Kaddarar ramlah book 1 complete - Chapter 5
Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 5: Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 5. Na dau jaka ta na nufi dakin Yaya Bilkisu, zuciyata na ta tunani. Ni…
4,496 words
Na dau jaka ta na nufi dakin Yaya Bilkisu, zuciyata na ta tunani. Ni kadai ce a gidan da ake juya kamar 'yar aiki. Na rasa me yasa Mumy da Yaya Bilkisu ke kallona haka. Duk da cewa na yi kokarin ganin an karbe ni da kauna a gidan nan, har yanzu ba su canza hali ba.
Na tuna da kalaman Fatima a makaranta
"Da kin san menene soyayyar uwa, da ba za ki taba ganin Mumy a matsayin masoyiyarki ba."
A yanzu, na fara fahimtar abin da take nufi. Duk da cewa ban yarda da dabi’unsu ba, amma maganarta tana da wata nasaba da gaskiya. Na fi jin soyayya daga wajen Mama fiye da yadda nakeji agidanmu.
Na cigaba da gyaran dakin Yaya Bilkisu, zuciyata cike da tunani.
Nana hadiza
09030569336ƘADDARAR RAMLAH
SHAFI NA TARA
Da zarar As'ad Babangida ya iso fadar mai martaba, sai aka fara masa kirari kamar yadda aka saba a gidan sarauta
A hankali ya shiga cikin gidan sarautar, yana kallon ko'ina da idanuwansa. Yau shekara ɗaya da rabi kenan rabon da ya taka wannan gida. Gidan da ya tsana fiye da komai da ba don iyayensa na ciki ba, da ko kusa ba zai sake taka shi ba.
Tun da ya kammala karatu, As'ad ya yanke shawarar komawa birnin tarayya, gidan mahaifinsa. Hajja, matar sarki ta biyu, tana zama a can tare da 'ya'yanta guda biyar Mamy Shamsiyya (ta farko), As'ad, Kanwarsa Zaitu (wacce ke zaune a London), Abba, da Fiddausi (ƙarama kuma fitinanniya). Sauran yaran kuwa na sauran matan sarki ne.
As'ad ya kasance mutum mai ra'ayin kansa wanda baya sha'awar rayuwar sarauta, shiyasa ya fi zama nesa da gidan mai martaba.
Tunda As'ad ya iso harabar fadar mai martaba, ake masa kirari da girmamawa, ana aika masa gaisuwa daga kowanne bangare. Mai sanarwa na fada ya ɗaga murya cikin izza "Gaisuwa ta musamman ga ɗan gidan sarauta, As'ad Babangida! Ɗa na biyu ga mai martaba, jikan sarki, hamshakin mai arziki da ƙasar ke alfahari da shi! Allah ya ƙara girma da ɗaukaka!"
Fadawa suka gyara zane suna kallon yadda As'ad ke takawa cikin natsuwa da girmamawa, ya na kara kusa da zauren sarki. Cikin fadar kuwa, an riga an sanar da mai martaba cewa As'ad ya iso. Sarki ya ɗaga hannu cikin jin daɗi, yana murmushi irin na mai alfarma.
A hankali, As'ad ya shiga cikin zauren fada. Ya tsaya ya sunkuyar da kai cikin ladabi, sannan ya yi gaisuwar sarauta
"Ranka ya daɗe, Allah ya ja zamanin sarki."
Sarki ya amsa da murmushi mai cike da kulawa
"As'ad, maraba da kai. Allah ya ƙara maka nasara da albarka."
As'ad ya samu wuri ya zauna a gefen sarki cikin natsuwa, yana kallon fadawa da 'yan uwa na gidan sarauta. Yana lura da yadda gidan ya sake samun kwarjini fiye da yadda ya barshi. Shekara ɗaya da rabi kenan bai taka fadar ba. Shi kam ba don mahaifinsa da mahaifiyarsa Hajja suna nan ba, da bai kara zuwa ba.
Sarki ya yi gyaran murya, ya kalli As'ad da kulawa, sannan ya ce
"As'ad, ɗana mai albarka. Yanzu haka ne? Sai ni na je inda kake saboda wata dabi'a ta ƙin sarauta? Ko in mutu ma baka da ikon zuwa ka ga iyayenka da yan uwanka? Kuɗi ba komai ba ne, As'ad. Ina gaya maka, duk arzikin da kake tunanin ka tara, a nan gidan sarauta ne tushen komai."
Ya ɗan numfasa kafin ya ci gaba da magana cikin natsuwa
"Kai fa ɗan gidan sarauta ne. Meye na gujewa gidan sarauta? Ban ce kada ka je Abuja ba, amma fa dole ka rike martabar gidan nan. Na aura maka mace sau uku, duk ka sake su. Me yasa baka son ƙara aure ne? Ka duba ‘yan uwanka, dukkansu suna da gida, suna da zuri'a sama da ɗaya. Wannan magana da nake maka ba shawara ba ce, umarni ne. Ƴar gidan Fulani, Maryam, itace nake so ka je ka gani. Wannan magana ta gama karewa."
As'ad ya sunkuyar da kansa cikin jin nauyi, sannan ya ce cikin ladabi
"To ranka ya daɗe, za a yi yadda kake so."
Sarki ya yi murmushi cikin farin ciki, yana jin daɗin yadda As'ad ya amsa. Ya ɗaga hannunsa yana addu'ar samun albarka a kan ɗansa.
"Allah ya sanya alkhairi. Ka je ka shirya, za a kawo Maryam nan fada gobe, domin ka ganta da idanunka."
Cikin girmamawa, As'ad ya durƙusa gaban mai martaba sannan ya ce da ladabi
"Allah ya taimake, a yi haƙuri, zanje inshaa Allahu."
Wannan ɗabi'ar tasa ce ta ladabi da girmamawa bai taɓa yin gardama ko musanta umarnin mai martaba ba, duk da rashin sha'awarsa ga rayuwar sarauta. Har lokacin da ya auri Ayshatu ma, shi ne ya bashi izini, kuma ya amince. Haka kuma sauran matan da ya aura duk da shi ne ya nemi izini kuma aka amince masa.
Cike da farin ciki, mai martaba ya amsa da murmushi mai cike da annuri
"Allah ya yi maka albarka, na baka izinin tafiya."
Da girmamawa As'ad ya miƙe, ya fice daga fadar mai martaba yana yi wa sarki addu'ar albarka da tsawon rai. Cikin zuciyarsa, yana jin daɗin yadda aka yi komai cikin sauƙi da girmamawa, duk da yana matuƙar guje wa irin waɗannan taruka na gidan sarauta.
As'ad na shiga bangaren mahaifiyarsa, wanda yake da kyau da tsari irin na gidan sarauta, sai ya tarar da kaninsa Abba yana cin abinci. Da ganin shi, Abba ya ajiye kwanon abincin ya miƙe tsaye, yana durƙusawa cikin girmamawa:
"Yaya barka da zuwa."
As'ad ya amsa da fara'a, yana ɗagowa da shi tare da ɗan runguma. Yana tambayar lafiyar gida da aiki. Abba ya amsa cikin ladabi, sannan suka zauna cikin tsari irin na gidan sarauta.
Bayan sun ɗan yi hira, Abba ya fara magana cikin natsuwa
"Yaya, da zaka yarda na nufi gidan Fiddausi, wallahi wannan fitsarar nata ta yi yawa. Anty Aysha ma ta kira ni, ta ba ni labarin yadda abin ya faru."
As'ad ya ɗan murmusa, yana jin mamakin yadda Aysha ta kira Abba
"Ka kwantar da hankalinka, Abba. Na riga na yi maganinta."
Kafin su cigaba da magana, Hajja ta sauko daga bene cikin hanzari, tana dubansu da fuskar rashin jin daɗi
"Abba! As'ad! Kuna tattauna Fiddausi kamar ba ku san darajar 'yar uwarku ba? Kun ga ai sai ku haɗu ku yi mana duka tare, ko? Abba, ka kiyaye ni akan Fiddausi. Ni na haife ku, ba ku kuka haife ni ba! Kun damarmun yarinya da maganganunku!"
Ta ɗan ja numfashi, sannan ta cigaba da fada cikin takaici
"Yanzu har Fiddausi zata je gidan As'ad sai matarsa ta ba da izini kafin ta ga ɗan uwanta? Yaushe kuka fara ba wa matanku wannan ƙarfi fiye da 'yan uwanku da kuke ciki ɗaya?"
Abba ya sunkuyar da kai cikin kunya, yana sauraron mamarsu. As'ad kuwa ya yi shiru, yana kallon yadda Hajja ke nuna damuwarta da ƙarfi
Cikin zafin rai, Hajja ta yi magana cikin ƙarfin murya
"Wallahi bazan taɓa yarda da wannan ba! Ayshatu ba ta da wannan ikon! Na gaya muku, dukanku!"
Cikin girmamawa, As'ad ya tsugunna har ƙasa ya gaisheta
"Hajja,Za'a kiyayye inshaa Allahu. ?"
Ta amsa tana tambayar yadda su Nawal suke.
"Alhamdulillah, suna Dubai, Hajja. Ta yi musu fatan dawowa lafiya."
Hajja ta yi gyaran murya, tana magana cikin nuna damuwa
"Maganar Fiddausi nake so mu yi. Daman taje kun ci mata mutunci kai da matarka. Duk lokacin da yarinya ta fara kuka game da mijinta, yakamata ku saurareta. Kuna ganin kamar Fiddausi ba ta da kunya, amma ai mace mai rauni ce. Kun san mahaifinku da girmama al'adar gida. Ni kuma bazan zuba ido rayuwar 'yata ta lalace ba. Kun sha gayamata mijinta yana biya mata buƙata, amma kullum cikin rashin kunya da fitsara take. To tayaya zata girmama namiji mara kuzari agado? Bata faɗa mini ba, sai yanzu da take cewa har magani aka nema babu ci gaba. Kuma duk kwayar da ya sha, ba tashi yake yi ba, sai jiri da kwanciya har asuba! Yaya aure zai yiwu haka?"
As'ad ya sunkuyar da kansa cikin ladabi
"Hajja, ki yi haƙuri, Fiddausi ce dai. Mun yi magana da mijinta, ba haka ya sanar da ni ba, shi ya sa na yanke hukunci. Amma duk yadda mai martaba ya faɗa, haka za mu yi. Allah ya zaɓa musu abin da yafi alkhairi."
Hajja tace
"Munif yana son Fiddausi sosai, bana tunanin zai iya sanar da kai matsalar. Amma ku tsaya mata! Ni shekaruna sun ja, ku zaku tsaya kamar iyayenta."
Abba yace
"Inshaa Allahu, Hajja, za mu gyara."
Hajja ta yi ɗan nishi kadan
"Maganar diyar Maryama fa? Ka amince?"
As'ad ya yi shiru na ɗan lokaci kafin ya ce
"Zabinku shine alkhairi, kamar yadda mahaifina ya umurce ni. Inshaa Allahu, da daddare zan je na ganta."
Sai Hajja ta ɗaga murya cikin takaici
"As'ad! Wannan biyayyar taka tana cutar da kai! Yanzu Haneefa zaka aura? Yarinyar da kowa yasan rashin tarbiyanta, kuma kasan mahaifiyarta makiyata ce! Wallahi tun da mahaifinka ya gaya min sai na ji bata kwanta mun ba! Ina roƙonka ka canja wannan shawarar."
Har sai da Abba ya sa baki
"Dan Allah, yaya, kada ka aureta. Haneefa fa? Haba yaya, auren nan da manufa!"
Hajja ta kara nuna damuwarta
"Biyayyarka ta yi yawa, As'ad. Yarinyar da aurenta fiye da biyar, duk ta kasa riƙe ɗaya. Na ƙarshe ma, sata tayi masa ya rabu da ita. Dan Allah, ka kiyaye."
As'ad ya girgiza kai cikin ladabi
"Hajja, ki yi mun addu'a. Bazan iya tsallake umarninsa ba."
"To Allah ya duba mu, ya yi muku albarka."
Bayan ya fita, Abba ya kalli Hajja cikin mamaki
"Hajja, anya ba asiri aka yi wa yaya ba? Wannan biyayya fa ta yi yawa!"
Hajja ta yi dariya
"Abba, mahaifinku ne yayi masa amma dai."
Abba ya ɗan nuna damuwa
"A'a Hajja, kar ki sani, dan Allah."
Ta yi shiru na ɗan lokaci tana nazari. Abba kuwa ya kalle ta yana mai nuna damuwa
"Hajja, wallahi abin da yaya yake yi yana bani mamaki. Wannan biyayyar kamar ba ta al'ada bace. Ko dai akwai wani abu a ƙasa ne?"
Hajja ta ja numfashi, ta dube shi da ido cikin natsuwa
"Abba, mahaifinku ne ya yi masa wannan Tun yana ƙarami, ya horar da shi da biyayya da ladabi. Babu wani sihiri ko asiri a cikin wannan lamari. Amma gaskiya ni kaina ina tsoron irin wannan biyayyar, musamman yadda yake tafiya akan batun Haneefa."
Abba ya girgiza kai cikin takaici
"Hajja, idan aka ce mutum ya yi biyayya, ai yana da hankali. Amma wannan kamar an mamaye tunanin sa ne. Haneefa fa? Duk gidan sarauta sun san halinta. Ina roƙon Allah kada wannan aure ya zama matsala."
Hajja ta ɗan yi dariya mai raɗaɗi
"Abba, mahaifinku ya yi imani da soyayyar danginsa da haɗin kai.
******
A cikin falon Maryama, Haneefa na zaune tana daddanna waya yayin da mahaifiyarta ta fito daga ɗaki tana kallonta da wani irin yanayi na tsananin takaici. Ta daka mata tsawa
"Dan ubanki! Haneefa, haka zaki fita da wannan shigar? Nayi miki dinki gashi can, show me your body! Ki saka shi ki cika. Ki yi dam! Ki ɗakko brazier guda uku ki haɗa. Wannan wandon da na siyo miki na cikon hips ki saka, ki ɗauki jan jambakinki ki sa. Wannan kwalliyar da na karɓo miki daga wancan mai gyaran fuska, ki yi amfani da ita. Kuma idan kina magana, kina narkewa, nagaya miki!"
Ta ja numfashi tana gyara gyalen da ke kafadarta
"Matarsa fa yar gayu ce sosai, kuma kyakkyawa ce duk da baƙaramin jiki gareta ba. Da kadan zata girmeki, amma fa dirine da ita! Kina jin ni kuwa? Ki tashi kiyi maza! Yanzu zakiga As'ad."
Haneefa ta gyara zaman rigar da ta saka, tana murmushi mai ɗauke da son zuciya.
"To Fulany," ta fada tana barin falon cikin jin daɗi. Zuciyarta fes, tana tunanin yadda zata burge As'ad. Tuni tunaninta ya tafi ga yadda zata sa shi ya kafe mata ido, yana ganin ita ce mace ta daban da babu kamarta.
Ta dauki wandon da aka kawo mata, ta saka brazier guda uku kamar yadda aka umurta, sannan ta yi make-up mai tsauri, tana mai danna jan jambaki sosai. Ta kalli kanta a madubi, ta gyara gashinta da wani irin salo na matan zamani.
"Yau fa sai As'ad ya san ni ce matar da ta dace da shi," ta fada a hankali tana murmushi mai dauke da kulle-kullen cin nasara.
A cikin zuciyarta, ta yi alkawarin cewa komai zai yiwu domin ta samu matsayin matar As'ad, ko da kuwa ta nemi taimakon Fulany don ganin burinta ya cika. Duk da cewa zuciyarta ta san cewa As'ad mutum ne mai tsari da kamala, hakan ba zai hana ta amfani da duk wani salo don ja hankalinsa ba.
Ta ɗauki wayarta, ta danna kira
"Mama, na shirya! Yanzu zan fito."
Fulany ta yi murmushi daga nesa tana jin sautin muryar 'yarta
"To haka nake so! Yi hakan da kyau ki ga yadda zai zuba miki ido."
Maryama ta fito daga ɗakinta tana tafiya da sauri zuwa falon inda ta tarar da Haneefa tana kammala kwalliya. Ta daka mata tsawa da murya mai ƙarfi
"Au Haneefa! Maza zo nan! Sarki ya sanar da cewa yana gidan yanzu, yana jiranki. Ga direba can, ki hanzarta ki tafi!"
Ta gabatar da wata ƙaramar kwalba na turare mai ƙamshi mai ƙarfi
"Karɓi wannan turaren. Gab da zaki shiga gidan sarauta, ki gogashi a wuyanki da kunnuwanki. Wannan garin kuma ki watsa shi a kafar hagu. Wannan abu sirri ne, na tabbatar da cewa zai ja hankalin As'ad."
Ta tsayar da Haneefa ta kalli ta cikin ido
"Haneefa, komai rintsi, kada ki soma magana da kowa sai As'ad. Koda suna gaishe ki, ki yi kamar ba ki ji ba. Kin ji ni? Kada ki ɓatamun aiki!"
Haneefa ta gyara tsayuwarta, tana gyada kai
"Na ji mama. Zan yi yadda kika ce."
Maryama ta yi ɗan murmushi mai ɗauke da nasara
"Kin ga yan uwanki suna kokari, amma ke kadai na yarda da ke. Ki kula sosai, kada ki yi wani abu da zai bata mana suna. IAs'ad yana da rauni akan mace mai kyau da nutsuwa. Ki nuna masa cewa ke ce zaɓin da ya dace."
Nana hadiza
09030569336ƘADDARAR RAMLAH
SHAFI NA GOMA
Da Haneefa ta shiga babban falon gidan sarauta, ta yi sallama cikin wani irin salo na kissa, muryarta na rawa tamkar wadda aka koya mata. Ta tsaya a gaban As'ad, tana zuba masa ido da murmushi mai ɗauke da natsuwa. Amma abin mamaki, ko kallonta bai yi ba. Ya ci gaba da duban takardun da ke gabansa tamkar ba ta ma wanzu a cikin ɗakin.
Haneefa ta ji zuciyarta na bugawa da ƙarfi, fuskarta na ɗaukar wani irin yanayi na rashin jin daɗi. Ita kam, ba ta saba da irin wannan wulakancin ba. A daidai wannan lokacin ne ta sake ƙarfafa zuciyarta, ta gyara tsaiwarta, tana murza hannunta cikin rashin gaskiya.
"Ranka ya daɗe, barka da yamma," ta faɗa cikin sanyi, tana matsa maganarta da wata irin murya mai sanyi da salon lalama.
Sai a wannan lokacin ne As'ad ya ɗaga kai ya kalleta, idonsa na yin wata irin ƙyaƙyƙyawar gani. Ya lura da yadda ta yi shigar da ba ta dace ba kaya masu matuƙar ɗaukar hankali, nonuwanta suna bayyana sosai, ga kuma uban kwalliyar da ta yi tamkar mai shirin rawa. Bai ce komai ba sai kawai ya yi ɗan share murya, sannan ya ce cikin sanyin murya
"Barka."
Haneefa ta ji zuciyarta na tsinkewa saboda yadda ya yi magana cikin natsuwa da girmamawa, amma ba tare da nuna sha'awa ko kaɗan ba. Wata zuciya a cikin kanta ta ce, "Idan na auri wannan, lallai izzata za ta karu. A tare da shi, zan zama cikakkiyar sarauniya!"
Batare da ta samu ƙarfin yin wata magana ba, sai ta zauna kusa da shi, tana ƙoƙarin jan hankalinsa. Sai da aka ɗan yi shiru mai tsawo kafin As'ad ya dube ta a hankali ya ce
"Akwai damuwa ne?"
Firgigit! Haneefa ta yi kamar wadda aka tsayar da numfashinta. Cikin rawar murya ta ce
"A'a, ranka ya daɗe."
As'ad ya yi wani irin numfashi, sannan ya miƙe tsaye, yana kallon agogon bango. Ya juya ya kalleta ba tare da nuna wata damuwa ba, sannan ya ce
"Mu kwana lafiya."
Haneefa ta ji tamkar ta nutse. Yadda ya miƙe tsaye, tsayuwarsa mai cike da kima da mutunci, sai zuciyarta ta shiga karkarwa. Kafin ta ankara, ta furta da ƙasa da murya
"Woow!"
As'ad ya juyo ya dubi ta kaɗan, amma bai ce komai ba. Yana fita daga falon, ta ji zuciyarta na bugawa da sauri. Wata irin soyayya da sha'awa suka lullube ta. "Wayyo Allah! Wannan kuwa namiji ne. Wallahi, As'ad ba kamar sauran maza ba ne," ta furta cikin ranta.
---
Da Haneefa ta koma gida, tana cikin farin ciki mai cike da fargaba. Fulany Maryam na zaune tana jiran ta dawo. Da ganin yanayinta, ta gane cewa al’amura sun fara tafiya dai-dai.
"Mama! Wallahi As'ad ya haɗu, kai... ai a hoto baiyi kyau ba! Yana da kwarjini, yana da kyau! Wallahi wannan fa hadaddan mutum ne, kai!"
Fulany Maryam ta yi murmushi mai cike da tsokana, amma a zuciyarta tana sake nazarin yadda Haneefa ke magana tamkar wadda ta ji ƙauna.
"Ke kam, ki nutsu. As'ad mutum ne mai ra'ayi da natsuwa. Dole ne ki kula da yadda kike magana a gabansa. Kada ki nuna damuwarki ko kaɗan. Ki kwantar da hankalinki. Ranar daura aure na kusa, kuma As'ad ba zai iya tsallake umarnin sarki ba. Kina da lokaci ki tabbatar da cewa ya kalle ki da idanun sha'awa. Ki yi amfani da turaren da malam ya ba ki."
---
Da dare, Fulany Maryam ta ɗauki motarta, ta nufi gidan babban malaminta, wanda ake kira "Mai Iko." Ta shiga falonsa cikin girmamawa, tana sunkuyar da kanta. Malamin ya kalle ta cikin murmushi mai cike da ruɗu.
"Tunda na ganki na san cewa labari ne mai kyau kike ɗauke da shi."
Fulany ta gyara zaman gyalenta, tana murmushi. "Mai Iko, gobe za a daura auren!"
Mai Iko ya yi wata irin dariya mai ban tsoro. "Na gaya miki babu wanda zai iya tsallake wannan auren. As'ad yana a hannunki yanzu."
Sai dai Fulany ta nuna ɗan damuwa. "Amma Hajja tana tsaye kan lamarin. Bana son matsala idan har ta gano wani abu."
Malamin ya kwashe da dariya. "Hajja ba ta isa ba. Tsohuwa ce, bata da ƙarfin karya maganata. Ai ita ba ta isa ba! Wataƙila tana da wani ƙarfin addu'a, amma kin san me? Wannan turare ki yi amfani da shi gobe. Ki turara kayanki duka da shi, sannan ki shiga cikin gidan sarki. Zaki ga yadda As'ad zai zama naki. Amma kuma akwai wani abu da ya dame ni."
Fulany ta ɗaga gira cikin tsoro. "Wane abu kenan?"
Malamin ya lumshe idanu, yana nazari. "Ina gani kamar wata inuwa tana tsaye kusa da As'ad. Wataƙila ba matarsa ba ce, amma ba zan iya ganin komai ba."
Fulany tace. "Innalillahi! Wata kila matarsa ce! Na gaya maka tun da farko cewa ita ce ke kawo matsala a duk lokacin da aka ce za a yi wani abu."
Malamin ya yi murmushi ya yi wata dariya mai cike da mugunta. "Na haɗa aikinta ita tun tuni, amma ina ganin cewa wannan inuwar tana da alaƙa da wani abu mai girma. Ki yi duk yadda na faɗa miki, burinki zai cika."
Fulany ta gyada kai tana jin ƙarfin gwiwa. "Babu wata matsala mai iko. Duk abin da kake buƙata zan kawo."
Malam ya gyara zama, yana murmushi mai cike da mugunta. "Bukata ta dai a biya kamar yadda na faɗa miki.”Zan ƙara bincike, amma ki tabbata burinki zai cika."
Fulany ta yi murmushi mai cike da jin daɗi. "Ba zan yi wata-wata ba, Mai Iko. Ga wannan, ka ci gaba da aikin."
—----
A gida, Haneefa na gaban madubi tana tunanin As'ad. Ta rungumi kanta cikin shauƙi.
"Mama, wannan mutumin ai kamar jarumin fim ne! Wallahi, idan na aureshi, rayuwata ta gama kyau!"
Fulany Maryam ta kalli 'yarta, tana jin cewa ta kusa cika burinta. Amma tana da ɗan fargaba game da yadda Haneefa ta fara shiga ruɗani. Ta san cewa As'ad ba mutum bane mai rauni ga kyawawan mata, sai dai wanda ya samu matsayi a zuciyarsa.
---
Washegari da safe na tashi da uban aiki. Tun farkon tashina na fara gyaran gida, saboda Abba yace kosai yakeso, ita kuma ya Billy shawarma. Ai kuwa saboda tsabar iyayinta har da caramel ma, ba tea ba. Momy kuwa tace in hada mata teba. Na tsinci kaina cikin wani irin aikin wahala, amma duk da haka ban nuna komai a fuska ba, na ci gaba da gyaran gidan.
Wajen karfe tara na gama duk wani aiki. Na yi wanka, sannan na dauko system dina da wayata, na saka su caji. Tun jiya maganganun Fatima ke yawo a cikin zuciyata. Na rasa yaya zanyi da kaina. Kai! Ni Instagram din nan da TikTok din ma, na rasa yadda suke. Ai ko bantaba shiga ba. Na zauna ina tunanin yadda zan fita yau zuwa birthday din Fatima. Duk da cewa tsoro nake ji, amma irin yadda Fatima ta rika bani kwarin gwiwa yasa naji kamar zan iya zuwa.
Na tsaya na tsara yadda zan fada wa Abba. Na tabbatar idan nace birthday din kawata ne, ba zai bari ba. Sai kawai na tsara cewa zan fada masa cewa babbar kawata ce aka kwantar a asibiti, kuma mu da yan ajinmu na Islamiyya zamuje dubata. Nasan zai fi sauki idan haka na fada masa.
Ina cikin tunani sai naji muryar Momy tana cewa, "Ke Ramlah, meye haka? Ki dafa mun tuwo, ki kuma hada wannan abincin." Na tsinci kaina ina jin haushi amma na dake, nace, "Momy kiyi hakuri, nazata shi kikeso in dafa."
A nan take ta sake cewa, "Wai me yasa kika canza ne?" Cikin jin haushin kalamanta, amma ina danne zuciyata nace, "Wallahi Momy, na zata shi kikeso."
Nan fa naji takun Abba yana sakkowa. Ina tsaye cikin nutsuwa, sai naji Momy ta soma canza magana tana cewa, "To ai addu'a nake mata akan kokarin da take yi. Ka san idan na fada 'ke Ramlah,' nasan bata karya ba. Shine nazo yin mata fada."
Abba yayi murmushi, sannan ya ce, "Haba Zainab, duk aikin da yarinyar nan tayi, ki ci abin da ya samu. Kada ki matsa mata."
Momy kuwa sai ta saki marairaice fuska tana cewa, "Abban auta, addu'a fa nake mata akan wannan kokarin nata."
Na ji dadin kalaman Abba sosai. Bayan ya gama magana, sai na shiga gaisheshi cikin ladabi. Nan take na fada masa cewa mu da yan ajinmu na Islamiyya zamuje dubiya da yamma. Abba yace "Adawo lafiya."
Bayan haka ya zaro dubu biyar daga aljihunsa ya mikomin yace, "Ki siyo lemo, ki kai mata."
Na tsaya kaina ya dauki nauyi. Yau nice zan yi wa Abba karya? Amma kuma idan ban fita ba, Fatima zata ji haushi. Na karba cikin ladabi, na gode masa har ya fita, zuciyata kuwa na cike da damuwa.
Wata muguwar harara Momy ta watsa min, har naji mamaki. Kamar ba ita ce ta gama yabona ba a baya. Cikin wata irin murya mai cike da takaici, sai naji ta ce, "Ba zaki tashi ki je ki gyara saman ba? Ko ni zan gyara miki?"
Bance komai ba, na mike cikin jin nauyi na nufi dakin. Na gyara ko ina yadda nasaba, hatta wandonta da breziyarta na wanke musu kamar kullum. Ina gamawa, na duba agogo, naga karfe daya har ta wuce. Na sauko kasa, sai naji yaya Billy ta kira ni, "Auta, ga undies dina can ki wanke min, please. Na bar pad a dustbin, kinsan ban son kazanta."
Wata irin zuciya ce ta taso min. Kamar in kifa mata mari wallahi.
Ina tsaye cikin mamaki sai naji muryar Momy tana cewa, "Kiyi sauri kizo ki dora mana abincin rana."
Na cije baki, amma na kasa boye haushina, sai nace, "Wallahi Momy nagaji, sallah nake shirin yi."
Cikin tsawa ta ce, "Dan ubanki! Ni kike gayawa kingaji? Uban wanene zai yi mun aiki? Gaki agida, meye amfaninki? To wallahi baki isa ba! Fitsararriya mara kunya! Dalla, shige kije ki dora abinci. Sha sha sha!"
Baiwuya na fashe da kuka. Yaya Billy ta ce, "Haba Momy, is okay mana." Amma Momy bata kulata ba. Na shiga kicin din cikin kuka, na dora musu abincin rana, sannan na tsaya nayi sallah a can cikin kicin din.
Dakyar na gama aikin duk sai karfe hudu na rana. Ina kunna wayata sai ga kira daga Fatima yana shigowa. Na daga, ina sallama, ta ce, "Haba Auta, dan Allah kizo mana. Ina ta jiranki tun dazu."
Bacin rai ya gama mamaye zuciyata. Na ce mata, "Gani nan."
Nan take na fita na sayi kati a banki, sannan na yi download din Instagram da TikTok har da WhatsApp. Ban gama bude su ba sai ga sakonni daga Khalil sun fara shigowa. Khalil dai tun ina yarinya yake kaunata. Dan uwana ne, dan uwansu Abba da Babansa cikinsu daya. Yanzu kuwa ya gama karatunsa har yana aiki, amma Abba bai yarda da soyayyarsa a gareni ba.
Ban bude sakonninsa ba, sai na duba wasu group chats da aka kara ni. Na lura akwai wani group da sunansa "Bad Boys and Girls", sai nayi mamaki. Ban dade da shiga ba, naji wani irin tashin hankali saboda kalmomin batsa da suke ciki. A take na fita daga group din, sauran group din ma na fita gaba daya.
Cikin fargaba da mamaki naji wayata ta sake daukar kira daga Fatima. Zuciyata na dukan uku-uku, da alama yau akwai zance.
Nana hadiza
09030569336ƘADDARAR RAMLAH
SHAFI NA GOMA SHA DAYA
A yayin da kawata Fatima ke can tare da mutanenta, sai ga wani sako daga gare ta
"Kai Fareed, ta amsa mun zata zo!" Fatima ta fada tana kyalkyale da dariya.
Ta juyo da murmushi mai cike da tsokana
"Dan Allah, ina son ka cire mata wannan kunyar tata. Idan da hali ma, ka jefa mata wani abu cikin lemon ta, ku rage mata zafi. Kana ganinta, ka rungume ta kadai, mutumina."
Bayan haka, Teemarh ta kalle ni tana dariya, ta ce
"Kin biya ni wallahi! Kiduba nan, na sanya miki 500k. Wallahi narasa dadin da nake ji a raina. Thank you!"
Gaba daya zuciyata ta cika da farin ciki da dan karamin tsoro a lokaci guda. A yau ne kawata Fatima ta shirya babban taro a gidansu taron da ke cike da alkhawarin nishadi da hango sabbin fuska. Na san dai ba komai ba ne idan Fatima ta sa abu a gaba taron zai yi armashi sosai.
Ina tsaye a daki, na zura abayata sannan na nufi falo don sanar da Mumy zan fita. Mumy tana tsaye a gaban murhu tana hada kayan abinci. Na matsa kusa da ita cikin ladabi.
"Mumy, zan je gidan Fatima. Zan dawo nan da nan."
Ta juyo tana kallona da murmushi mai cike da kulawa