Kenza eBookz

Kaddarar ramlah book 1 complete - Chapter 2

Kaddarar ramlah book 1 complete - Chapter 2

Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 2: Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 2. A cikin wani katafaren gida da ke tsakiyar babban birni, gidan da…

4,500 words

A cikin wani katafaren gida da ke tsakiyar babban birni, gidan da gini guda ya fi kwatankwacin wani ƙauye, wani mutum ne ya fito daga cikin toilet ɗinsa na alfarma. Bango na marmara ne mai sheƙi, bene na zinariya da fari mai haske, tagogi na gilashi masu ɗaukar hasken rana, da madubai masu bayyana komai da kyan gani.

Shi ne As’ad Babangida, ɗan sarkin Zubairu. Mutum ne mai kamala da mazantaka, cikakken jarumi mai ƙasaita. Shekarunsa kusan hamsin a duniya, amma kyawunsa da lafiyarsa na jikin samari ne. Jikinsa yana da lura da kulawa, fatarsa na sheƙi, ga murya mai ɗaukar hankali, da tabbas a cikin tafiyarsa.

A lokacin da ya fito daga wanka yana ta share fuska da tawul ɗin fata mai launin zinariya, mutum na iya gane cewa wannan bawan Allah ya taso a cikin ni’ima da arziki. Daga nan ya nufi babban ɗakinsa na kaya, wanda ke cike da rigunan Alƙebulan da turaren Dubai, agogo masu daraja, da takalma daga turai.

Ya zura jalabiyya mai nauyin zinariya, sannan ya ɗauki wayarsa mai tsada daga saman table din katako na Itacen India. Wayar ta haska logon kamfanin sa na SILIFAS Group, kamfani da ke sarrafa kayan ado, gidajen alfarma da ƙera turaren maza.

Kamfanin Silifas ɗin nasa yana daya daga cikin manyan kamfanoni da ke jan hankalin masu kuɗi a fadin ƙasar. Duk wani namiji da ya ƙoshi, to ya san turaren Silifas. Ya kuma san cewa daga hannu ko albarkacin As’ad Babangida ne – mutum mai kima, mai iyaka da daraja.

Ya tafi ya zauna a babban kujerar falo, inda masu taimakonsa suka shigo da takardu da wayoyi da zai duba. Ya duba agogo.

Hadimansa biyu suka shigo cikin natsuwa, kowanne sanye da shadda da rawani, suka durƙusa da girmamawa.

"Ranka ya daɗe, kamfanin silifas ɗinka na Legas sun ce sun kammala sabbin kaya da kake jiran shigo da su," in ji ɗaya daga cikinsu.

As’ad ya ɗaga hannu alamar ya fahimta, ba sai ya ce komai ba. A wajen As’ad, magana ba sai mai yawa ba isa na ciki ne, da kallo da numfashi.

Ya ɗauki wayarsa mai lamba biyu ta musamman, wanda aka tsara da suna "AB-Exclusive", wata nau'in waya ce da ake yiwa mutane 'yan takama.

Yana dubawa, ya ga sakon daga kamfanin mai mai a Sokoto, suna neman haɗin gwiwa da wani daga cikin kamfanonin gine-gine mallakinsa – AB Construction & Prestige Estate.

As’ad ya lumshe ido. Wannan ba sabon abu bane a gare shi. Ko da yake ya gaji dukiya daga mahaifinsa, shi ya ninka ta sau goma bisa gogewa kasuwanci.

Bayan ya gama karanta saƙon, sai ya miƙe tsaye. Jikinsa yana sheƙi da lafiya, da karfi. Kallon da zaka masa ya isa ka fahimci cewa yana daga cikin manyan mutanen da kasa kiji dasu.

ƙofar babban falo, wani dattijo mai murya da ɗan kaifi yana jira shi.

"Ranka ya daɗe, Masarautar Rano sun ce za su zo gobe da safe neman haɗin gwiwa akan gina sabuwar cibiyar kasuwanci da banki a yankin su."

As’ad ya tsaya, ya ɗan lumshe ido sannan ya ce da muryarsa mai sanyi amma mai ɗauke da izza

"Ku amsa musu. Ku shirya tsare-tsaren da ya dace. In na ce zan shiga abu, to tilas ya ɗauki martaba."

Dattijon ya rusuna, ya amsa da “To, ranka ya daɗe,” sannan ya juya da sauri.

Bayan As’ad Babangida ya kammala ganawa da masu shigowa , sai ga Sarauniyar gidan Hajiya Aisha ta bayyana cikin natsuwa da kamun kai. Ta shigo da sallama mai nauyin izza, wadda ta cika dakin da kwarjini. A jikinta ado ne na sarauta, tufafi masu kyan gani, da turare mai ɗaukar zuciya. Kallon da ta masa ya bayyana girmamawa da kauna, kirarin da ta kwarara kuwa sai da ya sa zuciyarsa ta narke.

Shi kuwa yana zaune a babban kujerarsa da kamanni irin na manyan maza. Ya kalleta yana murmushi mai nauyi, wanda ba kowa ke samu ba. Hannunsa ya daga a alamar izini, ya nuna mata kujera kusa da shi.

Ta ƙaraso kamar sarauniya, ta zauna da girmamawa, ta ɗan latsa ƙasa da tafin hannunta kafin ta furta da nutsuwa

“Ranka ya daɗe, dama ina so in ji batun tafiyarmu gobe. Yaran sun ce har yanzu baka basu amsa ba.”

As’ad ya ɗan yi shiru, yana kallon gabansa, kamar mai tunanin manyan al’amura. Daga bisani ya ce cikin murya mai ƙarfi da nutsuwa

“Akwai tafiya.”

Aisha ta saki addu’ar albarka a gare shi, da harshen mace mai sanin girman mijinta. Ta ce

“Dama Bilkisu ce zata je gida gobe. Nace mata ta jira, mu tafi tare. Tana son ganawa da iyayenta.”

Ya ɗan jinjina kai cikin karfin hali, ya ce

“Tashirya. Da safe zan shiga garin, in ga mai martaba. Sai mu tafi tare.”

Ta sunkuyar da kai cikin girmamawa, ta ce

“Na gode, ranka ya daɗe.”

Ta miƙe da kyau, ta fita.

Shekaru kusan 45 kenan da As’ad Babangida yake cikin aure. Matar sa ta farko ta rasu tun da wuri, ta bar masa ɗa guda ɗaya mai suna Umar. Umar yanzu gaba ɗaya rayuwarsa yana yi ne a Dubai tare da iyalansa. Yana da kyau, yana da natsuwa, amma ya fi son zaman can fiye da dawowa gida.

Bayan mutuwar matarsa ta farko, As’ad ya sake aure. Wannan matar kuwa ita ce Hajiya Aisha, mace kyakkyawa, mai aji, da nutsuwa. Yanzu haka tana da shekaru 37 a duniya, kuma tana da yara guda uku ‘yan mata biyu. Daya daga cikin ‘yan matan ta rigaya an daura mata aure. Ita kuma ɗayar tana nan a gabanta, suna kiranta da Nawal.

Nawal yarinya ce ta musamman sangartacciya ce da gata. Kyawu, tarbiyya da jin daɗin rayuwa duk suna tare da ita. Kusan ba ka fiye ganinta a Najeriya ba, saboda tana cika zama ne a Dubai tare da yayanta Can ne ta fi so, can ne ke faranta mata rai.

Hajiya Aisha, matar As’ad ta biyu, ce uwar gida. Ita ce mace mai hankali, mai cike da izza da daraja. Yar gayu ce ta gaske, wadda duk ta shiga za ka girmama ta. Bayan aurenta, As’ad ya sake auren wasu mata har guda biyar, amma abun mamaki babu ko ɗaya da ta taɓa haihuwa.

Ba sa jure zama da shi. Yana yiwuwa su zauna wata shida ko shekara daya, sai kowacce da kanta ta nemi saki. Wannan lamari ne da ya ba kowa mamaki, har ya sa As’ad ya fasa neman karin aure, duk da cewa zuciyarsa na da buƙata.

Wata rana yarinyar da ya aura a ƙarshe mai suna Maryam, ta zauna da shi, ta ce

"Ka ji tsoron ɗaukar hakkin yaran da ba su ji ba, ba su gani ba. Dan Allah ka zauna da matarka…"

Kafin ma ta gama, maganar ta tsaya masa a zuciya. Wannan kalma ɗaya ta sauya masa tunani. Ya fasa tunanin karin aure gaba ɗaya.

Sai dai har yanzu babu wanda ya gane dalilin da yasa ba matarsa ɗaya da ta daɗe da shi. Wasu na cewa halinsa ne mutum ne mai ra’ayin kansa da tsaurin hali. Ko da yake, mutum ne mai ibada da addu’a sosai, amma idan ya ce abu, sai Allah ne kaɗai zai iya sa ya canza.

Aisha kuwa, duk da cewar ta fi kowacce mace samun daraja a gidan, akwai abu ɗaya da ta kasa samu daga As’ad mulkinsa. Duk yadda ta ƙoƙarta ta mallake shi, ta janyo hankalinsa, ko da ta hanyar ƙauna ne ko magana mai taushi, As’ad bai sauka a karkashinta ba.

Sai dai ita Hajiya Aisha ta san inda zata taka. Ta san yadda ake tafiyar da namiji mai taurin kai. Da hankali da haƙuri, da kishi, da maganar mace mai wayo, ta kasance ita ke riƙe da gidan da komai ke gudana kamar yadda take so.

Rayuwar cikin gidan As’ad Babangida cike take da sirrika da ruɗani, amma a tsakiyarta, ita ce ta fi kowa shahara. Ita ce matar da ta fi iya jure halinsa. Ita ce ginshiƙin gidan.

Daga babban shashen mijinta, Hajiya Aisha ta nufi nata sashen wani ɓangare na gidan da ke nuna sarauta da jin daɗin rayuwa. Falo ne mai girma, cike da kayan alatu daga ƙasashen waje, fitilun gilashi suna haskawa cikin shudi da zinariya, sannu a hankali AC ke busar iska mai ɗanɗano da ɗumi.

Ta shigo tana tafiya da kwarjini kamar sarauniyar gida, sai kamshin turarenta ya cika wajen. Ta tarar da Nawal zaune a kan kujera tana danna wayarta, ana mata tausa da mai ruwan sanyi. Daga gefenta kuma Bilkisu ke kallo – Korean film ke tashi a giant screen ɗin plasma TV, wanda ke manne da bangon da aka lulluɓe da fatun fata.

Ta tsaya tana kallonsu, sannan da muryarta mai natsuwa da iko ta ce

“Bilkisu, ki shirya. Inji Habibie, gobe da safe zai shiga garin, zai tafi dake.”

Bilkisu ta kalleta cikin girmamawa, sannan ta ce

“To, mamah.”

Nawal kuwa ta ɗan turo baki, ta kalli ‘yar uwarta da ƙuruciyar shagwaɓa.

“Yanzu sis, kina nufin ba zaki bimu ba? Please mana…”

Bilkisu ta ɗan murmusa, ta ce cikin taushi

“Ki yi haƙuri sis, next time. I really want to see my parents.”

Hajiya Aisha dai ba ta ce komai ba. Sai zuciyarta ta ji wata ɗigon bakin ciki, musamman da jin cewa Habibie zai tafi tare da Bilkisu. Anya kuwa zata fasa tafiyarta ta Paris da ta shirya makonni? Sai kuma ta sake ta. Wata dariya ta suɓuce mata tana fadin cikin zuciya:

“Itama ai ba zata fara ba. Tasan wacece ni.”

Ta juya da fara’arta mai ɗaukar hankali, ta bar su cikin dakin, sai kamshin turarenta da sautin takalminta suka rage.

Bayan ta bar falon da 'ya'yan suke, Hajiya Aisha ta shiga ɗaya daga cikin dakunan nata na sirri wuri ne na musamman da ba kowa ke da damar shiga ba. Daki ne mai fadi, an kawata shi da madubai masu haske, fitilun kwali, da kwalabe masu launi na kayan mata daga ƙasashen waje.

Ta nufi wajen da take ajiye kayan mata na gyaran jiki, tsumi, turare da hadin gargajiya. Tana tafiya a hankali, tana tsiyaya a zuciyarta. Daya daga cikin kwanukan matsinta ta ɗauko, ta dora shi gabanta a kan faifan , sannan ta zauna, ta kwantar da hankalinta.

Cikin nutsuwa da kwarewa, ta shiga shan hadin tsumi, tana shafawa jikinta da tsari da salo irin na mata masu gata. Wannan ba shan kaya bane, wannan kula da martaba ce.

Tana kallon fuskarta a madubi, ta dan yi ajiyar zuciya. Bata jin dadin yadda take mu'amala da Habibie kwanan nan. Ko da yake tana da daraja a idanunsa, amma yana yawan kau da kai daga kusa da ita. Tana jin magungunan da take amfani da su, da hadin da take turawa jikinta, kamar suna ƙara nisantar da shi ba tare da dalili ba.

Shin ko ya gaji da ni? Ko akwai wata can da ke jawo masa hankali? Zuciyarta ta tambaya, amma ta goge tambayar da murmushin mace mai karfin zuciya. Ta dora turaren kwalliya a gefe, ta furta a hankali

“Ba zan ja da wata ba, sai dai ta gaji da kallo. Ni ƙadaice matarsa.”

Nana hadiza

09030569336ƘADDARAR RAMLAH

SHAFI NA HUDU

Idan zan gaya muku irin wahalar da nasha cikin ‘yan kwanakin nan, wallahi sai kun tausaya min. Aiki ne kawai nake yi babu hutu.

Gashi kuma momy ta sanar da yaya Abbas cewa kada ya kawo yar aiki. Ta ce wai ta bayar da cigiyar mai aiki.. Na sani, ba da gaske take ba.

Abin mamaki kuwa, duk sanda na dawo daga makaranta sai in tarar da gidan a hargitse. Da fari na dauka ko baƙi ke zuwa, amma daga baya na gane da gangan ake ɓata gidan domin in gyara.

Momy ta canza. A da kulawa da ƙauna take nuna min. Amma yanzu sai ta taga Abba kafin ta nunamun kaunar. Hakan yana cutar da ni sosai, amma bana cewa komai. Sai zuciyata ke kuka.

Duk rana da na dawo daga boko, zan fara gyaran gida. Bayan haka in dafa girki, in fita islamiya. Da daddare bayan magariba nake dawowa gida. Duk da gajiya, sai na hau wanke-wanke da sauran ayyukan da ba za a rasa ba.

Ina tuna lokacin da momy ke cike da ƙauna a kaina. Tana sona kamar ni kaɗai nake da ita a duniya. Amma yanzu? Idan na ga yadda take wulakantani, sai hawaye ya cika min ido. Na sha kuka a sirrance cikin makon nan.

Wata rana na dawo daga makaranta, na same ta a falo. Na tunkare ta a hankali nace, “Momy turarena ya kare, jikina ma ya soma wari...”

Sai kawai ta juya ta ce, “Ai ke yanzu kina ɗaukar kanki sa’ar kowa ko? Ga ki kwaila ce amma kina jin kanki kamar cikakkiyar budurwa.”

Kamar an zuba min ruwan sanyi haka na tsaya. Na kasa motsi. Na shiga shock. Duk da haka, na saki baki nace, “Ki yafe min idan nayi kuskure.” Na koma dakina cikin ɗaci.

Washegari kuwa abincin dare aka ci, amma ba a kirani ba. Na yi shiru, har na je na ce mata“Momy ba a kirani ba...”

Ta kalle ni da wani irin kallo tace, “Ke ai kin san kitchen din. Koni zan girka miki?”

Na durƙusa na bata hakuri. Na ce ko laifi nayi mata, ta yafe min. Amma sai ta wuce gona da iri, ta juyo tace

“Ki kama kanki a nan gidan! Gidan mijina ne, ba naki ba. Kuma idan kika ce zaki yi min magana gaban Abba, sai na saɓa miki da gangan.”

Yanzu haka muna tsakiyar jarrabawa a makaranta. Allah ne shaida, kawai rubutu nake yi, ba don nayi karantu sosai ba. Yaushe zan samu lokacin karatu ne, jikina gaba ɗaya gajiya ne gajiya da bautar Momee.

Da ace tana da sauƙin kai , da ba za ta bar ni ba har na zama mai wanke mata pant da bra dinta da kaina. Amma yanzu kuma sai naji wai tana gaya wa Abba cewa ciwon hannu ne ke hana ta wankewa. Ashe dai ni ce zan ci gaba da wanke mata komai.

A wannan satin, sai gashi naji Mumy na waya da Yaya Billy. Har kusan makonni biyu kenan ba ta dawo gida ba. Da farko ban san dalili ba, sai dai da safe sai naji Mumy tana cewa a waya

"Ai Dady As’ad ne ya ɗaga tafiyar, sai gobe zasuzo tare.”

Mumy tana ƙarfafa ya Billy

"Ki dai ci kwalliya sosai. Ki cakare, kin ji?"

Araina nace, ai ba sai an faɗa wa Yaya Billy tayi kwalliya ba. Ko yaushe haka take kamar aljana wadda bata taba gajiya ba. Shafe-shafen fuska da hoda,jambaki.

Amma fa, bana fahimtar dalilin da ya sa Mumy take hura mata wuta haka – sai na kauda kai, na cigaba da sabgogina. Allah ne kaɗai yasan bana jin daɗin jin zata dawo. Wallahi har cikin raina bana sha’awar ganin ta koma cikin gidan nan.

Na san idan ta dawo, azaba ce zata karu gareni. Na yi shekaru ina mata aiki kamar yar aikinta daga ɗebo mata ruwa, share daki, gyara kayanta, hatta jakar kwalliyarta idan ta fita, ni ke ɗauka. A gabanta, bani da wani daraja, kuma ba abinda nake yi ya gamsar da ita. Amma fa duk da wannan halin nata komai auta komai auta.

Yau Juma’a. Saboda haka, da wuri muka tashi daga makaranta, kuma bamu da islamiyya. Tun safe na tashi na gyara gidan, na shirya cikin kayan makaranta. Na je na gaida Abba, ya amsa da murmushi yana addu’a kamar yadda kullum yake yi. Bayan ya kare nasiha, na ɗauki jakata muka huce makaranta.

Kasancewar jarabawa muke yi, da zaran mun shiga ajin ake farawa. Bayan mun gama, muka fita waje. Kawayena suka fara hira kala-kala. A yawanci zancen samari suke yi ni dai shiru nake.

Sai Fatima, kawata, ta matsa kusa dani tana dariya. Tana riƙe da wani kwali. Tana cewa, “Kalli wannan.” Na kalle shi an rubuta a jikin kwalin Dwell Weight Gain Capsule. Na ɗago mata kai da tambaya a idona.

Sai tace, “Jiya nasiya. Magani ne na ƙara kiba. Ramlah, kema ki karɓa ki fara sha. Bakiga yanmatan ajin nan ba? Kowacce da nonowa da hips. Suna yi mana wani irin gayu. Amma mu kamar muciya...”

Na yi dariya, amma zuciyata cike da tunani. Gaskiya ne, ramar nan ta dameni sosai. Ina son in ga jiki na ya ɗan cika. Ko dan in daina zama abin dariya a idon wasu.

Na karɓa daga hannunta, ina tambayarta yadda ake sha. Ta bani bayani da fara’a. Na ji daɗi sosai. Na saka a jakata, muka tashi muka kama hanyar gida.

Kwana uku kenan da na fara shan maganin ƙara kiba. Babu wanda ya sani a gida. Ko Fatima da ta bani maganin, bata tambaye ni ko na fara ba. Na yanke shawarar sai na fara ganin canji a jikina tukunna zan sanar da'ita.

A cikin waɗannan kwanaki uku, abinda na fi lura da shi shi ne yadda yunwa ta ƙi barina. Kullum cikin ci nake. Da safe, da rana, da dare sai na ci abinci kamar jaka.

Har ita kanta momy ta fara zargina.

Ranar Laraba da rana, bayan na ci shinkafa da miya da gasasshen kifi, na ɗauki garin kunu da aka rage jiya, na zuba a kofi, na zuba sugar sosai, na sha gaba ɗaya. Sai na tashi na ɗauko biskit guda biyu na ci.

Momy tana zaune a falo tana kallon labarai. Ta kalleni da mamaki, tace

“Ramlah lafiya kuwa? Kwana uku kenan kina ta cin abinci kamar wadda ake tura. Ko mai sabon ciki ?”

Na ɗan yi dariya da ƙyar nace

“A’a momy, kawai yunwa ce fa. Nima ban san me yake damuna ba, amma ina jin ci kawai.”

Ta zuba min ido kamar tana nazarina. Amma ta kame. Sai tace

“Kar ki je kina janyo ciwon ciki da kanki fa.”

Na girgiza kai kawai, na bar falon. A zuciyata nace:Da sun san me ke faruwa da ni... ai da za su tsaya mamaki.

Kuma duk da yunwar da nake ji da abincin da nake ci, har yanzu bana jin canji sosai. Amma zuciyata cike take da fatan Ko da zai ɗauki sati biyu, in dai zan cika kamar sauran ‘yan mata, ni wallahi zan dage.

Na lula sosai gurin shan maganin. Kullum da safe, da dare, sai na ɗauka in sha, kamar maganin ciwon zuciya. Ranar Juma’ar nan, da na farka, na je gaban madubi sai naga fuskata ta kumbura. Kamar ba fuskata ba ce. Hankalina ya ɗan tashi, amma saboda yarinta da son ganin canji, sai kawai naji dadi.

Na matsa na kalli kirjina... ko su suma sun soma cika? Na dan bubbuga saman rigata da jin daɗi. A zuciyata nace, Yanzu dai na fara zama mace.

Sai na ɗauki maganin, na sha, na kuma sha afa ban daukeshi daga ƙan gadona ba.

Da safe na shirya cikin rigar makaranta, na je na gaida Abba. Ya dube ni sosai sannan yace

“Ramlah, lafiya fuskarki ta kumbura haka?”

Momy ma ta ɗaga kai da sauri tace, “Wai me ke damunki ne? Idan kin dawo daga makaranta zamu je asibiti.”

Na ce musu, “Ba komai, kawai yunwa ne jiya ban ci abinci da kyau ba.” Sai na yi sallama na tafi.

Ban san cewa yau ce ranar da komai zai fallasu ba.

Momy na shiga dakina don duba wani abu, sai idonta ya sauka a jikin kwalin maganin. Tayi saurin ɗagowa ta karanta. Da farko ta fara karantawa da siririyar murya, amma tana kai ƙarshe sai hawayenta suka zubo. Ta fito da maganin hannunta tana fadin

“Abba... ka duba wannan. Ka karanta ka gani da idanunka.”

Abba ya karɓa, ya karanta shiru. Bayan ‘yan dakiku sai ya kalli momy da murya mai nauyi yace

“Na wanene wannan? Waye ke shan wannan maganin?”

Momy ta share hawayenta tace, “Daga dakinta na samo. Ashe ita ce take shan shi. Ita ce take kumbura. Tana shirin janyo mana bala’i!”

Abba ya sauke ajiyar zuciya, yana girgiza kai.

Abba na zaune, kwalin maganin a hannunsa. Ya na kallon rubutun da ke jikinsa, fuskar sa cike da alamar damuwa. Momy kuwa bata bari ya gama karantawa ba, ta fara zuba kalamai:

“Abba, wallahi ban gane Ramlah yanzu ba. Kwana biyu kenan tana canzawa a idona, har na soma tsoro. Fuskar ta ta kumbura, jikinta yana sauyawa, ita kuma kamar ba ta lura da kanta ba.”

Abba ya ɗan ɗago kai da mamaki, bai ce komai ba.

“Sai abin ya taɓa lafiyarta kenan tukunna za’a dau mataki?”

Ta matso kusa da shi, ta zauna da girmamawa, amma tana kuka. Tana cewa

“Wannan maganin da na gani a dakinta fa? Idan wani abu ya faru da ita fa? Ashe ni za a ce na cutar da ita.”

Ta sake girgiza kai tana cewa, “Wannan capsule ɗin fa? Magunguna masu kara kiba ne da ke jawo cancer da cututtuka masu haɗari. Yanzu ace ita yarinya karama tana sha... kuma a gidana?”

Sai ta lumshe ido, hawaye na bin kuncinta

“Abba... da gaske nake... wallahi ni fa na rasa abin cewa. Da ace wani abu ya same ta, me za a ce? Ashe idan tayi rashin lafiya gobe, ba zan zama abin zargi ba? Kai kanka zaka iya cewa ina kallonta amma ban hanata ba Alhali bansan halin datake ciki ba.”

Abba ya shiru, ya sauke ajiyar zuciya. Sai ya ce a hankali, “Allah ya kyauta…”

Ba karamin zafi Abba ya ji ba, amma ba ya nuna komai a fili. Sai dai yana kallon Momy da kwalin maganin a hannunsa, kamar yana jiran jin karin zuga daga gare ta. Ita kuma, kamar ta jima da jiran wannan dama.

Ranar, kuwa Momy ta kama girki da kanta. Ta gyara falo, ta canza labule, ta zuba turaren wuta. Komai ta shirya kamar ba ita bace ta tayar da bala’i da safe. Abba kuma da zarar ya gama Abunda yakeyi ya fice kasuwa shiru kamar ba komai ya faru ba.

Ni kuwa a makaranta, sai wani jin daɗi nake ji a jikina. Ganin fuskata ta cika, jikina ya ɗan cika, sai naji kamar nayi nasara. Nida Fatima muna ta dariya, tana cewa

“Wallahi Ramlah, ki gani fa yanzu. In muka gama wannan kwalin, zamu sayi wani daban sai mu zama kamar ‘yan Instagram.”

Na kyaleta da dariya. A zuciyata nace “Kowa yasan me yake nema, ai da kyau ake bi ana shiga gaban mutane.”

Yayin da muka tashi daga makaranta, muka fito, muka same Malam Idi direban mota. Ya zuba min ido yace

“Auta wannan kumburin naki... anya ba sanyi baniba?”

Na fashe da dariya nace, “Ko ɗaya Malam Idi, kiba ce fa, ina jin dadin jikina yanzu.”

Shi ma ya kyalkyale da dariya yace, “Allah ya kara lafiya.”

Na dawo daga makaranta da yamma cikin gajiya, amma zuciyata cike da farinciki. Sai kallo nake yi wa jikina a madubi, ina murmushi. Na ji kamar wata sabuwar ni’ima ce ta sauka a kaina.

Na ci abinci fiye da yadda nake ci na haɗa da kek da kunun tsamiya. Bayan isha’i, na kwanta jikina cike da nauyi, amma zuciyata na motsi da daɗin canji.

Ban san lokacin da na lumshe ido na fada bacci ba. Sai kawai na ji azaba kamar wuta ta faɗo min a baya!

Wata irin zafi ce ta farka da ni daga barci!

ZAAFFF!!!

Na yi ƙara, na buɗe ido cikin firgici. Idanuwana suka sauka a kan Abba. Tsaye yake da bulala a hannu, fuskarsa ta cika da fushi.

“Ke Ramlah! Ashe guba kike sha kina boye mana?! Ashe kina neman mutuwa da kanki, a cikin gidana?”

Na ce da murya mai rawa

“Abba dan Allah… wallahi ban….”

ZAAFFF!!! ZAAFF!!! ZAAFFF!!!

Ya sake zane ni ba tare da sauraro ba. Wata bulalar ta doki gefen ƙirjina, wata ta shige min a bayana. Na zube a ƙasa ina kukan da ban taba yi ba a rayuwata.

“Sai kace ba ‘ya ba! Sai kace na samo ki daga titi! Wato kina neman kiba har da shan magungunan banza da za su kashe ki kafin ki kai shekara ashirin?!”

Na durƙusa da gwiwoyina, jikina na rawa, zuciyata kamar zata bar jikina. Na rarrafa zuwa gefe, amma kafin na isa gado sai na sake jin

ZAAFF!!!

"Abba don Allah!" Na ƙwalla. "Wallahi ban san me nake yi ba!"

Amma fushinsa bai daina ba.

"Kin girma da wauta! Kin raina ilimi da tarbiyya! Sai kin illata kanki dan uwanki?!"

Na fara haki da gumi, numfashina yana rikicewa. Har na soma jin kamar zuciyata zata tsaya.

“Wallahi yau sai kin sani,” ya ce yana rarrafe a kaina da bulala.

Na yi ta jijjiga kaina, ina kuka, ina kokarin kare jikina da hannaye. Amma bulala sai karfi take karɓa.

A can sama, a ɗakin Momy, tana jin komai. Amma shiru tayi. Maimakon ta sauko ko ta ce ya yi hakuri, sai dadi ya rufe zuciyarta. Ta ma juya gefen gado, tana cewa a ranta

“Ai sai an koya mata hankali. Tana ganin zata yi min fintinkau? Tasaka dariya.”

Ta rufe kunnen ta da bargo, ta lumshe ido da jin daɗin azabar da Ramlah ke sha.

Ni kuwa, na dawo can ƙasa cikin ɗaki, hawaye sun goge fuskar da na ji kwana uku tana cika. Jikina duk yana rawa. Zuciyata na dukan da ban taba ji ba.

Abba ya zube bulalar ƙasa a ƙarshe, yana haki kamar mai gudu. Ya dubeni da idon da bai daɗe da zafin bulala ba, amma har yanzu cike da takaici.

Abba ya tsaya bakin ƙofa, ya juyo ya kalle ni. Idonsa ya dan lafa daga fushi, amma yana dauke da alamar zafi a zuciyarsa. Ya numfasa da ƙarfi, kamar yana kokarin danne fushin da bai ƙare ba.

“Ramlah,” ya kira sunana da murya mai nauyi, “zauna ki saurare ni da kunnuwan ki biyu.”

Na gyara zama a ƙasa, jikina yana rawa, hawaye kamar ruwan sama. Amma zuciyata tana buƙatar jin kalmarsa fiye da bulala.

Abba ya tako zuwa gabana. Ya zauna a gefen gadon, yana kallona kai tsaye.

“Kiba? Kina shan guba domin ki cika jiki? Ashe hakan ya fi miki muhimmanci fiye da lafiya?”

Na durƙusa na ce da kuka

“Abba dan Allah... kayi hakuri. Wallahi na yi kuskure.”

Ya ɗan dafe kansa, ya girgiza shi, sannan yace

“Maganin da kika sha kin san yana illata hanta? Kin san yana iya lalata ƙoda? Kin san yana iya jawo ciwon da ba zaki warke ba? Kin san akwai mata da suka mutu sabodashi?”

Na sa hannuna a baki, kukan ya ƙara tashi. Abba ya dafa kafaɗata, yace

“Rayuwa ba ado ba ce kawai, Ramlah. Kyau yana da rana, amma lafiyar ki... ita ce ke da daraja fiye da komai.”

Ya cigaba cikin natsuwa

“Akwai masu kiba da basu da hankali. Akwai masu kyau da babu tarbiyya. Amma idan mace tana da ilimi, tausayi da kima ko tana da ƙiba ko a'a – kowa zai girmamata.”

Na kalle shi cikin hawaye. Na ce da murya mai rauni

“Na gane Abba. Ka yafe min. Wallahi zan daina. Zan tuba.”

Ya dafa gashina yace

“Na yafe miki, amma ki yafewa kanki. Ki zama sabuwa daga yau. Ki bar kowane abu da zai cutar da rayuwarki.”

Na rungume ƙafarsa da kuka, nace

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull