Kenza eBookz

Kaddarar ramlah book 1 complete - Chapter 14

Kaddarar ramlah book 1 complete - Chapter 14

Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 14: Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 14. Ya rasa dalilin da yasa soyayyarsa ga Haneefah ta fara mutuwa sannu…

4,487 words

Ya rasa dalilin da yasa soyayyarsa ga Haneefah ta fara mutuwa sannu a hankali. Yana zaune zai yi tunani, zuciyarsa ta fara tambayarsa

"As'ad wai me yasa har ka aure ta? Me kake tunani lokacin da ka amince da wannan yarinyar da yanzu ta zame maka ƙalubale a zuciyarka?"

Sai kuma wani sashe na zuciyarsa ya raya masa wani abu daban.

"Amma fa, Haneefah ta iya sarrafa namiji sosai. Ba kamar Ayshatu ba, wacce aikinta kawai shi ne kwanciya a yi mata romancing. Haneefah mace ce cikakkiya mai zafin nama, mai iya sarrafa namiji ta kowanne ɓangare."

Wannan tunanin na Haneefah ya sa tsigar jikinsa miƙewa cikin wani yanayi mai ƙarfi. Amma sai wani mugun raɗaɗi ya sake tunasar dashi matsalarsa ta rashin lafiyar da gabansa ke fama da shi. Nan take yanayin jikinsa ya sauya, zuciyarsa ta ɗau zafi sosai.

"Ya zama dole in nemi likita cikin satin nan har ƙasar Turkey. Dole na duba lafiyar nan," ya faɗa da zuciya cike da ƙudiri.

Wayarsa ta shiga ƙara cikin ladabi da nutsuwa. Ya ɗaga wayar yana faɗin, "Assalamu alaikum."

Cikin girmamawa, hadimi daga fadar masarauta ya sanar masa cewa, "Mai Martaba yana bukatar ganinka da sassafe gobe cikin gaggawa."

"To, na ji. Za a same ni," ya ce cikin sanyin murya yana sauke numfashi.

Cikin zuciyarsa sai ya raya, "Kenan Haneefah ta kai ƙarar nan zuwa fada? Ashe ta gama tsinke igiyar zamanmu kenan?"

Nan take ya kira P.A ɗinsa yace masa, "Ka shirya tafiya nan da ƙarfe takwas na dare. Ina so komai ya zama shirye."

Da isa gidansa, As'ad bai tsaya ko'ina ba sai kai tsaye zuwa bangaren Ayshatu, wanda aka kawata da kayan ado na zamani, dukiyarsa ta bayyana ta ko'ina cikin ɗakin. Ayshatu tana zaune kan kujerar alfarma, tana waya cikin yanayin ƙasaita, kafa ɗaya kan ɗaya tana wasa da igiyoyin gyalen jikinta.

Ganin As'ad ya shigo yasa ta yanke wayar cikin sauri, ta taso cikin ɗan kissa da ladabi, ta rungume shi cikin wani ɗan sanyi da sassanyar murya tana cewa, "Sannu da zuwa, Habibie. Na jima ina jiran dawowarka."

As'ad ya yi murmushi kaɗan yana dubanta da tausasawa, "Ayshatu, yaya gidan yau?"

"Lafiya ƙalau, Alhamdulillah." ta amsa masa cikin wata irin ƙayatacciyar murya mai cike da jan hankali.

Ya ɗan lumshe ido cikin ɗan gajiya yace mata, "Ina da kiran gaggawa daga fada. Mai Martaba yana nema na yanzu. Ko za ki iya shirya wa mu tafi tare?"

Ayshatu ta ɗan yi murmushi cikin salo da jan hankali tace, "A'a Habibie, yau kam jikina ba ƙwari sosai. Har yanzu ban huta ba. Amma ka je dai, ka gaida min Mai Martaba sosai, Allah ya kiyaye mini kai."

Ya ɗan murmusa ya ɗaga kai, ya fita cikin sanyi da girmamawa.

Amma yana fita, Ayshatu ta koma zaune cikin wata irin muguwar dariya ta mugunta da ƙissa. Dukiyar gidan da ƙayatattun kayan ado da fitilun zinariya suka haska fuskarta mai cike da murna. Tuni direbanta ya sanar da ita cewa Haneefah ta bar gidan, kuma wannan abu ya zame mata babban farin ciki mara misaltuwa.

"Ai wallahi babu kai babu wata diya mace a duniyar nan, As'ad. Yanzu na gama cin nasarar mallake zuciyarka gaba ɗaya." Ta ce cikin yanayin kissa da cikar buri, zuciyarta cike da alfahari da gamsuwa.

*****

Hajja zaune take a saman wata babbar kujera ta zinariya mai shimfidar tattausan bargon alharini. Fuskar ta cikin damuwa sosai, idanunta sun yi jajir saboda zafin hawaye da ke neman cinyeta. Kanta ya sunkuye tana ta share kwallar da take fita, zuciyarta na cigaba da raɗaɗi kamar ana watsa mata garwashin wuta.

Fiddausi dake zaune kusa da ita, cikin tsananin bacin rai ta sake kallon mahaifiyar tata ta ce cikin yanayi mai kaifi,

"Hajja wai ba kuka za ki yi masa ba? Kin manta irin abinda kika yi mini lokacin da matsalar mijina ta taso? Wannan abu da kika yi maraba da shi ne, kika goyi bayana . To yanzu me ya canza da kika shiga damuwa haka?"

Hajja ta ɗago da idanuwan da suka yi jajir saboda kuka, tana kallon Fiddausi da wani irin yanayi na rauni da takaici. Baki na rawa tace,

"Ba za ki gane ba Fiddausi. Wallahi ba za ki fahimci irin tozarci da wannan yarinyar ta jawo mana ba. Ba za ki iya fahimtar yadda zuciyata ke raɗaɗi yanzu ba. Wannan magana ta rage wa As'ad daraja, girmansa ya sauka, mutuncinsa ya karye! Kuma wallahi zuciyata bata yarda cewa Haneefah gaskiya take fada ba. Wannan makircin Fulani Maryam ne! Ina sane da yadda take!"

Fiddausi ta girgiza kai cikin takaici tana cewa,

"To ai ni na san wannan. Wallahi ni ba zan yi kaffara ba! Kin san wannan matar nan tasa mai suna Ayshatu? Wallahi malamai take bi tana hana masa zama da matansa. Wannan matsalar ba daga As'ad ba ce, daga wannan matar ce! Ku dai kalle ta fa da kyau, baku ganin yanayinta?"

Hajja ta ɗan dago hannu tana jan numfashi cikin rawar murya tace,

"Ke Fiddausi ki yi shiru mana! Ai matar mutum kabarinsa ce. Duk yadda kika ga mutum da matarsa, to, Allah ya tsara hakan. Idan akwai matsala to daga Ubangiji ce. Amma wallahi matan As'ad ba masu zama bane, na riga na san haka tun farkon faruwar wannan lamarin."

Fiddausi ta ɗan yi shiru, sai kuma ta ce cikin yanayin sanyin murya da tausayi,

"To Hajja na yi shiru, amma gaskiya ki daina kuka, ki koma ga addu'a domin ita kadai ce mafita. Kukan ba zai magance komai ba. Yanzu lokaci ne na addu'a da neman taimakon Ubangiji."

Hajja ta sake gyara mayafinta, zuciyarta na cike da damuwa, hawaye kuma na cigaba da bin kuncinta a hankali cikin zafin zuciya.

***

A wannan lokacin kuma, a wani ɓangaren daban na garin, As'ad yana cikin wani yanayi na tsananin kunci da damuwa. Duk da cewa ciwon kai yana yi masa azaba, amma zuciyarsa ce ta fi jin raɗaɗi saboda wannan mummunar magana da Haneefah ta kai fada.

Zuciyarsa ta ɗaure tamkar an yi masa ɗaure da igiyar azaba, yana ganin yadda wannan abu zai yadu cikin gidan sarauta, za a zagaya da zancen ko'ina. Wannan ba ƙaramin tozarci bane ga mutum mai daraja irin tasa. Duk dukiya da izzar da yake ji, sai ya kasa jure wannan tozarci da aka masa.

Ya zauna a gefen gadon alfarma mai shimfida ta musamman, idanunsa suka cika da hawayen zafi. Ya lumshe ido yana ambaton sunan Allah, zuciyarsa ta cika da raɗaɗin takaici,

"Ya Allah... Wannan tozarci ne fa da aka yi mini haka? Ta yaya zan iya kallon fuskar Hajja bayan wannan abun kunyar da aka yi mini? Ta yaya zan sake tsayawa cikin jama'a?"

Da wannan tunanin yaji tsigar jikinsa na tashi saboda tsananin ɓacin rai. A gaggauce ya mike ya shiga cikin bandaki wanda aka kawata shi da fitilu masu ƙyalli da madubai Ya yi wanka cikin hanzari, ya shirya cikin wasu kayan alfarma masu kyau da ɗaukar ido.

Da ya fito daga ɗakin nasa kai tsaye motarsa Mercedes Benz ta alfarma ce mai launin baƙi ta fisgi hanya zuwa filin jirgin saman da jirginsa ke jira domin ɗaukarsa. A cikin yanayi na damuwa da tashin hankali suka isa garin da za su sauka.

Ko da suka isa babban otel ɗin da aka kama masa, mai ɗauke da ɗakuna masu ƙyalli da alfarma, duk wannan bai hana zuciyarsa raɗaɗi ba. Duk gajiyar da ta yi masa yawa a jikinsa, amma bacci ya ƙi zuwa gare shi. Ya juya gefe gefe yana jin zuciyarsa na tafarfasa cikin damuwa.

Ya sake ɗago idanunsa da suka yi jajir da zafin damuwa ya kalli halittar gabansa wadda take kwance ba tare da wani motsi ba. Ya ji wani azababben raɗaɗi yana cizon zuciyarsa, cikin wata irin damuwa da takaici ya lumshe idanunsa yana furta,

"Ya Allah, ka kawo mini mafita daga wannan jarrabawar da ka jarrabce ni da ita. Wannan abu ya fi ƙarfin zuciyata da tunanina."

Sai dai ko yaushe ya rufe idonsa wannan mummunar magana ce take cigaba da yawo cikin zuciyarsa da tunaninsa, tana ƙara masa raɗaɗin da ya gagara zama cikin ransa.

Nana hadiza

09030569336ƘADDARAR RAMLAH

SHAFI NA TALATIN

Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!

Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!

Domin biyan kuɗi:

Acc Name: Bilkisu Sani Kaura

Acc Number: 7040402435 (OPAY)

Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:

09030569336 ko 07040402435

Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a

Arewabook @nanadiso10

https://www.arewabooks.com/book?id=6813670d91815df57bc25693

********

Da ƙyar As'ad ya samu bacci ya ɗauke shi, amma kafin gari ya waye sai ya farka, idonsa na cigaba da raɗaɗin da damuwa ta haifar masa. Da asubah ya tashi ya yi sallah cikin wata irin zuciya mai nauyi, daga nan ya zauna yana ambaton Ubangiji da addu'ar neman mafita.

Bayan ya gama addu'o'insa, sai ya ɗauki wayarsa cikin sanyin jiki ya kira Hajja. Duk da cewa zuciyarsa tana cike da kunya da nauyin wannan magana, bai iya hana kansa neman ta ba, saboda yasan tana cikin damuwa sosai hajja uwa ce wacce take mutukar son yaranta kasancewarta ita ba jinin sarauta ba Allah yayi ne dai ta auri sarkin.

Kusan sau uku wayar tana ƙara amma babu amsa, sai daga baya Hajja ta ɗaga murya a sanyaye cikin tsananin raunin zuciya tace,

"Assalamu Alaikum, As'ad."

Sai da muryarsa ta ɗan yi rawa kafin yace,

"Wa'alaikumus salam Hajja. Ina kwana? Ina fata lafiya lau."

Hajja tayi ajiyar zuciya sosai, ta share kwallar da ta fara zubo mata tace cikin nutsuwa,

"As'ad, ba lafiya ba ce ka sani. Wannan abu da ya faru yana neman girgiza mana mutunci da martaba. Wallahi baƙin ciki na ya fi ƙarfin abinda zan iya bayyana maka."

As'ad ya lumshe ido cikin rauni yana jin zuciyarsa ta ƙara damuwa.

"Ki yi hakuri Hajja. Allah ya sani ba da sanina bane wannan abu ya faru, kuma wallahi Na gwada magunguna kala kala amma munkasa ganin matsalar a likitance ance kalou nake amma zanfita asatin nan naga wani babban likitan ina cikin wani irin hali da ba zan iya bayyana miki ba."

Hajja ta ɗan yi shiru kafin ta ce da shi cikin hikima da nutsuwa,

"As'ad, ka san kai ɗan gidan sarauta ne. Kuma haka Ubangiji yake jarrabar bayinsa na ƙwarai. Ka daure zuciyarka, ka karbi ƙaddara, amma ka yi ƙoƙari ka nemo hanyar magance matsalarka cikin sirri da hikima. Kuma kar ka manta addu'a ce mafita ga komai."

Cikin jin daɗin wannan magana ya gyada kai kamar tana ganinsa, yace,

"Insha Allah Hajja, zan yi ƙoƙari. Na gode da wannan kalmar karfin guiwa."

Ta sake cewa da shi cikin kulawa,

"Ina maka addu'a dare da rana, Allah ya fito maka da gaskiya kuma ya ɗaukaka maka darajarka. Kada ka bari wannan abu ya karya maka zuciya ko kuma martabarka."

Cikin raɗaɗin zuciya yace,

"Na gode Hajja. Allah ya saka da alheri."

Ya kashe wayar zuciyarsa ta ɗan yi sassauci, amma kuma nauyin damuwa bai sauka ba.

*****

Dagarin Allah yawaye, As’ad ya sakko kasan hotel din inda motar alfarma ta fada ta zo ta ɗauke shi kai tsaye zuwa fadar mai martaba. Zuciyarsa tana cigaba da buguwa cikin damuwa da fargaba, saboda ba shi da tabbacin yadda mai martaba zai karɓe shi.

Lokacin da aka sanar da isowarsa, Wambai ya shigo da sauri cikin ɗakin mai martaba ya sanar da zuwansa. Mai Martaba ya ɗaga hannu cikin alfarma ya ce,

"A shigo da shi."

A hankali As’ad ya shigo cikin fadar, inda ya samu mai martaba zaune cikin matsayinsa na sarki, sauran manyan fadawa da sarakuna masu martaba suna zaune cikin girmamawa. Ya durƙusa gaban mai martaba cikin ladabi yana cewa,

"Ranka ya daɗe, barka da safiya."

Mai Martaba ya ɗan kalle shi da ido mai cike da iko da izza, sannan ya ce,

"As’ad, kana sane da abin da ya kawo ka nan yau. Wannan magana da ta fito daga bakin matarka, ta girgiza martabar wannan fada kuma ta girgiza martabarka kai kanka."

Cikin sanyin murya, As’ad yace,

"Ranka ya daɗe, wallahi wannan abu ya fi ƙarfin tunanina.” Yafada yana jin wata matsananciyar kunya da kuma tozarta.

Mai Martaba ya ɗan daure fuska yace,

"Ka san dai irin gidan da ka fito, kuma ka san darajar da ke gare ka. Ban yi tsammanin zan taba jin irin wannan magana a cikin dangina ba. Amma saboda na san kai mutum ne mai hankali da nutsuwa, zan ba ka damar ka binciki matsalarka cikin sirri, kafin wannan magana ta fita daga ikonmu gaba daya."

As’ad ya yi numfashi cikin jin sauƙi, yace cikin ladabi,

"Na gode ranka ya daɗe.”

Bayan anyi sallar azahar Mai Martaba Sarkin zaune yake a saman kujerar sa, yana sauraron karar Haneefah da As’ad cikin natsuwa da izza, a gefe kuma manyan fadawa da dattawan gidan sarauta na kallon shari’ar da zuciya ɗaya.

Haneefah ta shiga zauren cikin tsantsar kamala da nutsuwa. Shigar alfarma ta mata ce a jikinta, fuskarta cike da tsantsar ladabi.

Da ta durƙusa cikin ladabi, ta ce cikin muryar da ta cika zauren

“Mai Martaba, ranka ya daɗe. Ni Haneefah, bana iya ci gaba da zaman aure da As’ad.”

Wani ƙaramin surutu ya fara tashi daga gefe, amma Mai Martaba ya ɗaga hannu alamar shiru.

“Me yasa, Haneefah?” ya tambaya cikin tsantsar natsuwa da hikima.

Ta sadda kanta ƙasa, ta ce

“Auren da ba ya cika min buƙatata a matsayin mace bai da daraja a wurina. Ina girmama As’ad, amma gaskiya itace zan faɗa gabansa ba ya aiki. Kuma ni ina buƙatar zaman aure na gaskiya.”

Zaure ya dauki shiru.

As’ad ya durƙusa, bai ce komai ba. Kamar dutse, ya makale a inda yake. Kamar izzar da ke jikinsa ta narke gaba ɗaya.

Mai Martaba ya dafe sandar zinariya, ya ɗan jinjina kai cikin takaici.

“Zancen da ya fito daga bakin mace cikin gaskiya, ba a rufa shi da ƙarya. Idan har haka lamarin yake, kuma ba wata mafita, to…”

Ya juya ya kalli As’ad,

"Ka saketa cikin mutunci. Kuma na baka izinin a ɗaura maka aure da mace mai nutsuwa da hikima wadda zata kula da kai da darajar gidan sarauta."

As’ad ya kasa ɗaga kai. Cikin sanyi da radadi, ya furta:

"Na saketa."

*****

Cikin sanyin dare mai cike da sanyi da hasken farin wata, motar As’ad ta fice daga farfajiyar fadar sarki cikin wata irin hanzari. Duk da ƙanƙanin wannan tafiyar, ya ji kamar ya shafe shekaru masu yawa yana barin wurin. Ba haka ya so ba, ba haka ya yi tunani ba, amma shi fa mutum ne, ba shi da iko akan ƙaddarar Ubangiji.

Gaba ɗaya fuskarsa ta sauya daga As’ad ɗan gidan sarauta zuwa As’ad wanda aka ɗora masa tozarci mai zafin gaske. Kamar wanda aka ɗaure wa igiyar kunya da takaici, zuciyarsa tana azabtar da shi, tana ƙara masa raɗaɗin jin cewa ya rasa abin da ya fi kowane abu daraja ga namiji girman mutunci.

Direbansa ya kai kallonsa a hankali cikin madubin mota, sai dai kuma bai iya tambayar komai ba, domin ganin yadda zuciyar Yarima As’ad ta matse cikin mayuwancin hali.

Lokacin da suka iso hotel , ko tsaya gaisawa da masu hidima bai yi ba kai tsaye ɗakinsa ya nufa, yana jin kansa kamar an ɗaure masa nauyin da bai taɓa jin makamancinsa ba. Bai cire tufafinsa ba, bai yi wanka ba, ya zauna bakin gadonsa cikin tashin hankali, idanunsa suka cika taf da hawaye masu dumi.

“Ya Allah, wannan wane irin abu ne ya same ni haka?” ya furta cikin sanyin murya mai cike da raɗaɗin zuciya. “Ni As’ad, an kira ni mara kuzari, rago, wanda mace ba ta bukata?”

Ya lumshe idanunsa, zuciyarsa ta yi masa zafi sosai har yake jin kamar tana ƙuna. Tunawa da yadda Haneefah ta zubar masa da mutunci a gaban Mai Martaba da manyan fada ya ƙara cizon zuciyarsa. Ya rasa yadda zai iya haɗa ido da kowa a cikin gidan sarautar nan, musamman mahaifiyarsa Hajja Sa’adatu.

“Babu wata uwa da za ta so jin cewa an kira ɗanta da marar amfani, wanda ba shi da wani ƙarfi ko kuzari,” ya sake faɗa wa kansa cikin tashin hankali, yana jin numfashinsa na fita da ƙyar saboda ƙuncin zuciya.

Gaba ɗaya ya kasa kwanciya, bacci ya ƙaurace masa, kuma duk lokacin da ya lumshe ido, sai maganganun Haneefah suke dawo masa suna zagaye masa cikin kai kamar faifan rediyo. Ba zai iya jure wannan tozarci ba, ba zai iya zama ya zuba ido ba. Sai kawai ya ɗaga waya cikin hanzari, ya kira PA ɗinsa yana umarnin cewa

“Ka shirya komawa gida, bana son ko da kwana ɗaya ya riske ni a wannan gari. “

PA ɗin nasa ya yi ƙoƙarin yi masa magana, amma muryar As’ad ta fito da tsananin damuwa da ƙarfin zuciya

“Ban buƙatar tambaya, kawai ka tabbatar jirgin ya shirya kafin gari ya waye.”

A cikin wani ɗan lokaci kaɗan, komai ya shiryu domin tafiyar Yarima As’ad. Da sassafe, jirgin As’ad ya bar filin jirgi yana mai ɗauke da zuciya mai cike da damuwa da nauyin kunya.

Yana zaune cikin jirgin, idanunsa sun yi jajir da rashin bacci, zuciyarsa ta ƙara cika da raɗaɗin da ya hana shi nutsuwa.

Hawayen da suka taru cikin idanunsa suka fara gangarowa kan fuskarsa a hankali. Bai yi tunanin ranar da zai shiga irin wannan halin ba. Sai dai babu yadda zai yi, domin haka Ubangiji ya tsara masa ƙaddararsa.

******

A wannan lokacin kuma, gidan sarautar ya zama tamkar an kunna wutar gulma wacce ke bazuwa da hanzari a dukkan lungu da saƙo na fada. Ba wani abin da ake magana sai tozarci da abinda ya sami Yarima As’ad.

Wasu daga cikin fadawa sun taru suna hirar ƙasa-ƙasa da ƙanana maganganu masu cike da izgilanci duba dashi As’ad baya shiga harkar kowa baya magana da kowa komai nashi daban da yaran sarki shiyasa dayawa aka tsanesa duba kuma da irin dukiyar da Allah yabashi fiye da kowa ciƙinsu.

“Wai ku ji As’ad Ashe wannan girman kan nasa duk na banza ne kawai! Mutum kamar shi ace wai bai iya komai ba wajen mace?” wani daga cikinsu ya ce cikin dariyar ƙasƙanci.

Wata kuma ta ɗauki zancen tana cigaba da faɗin

“Wannan magana ta wuce tunanina. Ai wallahi sai yanzu na gane cewa duk wannan izzar da yake yi mana a fada, babu komai a ciki sai rawar kai kawai. Ashe gabansa ma bai iya tashi ba?”

Wata mai hidima tana zaune tana tsintar wake ta ce cikin sigar zargi

“Ai ina ganin laifin matan nan nasa ne, wato Haneefah. Duk yadda mutum yake ai kamata yayi ta rufe masa sirri. Wannan fa ba karamar magana ba ce, sai ga shi har gidan sarki ta kai shi!”

Wata kuma mai hikima ta jinjina kai tana cewa cikin sigar nasiha

“Ai gaskiya ba abin dariya ba ne. Wannan magana ta shafi martabar gidan sarautar gaba ɗaya. Amma yanzu an riga an yi, kuma an ji da kunne, an gani da ido. Yarima As’ad dai ya gama shiga tasku a idon duniya.”

Nana hadiza

09030569336ƘADDARAR RAMLAH

SHAFI NA TALATIN DA DAYA

Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!

Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!

Domin biyan kuɗi:

Acc Name: Bilkisu Sani Kaura

Acc Number: 7040402435 (OPAY)

Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:

09030569336 ko 07040402435

Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a

Arewabook @nanadiso10

https://www.arewabooks.com/book?id=6813670d91815df57bc25693

********

Fulani Maryam zaune take cikin ɗakinta mai kyau, tana ta murmushi kamar wadda aka ba labarin da take jira. Ta yi shiru, tana murza tasbaha, amma zuciyarta cike take da farin ciki. Duk wanda ya kalleta, sai ya san tana jin daɗi “Alhamdulillah. Yau burina yacika As’ad ya ɗanɗana abinda na daɗe ina jira.” takarasa faɗa tana kyalkyalewa da dariya. Ta kwanta cikin kujera mai laushi, ta lumshe idonta tana faɗin “Mutumin da ya raina ni, wanda ya wulakanta diyata, gashi yanzu duniya na masa dariya. Lokacin da haneefah tafara nunawa tana kaunarsa yace Allah yakiyaye ya haɗa zuri'a da maryamu uwarsa kuma ta mulkeni yanzu kuma da karfin iko na Nasa ya aureta nakuma yi Amfani da'ita sunansa yaɓaci ɓaci na har abada tabbas wannan iitace nasara. Kuma wace ta karya shi? Haneefah Diyata. Ashe mace na iya fasa gini da magana guda!”

Ta yi dariya mai ɗan ƙara, “Duk kuɗinsa, duk mulkinsa, ba su iya kare shi daga mace ba! Yanzu As’ad ya zama abin dariya!” Sai ta juya ta duba hasken fitila a ɗakin, ta ce “Na fi jin daɗi ne saboda mahaifiyarsa Hajja tana cikin damuwa. Ai jin daɗin nasara shi ne lokacin da wanda ya ƙyashi ke kuka, ke kuma kina dariya.”

********

Tunda Sarauniya Amina matar sarki ta farko ta shigo zauren fadarta, dariya kawai take ta yi, irin wacce ke bayyana ƙosasshiyar zuciya da shirin badala. Ta kalli baiwarta da idon umarni “Ki bamu guri.”

Baiwar ta ja da baya cikin ladabi, ita kuwa Sarauniya ta zauna bisa kujera mai madaurin sarauta, ta ɗauki wayarta ta kira Ayshatu wacce take ɗaukart kamar ’ya’yanta dan itace sanadi har tasamu ta auri As'ad ita tashige mata gaba tana tunanin ta wannan hanyar ce zata mulkeshi sai gashi data auresa batama samun ikon ganinsa kamar yadda taso shiyasa ta dora mata tsanar duniya duk da batasan tana mata kiyayya ba kuma itace wacce take zuga sarki akan a aura As'ad mata. Ayshatu ta ɗauki kiran, Sarauniya Amina ta fara magana cikin nuna mamaki da zazzafar dariya “Garin yaya kika yi wannan sakarci da har za a samu damar zagin mijinki? Kin san irin abinda Haneefah ta ce kuwa?”

Ayshatu ta ɗan runtsa ido, cikin nutsuwa ta ce “Lafiya kuwa? Me ke faruwa? Me haneefah tace akan habibie??”

Sarauniya ta amsa da muryar da take hade da dariyar raini “Haneefah tace mijinki ba shi da ƙarfin biyan mace bukata! Kin ji kalmar nan da kunnuwanki?”

Ayshatu kuwa bata bari a zubar mata da mutunci ba. Cikin natsuwa, amma da ɗsn dariya, ta ce “Ai wannan ce matsalarsu. Ni da haka nake son abuna . Na fi son zaman lafiya da kwanciyar hankali, ranki ya daɗe. Abuna ya jima yana min dadi ba tare da damuwa ba.”

Sarauniya Amina ta ɗaga gira, mamaki da baƙin ciki yacika mata rai tabbas tasan halin ayshatu zatayi abunda yafi haka ma makirace ta karshe sannan shu’uma ce sosai sai tacigaba da kallon wayar kamar tana nazarin Ayshatu sai kuma tace “To shiyasa ashe baki ci gaba da haihuwa ba kenan? Duba shekarunki da lafiyarki, amma yara biyu kacal?”

Ayshatu tace “Yara biyu da Allah ya bani sun ishe ni. Banson hayaniyar yara da yawa kin san halina. Ni zaman lafiya da kwanciyar hankali nake so. Dan su ne ginshikin farin ciki na.”

Ganin kar tayi mata fitsara yasanyata Sukayi sallama cikin ladabi, Ayshatu ta kashe kiran. Amma da zarar an katse, sai Sarauniya Amina ta fashe da dariya mai ƙarfi dab ita kaɗai tasan abunda ke ciƙin zuciyarta.

“Babu As’ad, babu mulki har abada! Na nisanta shi da iyayensa yanzu kuwa zai zama cikakken wulakantacce, In shaa Allahu! Har hauka ma sai yayi!” Sai ta fashe da dariya, wacce ke cike da alamar mugunta da makirci.

************

Da sallama mai rauni ta turo ƙofar babban ɗakin, Jamila ta shigo da wani irin ɓacin rai da harararta kaɗai za ta iya cin zuciya. Dakin ya yi shiru, sai bushewar numfashinta da gigin zuciyarta suka cika sararin wajen.

"Ke Haneefah! Wannan aikin da kika yi kina ganin daidai ne? Wannan mutumin da ya daga ki sama, wanda ya dora ki akan turbar rayuwa, wanda ya cire ki daga duhu ya miki hidimar aure ya sanyaki amakaranta tun kina karama har yafiddake waje? yanzu shine kika jefa cikin kunya da tozarci?"

Jamila ta taka zuwa gaban Haneefah, tana duba ta kamar wadda take so ta fahimci dalilin da yasa ’yar uwarta ta aikata abin da zuciyarta ta kasa ɗauka.

"Ko da kuwa gaskiya ne, shin bazaki rufa masa asiri ba?Wannan shine sakayyar alherinsa?"

Anty Jamila ce, ɗiyar Fulani Maryam macce mai tsananin bin doka da tsari. A gidan su, mutane suna kiranta "Malama", saboda tsantsar kamun kai da tsoron Allahnta. Da wani bai san asali ba, zai rantse ba ’yar Fulany Maryam bace.

Haneefah, da idanu sun cika da hawaye masu nauyin zuciya, ta ce da ita ƙasa-ƙasa,

"Yaya Jamila, ba sharri nake ba... gaskiya ce kawai nake faɗa. Kinsani gaba, sai masifa kike. Amma wallahi, ban masa

ƙarya ba."

"Zaki rufe min baki ko sai na miki illar da ba za ki manta ba? Mama ke goyon bayanki, kina iskancin da kikaga dama. Sai dole kinyi masa sharri kamin ki rabu da shi? Kin manta ke aurenki biyar yanzu? Wannan na shida ne, wallahi na rantse, ba da son ransa ya aure ki ba. Kuma ki rubuta ki ajiye sai kinyi danasani wallahi."

Fulani Maryam ta shigo cikin kwanciyar hankali, amma idonta ya cika da baccin rai

"Jamila, tashi ki bar min ɓangaren. Ba za ki ci mutuncin yarinya a idonna ba. Kin manta ita fa ‘yar uwarki ce. Idan har ta yi kuskure, ai ba haka ake gyara ba. Wani banza marar kishin ‘yan uwansa ne kike fushi akansa?"

Jamila ta kalli mahaifiyarta da kai a ƙasa, ta dan furta cikin wata murya mai rauni,

"Allah ya baki hakuri Mama. Sai an jima."

******

Tunda jirgin alfarma ya sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe, Abuja, komai ya kasance a cikin tsari na musamman. Motocin convoy ɗin mai girma As'ad manyan *Mercedes Maybach* da *Range Rover Autobiography* sun ɗauke shi kai tsaye zuwa katafaren gidansa dake Maitama. Ana buɗe masa kofar motar, ya fito da launin gilashinsa mai *designer cut*, yana dafe kansa kamar wanda ke ƙarƙashin nauyin wata zuciya da ke tafasa.

Jikinsa na ɗauke da wani irin zazzabi mai sanyi da dumi a lokaci guda nau’in da ba jiki ke yi ba, amma zuciya. Ba ya magana, ba ya kallon kowa. Kai tsaye ya wuce ɗakin wanka nasa na alfarma, inda ke da jacuzzi mai ɗaukar mutane uku, ruwayen *essential oils* da *aromatherapy* sun cika ɗakin da ɗan kamshi mai ɗaukar hankali haɗin vanilla da sandalwood.

Ya cire kaya cikin kasala, jikinsa na rawa a hankali. Ruwa na dumi ya fara zagaye jikinsa kamar yana shan numfashi na sabuwar duniya. Amma hankalinsa baya nan yana nesa. Kalmar da ta daki zuciyarsa kamar takobi mai kaifi ita ce

**“Haneefah ba za ta iya zama da nakasasshen namiji ba.”**

Zuciyarsa ta rikice. Jijiyoyin kansa sun kumbura kamar ana busa iska a cikinsu. Ya lumshe ido, ya saka kansa cikin ruwan jacuzzi kamar yana buƙatar ruwa ya ɗauke masa tunani. Ya fitar da wani gajeren numfashi mai nauyi, ya ɗauki wayar dake gefensa iPhone 15 Pro Max, ya dannata ba tare da tunani ba. Sai kawai ya furta, cikin murya mai rauni, amma cike da buƙata

**"I need you... kusa da ni, Aishatu."**

Ya kashe wayar. Bai jira martani ba. Hannunsa yana riƙe da kansa kamar yana ƙoƙarin hana jijiyoyin zuciyarsa fashewa. Jacuzzi ɗin mai hasken milk na ci gaba da motsa ruwan da ke masa lulluɓi. Domin daɗin jiki, babu; daɗin rai kuwa? Ya ɓace tuni.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull