda ta zauna akan kujerar.

"Haba zaunawarka mana"

"Aa nan ma ya wadatar, na same ku lafiya"

"Lafiya Kalau Alhamdulillah, ya hanya"

"Alhamdulillah"

"Maa Shaa Allah baka ci komai ba?"

"Already sai da na ci abinci na fito"

"Tohm, ina godiya dai Aliyu daka saurare ni kuma ka ni umarnina a matsayina na step mother din Kameela, hakan ya nuna kai yaro ne mai jin magana mai biyayya kuma mai tarbiya, na jidadi sosai Allah ya maka albarka"

"Ameen"

"ka shiga bangaren na su ne?"

"Aa na fara zuwa nan ne tukuna"

"To yayi kyau, da har jiya nake cewa ina son na sake kiranka, domin Kameela gaba daya ta fara fita hayyacinta abincin kirki bata iya ci, yarinyar nan tana sonka kai ma kuma na san kana son matarka, ni ban san me yake shiga tsakaninku kuke ta samun matsala ba"

"Kameela ta cika kishi ne, da abun da ya kai da wanda be kai ba duk na kishi ne a gurinta, bata tsayawa ta saurara kuma bata amfani da tunani kamin ta aikata abu, amman dai In Shaa Allahu ba za a sake jin kam mu ba"

"Hakan yayi kyau domin na tabbatar ita ma kanta a yanzu ta dauki darasi kuma zata gyara"

"Allah yasa"

"Ameen"

Mama Barakat ta ji kamar ta masa maganar Emily sai kuma ta ji rashin dacewar hakan, domin be kamata ta shiga tsabgar rayuwarsa ba, bayan kuma ta fada masa Kameela bata fada musu komai ba, sai kawai ta sauke numfashi ta ce.

"Tashi ka tafi, ka yi hakuri da duk abun da zaka ji ko ka gani gurin Hajiya, kasan ita uwa dole ta nuna bacin rai idan aka taba mata ya, balle ma Kameela bata fada mana dalilin dawowarta gida ba, amman dai duk yadda zaka yi ka yi iya kokarinka ka tafi da matarka, Allah ya kawar da fitina a tsakaninku"

"Ameen na gode Mama, tafiyar ta zama ta gaggawa ban riko komai ba, sai dai idan na koma In Shaa Allahu"

"Haba ina ce ai an zama daya, idan zaka zo gida sai ace dole sai ka riko wani abu? Yanzu ai mun zama iyayenka ba surukai ba, saurarena da kai yi kawai ka bi shawarata Wallahi ya fi duk wani abu da zaka ba ni na gode"

Yayi mata sallama ya tashi ya fice ta bishi ta kallon burgewa tana jin ina ma ace daya daga cikin yayanta yake aure yadda yake da biyayya da jin magana haka. Motarsa ya shiga ya yi mata key yayi reverse ya shiga bangaren mahaifiyar Kameela yana faka motarsa tana fitowa tare da kanwar Kameela cikin shirinta da alama fita zata yi, Aliyu ya fito mota ya nufo inda suke sai Hajiya ta yi kamar bata ga Aliyu, sallamar da yayi ma kanwar ce ta amsa masa shi ma cikin rainin wayo domin basa kallonsa da daraja gaba daya, ya mika mata gaisuwa bata amsa ba sai kokarin shiga mota take.

"Hajiya Gurinki na zo"

Ya dago ta kalleshi a wulakantacce kai kace ba shi da gata ko kuma dan talakawa ne.

"Ina jinka?"

Ya danna tafarfasar da zuciyarsa ke yi.

"Na zo ne akan maganar Kameela"

"Ina jinka bani da lokacin batawa fa fita zan yi, kuma saboda kai ka san ba zan fasa fitar da zan yi ba"

Ya hade yawu zuciyarsa na bugawa da karfi.

"Ina son na dauke ta mu koma ne"

"Kam uban nan"

Kanwar ta fada Hajiya kuma sai ta fito motar

"Ka dauke ta ku koma saboda a titi ka aureta? Ko kuma an fada maka bata da kowa? Ai ko baranta muka yi aka ba mu ita sadaka ba zaka shigo haka nan kawai ka dauke ta ku tafi ba, kuma ta inda aka hau ice ai ta nan ake sauka, kai karan kanka baka isa ka zo na tsaya tattaunawa da kai akan matsalarku ba, idan ma bikonta za zo toh ba kai ya kamata na gani ba, domin kai ka maida auren kamar wasan yara, haka kawai dan ta maka dadi zaka turo yarinya gidansu, yanzu kuma da ta yi maka dadi ka shigo kana fada min zaka dauke ta ku tafi, ai ba ni na baka aurenta ba ubanta ya baka aurenta kuma shi kansa yanzu yadda ransa ya bace ba lallai ne ya yarda yarsa ta koma inda ba a san darajarta ba, daman can abu ne da Allah ya riga ya tsara babu yadda za'ayi, amman da na san idan ka aureta haka zaka wulakantata kai da iyayenka ba zan yarda Kameela ta aureka ba ko zata mutu"

"Iyakar abun da zamu tattauna tsakanina da Kameela ne Hajiya ban da iyayena, domin iyayena babu abun da suka mata sai alheri, kuma ina tunanin da ace baki ga alamar za a rike Kameela da daraja ba, da ba za ku ba ni aurenta ba"

A take Hajiya ta zaburo masa da fada.

"Alherin me suka mata? Me suka kulla mata tun da aka yi auren? Duk tsabanin da kuke samu ummi ta taba tako kafarta gidan nan da sunan danta yayi ba daidai ba zata bada hakuri? Mahaifinka ma harkokin siyasarshi kawai ya saka a agaba, yanzu din ma ai ba kai ya kamata ka zo ba iyayenka tun da ba daga mu sai kai muka baka aure ba, kuma Kameela ba daga sama ta fado ba tana da gata, kar na sake ganin kafarka gidan nan da sunan biko wannan iskanci da tsageranci na surukan zamani ni ba zan dauke shi ba, kana neman bata min lokaci ina da abu mai muhimmamci a gabana"

Readers Also Read