Kenza eBookz

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 106

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 106

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 106: Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 106. .......Shiru Najma tai taƙi…

4,219 words

.......Shiru Najma tai taƙi motsawa, sai yay murmushi, tare da kama lafayar ya yaye gaba ɗaya. Ganin hawaye share-share a fuskarta ya ce, “Oh oh kukan dai har yanzu bai isa ba ƙanwar Yaya Fawzan”. Sai ya jawota jikinsa kawai ya rungume. Kamar jira take sai ta sake sakar masa kukan. Shiru yay yana shafa bayanta a hankali, a cikin kunenta ya ce, “Kodai nima na tayaki muyi kukan kamar ƙyafi saurin gamawa da wuri”. Ƙwace jikinsata ta shiga ƙoƙarin yi tana ɗan kai masa dukan wasa a ƙirji kaɗan-kaɗan, ya sanya dariya yana ƙoƙarin riƙe hannun, kafin ya kaita kwance ya rufu a kanta yana bin fuskar tata da wani narkakken kallo. Baki ta tura masa. Ya ɗan ja lips ɗin kaɗan da faɗin, “Na tayaki kukan muyi saurin gamawa?”. Kanta ta girgiza masa. Ya ce, “To kema daina in gani”. Hawayen ta shiga sharewa da lafayar, sai da ta goge su tas ya ce, “Inyeee kaga amaryar Fawzan, kinfa daina kukan da gaske dama lallashina ake jira kenan”. Murmushi ya suɓucema Najma. Ta kauda fuskarta gefe tanayi. Shima murmushin yake mai ƙayatarwa, kafin ya maido fuskar tata suna kallon juna. Lips ɗinta ya ɗan sumbata tare da faɗin, “Karna ƙara ganin hawayen nan kinji ko. ALLAH yay miki albarka. Ya bamu zaman lafiya, ALLAH yasa yau mu samo Baby mai kama dake ƴar mutan Zaria”. Hannu tasa ta rufe fuskar ta da faɗin, “Nidai a'a”. “Miyasa?”. “Ba yau ba, yau bana jin daɗi, kuma mai kama da kai nake so dan mutan Darma”. Murmushi yayi da faɗin, “Ko kuma za'a min wayo ba. Dama yayanki ya turon saƙon gargaɗi, danna tabbatar masa sai na rama abinda yayma ma ƙanwata akan ki. Amma maimakon ya jira yaga yanda za'a ƙare har ya nuna karaya kamar ke”. “Ba karaya mukai ba muma, hanyar lafiya a bita da shekara ne kawai”. Dariya yayi mai ƙayatarwa, sai kuma ya tashi itama yana tadata ya ce, “Hakane kuma Love. Bara to na bi a hankali muyi tafiyar kunkuru. Oya muje alwala”. Sunyi alwala da taimakonsa. Bayan sun fito ya sanya musu sallaya suka gabatar da salla. Kazar da AA ya siya musu yace tazo suci. Tace ta ƙoshi. Murmushi yayi da kulawa yace, “Yayanki ne ya saya miki fa bani ba balle kiyi tunanin zance ki biya ni. Oya come and eat ba abinda zai faru”. Babu yanda ta iya dole taci kazar nan sai dai babu sakewa, hasalima bata mata wani daɗi ta riga ta sakama kanta damuwa da tsoro. Ya fahimceta tsaf sai kawai yay murmushi. Fita yay yace tai shirin barci. Shima zaije yayo. Kanta ta jinjina masa, yana fita taita addu'a ALLAH yasa matarsa ta hanashi dawowa. Da wannan addu'ar ta daure tai shirin barcin, ta ƙara shafe lungu da saƙo na jikinta da ƙamshi sannan ta kwanta zuciyarta nata rawa. Waya ta ɗauka ta turama Maanal saƙo, sai dai shiru fin minti biyar babu reply. Ta fahimci tayi barci dan haka ta haƙura ta ajiye wayar tai lamo a kwance....

Fawzan kam na fita sama ya haura ɗakinsa. Babu kowa a falon, amma duk datti bai samu gyaran arziƙi ba kamar yanda aka gyara ƙasan aka saka turare mai daɗi. Kansa kawai ya girgiza ya shige bedroom ɗinsa. Yana cikin zame kaya zai shiga wanka aka turo ƙofar aka shigo. Haka kawai yaji a ransa Nibras ce. Duk da bai tsammanin ganintan ba amma yasan ita kaɗai ce dai zata shigo masa ɗaki haka kai tsaye. Ita ɗin ce kuwa, sanye cikin kayan barci da sukai mata ƙyau. Dan ma ramar da tayi a bayyane take ga mai kallonta. Sannan kallo ɗaya ya fahimci tayi kuka. Bai tanka mata ba ya wuce closet abinsa. Ta bishi da kallo zuciyarta na zafi. Sai kuma ta cije baki tana hararrar inda yabi. Ƙofar ɗakin ta sakama key, ta nufi bayan gado ta ɓoye key ɗin inda bazai taɓa tunanin ta saka ba. Sannan ta koma gadonsa ta haye ta kwanta. Abinma abin dariya, wadda ake kawowa da tsiya-tsiya ce yau ta kawo kanta, lallai Najma kinzo da ƙarhinki😜. Malam ango Yaya Fawzan, tsaff aka gama gyara jiki aka fito ana zuba murmushin yau za'a sha warkajami. Amma mi sai idonsa ya sauka akan Nibras dake kwance a gadonsa ɗai-ɗai. Kamar zai yi magana sai kuma ya fasa, ya ciro kayan barci ya saka masu taushi da ƙyau. Sannan ya feshe jikinsa da kalolin turare masu tsada da bala'in ƙamshi. Daga closet ɗin ya fito gaba ɗaya ya nufi wajen mirror kamar bai ganta ba ya gyara sumar kansa da kwantacen gashin fuskarsa sannan yazo ya ɗauka wayarsa a bed side drawer ya nufi ƙofa batare daya dai tankama Nibras ɗin ba. Sai me yana taɓa ƙofa yaji gam. Ya murza handle ɗin ya sake murzawa amma ko motsi alamar tabbacin a kulle take. Juyowa yay ya zubama Nibras ɗin ido, cikin hana kansa hasala ya ce, “Miyasa kika kulle ƙofar nan?”. Shiru ta masa taƙi ko motsi. Ya sake magana nan ma tai shiru. Sai ya tako ya dawo cikin ɗakin ya tsaya a bakin gadon nesa kaɗan da ita ya ce, “Bani key”. Sai yanzu ta kallesa ta watsar, sai kuma ta taɓe baki tace, “Ka bani ajiya ne?”. Shiru yay yana kallonta, ya dai hana kansa yin fushin da take son yayi ya ce, “Amma kin san bana cire key a ƙofa, kuma kece kika shigo bayan ni. Mima ya kawoki ɗakina yau?”. “Oh ka cireni daga matarka ne da har kake tuhumata miya kawoni ɗaki?”. Wani banzan murmushi yayi yana jinjina kansa. Sai kuma cikin taɓe baki yace, “Kema kin san cireki a wannan matsayin babu rana kam, dole ki cigaba da zama a inda baƙya so, ki kuma cigaba da ganin abinda baƙya so, ki kuma dinga hangen abinda kike son a haramun gareki na har abada.” Sosai kamalamsa suka daketa, suka kuma ciji zuciyarta ƙwarai da gaske. Dan har sai da tai ɗan jimm tana kallonsa alamar maimaitasu take a zuciya tana musu fashin baƙi. Barin inda take yayi ya nufi closet duba sauran keys ɗin, sai dai abin mamaki babu ko ɗaya alamar duka ta kwashesu kenan. Baice komai ba ya dawo inda take, camak ya birkiceta yana dubawa a jikinta har cikin b ɗinta dan yasan zata iya sakawa amma babu. Ya duba bed side drawer nan ma haka, ya koma ta mirror nan ma haka. Sosai ransa ya fara ɓaci, cikin tsawa ya ce, “Nibras bani key kafin daga ni har ke rayukanmu su ɓaci yanzun nan”. “Oh oh yo su ɓaci mana. Key ne dai wlhy bazan bayar ba ko zaka kasheni, sai dai mayyar ta kwana ita kaɗai”. Shiru yay yana kallonta. Ƙasan ransa yana mamakin shi kuma take kishi yau, kai lamarin wannan yarinya sai ita. Tunda ya fahimci fitina take son suyi bako zai biye mata ba. Komawa yay wajen sofa ya kwanta, ya ɗauka wayarsa ya shiga kiran Najma. Sai da ta kusa tsinkewa ta ɗaga cikin yanayin barci amma a zahiri pretending ne. Shima ya fahimci hakan sai yay murmushi. Ƙasa-ƙasa yace, “Kina nufin har kinyi barci baki jirani ba Love!?”. Cikin shagwaɓa ta ce, “Ai nasan ka gaji Yaya, kaima zakai kwanciyarka ne ka huta abinka, shiyyasa ma na kwanta harna rufe ɗaki”. “Anya ya dace amarya ta rufema ango ɗaki a daren farko?”. “Yaya ba daren farko bane ai ka manta na uku ne, yau fa kwanana biyu na uku zanyi”. “Uhm haka ne kuma fa. Love mai wayo”. Murmushi Najma tai mai sanyi tana rufe fuskanta kamar tana a gaban shi. Shima sai ya murmusa da sake sauke murya a ƙasa ya ce, “Da gaske kina son na barki ki kwana ke kaɗai?”. A sanyaye tace, “Eh ALLAH kuwa, kaga akwai gajiyar hidima yau ansha zirga-zirga, ga iyayenmu duk basu tafi ba. Please Yaya kayi kwanciyarka, nima na kwanta anan kawai”. Murmushi yayi yana cije lips. Jikinsa gaba ɗaya ya gama saki. Wani irin buƙatar son kasancewa da ita yake ji ƙwarai da gaske. Amma sai ya sauke ajiyar zuciya. Cikin sirkawar murya yace, “Shike nan na barki Love, kiyi barci cikin aminci. Amma ya kamata nazo ko ɗan goodnight kiss a bani ai ko?”. “A'a basai kayi wahalar dawowa ba zan maka daga nan. Muhchhh!!!”. Ta sumbaci wayar tare da yankewa ƙitt. Sosai Fawzan yay sumar kwance, sai kuma ya runtse idanunsa yana mai cije lips tare da karanto addu'a domin samun saisaituwar lamarinsa. Ƙyaleta yay bai sake kira ba. Yay shiru yana tunani sai ya juyo dariyar Nibras cike da ƙularwa. Da ƙyar ya iya danne zuciyarsa yay mata banza. Amma wlhy ji yake kamar ya tashi ya lakaɗa mata dukan ban gishiri. Amma ba komai, baya buƙatar ramawa ta haka. Tunda tace da shi zatai game zata sha mamaki wlhy. Tasowa yayi yazo ya hau gadon ya kwanta, ya kashe fitilar ɗakin yana jinta tana ƴan waƙe-waƙen iskancinta yaba banza ajiyarta. Aiko ya jima kafin barci ya ɗaukesa, ita ko baima san lokacin da tai nata barcin ba........✍️

🤣🤣Ashe Nibras ɗin nan hegiyar kanta ce ina tausayinta

*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*

*+234 805 568 7449*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_💞AJIYA A DUHU....💞_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R

_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_

*_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣3️⃣

______________

.......Anan ko Babban Yaya yana garden abinsa yana aiki, sai da yaga sha ɗaya tayi sannan ya taso. Har lokacin gidan da ƴar hayaniya sai dai bamai yawa ba. Amma ganin fitilu akowane sashe idan ka cire sashen su AA ya fahimci wasu basuyi barci ba kenan. Sashen nasa ya shiga, kai tsaye ya wuce sama ɗakinsa. Yana jiyo ƙus-ƙus a ɗakin Saheeba baibi takai ba. A nan ɗin ma dai kowa yabar sashen ƴan uwan su Ameerah duk sun koma gidan Hajiya Shuwa. Sai Saheeba dake can a ɗakinta tare da uwarta da Nuratu da Hajiya Turai. Kuka take yi suna lallashinta. Sai maimaita masu take ƙirjinta kamar zai fashe. Sudai sunata tausarta ga ruwan rubutu an bata ta sha. Daga haka suka shiga kitsa abubuwansu har Baban yaya ya shigo bama su sani ba. Dan jin ba'ai masa rakkiya ba sunyi tunanin ma bazai kwana a sashen ba yau ma tunda gidan akwai baƙi har yanzu. Wanka Babban yayi ya canja zuwa kayan barci masu laushi da nutsuwa. Ya feshe jikinsa da turare sannan ya fito. Har yanzu yana jin ƙus-ƙus a ɗakin Saheeba. Yay ɗan jimmm sai kuma ya wuce abinsa kawai ya sauka. Bai san minene RK ya bashi ba yace inji Ajwaad, amma dai yana jin ƙamshin nama da zafinsa, sai dai zuwa yanzu ya huce dan haka ya nufi kitchen da ledar. Koda ya buɗe kuwa kaza ce lafiyayya da hadin salad, sai fresh milk. Kazar ya cire ya saka a bowl ya ɗumama. Sannan ya canja mata bowl ya saka a tray da plate ya saka madarar da cups guda biyu ya fito. Taku yake a hankali har ƙofar ɗakin da Ameera take ciki. Yay ɗan jimmm kafin ya murɗa handle ɗin a hankali ya shiga. Ameerah na kwance barci ita yama fara ɗibarta dan tayi tunanin bama zai shigo ba tunda gidan da baƙi, harta gyara jikinta ta canja lafayarta zuwa kayan barci masu ƙyau da laushi sai ƙamshi mai daɗi ke tashi a jikinta da ɗakin. Buɗe ƙofar ta sa ta farka, sai dai da yake fitilar ɗakin na a kashe sai lamp ce kawai a kunne ta gefenta itama ta sa hasken kaɗan sai ta buɗe ido tana kallonsa ta ɗan duhun. Tana ganin zai kunna hasken ɗakin ta maida idanun ta sake lumshe wa. Fitilar ya kunna mara haske sosai, kafin ya cigaba da takowa a hankali har zuwa bakin gadon. Ya ajiye tray ɗin a ƙasa ya kai zaune gefenta jikinsu na gogar na juna. Sai da ya mata kallon fin minti ɗaya kafin yay magana cikin miskilar muryarsa. “Uhmm dama amare na barci a ranar daren farkon su?”. Murmushi tayi amma bata motsa ba. Sai shima ya murmusa. Tare da kai hannunsa a karo na farka ya dafa ta. “My Soha ince kin min alƙawarin yau gaba ɗaya tawa ce ni kaɗai? Mizai sa kuma ki ƙare da pretending?”. Yanzu ma murmushi tayi, ƙasa-ƙasa ta ce, “Ba pretending nake ba barci nake da gaske. Dan na zata kaima ka kwanta”. “Uhm-uhm my Soha, ango yay barci shi kaɗai a daren farko ai babu lafiya kenan, dole a nemo likita ya duba shi”. Kaɗan ta jiyo ta kallesa, zatai magana ganin ita yake kallo shima sai ta kasa tai ƙoƙarin juyawa. Murmushi ya saki a karo na farko, sai kuma ya kamata ya ɗago ya zaunar. Kallonta yake sosai, hannunta na cikin nashi yana murzawa a hankali. Ita dai kanta a ƙasa ta gagara kallonsa. Fin minti ɗaya suna a haka kafin ya ɗaura hannunsa a haɓarta ya ɗago fuskarta da ƙyau. Cikin matso da tashi fuskar gab da tata ya ce, “Mi my Soha taci?”. Idannunta a lumshe ta ce, “Sohan ka bata jin yunwa”. “Ban yarda ba, dan bazan yarda ta kwana da yunwa ba gaskiya”. A hankali tai ƙoƙarin buɗe idannunta a kansa, sai kuma ta kauda kai dan bazata iya jurar kallon nasa ba. Shima sai bai matsa ba ya jawota jikinsa a karo na farko ya rungumeta tsam-tsam. Ajiyar zuciya suka sauke a tare. Cikin kunne ya raɗa mata abinda ya sanyata jin kunya. Tako ɓoye fuskar tata sosai a jikinsa. Murmushi yayi na tsawon lokaci, kafin ya ɗagota tare da miƙewa ya taimaka mata itama ta sakko. Gaban tray ɗin ya zaunar da ita shima ya zauna. Sai kuma ya matsota jikinsa cike da kulawa ya dinga bata naman da kansa. Itama sai ta dinga ɗiba tana bashi a kunyace matuƙa. A mamakin su sunci sosai, da alama duk suna jin yunwa dama. Hakama fresh milk ɗin sun sha, ya tattare komai ya maida gefe sannan ya sake ɗagata yace, “Oya muje ai brush da alwala.” Batai musu ba ta bishi, tana jin tsoron, amma tana gani zai ɗaga mata ƙafa yau kodan baƙi dake gidan. Musamman yanda bai nuna mata komai a kan hakan ba har yanzu. Sunyi brush ɗin tare da alwalar suka dawo. Ya saka musu sallaya sukai sallar. Ya dafa kanta yay addu'a kamar yanda addini ya koyar da mu sannan yay mata nasiha akan yanayin zamansu a yanzu. Ya kuma bata haƙuri akan nanda ɗan lokaci itama za'a gama nata sashen ta koma. Cike da girmamawa tace babu komai. A hakan ma ai normal ne tunda sashen babba ne. A hakan ma sai mutum yaso wani zai san da wani. Dan ko bedrooms ɗin ƙasan an killace su ne a gefe saima ka shigo falon ka gama bulayinka baka san da su ba. Yaji daɗin sauƙin kanta, dan haka ya miƙar da ita yana faɗin, “Saura barci, dan na gaji matuƙa kwana biyun nan babu hutu”. Murmushi kawai tayi batace komai ba. Da taimakonsa ta hau gadon ta kwanta, maimakon shima ya kwanta sai ya zauna yana ɗan duba wayarsa. Sai da ya bata damar nutsuwa a kwancen na kusan mintuna goma sannan ya ajiye wayar ya kashe fitilar ɗakin ya kwanta. A hankali ya nutsata jikinsa, cike da hikima da halin girma ya raɗa mata, “Kinyi barci baki kwaranye ma mjinki kishirwar dake damunsa ba My Soha!”. Gaban Ameerah ya faɗi, amma sai ta daure ciki-ciki ta ce, “Ayi min afuwa na gaji ne kawai, kuma kaima ina son kayi barci ka huta”. Murmushi yayi yana shafa bayanta cike da wayo, kamar bazai amsa ba sai kuma ya ce, “Karki damu zan sauke miki gajiyar gaba ɗayanta tabi iska, na lulluɓeki da ɓargon samun lada mai aminci. Sannan na biki da addu'ar shiga aljanna kusa dani in sha ALLAHU”. Har cikin rai taji kalaman nasa, dan haka ta ɗan sake nutsa jikinta tana sauke numfashi. Batayi magana ba, shima kuma bai bata damar yin ba ya ɗago fuskanta ya manna lips ɗinsa akai. Daga haka wasan ya fara canja salo zuwa na gaskiya. Tun tana tunanin iya takalar faɗan zai tsaya harta fahimci yaƙin za'ai babu ɗaga ƙafa. Abinka da manya da suka gama sanin wacece macen a zahiri da baɗini cikin hikima da tausasawa yake binta. Ita kuma tana nuna dauriya da jarumta duk da a sharar fagen ta bada haɗin kai itama. Sai dai fa a fagen ni sabun shiga ce kuka ta sanya masa da roƙo na yayi haƙuri ya barta. Amma ina Babban Yaya ya kwace da yawa, addu'a ce kawai zata iya tarosa maybe a wannan yanayin. Dan kuwa ya shiga wata sabuwar duniya ce mai abubuwan ban mamaki da al'ajabi. Kafin yau idan akace mata suna suka tara, ko matan nada banbanci sai yay ta mamakin ta ina? Kuma ta yaya? Wani lokacin har ƙaryatawa yake a zuciyarsa. Dan a ganinsa duk mace dai ai sunanta mace kawai. Amma a yanzu kam ya shaida ya kuma fahimci inda aka dosa tsaf sai dai ya zama malamin wasu kuma. Ba Ameerah data fita a hayyacinta ba take shan kuka shi kansa badan kar ace yayi abin kunya ba kukan zai sanya wlhy. Amma dai kada girma ya faɗi bara ai ta kurma kawai. To lallai kuwa ta kurman akai, dan faɗan kurma nacinsa yawa ne da shi har sai ya fanshe yake iya haƙura.....

Anan ɓangaren su Maman Saheeba bayan sun gama tausarta da tsara mata makirci kala-kala suka fito domin tafiya suka barta da Nuratu. Sun fito da tunanin ai Baban yaya bai shigo ba Hajiya Turai tace, “Nikam Nana rakani naga amaryar ma. Dan ina son ma na karanci yanayinta”. Babu musu Maman Saheeba tace, “Muje”. Maimakon suyi hankali ganin fitilar falon a kashe su fahimci kodai mai gidan ya shigo sai da yake kan baya ja basuyi wannan tunanin ba suka tunkari inda bedrooms ɗin suke. Aiko suna isowa gaban na farko babu shiri suka ja uban birki, jiki na rawa Nana ta kama hannun Hajiya Turai suka juya suka fice suna bige juna. Saida suka fito gaba ɗaya sannan Hajiya Turai tace, “Ikon ALLAH dama munafukin mutumin nan ya shigo? Yau kuma jarabawar data sameku na jiyo Ajwaad nima ta ritsa dani.” Gaba ɗaya Maman Saheeba ta kasa magana. Dan gaskiya al'amarin yazo mata a bazata bakamar nasu AA da sukai da gayyaba daman. Sunja tsahon lokaci bata iya cema Hajiya Turai komai ba. Harma ta fidda ran zatai maganar..........✍️

🤣Wanda bai ji bari ba dai. Tsoffin kawai🙄

*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*

*+234 805 568 7449*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_💞AJIYA A DUHU....💞_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R

_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_

*_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣4️⃣

______________

Alhamdulillah! Shin kunada labarin MG’s Beauty Lounge zai buɗe a ranar Litinin, 2nd June 2025 – daidai lokacin Sallah!😍

‘Yan mata da mata masu son kyau a Kaduna, lokaci yayi da za ku haskaka a wannan Sallah! MG’s Beauty Lounge ya buɗe da kwalliya, tsafta da ƙamshi irin na sarauniyar zamani!

Ga abin da zaki samu idan kika ziyarce mu:

Gyaran gashi da kitson zamani

Kwalliyar Sallah mai ɗaukar ido

Wanke ƙafafu da pedicure mai sanyaya rai

Kayan gyaran fata na gaske

Lalle mai kyau da salo na zamani

Tura-turai, humra, incense da ƙamshi masu daɗi

Shirin amare da na musamman

Ba kawai gyara muke ba – kulawa ce ta musamman ga kowace sarauniya. Zo ki ji daɗin wanke ƙafa, lalle, kwalliya, ki saya kayan kyau da ƙamshi – komai a wuri guda mai kyau.

Adireshi: Block 21, Nnamdi Azikiwe by Makarfi Road, bayan gidan Indomie, kusa da Sorera Restaurant, Kinkinau, Kaduna.

Tambaya/Booking: WhatsApp: 08062991549 Kira: 09016108092 / 08064532391

Ki zo ki gani da idonki – ki ji daɗin sauyin MG’s Beauty Lounge. Bi mu a IG & TikTok: @MGsBeautyLounge

____________

........Ita ko Saheeba bayan fitarsu bathroom ta shiga, hawaye sun gagara tsaya mata sai kissima abinda zai faru yau tsakanin Babban Yaya da amarya take. Ita ta sani bazai iya kauda kai ba wlhy, musamman da suka jima basa taren nan. Kuka ta sake ɓarkewa da shi tana jerama familyn Darma kaf ALLAH ya isa da tsine musu. Tare da addu'ar in sha ALLAHU suma duk sai amma yaransu kishiya. Tadai gama bore-borenta ta fito. Ta canja kayan barci maimakon ta kwanta abinta dan Nuratu harta fara barci sai shaiɗaniyar zuciyarta ta ingizata wai taje taga ko Babban Yaya ya dawo. Haka kuwa ta fito, ɗakinsa ta nufa, tana buɗewa uban ƙamshin turarensa daya baza ya cika mata hanci. Ta kunna fitilar ɗakin, babu kowa a ciki sai alamun anyi amfani da ɗakin ta gani. (Kenan ya dawo har ya tafi ɗakin shegiyar ita ko sallama bata samu ba) Ta ayyana a zuciyarta. Ɗakin ta rufe ta shiga sakkowa ƙasa, (idan ka saba abu, ko a karan kanka saika aikata shi kake jin daɗi koda zaka cutu) ɗabi'ar laɓe ta riga ta shigi Saheeba ƙwarai da gaske. Duk da duhun falon haka ta dinga tafiya cikin sanda da laluben hanya har bedrooms ɗin Ameerahn a yanzu. Yes tafa ji kukan Ameerah kafim ma ta ƙarasa ga ƙofar amma ta fi yarda da gara dai ta matsa sosai ta tabbatar duk da yanda zuciyarta ke duka da ƙarfi kamar zata buɗe ƙirjinta ta fito. Aiko harda su kanga kunne a jikin ƙofar, tako jiyoma kunnenta abinda yafi wanda take buƙatar jin. Dan har babban gwaska taji nasa kalamin. Kar-kar jikinta ya fara rawa, hawaye suka ɓalle suna rige-rigen zubowa. Ruff idannunta suka mamaye da duhu alamar jininta ya haura sama sosai irin lokaci ɗayan nan na bazata. Da ƙyar ta iya riƙe ƙirjinta dake bugawa kamar zai buɗe ta fara bin bango tana jan numfashi da ƙyar. Kaɗan ya rage itama dai ta maimaita na Mamy a stairscase, ALLAH dai ya taƙaita mata wahala sai tuntuɓe da tayi ta fasa babban yatsar ƙafarta. Tana zuwa stairs na kusan biyar ɗin ƙarshe tafiyar ma ta gaggareta dole ta duƙe ta koma rarrafe. Da haka ta ƙarasa kai kanta cikin bedroom ɗinta sai Nuratu jin nishinta tayi da kakari. A fitgice ta tashi tana kallon ta, sai kuma ta sakko tana faɗin, “Aunty lafiya kuwa?”. Ina Saheeba neman shiɗewa take, dan a rayuwa kunnenta bai taɓa juyo mata mummunan al'amari irin wannan ba. Bata taɓa jin nadamar yin laɓe ba irin yau. Ko lokacin da suka ji na Maanal ita batai ko gezau ba Mamanta ne da Mamy suka ruɗe. Da ƙyar Nuratu ta kamata zuwa kan gado, ta bata ruwa tasha. Kamar jira tana gama shan ruwan ta ɗaɗe da kuka. “Na shiga uku Nuratu, na shiga uku. Shike nan wlhy nasan ma na rasa Daddyn Naufal, na rasashi an aura masa mayya ƴar masu asiri da tsafi azzalumai sun rabani da mijina, sun rabani da shi shike nan na mutu ni Saheeba. Yau ni da kunnena nake ji Daddyn Naufal na jerama wata manyan kalaman da bai taɓa ambata min ba koda wasa duk ƙoƙarin da nake na shan abubuwa dan faranta masa rai. Wlhy ko uhum bayayi idan yana tare da ni. Nuratu surutai fa yake, yana jera mata zantuka masu girma da nuna mutuntawa da jaddada mata ita ta daban ce, tafi sauran mata, bai taɓa sanin mace haka take ba se yau, kenan ma ni ashe baya jina a ransa, na shiga uk......” kuka ya sarƙeta ta kasa ƙarasawa. Cikin takaici Nuratu ta ce, “Kai aunty wai laɓe kikaje kima Yaya? Ina gaya miki gaskiya akan wannan halin amma baƙya yarda, ai gashi nan kin jiyo abinda yafi ƙarfinki. Wannan banzan halin da kuka iya keda Mama haka kuka sakani naje na jiyo a sashen Yaya AA ni da Mamy gashi nan har yanzu na kasa samun zaman lafiya a rayuwata, ina ƴar ƙarama dani hawan jini ya haye min. Sau dubu zanga matarsa yanzu sau dubu abinda ya faru yake faɗo min a zuciya. Hakan kuma na sakani ganin ta min nisa, ta mamaye komai ta yanda koda zan samu sai dai saura, jina nake kamar Maanal ta fini daraja da cika mace. Balle ke dake tare da mijin nan har kije ki musu laɓe a irin wannan ranar, wannan lokacin. Mtsowww! Kin cuci kanki”. Kuka sosai Saheeba keyi, kalaman Nuratu na sake ƙona mata zuciya. Har ji take ƙirjinta na mata wani kalar turiri na hayaƙi. Taci kuka sosai har asubahi bata huta ma kanta ba. Nuratu kam tuni ta juya tai barcinta bayan itama ta gama nata hawayen tunawa da AA maybe shima yana can yana nashi karatun, ta tuna yanda ya wani rungume Maanal a ɗazun da goyatan da yayi. Ita dai ALLAH ya rufa mata asiri barci ya saceta tabar Saheeba a halin ha'ula'i...

______★

Readers Also Read