Kenza eBookz

Ƙaddarar ramlah book 1 complete na nana diso - Chapter 34

Ƙaddarar ramlah book 1 complete na nana diso - Chapter 34

Ƙaddarar ramlah book 1 complete na nana diso Chapter 34: Ƙaddarar ramlah book 1 complete na nana diso Chapter 34. Domin biyan kuɗi:

3,312 words

Domin biyan kuɗi:

Acc Name: Bilkisu Sani Kaura

Acc Number: 7040402435 (OPAY)

Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:

09030569336 ko 07040402435

Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a

Arewabook @nanadiso10

https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693

********

Ina tsaye a bakin ƙofar gida, ƙafafuna kamar an dasa su a ƙasa. Jikina ya mutu da jin nauyin zuciya. Sai na ji muryar Abba da nutsuwa "Zo ka karɓi matarka, Bashari. Allah ya baku zaman lafiya. Allah ya kiyaye hanya.”

Wannan kalma ta cika duniya ta. Ita ce kalmar da ta rufe duk wata damar da nake da ita kalmar da ta maida ni cikakkiyar amarya... ga wanda ba raina ya zaɓa ba. Bashari ya tunkaro ni da murmushi, sai dai ba murmushin annuri bane, murmushin mugun niyya ne irin wanda ya fi dariya tsoro.Hakoransa sun yi ja, suna nuna tarihin ƙonewar sigari da shaye-shaye. Zai iya ban dariya idan bana kuka. Yana takowa dabal-dabal kamar wanda ya saba da rawa, ba da ɗabi’a ba. Sai ya nufo kusa dani, ya rik’e hannuna da hannunsa mai kamar na maƙerin wuta. Atake... Na fashe da kuka.

Kukan da ba na jin zafi ba, sai dai na karayar da bata da mafita.Abba ya nufo, “Yabashi ni…” Ni kuma ina nan, ina ji, ina gani. Zuciyata na kai ƙololuwar karaya.

Na san yau, gidan da na taso a ciki ya sallameni. Sallama da hawaye ne, ba da albarka ba. Abban da ya renini shine yau ya mika ni ga mutum da ba ya jin tausayin da yafi na rakumi.

Daga wannan rana na daina kiran kaina “amarya.” A ranar da na hau motar Bashari, na san rayuwata ba zata sake komawa kamar da ba. Mun hau mota cikin ruwan dare. Na zura hijabi na launin ruwan kasa, ko da kuwa zuciyata ta fi kowane dare duhu. Bashari na gefena yana tuki kamar yana tuka wuta.

Motarsa irin tsofaffin Honda ne, ruɓabbiya, mai kujeru da ke cika da ƙura da wari. Inna lillahi… “Zan daure,” na faɗa a zuciyata. “Idan aure ne, zan jure.” Amma da kyar na iya numfashi. Wari ke tashi daga bakinsa kamar cakuda sigari da giya da wariyar ciki.

Yana dariya, yana tari, yana kurɓar wani ruwan da ban sani ba. “Ke Ramlah,” ya ce da murya kamar wani tsohon rago, “Kin saba da kauye kuwa?” “A’a,” na ce da ƙanƙantar murya. “To yanzu nan zaki zauna. Zaki koyi zaman gaskiya. Nima zan koya miki yanda ake zama da miji!” Ya ƙara dariya dariyar da sai mugunta ce kadai za ta iya haifar da ita.

Nikam na rasa irin wannan uba da Allah ya bani. Abba... mahaifi na dai, amma kamar ba shi. Mumy ce ta fi kowa hannu a cikin lamarin da makircinta da kaifin harshe ta juya zuciyarsa. Abba ya san Bashari ya san dabi’unsa, ya san irin rayuwar daba da rashin mutuncin da ke cikin shi. Amma saboda momy, sai ya watsar da ni, ya amince da auren da na ƙi, har ya tura ni wani kauye, inda babu kulawa, babu jin daɗi, babu gata.

Amarya ce ni, amma babu lefe, babu sabbin kaya, babu wani muradin aure. Sai tursasawa, sai shiru, sai kukan zuciya. Muryata ta mutu a cikin gida, murmushina ya shige ƙasa. Idanuwana suka cicciko da hawaye, masu zafi da nauyi. Na share su da sauri, na dafa ƙirjina, ina furta da karamin murya “Ya Allah, ka jikan mahaifiyata. Ka bani mafita daga rayuwar da aka zubamin da ƙarfi, ba da niyya ta ba.”

Tafiyarmu ta ɗauki fiye da awa uku a ƙarƙashin guguwar dare. Motar tana rawar sanyi, kamar zuciyarta ma na kuka. Ruwan sama na ta bugun gilashin taga da ƙarfi kamar yadda tsoro ke bugu a zuciyata, har yana kara da numfashina.

Shiru ne ya lullube cikin motar. Ban iya magana ba, ban iya kallonsa ba. Na kifa kaina a ƙirjina, idanuwana a lumshe, zuciyata na karanta addu’a cikin sirri

Sai da muka kusa fita daga cikin dajin hanya kafin ya ce wani abu. Muryarsa mai sanyi, amma babu tausayi a cikinta “Ki share hawayen nan. Wannan ba kuka ne zai canza ba. Wannan shi ne rabonki.” Na juyo a hankali, na kalleshi. Idanunsa basu motsa ba, kamar mutum ne da zuciyarsa ta dade da daskarewa. Na kasa cewa komai. Har murya ta min nauyi.

Da muka iso kauyen, rana ta ɓace gaba ɗaya. Duhu ya fara ratsa sararin sama, iska mai ɗauke da wari da danshi na kada bishiyoyin da suka yi tsufa a bakin gidaje. Bishiyoyi ne dogaye, suna sossai kamar shaidu ne na wani zamani mai nauyi.

Kasa cike da laka ce. Kowane mataki da nake ɗauka yana haifar da faɗawar takalma cikin danshi. Motar da muka zo da ita ta tsaya ba nesa da wani gini wanda Bashari ya ce shine “gidanmu”.

Ginin kamar ya dade yana fama da sakaci. Bango ne fari amma an rufe farinsa da tabon duhu kamar jinin dabbobi ko ruwa mai wari da ɗumi. Gaba ɗaya babu kofar arzuki sai wani tsohon karfe da aka jefa a bakin ƙofar wanda ma ya gaji da tsufa. Gidajen da ke kusa da shi suma ba su fi wannan ba wasu da rufin da ya karye, wasu da tagogi marasa gilashi, wasu ma tamkar gida ne da aka manta da su gaba ɗaya.

Na tsaya a waje, zuciyata na bugawa da karfi. Tsoro ya rufe ni. Idanuwana suna kallon wannan ginin da ba zan iya kira gida ba.

Bashari ya juyo, yana fuskanta da ɗan daga kai, kamar wanda ya gaji “Shigo mana!” ya ce da tsawa. Na ja numfashi na danne kuka, na daga ƙafata cikin jiki-jiki, na shiga ciki kamar mai tunkarar masifa. Cikin gidan yafi ban tsoro fiye da waje. Wani ƙamshi mai nauyi ya buga min hanci haɗin gumi, sigari, ƙwaya da datti. Idanuwana sun fara saɓa da duhun wajen, sannan suka hango Wata tabarma ce daya, mai ƙyama da tabo, a tsakiyar daki. A gefe akwai gado, amma katifar da ke kasa kamar rubewa tayi. Buhun shinkafa ne a wata kusurwa, an daura wasu riga da suka baci a kansa. A ko’ina kuma akwai ledojin sigari, kwalaben lemo da tsakuwa, wasu a bude kamar an sha kwaya a ciki. Ban iya matsawa ba. Na tsaya cak, na dafe ƙirjina. Wannan ne gida? Wannan ne aure? Wannan ne rayuwar da zan fara?

Na tsaya a bakin kofa, jikina na rawa. Hannayena biyu na matse su a ƙirjina. Na kalli dakin, idanuna sun cika da hawaye.

Sai Bashari ya juyo da ido mai nuna jin haushi “ki shigo mana! Ko kuna so makwabta su zo su ga ki a waje?”

Tsawar tasa ta katse numfashina Sai naja numfashi, na shige ciki a hankali kamar wata yarinya da aka tura rami. Tunda na shiga, zuciyata ke ta cewa "Ya Allah, ka jarrabe ni da jarabawar da zan iya ɗauka... ka tsare ni daga kaskanci da cutar zuciya."

Na kalli dakin da na shigo cikinsa bangon nan mai dusar tabo, rufin da kwari ke zagaye kamar suna shagali, katifar datti cike da ƙura da wariyar faduwar rana. Ina tsaye tun fitowarmu daga mota har yanzu ban iya zama, ballantana na kwanta. Kowane gefe na dakin wani abu ne ke sheƙi da ƙazanta. Na dubi sama, inna lillahi…

Sai ga Bashari ya dawo daga dakin waje da wata tsohuwar tsintsiya da ke zazzare kamar wadda karnuka suka baje kai a kanta. Ya miko min da murya mai ban tsoro “Ga tsintsiya. Ki share. Gidan mace ke nan fa, ko? Ni ba shara nake ba.” Na karɓa ba tare da kallo ba, na fara share-share da gwiwa. Kamar raina yana fita da kowanne gefe da na goge. Datti kamar shanƙo yana tashi sama, numfashina ya fara ɗauke wa. Na dinga janyo shara, ledoji, kwali, buhun wake da ya ɓarke, da kwandon gawayi da aka jefar a tsakiyar ɗaki. Hankali na yana rawa. “Ya Allah… Wannan aure ne ko hukunci?”

*****************

Nana hadiza

09030569336ƘADDARAR RAMLAH

SHAFI NA SITTIN DA HUDU

Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!

Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!

Domin biyan kuɗi:

Acc Name: Bilkisu Sani Kaura

Acc Number: 7040402435 (OPAY)

Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:

09030569336 ko 07040402435

Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a

Arewabook @nanadiso10

https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693

********

Ban gama sharewa ba, sai ya koma yafita daga daƙin alokacin ne nafito daga dakin ina neman abun shara amma babu tsaya gefe da gun uwar ɗakin, a cikin wani irin yanayi da babu kalma a duniya da za ta iya fassarawa. Hannuna na riƙe da ƙaramin yatsa na tsintsiya, amma zuciyata cike take da wani nauyi da ba na jiki ba nauyin ruhi ne da tunani, nauyin da nake jin kamar zai taɓe ni.

Ina son in kwashe, amma ban san inda zan zubar da sharar ba. Ko'ina ya cika da tarkace. Wajen ya fi kama da dandalin bola fiye da gidan zama. Duk inda idanu suka kai buhuna, ledojin sigari, kwantena na giya, da tarkacen da ko baƙin rana ba za ta iya bayyana su.Na ɗaga kaina a hankali, zuciyata na juyawa da tambaya mai raɗaɗi "Ina Ramlah? Ina yarinyar da ta taso cikin tsafta da mutunci? Wacece wannan da ke tsaye da tsintsiya a hannu, da hawaye a ido, a cikin kazanta mara iyaka?" Kafin in samu amsa daga zuciyata, sai na ji muryarsa a bayana ta fito da ɗumi irin na wuta a ƙarƙashin kankara “Ramlatu, idan kin gama sharar, sai ki watsata nan.” Kalmar tasa kamar ta fasa kunnena. Duk wani yunƙurina na kwantar da hankali ya watse. Na tsaya cak, numfashina ya ɗan tsaya. Amma ban juya ba. Ban ce komai ba. Sai zuciyata kawai da take ta bugawa tamkar ana dukan ƙaho cikin daki mai kaɗaici.

Na ɗan matsa da ƙafafuna a hankali, ina ƙoƙarin jure wa warin da ke hana numfashi. Kowanne numfashi kamar ana shaƙa min ƙanshi ne da daddadɗen datti na dan Adam, na sigari, na sharar da ba a taba kwashewa ba. Idona ya kai can gaban ɗakin, inda wani kwando mai fashewa da tarkace ya tsaya kamar wani gini. Amma kafin in ɗan taka gaba, sai na ji motsi a bayana.

Kafin na juya gaba ɗaya sai kawai na hango shi Bashari. Ya durƙusa yana dibar wata sharar ya zubata cikin rigarsa kamar zai ɗora wa kansa naɗi ne. Rigarsa ta baci sosai. Ta tashi da kazanta, Da wani irin yanka da kuzari, ya fizge rigar nan daga jikinsa, ya jefar da ita a gefe. Sai gurnani yayi, yana dariyar da ta fi kuka firgita mutum. “Menene amfanin hanuna idan ba zan kwashe ba?” ya faɗa da ƙarfi, yana kallona “Haba amarya! Wannan ai shine auren!”

Batare da nace ko na zaci zan jure ba, sai kawai na koma cikin dakin. Zuciyata tana ambaliya da wani irin ciwon da ba a gani da ido. Kowane numfashi da nake fitarwa yana cike da nauyin da zuciya ba ta saba da shi ba.

Na kalli dakin ko da za a ce mafarki ne, da na farka. Amma wannan gaskiya ce ni da mijina Bashari, a wannan gida da ba zan iya kira "gida" ba. Babu ko tabarma mai tsafta da zan zauna kai, sai wani kazamin katifa, wanda ko dabbobi ba za su kwana a kai dan jin daɗi ba.

Ina tsaye, idona na juyawa a dakin. Idan da wani gurin da zan buya in kuka, da na je. Sai ashe… ban yi sallar la’asar ba. Ba magariba ba. Ba isha’i ba.

Na ji wani nauyi ya sauka a zuciyata. Na mike a hankali kamar mai ɗauke da duhu a ƙirji. Na fita daga dakin, kafafuna ba sa jin ƙasa saboda kazanta da rashin kwanciyar hankali.

Sannan na nufi bandakin gidan…

Da na shiga sai kawai numfashina ya tsaya cak. Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!

Bandakin akwai kazanta lafiyayya.

najasa ko'ina kokuma nace warin fitsari duk yana tashi.leda da tsintsiya a kofar shigowa. Bakin bandakin kuwa, wani irin gumi da wari ke fita daga ciki har yana guba zuciyata.

Sai na tsaya ina kallon kaina. “Ni Ramlah, ‘yar mutunci, wadda ta taso da tsafta da tarbiyya yau ga ni a nan, ina shirin yin ibada a wuri da kowa zai gudu.”

Na juya, zuciyata cike da rashin mafita. Amma Allah bai manta da bayinsa ba. Na hango OMO can gefen rijiyar gidan. Sai kuma na lura Allah ya taimake ni akwai ruwa a famfon filin! Kuma akwai lantarki a cikin gidan, dakin, da ma bandakin.

Da sauri na shiga wanke hannu, kafa, da fata. Na kunna famfo na fara tara ruwa a cikin roba. Duka jikina ya cika da wani kazamin zargi kamar cuta tana yawo a fatar jikina. A gaskiya ina fama da kaikayin gaba, sannan har yanzu ina jin wani babban infection a jikina wanda ba a taba masa magani ba. Amma sai dai na mika kaina ga Allah, mai yaye dukkan ciwo.

Na jure, na yi wanka. Duk da haka, jikina bai daina jin zafi ba zafi daga cikin zuciyata ne, ba daga waje ba. Na ɗauro alwala. Na ɗauki hijab dina da towel, na koma cikin ɗaki. Tabarmar da ke wurin ko kallonta ba zan iya ba, balle in shimfiɗa ita in yi sallah. Hakan yasa na shimfiɗa dankwalina na a ƙasa na tsaya a kansa cikin daren duhu da wari.

Na ɗago hannu sama, zuciyata na ta ambato addu’a cikin kukan da ba ya fito da sauti. Sai zuciya na ta kuka hawaye kawai suke sauka.

Wani ƙara kamar an kwankwasa ƙofa da sanda ya katse mini sallah. Ba sallama, ba knocking, sai kawai aka turɓude ƙofar da ƙarfi. Na yi firgigit, zuciyata ta buga da karfi.

Bashari ne. Ya shigo batal-batal, ba rigar sama, jikinsa cike da gashi da zufa mai wari. Ya riƙe wani tsohon kwano da leda a gefe, ya ajiye a gaban dankwalin da nake shimfiɗe a kai, sannan ya wuce ya tsaya a jikin bango yana goge zufa. “Ga tuwo nan, kici kamin safiya. Gobe zan siyo miki kayan girki… kada ki kwanta da yunwa, kin ji?” Muryarsa ta cika da umarni da ba'a iya musawa. Amma warinsa ne ya fi komai karfi wani cakudadden ƙamshi ne na gumi, tabar sigari, da wani wari kamar daddawa da aka ajiye tsawon shekara. Na rufe hanci da gefen dankwalina, amma ina? “Ina zaki kai hancin ki? Ko bakya jin magana ne? Maza ki bude!” Sai da ya yi tsawa kafin ya juya ya fita, yana barin ƙamshi a ƙofofin numfashina. Ban san da numfashi nake yi ba ko da zuciyata.

A hankali, na daga kwanon.

Miyar… Ya Allah!

Wata bakar miyar tsami ce, mai kamshin citta da ganyen kabeji da ya gogu. Tuwon kuwa? Sai ka rantse da itacen gawayi akai masa bakikkiri, kullu, kuma yana fidda ƙamshin daddawa da ya farfashe.

Yunwa ta yi ƙarfi. Sai da na kai kwanon bakina, amma da farko na runtse idona.

Gaba ɗaya jikina ya karaya da sauƙin wannan wulaƙanci. Ban ci ba na ɗan ɗanɗana ne, sai kuka ya kwace mini. “Ki cinye, nace miki fa! Kina so nayi fushi ne?” Ya dawo da sauri, yana kallona da wani irin azababben yawu da hayaƙi na fita daga bakinsa. Na ce, “Wallahi bana jin ƙarfi…” “Cinye! Ko dai ki ci abinci ko kuma” ya zuba min ido yana washe haƙora, “ko kuma ki ci da hannu na in baki?.” Na fara turawa cikin tsoro. Hannu na rawar jiki, kaina a ƙasa, hawaye yana zuba cikin miya, yana hade da tuwo. Amma yana ci gaba da kallona da dariya mai tsoro. Yana faɗin Amaryata Amaryata.

Yana fita daga ɗakin, na ji yana taɗi da wasu

“Kai bash,” daya daga cikinsu ya faɗa, wanda naji an ce Abdul sunansa, “ Ya yi dariya mai hadewa da tari. “Sai Oga, sai Oga!”

“Kai Bashari, wallahi yau ka ci rabonka!”

“Kai! Wannan ba amarya ba ce alfarma ce. Uwar kyauta!”

“Sannu da saukar kwallo, wallahi muna murna!” Suna fadin haka ne, kowannensu yana riƙe da sigari, wasu da kwalbar ruwa mai duhu a hannu, suna murnar ganin sabuwar "amarya" ta Bashari. Wani daga cikinsu ya turo baki yace “Oga, amarya ta sauka, amma fa dole ne ka sanya mata tsaro kar kulya su shige gidanka.”

*****************

Nana hadiza

09030569336ƘADDARAR RAMLAH

SHAFI NA SITTIN DA BIYAR

Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!

Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!

Domin biyan kuɗi:

Acc Name: Bilkisu Sani Kaura

Acc Number: 7040402435 (OPAY)

Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:

09030569336 ko 07040402435

Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a

Arewabook @nanadiso10

https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693

********

Tun bayan tafiyar Ramlah da Bashari, mumy ta rufe kanta a dakinta tana kuka. Kukan da a zahiri ke kama da na tausayi, amma a cikin zuciyarta wani irin kwanciyar hankali da murna suke yawo. Da kyar take iya boye farin cikin da take ji, ganin cewa ta cimma burinta ta ruguza Ramlah ta murƙushe kyakyawar makomarta. Ta dade tana karkarwa da zubar da hawaye, tana motsa baki kamar mai karanta addu'a.

Wayarta ce ta yi kara. Tayi saurin dagawa, tana kauda hawayen da take kwaɓawa, tana murza idonta kamar ba kuka take yi ba. "Sai dake Zainabu "Cewar murya daga dayan bangaren wayar. " Aiki ya kammala. Su Ramlah rayuwa ta kare. Bakin ciki zai hadu ya kasheta. Wanda yaja dake bai sanki ba Zainabu!" Mumy tayi murmushi, amma ta daure muryarta cikin tsananin farin ciki. "Wannan abunda kikayi Zainabu, kin tabbatar min da ke diyar yakaka ce. Kin gama min da babin yarinyar nan. Kuma yanzu... yanzu sai ki samo dan masu kasar mai kudi ki haɗashi da bilkisu Hakan ne zai yi daidai." Sunata dariya da tsokana,cike da nishadi da murna, kamar ba su da zuciya ko tausayi. Sai ga karar Ana bude ƙofa. A firgice ta kashe wayar. Abba ne ya shigo dakin. Yana sanye da farin dogon riga, fuskarsa cike da gajiya da damuwa. Ya tsaya, yana kallonta, ya ce "Yanzu saboda Allah Zainabu, bazaki bar kuka ba? Tun safe har dare, kuka kawai kike yi? Wannan adalci ne gareki da zuciyarki? Ramlah aure fa tayi ba wani abunne yasameta ba kuma jnada tabbacin Bashari zai kula da'ita kamar ke. Mumy ta durƙusa kasa, ta fashe da wani irin kuka. Kukan da idan baka san ta ba, za a rantse da cewa kukan gaskiya ne. "Abban Ramlah... bazaka gane halin da nake ciki ba. Ramlah itace ni, ni ce Ramlah. Na dauke ta tamkar ɗiyar cikina Yadda nakeson Ramlah kaikanka kasan banson Bilkisu. Bazan iya samjn zaman lafiya ba sai naji muryarta. Don Allah kakira min ita."

Abba ya matso kusa da ita, ya dafa kafadarta. Cikin nutsuwa ya ce "Na gode Zainabu. Na gode da kulawar ki Na gode da juriya da ƙoƙarinki wajen rainonta. Allah ya saka da alkhairi. Nagama waya da su. Sun ce sun isa lafiya. Tana cikin koshin lafiya.”

********

*************

Tunda Bashari ya fice daga gidan, zuciyata bata samu natsuwa ba. Rayuwata kamar an jingina ta ne da bango, babu hanyar fice. Ban iya cin tuwon da ya kawo min ba, ko loma biyu cikakkun ban iya hadiyewa ba ga warinsa da tsanarsa, kamar zai fashe cikina.

Nayi shiru, na mike zuwa bakin pampo na gidan, na sha ruwa sosai, amma maimakon jin sanyi sai zuciyata ta sake rikicewa. Na koma cikin ɗakin da Bashari ya ajiye kayana, wanda ya sha bamban da ɗakin mutum, balantana wanda ake kira gida. Katifar da ke cikin ɗakin yagalalliya ce ta cika da datti da wari. Na kalli katifar, zuciyata na harbawa da tsoro da kuma kunya. Na runtse ido, amma kallon kazantar da ke cikin ɗakin ya ci gaba da bayyana a zuciyata. Sai na koma palon gidan inda ma akalla iska ke shigowa, duk da akwai kura. Na karkabe wata tsohuwar tabarma, na shimfiɗa zanina, Nayi filo da jakata. Na kwanta. Wallahi, bacci ya ki zuwa. Idanuwana biyu, zuciyata biyu, numfashina na taƙaici kamar an ɗaure shi. Duk da gajiyata, sai kawai na lumshe ido. Tsoron dawo war Bashari, tsoron rayuwar da ke gabana, tsoron kaina... sun mamaye zuciyata.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull