Kenza eBookz

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 46

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 46

Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 46: Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 46. Yau juma'a, koda Maanal taje…

4,224 words

Yau juma'a, koda Maanal taje office signing kawai tayi ta fito. Dama tama tsayar da mai taxi ɗin daya kawo ta. Tana ƙoƙarin shiga taxi ɗin motar AA ya shigo. Kallo ɗaya taima motar ta ɗauke kanta ta shige abinta. Sai dai tana ƙoƙarin rufe murfin taxi ɗin idannunta suka sauka akansa. Shima kallona yake cike da wani yanayi na tuhuma-tuhuma, mamaki, da kuma kewa. Fuska ta yamutsa tare da ɗauke idanunta a kansa tace ma mai taxi ɗin, “Muje”. Mai taxi da bai san mike faruwa ba yaja motarsa yay gaba... Daga Mawaad Company wajen gyaran jiki aka sauketa. Dan Didi nacan tare da Barrah. Itama gyaran jikin aka shiga yi mata, dan Manaal ƴar gaye ce. Aka mata ƙunshi dai-dai misali baƙi da ja kaɗan da yay mata ƙyau kamar itace ma amaryar. Dan Didi sai tsokanarta take yi. Ita dai murmushi kawai take yi batare da tace komai ba. Basu baro wajen ba sai la'asar. A gajiye suka shigo gida. Nan ma kuma basu zauna ba suka ƙarasa shirinsu. Biyar da rabi a train station tai musu. Sun iso Kaduna ana magriba. Amal ce da su Munaya suka zo ɗaukarsu. Ai fa Munaya ta maƙalƙale Maanal dan ALLAH ya haɗa wannan ƙauna. Gashi kuma Munaya na kama da Maanal ɗin sosai. Sun iso gidan cike da mutane, dan yau za'ai mothers event. Ɗazun akayi Sister & brothers event da ƙannen Yazeed suka shirya ma amarya. Kusan ma duk danginsu ne a wajen sai ƙawayen amarya. An kuwa rankwashe an ƙwalle dan ango kansa dole ya halarci wajen bisa tirsasawar Hajiya Yaya. Kasancewar su Maanal na wajen gyaran jiki basu maida hankali a gani ba. Koda yake ita bama tana bibiyar komai bane, Didi ce idan ta gano da Amaal ke bata labari. Koda suka fito a mota da yawan mutane sukai musu caa da idanu. Wasu ma har suna ɗan ƙus-ƙus. Cikin ikon ALLAH kuma Maanal na fitowa akan Yazeed ta fara sauke idanunta. Ya fito daga sashen Daddy abokansa kusan shida da duk ta sansu zagaye da shi. Yayi masifar ƙyau cikin shadda ɗinkin tazarce, ga hula ya murza fuskarsa na fidda wani annurin gyaran fuskar da yasha. Sosai ya zama wani sakwakwa saboda ganin Maanal. Har takai suma abokan nasa duk suna zuboma inda sukaga yana kallo idanu. Suma dai kamar sun ɗan shiga shock da gannin Maanal ɗin, sai sukai duru-duru. Ɗauke kai Maanal tai tare da jan hannun Munaya da Barrah tai wucewarta sashen Ammie. Haka kawai ta ɗan ji ɗaci a ranta. Sai faɗi take, (yace bai son aure amma gashi yana faman zuba kwalliya da washe baki kamar tsohon gwauro) a fili kam miskilar fuskarta ta shanye komai. Suna shiga ta saki su Barrah ta ɗane Ammie. “La'ila yarinyar nan wai karyani zakiyi ne dan ALLAH”. Ammie ta faɗa tana kai mata mintsini. Dariya Maanal ta sanya da sake mamaye Ammien sosai. Sai kuma ta mata kiss a gefen fuska tana faɗin, “I miss you sweetie na”. Dariya ƴan falon suka sanya. Dan dangin Daddy ne da suka sauka anan sashen Ammie ɗin. Sai yanzu Maanal ta farga da mutane. Sai kuma taji kunya ta shiga ɓoye fuskarta a jikin Ammie. Nan ma dariya kowa ke mata har dasu Amaal da suka shigo. Sai kawai ta janye jikinta ta nufi bedroom ɗinta da gudu. Dan tasan duk rintsi Ammie tasan zasu zo bazata bari kowa ya shiga ɗakin ba tunda ma akwai na baƙi ai. Aiko babu kowa ɗin, an dai gyarshi tsaf yanata ƙamshi.....

Bayan sun huta Ammie ta sakasu shiryawa domin zuwa wajen event ɗin. Maanal taso ta turje. Amma Ammie taita lallashinta. Dan bata son Manaal ɗin ta zauna a gida a fassara zaman nata da wani abu daban. Haka badan taso ba ta shirya tsaf cikin wani swiss lass fitted gown datai masifar zauna mata a jiki. Ta zauna tai kwalliya dan a ɓangaren kwalliya ma Maanal artist ce sosai. Ta koya kuma ta iya saboda sonta da ado, dan ma yanzu kura tayi lafiya. Su Amaal ma har Ammie duk itace ta musu kwalliyar, tai ɗauri daya saka kitsonta fitowa ɗas kamar ka lashe. Koda suka fito babu wanda bai yaba ba a falon. Wasu a dangin Daddy ɗin har suna faɗin, “Kai jama'a yarinyar nan ma ai tafi amaryar ƙyau da komai ga nutsuwa wlhy. Amma uwarsa na neman cuta masa. Ga yarinya mace har mace Masha ALLAH”. Ita dai Maanal da su Ammie babu wanda yace komai. Haka suka fito compound. Kusan duk an wuce. Sai ɗai-ɗaikun mutane a gidan da suka rage. Dan ana kai wasu ne ana dawowa. Dole Maanal taja mota ɗaya, Amaal taja ɗaya Shahidah ma haka. Dan mota uku sukai, a hakan ma a ɗan matse suke dan Ammie tace bazatai driving ɗin dare bane dan Daddy ya hana.....

___________★

Gida ne katafaren gaske daya amsa suna gida. Komai a cikinsa tsari ne irin na gogaggun ƴan boko da sukaci suka yada kai aka kuma tashi a cikin rayuwa irin ta turawa. A nutse farar bafulatanar dattijuwar ke sakkowa daga staircase ɗin dake tsaye ƙam a tsakiyar katafaren falon tamkar an zana. Sosai ta manyanta, sai dai tsufane irin na masu jin daɗi da babu wahala. Ga ƙaramin jikin Fulani ALLAH ya bata. Cike da girmamawa masu aikin dake ta ƙoƙarin shirya abinci a ƙaton dining table suke mata sannu da fitowa. Amsa musu tai da kulawa. Kafin ta furta, “Babu wanda ya fito ne har yanzu?”. “Eh Mah-mah, amma Alhaji ƙarami da Yaya Rafeeq yanzu suka dawo suna a sashen Yaya Rafeeq”. Kanta ta jinjina kawai. Sai kuma ta sake juyawa upstairs ɗin tana faɗin, “Ku ƙarasa wani yay kiransu. Bara nama Doctor magana”. Daga haka ta sake hayewa saman. Fin mintuna goma sai gasu sun fara firfitowa. Kamilallen tsoho da akaga jiya akaga yau Dr Kasheem Kura ne ya fara fitowa matarsa Hajiya Maryam Ishaq Darma biye da shi. Sai ga kuma wata matashiyar mata da bazata wuce shekaru talatin ba da ɗoriya itama. Sosai take kamanni da Mah-mah da su Oum. Hakan na nufin itama ta fito daga tsatson Baffa Ishaq Darma ne. Yara biyu biye da ita ƙyawawa da shekarunsu zasu iya kaiwa biyar da bakwai. Da gudu suka barta suka nufi tsoffin kakanninsu. (Rufaidah kenan, itace Autar su Abah, dan Baba Umar Ishaq Darma mahaifin Abah ne ya haifeta. Itace kuma ke auren Sulaiman ƙanin Oum dake bima Hajiya Majdiya, RK kuma ke bi masa. Yaransu uku duk maza, babban mai shekara tara bai kai ga fitowa ba. Suna zama a dining ɗin RK da Sulaiman da suke kira Alhaji Ƙarami suma suka sakko. Hira suke suna dariya kamar wasu abokai, duk da Alhaji Ƙarami ya girmi RK nesa ba kusa ba akwai shaƙuwa mai yawa a tsakaninsu. Rayuwar Turai sun tashi sune abokan juna, sune ƴan uwan juna. Suma duk kujera suka ja suka zauna, bayan RK ya gama ɗaga yaran sama suna dariya. “Barka da dare Abbu, Mah-mah barkan ki”. Murmushi Hajiya Maryam da Dr Kasheem sukayi a lokaci guda idanunsu akan RK da yay gaisuwar. Cike da kulawa Mah-mah ta ce, “Auta anya tuzurancin nan bai isa ba haka nan? Na fara gajiya da baka abinci fa a gidan nan”. Kai RK ya shafa yana murmushi, sai kuma ya kalla Abbu. “Abbu ai kai baka gaji da kawowa naci ba ko?”. “Nima kamar na kusa fara ƙorafi irin Mah-mahn ku”. Dariya suka sanya gaba ɗaya. Alhaji ƙarami ya ce, “Abbu kaima bazaka bashi kariyaba yau?”. “A'a ina zan bari aima Autana tawaye Alhaji ƙarami. Kawai dai nima ina son yayi auren ne na gaji da ganinsa haka nan.” “Ai ni nama daina cewa komai Doctor. Amma gab nake da dubawa cikin ƴaƴan dangi na aurama Rafeeq da Ajwaad da Najeeb. Su ukun nan tuzurancin su ya ishi kowa a family ɗin nan. Garama su yanzu suna a ƙasar tasu, shiko Najeeb yaje ya tare a ƙasar turawa da anyi magana yace bussines”. Fuska da murmushi Abbu ya ce, “Insha ALLAH zasuyi kwanan nan. Dan autanki dai gobe zamu tattauna akan nashi batun. To Inaga Ajwaad ɗin da Najeeb ɗin ma duk za'ayita ta ƙare, dan ta bakin Kamila sai an biyo musu ta bayan gida.” “To ALLAH ya tabbatar da alkairi”. A tare duk suka amsa da Amin, kafin kowa ya fara ƙoƙarin zuba abinda yake buƙata a plate ɗin da ya ɗauka. Dining ɗin RK ya ɗan kalla sai kuma ya duba Rufaidah. “Ƙanwa! Wai ina spider man ne?”. Baki ta ɗan taɓe da faɗin, “Yana ɗaki Yaya Rafeeq, fushi yake har yanzun. Daga ni har Mah-mah ya daina kulamu a gidan yau. Tunda kuka fita ma bana tunanin mun gansa, shi a dole sai yabi Mamy Abuja bayan kuma ga makaranta ba hutu akayi ba”. Dariya Abbu yayi, cike da manyantaka ya ce, “Ai laifinku ne. Daga ke har Maman taki kun cika faɗa ne. Shi kuma ku lura yaro ne da bai son yawan hayaniya, komansa irin na iyayensa ne Ajwaad da Fadeel, shiyyasa ma yake ƙulafucinsu, dama kun barshi yabi Kamila ɗin sai a maidoshi ranar lahadi”. “Tab Abbu murɗa-murɗa kenan. Garama Fadeel ɗin da ɗan sauƙi. Amma wannan Autan na Aunty Babba sai ita wlhy. Ai sai mu tattara idan yayi aure mu maida masa can su ƙarata. Dama ai duk duniya ba wanda Abdull ke ƙauna sama da Ajwaad”. “To ai hali yazo ɗaya ne”. Cewar Alhaji ƙarami. Dariya duk sukayi, sai kuma RK ya miƙe yana faɗin, “Ina zuwa bari na fito da shi.” abincin su sudai suka cigaba da ci. Kusan mintuna biyar kuwa sai gashi ya fito goye da matashin yaron a bayansa. Sosai yake kamanni da Alhaji ƙarami. Kai da ka gani kasan shi ya haifi abinsa. A kujerar kusa da shi ya saukesa, shiko yaron sai wani ciccin magani yake. Yaki ƙallon kowa. Dariya sosai Abbu yake gumtsewa, dan ganin Mah-mah da Rufaidah da yaran ke kira Ummy na hararrar yaron. Shi kuma sai wani ƙara tsare gida yake yi. “Ni mutum ma idan ya sake shiga sabgata a gidan nan ba sai nayi kuli-kulin rakiya da shi ba”. Cewar Mah-mah. Aiko Abdull sai ya sake tura baki gaba yaƙi kallonta. Kasa haƙuri Abbu da RK da Baba Ƙarami sukai suka sanya dariya... Haka sukaci abincin nasu cike da raha. Dan akwai shaƙuwa mai ƙarfi a tsakanin wannan zuri'a. Musamman daya kasance mahaifinsu mutum ne mai sauƙi da sanyin hali. Dan kaf halayen Rafeeq irin nashi ne. Mah-mah ce ma mai ɗan zafin yanayi............✍️

09032345899

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_💞AJIYA A DUHU....💞_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R

_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_

🅿️➖8️⃣9️⃣

______________

........Shigowar su Maanal cikin hall ɗin ya matuƙar ɗaukar hankali. Dan a dai-dai lokacin da ake addu'a ne. Wajen ya kasance tsit. Suko yanda aka zubo musu idanun bai damesu ba. Sai ma wajen zama da suka samu aka ƙarasa addu'ar da su. Kafin a fara abinda ya shafi mutane. Duk motsin Maanal a idon Yazeed ne, ita ko taƙi yarda ma ta kalla inda suke shi da amaryar tasa da tasha ƙyau. Itama amaryar hankalinta duk yana akan Maanal ɗin, sosai take jin tsanarta, amma tsoron nunawa take a gaban Yazeed. Dan ranar data nuna ɗin ya tabbatar mata zai iya fasa aurenta akan Maanal. Dan haka ta kiyaye idan tana son kasancewa da shi. Dole ta kama kan nata take kuma yin taka tsantsan. Amma a ranta wata irin wutar ƙiyayyar Maanal ce mai ci da zafi da ƙarfi ke sukarta. Hakama mahaifiyarta Aunty Sabuwa. Dan ko yanzu taso yin abinda zai wulaƙanta su Ammie a wajen mai bima Hajiya Yaya ita kuma Sabuwar yayarta ce ta ƙwaɓeta. Dan ita tana da hankali da sanin yakamata matuƙa..

Taro ya tashi lafiya. Ammie ce kawai taje taima amarya da ango liƙi. Amma su Amal duk ƙi sukayi, balle Manaal da dama ko motsawa batai ba. Hasalima charting suke ita da RK hankali kwance. Ana tashi sune ƴan gaba-gaba a masu wucewa gida. Yanayin gajiyar tafiya da rashin samun isashen hutu suna shigowa gidan kowa makwanci ya nema. Washe gari safiyar asabar aka tashi da shirin ɗaurin aure. Sai yinin biki da Hajiya Yaya zatayi. Zuwa dare ayi dinner sannan a kawo amarya. Sai washe gari walima da buɗan kai baki ya tashi. Duk da nan gidan anguna ne bana su amarya ba cike yake...

Sosai abin duniya ya dami Yazeed. So yake yaga Maanal amma hakan ta gagara. Dan jiya daga wajen mothers event ɗin nan dole hotel ɗin da abokansa suka sauka yaje ya kwana. Ya kira wayarta kuma a kashe. Yanda ya kwana da ita a rai ya sashi zuwa gidan yau da wuri. Dama anan sashen Ammie aka haɗama abokansa breakfast, sai ya samu damar fakewa da hakan kuwa. Bayan ya gaishe da dangin Daddy dake nan sai ya zauna suka cigaba da hira. Dan yaga kowa tsakanin Shahidah da Amaal dake shirya abincin abokan nasa da Aunty Sakina amma babu Maanal. Cikin raɗa-raɗa yake tambayar Munaya da tazo gaisheshi. “Uncle sun fita ita da Aunty Amrah.” Sai da ya kalla agogon hannunsa da mamaki ya furta, “Fita kuma da safen nan? Ina suka je to?”. “Nima ban sani ba”. Shiru kawai yayi ransa na ƙara jagulewa da tunani. Sai kuma ya miƙe ya fita. Can waje ya koma ya tsaya a ƙofar gida. Duk ma inda suke ai dole in sun dawo tannan zasu shiga gidan. Yana a wajen kusan minti talatin yana dakon jiransu sai ko ga napep ta tsaya a ƙofar gate ɗin. Amrah ta fara fitowa tana dariya, sai Maanal fuskarta da murmushi, da alama dai wata maganar suke data basu dariyan. Su duka hannayensu da kaya. Amrah ce ta fara lura da yayan nasu, ganin yanda ya tsume fuska ya sata haɗiye dariyarta. Ita dama Maanal tuni ta daina murmushin duk da bata gansa ba, sai da ta juyo zasu nufi hanyar shiga idonta ya sauka a kansa. Ɗan turus tayi tana kallonsa, sai kuma tai ƙoƙarin janye dubanta a kansa a taƙaice ya ce, “Good morning ” ta raɓa zata wuce. “Zonan”. Ya kirata a dake. Cak ta tsaya, jitake kamar tace bazata zo ba. Amma dai ta dake ta dawo da baya, yayinda Amrah ta amshi kayan hannun nata. Dan daga gidan Amaal suke, ɗinkunan su ne da tela bai samu gamawa ba sai jiya, shi kuma mijinta ya amso jiya da dare shine yau Maanal ɗin suka je ɗakkowa a gidan... “Fushi ake dani ko?”. Ya faɗa cikin kwantar da murya, kamar ba shike tsume fuska ba. Batare data kallesa ba ta ce, “Mi kamun da zanyi fushi da kai Yaya. Kawai dai yanayi ne”. Murmushi ya saki mai armashi. Sai kuma ya sake matsowa kusa da ita sosai. Cike da lallashi ya ce, “To nidai ina roƙon afuwa dan ALLAH. Har yanzu kuma baki maida wayarki ba ne?”. Kallon wayar tata dake hannunta tayi, batare data kallesa ba. “Kwana biyu da suka gabata na maida.” “Shine kuma koma a taɓani. Naso sauka Abujan sai aka samu matsala. Dan bammayi zaton ganinki a kd ɗin ba”. Yanzu kam murmushi ta saki, murmushin daba cika gani yay a fuskarta ba. Sai dai batace komai ba. Kafin shima yace wani abu wasu ƴan uwan Hajiya Yaya suka iso. Wani shegen kallon banza suke zuba mata, dan labarinta duk ya gama karaɗen danginsu daga jiya. Yayinda shi kuma Yazeed hankalinsa ke a kansu yana musu sannu da zuwa. Da wannan damar Maanal ta zame jikinta ta gudu. Sai waigawa yay yaga wayam bata a wajen. Yaso bin bayanta, sai baƙin suka sake janye hankalinsa dole ya haƙura......

_________★

Da mamaki Oum ke kallon AA dake shaƙar barci a gadonta. Da alama ma ya manta da yau zasuyi tafiya. Tunda suka kammala breakfast yau a ɓangarenta su duka gidan aka cigaba da hira shi kuma ya tashi ya shige bedroom ɗinta basu sake jin ɗuriyarsa ba. Umarnin zuwa kowa ya shirya da Abah ya basu ya saka kowa tashi ya nufi shiryawa. Ita dama cikin shirinta take dan haka ta shigo domin ganin mi AA ɗin keyi a ɗaki, kawai saita ci karo dashi a bargo ma ga ac ya ƙure. Ac'n ta kashe, kafin ta ƙarasa gaban gadon tana kiran sunansa, dan tasan bashi da nauyin barci. Idanu kuwa ya buɗe a hankali ya sauke a kanta. “Kowa nacan ya shirya kai kana nan kana barci Auta?”. “Oum ALLAH ni barci nake ji, weekend ɗin nan nefa mutum ke ɗan samu ya huta. Wai inama za'aje ne?”. “Koma inane idan munje zaku gani. Kuma ka tashi kafin Abah ya shigo ya samu baka shirya ba”. Fuska sosai ya ɓata. Sai kuma ya yaye duvet ɗin ya tashi tare da sakkowa. Oum dai na tsaye tana kallonsa. Gadon ya fara ƙoƙarin gyarawa. Oum ɗin ta dakatar da shi. “Kaga barshi jeka shirya zan gyara”. Kafaɗa ya maƙe mata ya cigaba da gyarawa, sai da ya gama tsaf sannan. Wannan ba komai bane a garesu su duka. Dan Oum ta riga ta horesu da aiki har girki babu wanda bazai iya yi ba su duka ukun. Yana fita tayi murmushi, dan tasan a cike yake fam. Itama ɗan shishshirya abinda take buƙata ta shiga yi...

Kusan sha ɗaya duk sun fito cikin shiri, AA ne ƙarshen fitowa cikin ƙananun kaya. Aiko Abah ya korashi canjawa. Oum ya kalla a shagwaɓe, ta masa alamar ba ruwanta. Sai ya tura baki ya koma. Aiko Fawzan ya shiga dariya da tsokanarsa. Babban yaya yayi murmushi su Nibras na taya shi dan sun san su dai babu damar yi a zahiri. Abah ma murmushin yayi, yayinda Mamy tai kamar bata san anyi ba. Bai wani jima ba sai gashi ya fito cikin wani arnen yadi omo blue daya ji ajiyayyen ɗinki. Ya kawo hula ya murza. Kusan su duka sai da suka ambaci masha ALLAH a zukatansu. Dan manyan kaya nama AA masifar ƙyau shi kuma baya son sakawa. Nibras kam ji take kamar ta haɗiyesa ta huta. Fawzan da bakinsa baya iya shiru ya shiga yimasa hoto da faɗin, “Kai wankan nan gaskiya bai kamata ya tafi a banza ba tuzurun gidan mu. Dolene na poster ka a media ko zamu samu wata tace tana so mu haɗa mata da cin hanci.” Dariya su Abah suka sanya. Oum ta ce, “Yarona yafi ƙarfin sai an haɗashi da cin hanci sannan ya auru. Fawzan ka kiyaye mu”. “Oum kada fa ku cika baki, yanzu yayin yara ake masu jini a jika shi kuma ya zama tuzuru”. AA dai bai kulashi ba. Sai ma kama hannun Anum yay suka shige mota. Aiko zaram Nibras ma taje jikin motar ta tsaya. Babu wanda ya damu da hakan, sai ma Abah da Oum da Mamy suka shiga tasu motar tare, Babban yaya ma ya shiga Saheeba ta shiga kusa da shi. Sai Naufal ya shiga baya. Can kuma AA a mazaunin driver Fawzan ya shiga kusa da shi Nibras da Anum suka shiga baya. Fawzan yasan AA ba ƙaunar tuƙi yake ba a rayuwarsa, dan haka ya kallesa da faɗin, “Zaka iya kaimu har Kaduna babu wata damuwa”. Kallonsa shima AA ɗin yay da faɗin, “Wai dama Kaduna zamuje? To yin me?”. “Nima ban sani ba, amma biki Abah yace ai kamar”. “Yanzu saboda zuwa biki aka hanani barci na. Kuma dan ALLAH ba sai a tafi a train ba”. “To ya muka iya, kasan Abah da Oum akan son dangi. Ni kaina yau inada wani ɗaurin aure a cikin Abujan nan, yanzu dai bani driving ɗin kawai”. “No barshi muje, idan na gaji sai ka amsa”. Cewar AA yana yin horn. Shi ya fara fita, Babban Yaya biye da shi sai drivern Abah a ƙarshe. Haka suka ɗauki hanya a jere gwanin sha'awa. Babu damar yin gudu dan in ana tafiya tare da Abah dama babu zancen gudu yaci ƙaniyar mutum. Sai dai abinka da lafiyayyun motoci cikin amincin UBANGIJI sha biyu da kusan arba'in a Kaduna tayi musu. Babban Yaya da Abah suka koma motar AA. Nibras suka haɗe da Saheeba data amshi tuƙin Babban yaya, oum da Mamy suna tare da driver. Su gidan Ammie aka nufa da su. Su kuma su Abah suka wuce masallaci domin yin sallar juma'a da ɗaurin aure. Invitation card ɗin Abah ta miƙama AA. Bayan ya gama dubawa ya juyo yana kallon Abah ɗin, dan suna baya shi da Babban Yaya. “Abah kasan nifa ba wani sanin Kaduna ɗin nan nayi ba.” “Eh mu samu mai napep ai zai kaimu in sha ALLAH”. Haka kuwa akayi, dan da mai napep duka samu ya jagorancesu har zuwa masallacin da aka rubuta a jikin katin. Sun kuwa samesa cike da jama'a, da alama akwai wasu ɗaurin auren bayan wanda suka zo.....

____★

Su Oum ma sun isa gidan Alhaji Usman Chalawa. Tun fa a kallon anguwar jikin Mamy ya fara ɗan sanyaya, dan tayi zaton har yanzu su Ammie a irin waccan rayuwar ta baya suke. Ko dataga gaban ƙaton gate ɗin da sukai parking sai tai ɗif. Godiya driver yay ma mai napep ɗin daya jagorancesu suma, Oum ta masa alheri sannan suka samu waje sukai parking a nan gefen gidan. Akwai ƴan biki dake ta shigi da fita dan haka suma suka shige. Tabass gida ne babba kuma sashe-sashe. Duk da nasu yafi ƙawa da girma sun san anan ɗin ma babu raini gidan masu akwai ne. Basu san inda zasu nufa ba dan haka Oum tai ƙoƙarin kiran layin Shahidah. Bugu biyu kuwa ta ɗaga, cikin girmamawa tai sallama da fara gaishe da Oum ɗin. Murmushi Oum tai tana amsa mata, kafin ta ɗora da faɗin, “Gamu a harabar gidan ku bamu san ina kuke ba”. Cikin mamaki da kuma rashin fahimta Shahidah ta ce, “Oum gidan mu? Wai nan Abuja?”. “A'a Kaduna, inda ake biki”. Ai ji Shahidah tai tana neman rikicewa. Hakama Amal ta saki soson shafa hodan hannunta tana kallon Shahidah. Suna a ɗakin Maanal ne suna shiryawa dama. Dan sai yanzu suka samu dama saboda aiki. Cikin sauri Shahidah ta yanke kiran, ta ja mayafi Amal biye da ita suka fito. Su Ammie na falo da su Hajiya Majdiya da suka kwana anan suma. Tambayarsu Ammie take lafiya? Ina zasu haka?. Batare da sun tsaya ba sukace suna zuwa. Cike da farin ciki Oum ta kama Amaal da Shahidah ta rungume a jikinta. Musamman ma Amaal da sai yau ne ita suka gaɗu. Itama dai Mamy murmushin yaƙe ta shiga yi, yayinda Saheeba keta wani faman taɓe baki. Nibras dai ƴar kallo ce, dan ita dama nata baƙin halin akan AA ne kawai. Sashen Ammie su Amaal suka musu jagora, inda shigowar tasu tayi dai-dai da miƙewar Ammie da Hajiya Majdiya dan zataje ɗakin Ammien tai salla. Cak Ammie ta tsaya kamar wadda ta suma. Itako Hajiya Majdiya ta shiga ƴar dariya tana kallon yanda Oum da Ammie ɗin suka tsaya suna kallon juna kamar kaji. Kai daka kalla Ammie kasan a ruɗe take, dan jin take kamar irin mafarkin data saba yi ne akan Oum ɗin. Ɗan jujjuyawa tayi ta kalla kowa a falon, ƙarshe ta sauke idonta akan Amaal da Shahidah da duk suka koma yanayin tsoro. Dan su fargabarsu basu san yanda su Oum suke a zuciyar Ammien tasu ba a yanzu. Saboda tunda aka rabu bata sake yin maganar waninsu ba..........✍️

09032345899

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_💞AJIYA A DUHU....💞_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_My TikTok account 👇_*

https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram👇🏻_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

*_Arewabooks_*

Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30

*_WhatsApp channel_*

https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R

_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_

🅿️➖9️⃣0️⃣

______________

........Sai kuma a mamakinsu sukaga a hankali Oum ta nufi Ammie. Ai tuni itama Ammie ta zaburo kansu suka rungume juna. Hakan ba komai bane, dan duk wanda yasan tarayyar Ammie da Oum yasan alaƙace mai ƙarfin gaske irin ta yaya da ƙanwa ciki ɗaya. Ciki ɗayan ma irin wadda akafi shaƙuwa ɗin nan. Su duka hawaye suke yi, hawayen kewa da begen juna da farin cikin sake haɗuwa a gaɓar da babu zato babu tsammani musamman ga ita Ammie. Ɗayan ƙaramin falon Ammie dake a rufe dan kar mutane su ɓata Amaal tazo ta buɗe. Sai da su Oum suka gaggaisa da mutane anan falon sannan suka shiga. Gaba ɗaya Ammie ita tama rikice, ta rasa ina zata kama ina zata saka su Oum. Yayinda su Oum keta sake mamakin ganin yanda ta canja, duk wanda yasan Ammie a shekarun baya ya ganta a yanzu za'a iya kwana ana gaddama da shi akan ba ita bace ba. Gaba ɗaya ta zama matar manya. Tayi ƙiba ta ƙara haske da cikar kamala. Dan ita kanta Mamy a wannan gaɓar jitai ta raina kanta. Saboda ko suturar dake a jikin Ammien ka kalla kasan lallai nagaba yayi gaba yanzu kam, na baya sai labari. Gefe kuma ga ganin Hajiya Majdiya a tare da Ammie ɗin ya sake tabbatar ma Mamy lallai dama Oum na tare da su Ammie kenan take munafuntar ta (kun san idan mutum nada halin banza kullum gani yake haka kowa yake ma😏)....

Readers Also Read