Kenza eBookz

Abokin rayuwa Complete by khadeeja candy - Chapter 55

Abokin rayuwa Complete by khadeeja candy - Chapter 55

Abokin rayuwa Complete by khadeeja candy Chapter 55: Abokin rayuwa Complete by khadeeja candy Chapter 55. Daman ya raya a ransa Fatima bata gida, ya san da…

4,415 words

Daman ya raya a ransa Fatima bata gida, ya san da tana gidan ta yanzu ta matsa an kawota gurin Emily ko dan ta ga sabon gidan da Emily take. Aliyu be tambaya me ya faru ba, hawayenta kadai sun sanar masa ba ayi da dadi a gidan ba da suka iso gida ya faka motar sai ya fito ya bude mata ya riko hannunta ta fito yana janye da ita har cikin falonsu.

Saman kujera ta zauna shi kuma ya risina gabanta yana kallonta. Kamar jira take kawai ta fashe masa da kuka tana fada masa abun da ya faru. Yanayin fuskarsa ya sauya zuwa damuwa, sai dai be ce mata komai ba ya mike tsaye ya shiga dakinsu ya dauko wayarta data bari a gidan ya dawo falon, da kansa ya saka number Turhan dake wayarsa cikin wayarta yayi dialing sannan ya mika mata. Kallo daya ta yi ma wayar ta gane number Turhan ce saboda number bata Nigeria ba ce kuma akan rigimarsu ake ta san ba zai wuce ya kira mata Turhan din kai tsaye ba.

"Are you okay with that?"

Ta tambaya cikin kuka ya daga mata kai, sannan ta karba shi kuma ya zauna gefenta ya saka hannunsa daya cikin nata domin karfafa mata guiwa.

"Hello..."

Ta fada cikin sautin dake nuna ta yi kuka. Turhan yayi shiru be ce komai ba, ba dan kuma be fahimci mai magana sai dan kiran ya zo masa ba a lokacin da yake tsammani ba.

"Turhan Aisha ce Emily"

"Me ya faru? Me yasa kike kuka?"

Ya tambaya daga dayan bangaren.

"Na tafi ganin Fatima Ammy tace ka tafi da ni? Meyasa?"

Ya lumshe ido ya shafa goshinsa a tunaninsa zata fada masa Aliyu ya mata butulci ne.

"Bata min bankwana ba, tun da na yi aure bata zo gidan nan ba, a can bata san kowa sai kai, ta yi kankanta ta fuskanci kalubalen masarautarku a yanzu, kuma ni ina son ƴata, karka raba wannan soyayyar dan Allah, idan ma ba zaka yarda ta zauna a gurina ba, ka barta ta zauna a gurin Ammy mana, idan na so ganinta sai na tafi can na ganta, ka ce ba zaka sake cutar da ni ba miyasa ka yi haka?"

Tun da ta fara maganar be ce komai ba sai da ta gama.

"Kamin na dauke ta na yi magana ke, kuma alamunki be nuna min kin yarda ba, sannan na fada miki ba zan taba bari a taba ta ba, na zo da ita saboda ina sonta akusa da ni, kuma nan din ma gida ne, ya kamata ta san kowa kowa ya santa, idan tana bukatar zama a can ko nan zata zauna, amman gurin Ammy ba gurinki, Ammy ma da kanta ba zata bar ni na zauna da ita a nan ba, kuma ba zan so karatunta ya kasu guda biyu ba"

"Zaka dawo da ita kenan?"

"Zan dawo da ita, na yi nufin ta zauna na dan lokaci, amman yanzu tun da hankalinki ya tashi zan dawo da ita satin nan"

"Na gode, tana kusa da kai"

Yayi shiru na tsawon lokaci kamin ta ji muryar Fatima cikin haki tana fadin

"Momy?"

Emily ta kara matse wayar a kunnenta.

"Fatima, kina lafiya"

"Lafiya kalau, Momy i miss you"

"I miss you too baby, kina lafiya babu wani damuwa?"

"Babu, ina yin wasan doki yanzu, Momy na iya hawan doki, Momy Zaki zo?"

"Aa"

"I miss you"

"I know, babanki ya ce zai dawo da ke gurin Ammy za mu ga juna a can"

"Okay Momy i love you, ki rika kirana kinji Momy?"

"Tohm, idan wani yayi miki wani abun da baki ji dadi ba ki fadawa Babanki kinji"

"Tohm momy gidanki yana da kyau"

"Eh"

"Mu ma nan yana da kyau"

"I know, zan aje waya sai an jima"

"Okay bye i love you"

"I love you too"

Ta kashe kiran sannan ta kalli Aliyu.

"Na gode"

"Anything for you"

Ta kashe wayar. A ranar ta kwana da salama babu tunanin Fatima ko son sanin halin da take ciki. A kokarinsa na faranta mata kuma washe gari ya saka ta shirya da wuri ya sauke ta gidan Mama Baraka shi kuma ya wuce aiki bayan ya gaisa da ita cikin mutunci da girmamawa. After ya fice falon ne Mama Baraka ta kalli Emily tana murmushi ta ce.

"Kin yi dace mijin, Aliyu ya dade yana burge ni, wani lokacin har cewa nake be dace da Kameela ba, ashe an kaddara zai rabu da ita ya aure yata ne, ya zama sirikina, ina jindadin yadda yake nuna kulawa da damuwa akanki"

Emily ta yi murmushi.

"Yana da kirki, ga addini"

"Kusan fa duk wasu dabi'u da hallaya da ake so a gurin namiji Aliyu ya hada su, Allah yasa mutuwa ce zata taba, ga Ummi ma tana kaunarki baki da matsala ta ko'ina"

"Alhamdulillah"

"Allah ya datar da yan'uwanki su ma, su samu mazajen na kaurai"

"Ameen, har da ke ai Mama, ko Babansu Kameela zaki komawa?"

"Kai anya, ai aurena tsakanina da shi ya kare, kuma ni yanzu ba wani auren zan sake ba, kula da ku ya wadatar, sai idan na ga na aurar da duka yayana"

"Allah ya nuna mana"

"Ameen Ya Rabbi, kina da labarin Fatima?"

"Eh..."

Emily ta bata labarin abun da ya faru jiya..

"Daman Aliyu ya fada min yana ganin kamar bata nan"

"Ya zo nan ne?"

"Eh ya kan biyo, har alheri yake kawo min, da nake tambayarsa ya kike kuna da labarin Fatima yake fada min yana ganin kamar Turhan ya tafi da Fatima"

"Be taba min zancen ba"

"Ni da har na yi zaton wata kila yana jin tsoron ko kar Rito yake ki bitto? Ya cutar da ita ne da shi shiyasa Turhan din ya dauke ta suka koma can, sai yace aa ba wannan matsalar ba ce, ai Vito ya dade da mutuwa"

Wani rudududun Emily ta ji kamar saukar cida, ko a mafarki bata taba mafarkin Vito ya mutu ba, bata ma taba mafarkinsa tun da ta bar gidan?

"Ya mutu yaushe? Innalillahi Wa'inna ilaihirraji'un"

Ta kai tsaye numfashinta na rawa, jikinta ma haka nan da nan hawaye suka taru a idonta sai kuka.

"Miye abun innalillahi a mutuwar kafiri kuma mutumen da ya addabeki? Yake neman rayuwarki data yarki da ta mijinki? Daman baki san ya mutu ba?"

"Wallahi ban sani ba, Aliyu be fada min ba, babu wanda ya fada min, yaushe ne?"

"Zuwansa na karshe da yayi muke wannan maganar da shi"

"Miyasa suka kashe shi? Why not su kama shi su hukunta shi, be cancanci kisa ba"

"Mutumen dake kashe mutane? Kuma idan yana raye ke kanki ai rayuwarki na cikin hatsari"

"Kawai ya fada ne, amman ba zai iya komai ba, ba mamaki lokacin da ya turo min sakon baya cikin hayyacinsa ma, Vito ne mutumen da ya fara taimakon rayuwata, ya maida ni mutum na zama yadda nake a yau, miyasa za su saka masa ta wannan hayyar? Ban kyauta masa ba, ni ce sanadi be kamata ba"

Kuka take sosai kai kace Aliyun ne ya mutu ma, daker ta iya janyo wayarta ta kira Aliyu. Jin muryarta da kuka yayi mugun daga masa hankali.

"Innalillahi Wa'inna ilaihirraji'un, me ya faru Qalbina?"

"Me... Me... Me... Yasa kuka kashe Vi.. Vito?"

"Kun yi magana da Mama ne?"

"Mutumen da ya taimaki rayuwata ya so ni shi zaku kashe, ya zama kamar na ci amanar sa kuma sanadina ya rasa ransa, bayan ka yi min alkawarin ba zaka kashe shi ba"

Tana kuka tana maganar. Kashe wayar yayi sai ta kara fashewa da kuka sosai tana jin silarta komai ya faru, bata kyautawa Vito ba, be cancanci irin wannan sakamakon daga bangarenta ba. Babu jimawa Aliyu ya faka harabar gidan domin yana jin kamar ba zai iya jure rarrashinta ta waya ba, ba lallai ta fahimce shi ba.

Ya shigo falon babu ko sallama a lokacin Emily ta ci kuka sosai har idonta ya kumbura, Aliyu ya zauna kan kujera ita kuma tana zaune kasa rike da dankwali a hannu sai sharbar kuka take.

"Na yi rarrashinta har na gaji ta ki ta yi shiru"

Mama Baraka ta fada cikin yanayin damuwa. Aliyu ya kai hannu ya karbi dankwali ya rike kanta ya shafe mata hawayen.

"Wallahi Wallahi ba mu muka kashe shi ba, ba ta sanadinmu aka kashe shi ba, ko da aka aje an samu police har sun dauke garwarsa da ta matar da yake tare da ita, Chidimma sun kaita gurin aje gawa, lokacin da na nunawa Daddy sakon da ya turo miki, sai Daddy yace na sanar da Turhan saboda kar wani abu ya faru tun da har ya dauka Turhan kika aura ba ni ba, kuma Fatima tana gurinsu saboda kar ayi sake ya cutar da ita, na san Turhan ba zai saurare ni ba, ko ya dauki abun da muhimmanci shiyasa na aikawa Ammy da sakon, kuma na tabbatar mata ana kan nemansa, da sakon da ya turo miki aka yi amfani da Location din sim din aka gano inda yake a Lagos, amman ko da aka tafi sai aka samu gidan a rufe da shairdar police saboda an yi musayar wuta a gidan makota suka kira police amman ko da suka zo aikin gama ya gama sai gawa suka dauka, sun turo mana komai sun mana bayani, kuma da suka zurfafa binciken sai aka gano abokan sana'arsa ne suka masa wannan aikin, ba daga mu ba ne, Ki yarda da ni Aisha Wallahi tallahi a haka muka samu shi, sun turo mana hotuna, ban fada miki ba ne saboda ina jin tsoron kar hankalinki ya tashi"

Yana maganar yana share mata hawayenta da dankwalin. Mama Baraka ta ce.

"Daman su irin wadannan mutane ai basa tsawon rai, saboda sana'arsu ta shadari ce suna neman rayuwar wasu ana neman ta su"

"Haka ne, amman Wallahi ba daga mu ba ne"

Ta kwantar da kanta jikin Aliyun da ya sauko kasa yana kokarin fahimtar da ita. Mutuwar Vito wani abu da ya tsaya a zuciyar Emily kuma ya zauna zaman da ba zai taba yiyuwa ta manta ba, daga lokacin da ta ji labarin mutuwarsa sai ya zama bata da walwala saboda tana ganin shi ma ya cancanci farinciki, ta bangaren da take jin sanyi da ya kasance ba Aliyu ne ko ita ba ce siyar mutuwarsa, da ba zata iya yafewa kanta ba.

Haka Aliyu yayi ta fama da ita yana nuna mata amfanin mutuwarsa, da kuma tausaya mata har ta fara kwantar da hankalinta. Ba ma kamar ranar da Mama Baraka ta kirata ta sanar mata Ammy ta aiko da Fatima gidan Mama Baraka saboda bata san gidan Emily ba. Ammy ta yi hakan ne saboda bata son aika direbanta kai tsaye gidan Emily din ne, kuma daman bata san gidan ba saboda sanin gidan da Emily take rayuwa da Aliyu baya cikin lissafinta a yanzu. Mama Baraka ta aiko Misira ta kawo mata Fatima a ranar farinciki da far'a kamar su kashe Emily da Fatima. Sosai Emily ta jidadi da yarta bata rame ba, kuma bata labarta mata wani abu marar dadi da aka mata ba, sai ma jindadi da take fada mata da wasu abubuwa da ta iya a zuwanta garin, tana ta bata labarin yadda masarautar take da mutanen cikinta. [9/5, 12:32 AM] 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆: https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08?mode=ac_t

*🍒 ABOKIN RAYUWA 🍒*

*© Khadeeja Candy*

Page 7️⃣5️⃣

Kin dade kina sha'awar sayen kaya a wajen Khadeeja Candy amma ba ki samu dama ba? Kin shirya fara tanadin kayan Sallah ko na azumi tun yanzu? Ko kuma tanadin kayan auranki ko na 'yarki? To, ga sauƙi ya iso!

ADASHE NE NA GATA! Ki zuba kuɗi, ki ɗauki abin da kike so daga:

Sutura da zannuwan gado

Kayan kitchen

Kayan electronics (fridge, freezer, washing machine, gas cooker, da sauransu)

Talkami da jaka

Zanen gado

Frames (flowers decoration ko standing ones)

Console mirror

Boxes na Lefe ko na traveling.

Warmers iri-iri

Food flask iri daban-daban

Jugs da flask. Kai abin fa sai wanda rai ya so!

Sauƙi ya zo, za ki mallaki duk abin da kike so a wajen Khadeeja Candy cikin aminci da kwanciyar hankali, babu cuta babu cutarwa.

📌 Tsarin: Zubi ne wata-wata da kuma sati-sati. 📌 Akwai sharudda da ka'idoji.

Domin ƙarin bayani, ki/ka tuntube ni ta wannan lamba: 08036126660 Ko ta hanyar WhatsApp 👉 Danna nan https://wa.me/message/2Y7RIJEODZO2K1

Ko kuma ku yi join WhatsApp Group https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08?mode=ac_t

Thank you 😍 🙏

Yana warware hannunsa da yayi alwala ya ce.

"Ki shirya ina dawowa daga Sallah za mu tafi mu kaita"

"Da gaske wai ba zata kwana nan ba? Ni ma fa ina da hakki da ita"

Ta fada a shagwabe.

"Toh haka Mama Ta fada min, za su aiko a dauke ta da karfe 9pm"

"Kai ba zaka saka baki ba? Yaushe rabon da na ga yarinyar nan ta zo kuma sai ace ko kwana ba zata yi ba?"

"Yanzu indai ba son kike Turhan ya zo gidan nan da wukarsa ya kwantar da kaina ya yanka ni ba, ina ni ina saka baki a lamarin yarsa? Hakuri za ki yi idan suka ga kamar ba ki damu ba za su daina, damuwar suke so daman ai, ni na tafi masallaci"

"Allah ya dawo min da kai lafiya"

"Ameen I love you"

"I love you"

Fadawa junansu kalmar suna son junansu wata sara ce da Aliyu ya koya mata, ba ya fita be ji kamar daga bakin matarsa ba, ita ma bata yarda ya fice be fada mata ba, furta kalmar i love you yana kara danko kauna da soyayya a tsakanin masoya ko da yaushe musamman wadanda suke son junansu. Kamin da dawo ta zubawa Fatima abinci ta kara ci ta shirya ita ma ta shirya. Key ya dauka da wallet ya rike mata kofar falon ta fita sannan ya fita ya rufe, mota ma shi ya bude mata ta shiga ta rumgume Fatima a jikinta.

"Ba zaki barta ta zauna baya?"

"Aa na fi son ta zauna a jikina"

Ya kalli yadda ta lankwashe kai tana ta zuba masa shagwaba. Ba zai iya hanata ba, duk yana ganin kamar zaman zai taba ta, sai kawai ya kai hannunsa ya gyara zaman Fatima daga jikin Emily zuwa kafafuwanta. Sannan ya zagaye ya shiga dayan bangaren ya tashi motar yana tukin yana kai hannunsa ya daga Fatima idan ya ga ta kwanta jikin matarsa. Gaban wani katon shagon kayan alatu ya faka ya shiga yayi manyan ledodi uku ya dawo da su bayan mota ya zuba sannan yaja suka cigaba da tafiya.

Harabar gidan Mama Baraka suka faka Aliyu ya fara fita ya zagaya ya bude mata ya riko Fatima ta fito sannan ya riko hannun Emily ta fito ya bude back seat din ya dauko ledodin biyu ya rike.

"Ba uku na gani ba?"

Ya ja hancinta sannan ya rufe motar.

"Daya ta ki ce"

Ya dafa kafadarta kamar wata kawarsa.

"Uhm Qalbina, dazun Mama ta kira ta ce muna da bako tace na kawo ki bayan na dauki Fatima, sai na ce mata ta mana hakuri har sai idan zan kawo Fatima"

"Waye?"

"Sai kin shiga zaki gani"

"Turha?"

"Maybe..."

"Ba zan shiga ba, idan ya fada maka wata magana marar dadi fa? Kasan ba zan kyale ba"

"Ke yanzu kin shirya fada da kowa akaina kenan?"

"Har da kai kanka ba zan bari ba"

Ya bude ido.

"Eyyyy"

"Uhm"

"Ba za ayi komai ba, muje ciki dai"

Ya sauke hannunsa daga kan kafadarta suka jera suna tafiya, zuciyarta bata hararo mata kowa ba sai Turhan, wata kila zai fada mata wasu dokoki ne ko kuma yace zai sake dauke Fatima gaba daya. Shi ya fara rike mata kofar ta shiga sannan ya shiga, daman Fatima ta dade da shiga ta bar su a waje. Ta shiga da sallama tana ta rabon ido bata ga kowa a falon ba sai Mama Baraka da Fatima ke jingine da ita suna gaisawa. Emily ta kalli Aliyu yayi mata murmushi ta yi zaton karya yake dan kawai ya daga mata hankali ya fada mata haka, saboda haka ta taka masa kafa da kafarta sannan ta wuce kusa da Mama Baraka ta zauna suna gaisawa.

"Ya ce mim wai ina da baki, ashe ba gaske ba ne"

Mama Baraka ta kalli Aliyu.

"Gaskiya ne, Aliyu je ka shigo da su, suna nan BQ da ka zagaya baya ta nan kadan zaka gansu"

Sai da ya mike tsaye ya fice sannan Emily ta kalli Mama Baraka ta ce.

"Su waye Mama?"

"Wai tsohon mijinki ne... Ko Hamza ko Khaleefa, Ummi ta turo su gurina, saboda sun tafi can ita kuma bata nan sai ta kirani tace wai sun zo gidanta ne suna son magana da ke, ita kuma bata ma garin yanzu kuma tana ganin duk wani abun da ya shafe ki mijinki ya kamata a tuntuba ko ni"

Fuskar Emily ta sauya sosai zuwa wani yanayi mai kama da fushi da damuwa. Sai dai bata ce komai na har aka turo kofar falon Aliyu ya fara shigo sannan mahaifiyar Khaleefa ta shigo tare da shi da wani kawonsa, duk a kasa suka zauna sai Aliyu ne ya zauna a kujera, Emily ta kalli Khaleefa da rabin fuskarsa take a kone idonta na cika da hawaye rayuwar data manta take tunawa a yanzu.

"Toh ga su nan, sun min bayanin komai kuma sun roki alfarmar a kira ki su roki yafiyarki, na yi magana da Aliyu yace yanzu kina murnar zuwan Fatima a bari sai dare idan kun zo kawowata kar a yi ruining din moment dinku"

"Ina wuni Aisha"

Cewar Mahaifiyar Khaleefa. Emily ta kasa amsawa hawaye na sauko mata, kewar ɗanta ya dawo mata farko.

"Wata kila la lallai ki gane mu ba, duk dai Hajiya ta miki bayani kuma ta mana bayanin komai, ashe kin gane mahaifiyarki Aisha, muna miki murna ta fada mana kin yi aure shi ma muna miki fatan alheri, mun zo nan ne saboda neman yafiyarki, abubuwan da suka faru wadanda ba su yi dadi ba, musamman tsakaninki da Hamza, ki yi hakuri ki yafe masa dan Allah, Wallahi abubuwa masara dadi sun faru kuma mun san hakkinki ne, rayuwa ta zama babu dadi, musamman ma yanzu da ya koma gida saboda mai gidansa ya koresa saboda ke, ya fada mana ya ganki amman an hana shi magana da ke, tun da ya koma kullum cikin maganarki yake, daga karshe muka yanke shawarar zuwa kai tsaye mu nemi yafiyarki"

Cikin tsoro da fargaba Mahaifiyar Khaleefa take magana. Khaleefa ya dago idonsa da suka zare tsabar yunwa da wahalar ciwo ya kalli Emily da a yanzu ko kafarta be isa ya taba ba ya ce.

"Ki yi hakuri Aisha na san ban kyauta ba, na san na zalunce ki na cutar da ke, amman ki yafe min, Wallahi na yi nadama kuma na yi ta nemanki amman ban same ki ba, ban san inda zan ganki ba"

"Kowa ya cuceka sai kawai ya zo ya ce ka yi hakuri shikenan aikinka? Ka cutar da ni, ku biyun nan baku ragawa rayuwata ba, kara Ammy ta nuna min soyayya a baya, amman kai mahaifiyarka tana kallo ka tsake ni, na bar gari na kama hanyar da ban san kowa ba, kuka wulakanta ni kuka wofintar da ni saboda kawai ba ni da kowa, kasan ina da cikin ɗanka amman baka damu da halin da zan shiga ba, idan jininku ce za ku yarda ayi mata haka? Na haihu a titi kamar na haifi shege, na dinga wahala da shi kamar ba shi da uba, har ya bar duniya be san ubansa ba, wai saboda kawai ni mushirika ce na musulunta na bar addini na bi na ku, kuka rika kirana tubabbiya kowa ya kasa tsaya min, kuka hade min kai bana jin sanyi kowa, bayan kuma kai ka rabo ni da inda nake da gata, ka yi aure baka fada min ba sai da na ji, kuma haka be maka ba, kuka bini da gori kuka koreni gidan, sanadin wahalar da ma sha na haifi ɗana ba lafiyayye ba"

Tana maganar tana kuka sosai kukan dake taba zuciya, Aliyu kallonta kawai yake yana kara jin tausayinta da kaunarta suna shiga ransa. Khaleefa ya girgiza kai yana kuka.

"Wallahi hakkinki be barmu ba, bayan kin tafi rayuwa bata mana dadi ba, gidan da kika bar ni ciki ni da matar da na aura gobara yayi komai ya kone, ni kaina daker aka fitar da ni ciki, kalli yadda jikina yayi fuskar babu rabi Aisha, matata bata fita ba, sai yara biyu kawai data haifa min aka samu ceto wa, bangaren mahaifiya aka siyar a gidan aka shiga nema min magani amman har yau ban warke ba, saboda ba ayi treatment din yadda ya dace ba, yanzu haka idan yanayi ya sauya na zafi wutar tana taso min, sun ce akwai cutar har a cikin cikina, Wallahi ba mu da komai a yanzu Aisha, kuma na san hakkinki ne dan Allah ki yi hakuri ki yafe min, aiki ma ya gagara samuwa a gareni sai daker aka dauke ni a gidansu Alhaji Aliyu, ashe shi ma rabon na ganki ne, tun bayan da ya tura ni gida kuma ban sake samu komai ba, ana ba ni da albashin amman kullum gurin magani suke karewa, abun da za'a ci ma wahala yake mana, shin duk ba hakkinki ba ne? Ki yafewa min na zo neman yafiyarki ne da tambayar cikin da na barki da shi"

"Na haifi ɗanka da wahala da bakinciki da ciwo, ya rayu da rashin sanin waye ubansa, ciwo ya wahalar da shi, amman abubuwa sun yi sauki da na hadu da Vito, ya taimaki rayuwarmu kamin na rasa shi, ya rasu cikin ruwa ya fada ba tare da mun sani ba, da taimakon mijina an yi masa sutura an masa sallah an kai shi makabartar musulmi. Zancen yafiya kuma ba zan yafe ba, wannan shari'ar sai an yi ta"

Hankalin Khaleefa ya tashi jin cewar ɗan da aka haifa ya mutu, sai dai tashin hankalin be kai na jin furucin ba zata yafe masa ba. Shi da mahaifiyarsa da kawunsa da suka zo suka shiga bada hakuri. Aliyu ya mike tsaye

"Khaleefa, ina tunanin zai fi kyau ku kuma inda aka ba ku masauki a yanzu, gobe da safe idan kun karya sai ku koma garinku, Ummi na da numberka zan karba, duk lokacin da hankalin Matata ya kwanta ta ji zata iya yafe maka zan kiraka"

Khaleefa ya kalli Aliyu...

"Ranka ya dade ka fahimce ni, idan na koma ba tare da yafiyar Aisha ba, ban san iya abun da zai faru a gaba ba, wata kila rayuwar ba zata kai lokacin da kake zato ba"

"Amman tana cikin damuwa yanzu ba lallai ta yafe maka ba"

Mama Baraka ta fada.

"Bana cikin damuwa, na samu iyali yan'uwa da uwaye, ma samu miji ina da ya, rayuwa ta sauya na gamsu da abun da aka ba ni a yanzu, na gamsu da wannan sakamakon, kawai dai ba zan iya yafewa ba ne"

Aliyu ya nunawa Khaleefa hanya yana jin kamar ya kai masa duka.

"Please..."

Khaleefa ya kalli Emily yana mamakin yau shi ke zaune a kasa tana kan kujera, yau shi yaje neman yafiyarta tana kin yafe masa, yau ita take da mijin da yake kira da maigidansa, ga duniya ta samu tana gida mai kyau gaba daya ma ta sauya kamar ba ita ba, babu wanda zai fadawa cewar ya taba aureta ya yarda. Baya son jayayya da Aliyu saboda ta bangarensa albashi ke shigo masa duk da baya tuka musu mota a yanzu.

"Tohm na barki lafiya Aisha, ina jiran ranar da zaki yafe min, mun gode Hajiya"

Ya nufi hanyar fita yana hawaye mahaifiyarsa kuma na kuka wiwiwi kawunsa kam tun da aka shigo ya ma kasa cewa komai. Bayan sun fita Mama Baraka ta kai hannu ta shafa fuskar Emily.

"Dan Allah ina sake rokin yafiyarki, ki yafe min, duk ni ce silar shigarki wannan halin"

Emily ta kwanta jikinta tana kuka, Mama Baraka ma kuka take tana kara jin tausayin Emily sosai. Aliyu ya sauke kansa kasa. Fatima ta nufi inda Aliyu yake tsaye

"Wanene wannan? Ni ban gane abun da ake ba"

"Mahaifin London ne"

"Amman fuskarsa ta kone fatar wuyansa ta hade, gobara aka yi a fuskarsa?"

Aliyu yayi murmushi ya duka ya dauki Fatima ya fice da ita yana mata hira.

"Na Wahala, a baya rayuwa bata ɗanɗana min dadi ba, na shiga tasko kala kala, an nuna min ƙyama, babu wanda yake damuwa da matsalata, na zauna a gidan Khaleefa abun da zan ci ma sai ya gagare ni, sai na yi wankakau, ina jin ciwo ya hana ni zuwa asibiti sai a biyo kamar zan haifi shege, amman da amaryarsa ta samu cika suka rika murna, ni gaba daya ban haifi yarana da farinciki ba, mazan nan biyu ba su dandana min komai ba sai azaba da rashin imani, bana kaunar ko ɗayansu har abada... "

Emily tana fada tana kuka. Mama Baraka ta kasa cewa komai saboda ta san ita ce silar komai da ace bata jefar da yarta ba da duk ba wannan labarin ake ba. Suna haka yar da Ammy ke riko ta shigo da sallama Mama Baraka ta amsa Emily na share hawaye, har ta gaisa da Mama Baraka ta tambayi Fatima idonta na kan Emily.

"Fatima kamar tana waje ko? Tare da Aliyu"

"Okay, bari na tafi daman na zo daukar ta ne, babanta yana can yana jira"

"Okay tana nan waje"

Ta mike tsaye sai Emily ta nuna mata ledodin dake aje gefen kujera.

"Ki tafi mata da wannan kayan nata ne"

"Tohm"

Ta dauka ta fice. Aliyu be dawo falon ba sai da ya tabbatar hankalin matarsa ya ɗan kwanta da ya shigo sai yake ta kallon fuskarta, baya son yayi zancen ta sake tuna damuwar kuma he need to hug her ko zata ji sanyi dan haka ya ce.

"Bari mu tafi gida dare yana yi, direban ya dauki Fatima sun yafi"

"Eh ta shigo nan ai, yarinyar da ta kawo ta, ban san ko za su sake kawota ko kuma aa"

"Yace zai barta a gurin Ammy ai, idan tana nan da sannu zata dawo hannunmu, ita da kanta zata yi hankalin yin haka ai"

"Haka ne, haka yayi miki Aisha? Idan ba miki ba ke ma kina da hakki sai a masa magana"

Mama Baraka ta tambaya.

"Yayi ko ba komai ya kula da yarsa ba kamar Khaleefa ba"

Readers Also Read