Kenza eBookz

Al'amarin maryam Complete - Chapter 44

Al'amarin maryam Complete - Chapter 44

Al'amarin maryam Complete Chapter 44: Al'amarin maryam Complete Chapter 44. Tanata fargabar haduwarsu, kamar ya sani ya kyaleta sai data kwana 4 da dawowa…

3,832 words

Tanata fargabar haduwarsu, kamar ya sani ya kyaleta sai data kwana 4 da dawowa lokacin ta saki jikinta sannan ya far mata. Ai kuwa ta dunga ihu suna kokawa, har ta tashi Mimi dake kan gadonta a gefe dole ya haqura karta tara masa yan aikin gidan a wannan daren. Kwana biyu ana abu daya ya gaji ya tambayi ishaq "ishaq wai in mace ta haihu qara matsewa take ne?" ishaq bai bashi amsa ba sai dariya da yunduga kyakyatawa, ya fuskanci matssalar Bature dan shima sunyi haka da Farida. Sai da ya gama dariyar ya bashi amsa "in mai kyan jiki ce tana kuma kamewa tayi tsam, musamman in suka samu kulawar jego. Kawai abunda xakai, kabi a hankali kamar daren farko da haka har ku saba" yabi shawarar ishaq, akuwa aka wuce gurin. A Kullum yakan godewa Allah da kuma fadawa Mimi cewa, shifa gani yake kamar ba daga jikinta mima ta fito ba kuma ko cikinta bai nuna alamar wata halitta ta kwanta ba, a taqaice dai Mimi tana cikin mata masu kyan jiki wannan flat tummy din da yake masifar so tananan ana masa gayu da ita.

Sukaci gaba da rainon mima,duk sanda ka duba dp din Bature mima ce a jiki, anty mami koda yaushe cikin aiken kayan mima take. Suna tsoron karta kuma samun ciki, hankalinsu ya kwanta da suka gane Mimi tana cikin irin matannan masu tsaftar shayarwa. Má'ana wadanda basa period in suna shayarwa dan haka suka sake suna gurxar amarcinsu.

Mima kyakykyawar gaske kamanninta da mumy sai qara fitowa suke, amma yar siririya ce sosai kamar little kamar yadda little tai musu fatan ta haifi irinta. Tana da sumar kai sosai kamar ta Mimi, ta taso cikin farin jinin mutane kowa sonta yake Mimi dai tana tsananin kau da kai akan mima kamar ba diyarta ba kowa ya sheda hakan.

Tana shekara daya Anty mami ta aiko da kudi da kaya akai mata birthday acan kano gidansu na sharada kuma kowa ya hallata an kashe kudi sosai. Mumy tunda aka haifi mima duk wanda xaiyi dinki acikin yayanta saita karbi ragowar kayan ta ajiyewa mima, kafin ta shekara antara mata natives sunfi akwati daya. Zuwansu kano birthday mumy ta bawa mama kayan ita kuma ta auna mima aka tsantsara mata dogayen riguna Kamar yan kanti masu jeluna, ta ajiye a gurinta dan tayi shirin dauke mima ne sabida son diyar take fiye da duk yayanta da jikoikinta (abun cikin kwai yafi kwan dadi)

Wannan karan kudin hayar gidanta yana xuwa gaba daya ta dauka ko shi mijin bai sani ba ta biya musu umra kusan su 6. Ita da Faty, mama da mumy, little da Bature. Kana ta biya wasu kudin aka hada harda yayan Faty da mima dan Mimi yanxu kudi take samu kota ina business dinta ya fadada kuma har yanxu bata daina yiwa mom adduar fatan alkhairi ba dan itace tushen komai.

Ranar da Bature yaji abunda Mimi tayi yayi mata godia da alqawuran soyayya sunfi cikin 80 leaves.

Mumy kuwa ta kasa boye farin cikinta kamar bata taba keta haxo ba, duk inda taje ko akazo mata kaji tana cewa "umra xamu ni da little da fadima. Maryam matar Bature ce ta biya mana dukkanmu" wannan karan ma matan Baffa suka kuma haukacewa, amma babu yadda suka iya dole mama ta dauki jikanta suka wuce.

Anyi umra lfy, Mimi tasha adduar fatan gamawa lfy a gurin duk wadanda ta biyawa umra din.

Basu jima da dawowa ba tayi shirin yaye mima kuma ta fadawa mama. Ana gobe xata yayeta mama taxo Abuja huxaifa ya kawota a motarta. Suka kwana, washegari juma a ta dauki mima xasu tafi, Bature kamar xaiyi kuka yace "Allah sarki mima yanxu na daina ganinki sai takalmanki da kekenki?" mama tace "to mara kunya baka isa dai ka hanani tafiya da ita ba, dan wannan yar tun tana ciki akaimun kyautarta dama jira nake a cire a gora intafi da abata" Mimi tana kallonsu tace "mama kamar yadda nayi alqawari a baya ba, na baki ita duniya da lahira, nasan xaki mata kulawar da koni baxan mata ba" tace "hakane uwata MARYAM" aka kwashe kayan mima tas har kekenta aka xuba a mota, dakyar aka banbareta daga jikin Bature tana kuka yanayi suka shiga mota suka tafi. Daga uban har yar sun bawa mama tausayi, ta dura mata freso ta bata rubutun yaye da akai mata ta jijjigata tai bacci. Mimi da Bature haka suka wuni wani iri, batasan tana son mima ba sai yanxu, gwarancin mima har gixo yake mata. Xuwa yamma zazzabi ya rufeta sosai ga ciwon nono. Yaje gurin ishaq ya karbo mata wani maganin ciwon nono wanda ya siyo musu ita da Farida a singapore dan ba a samunsa a qasar nan, tanasha ta watstsake xuwa dare kuma tayi mamakin ganin nononta bai fadi ba yananan dam dashi kamar bata haihuba maganin nada kyau shiyasa ba ko ina ake samunsa ba.

Acan kano mima ta saki ranta sabida maganin dangana da aka bata, tayi qiba sabida samun kulawa ta musamman, tuni ta shiga harkokinta ga yara a gidan ga kuma dady wanda duk abunda yaci saiya bawa mima. Kuma kulawa yake bata sosai ko shurin mima kayi cikin rashin sani saiya rama mata.

Mumy duk weekend saita turo an dauki mima ankai mata ita ta kwan biyu acan. Kuma Kullum little tana bisa hanya mumy tana cewa taje tagano mata mima kar mama tana wannan haqurin nata matan Baffa su dunga yiwa mima mugun hali yadda dukaiwa Mimi. Duk sanda little taxo tana komawa mumy da saqon qalau taga mima, kuma tana ganin mama baxata bari a taba mima ba balle ai mata mugun abu dan bata de haquri akan mima ko kadan.

Mima yar gatan iyaye da kakanni duk sanda taje gidan mumy saita dakko make up kit din Anty little kamar yadda take kiranta, ta xauna ta dame fuskarta kamar yadda taga little nayi. In little ta farga da barnar mima saita duddumeta intai kuka kuma taxo tana lallashinta.

Mimi da Bature kuwa soyayya aka balle kamar farkon aurensu, suna planning na calendar ko withdrawal method, dan Bature yaqi yadda suyi allura ko saka roba yace duk suna da illah kamar yadda ishaq ya fada masa.

****** ******* ******** **

Tafe take cikin motarta sanyin AC na bugata, tagaji liqis yau sunyi mahawara mai zafi a court amma Alhamdulillah sunyi nasara. BARRISTER MARYAM AL 'AMIN ce, wacce ta fara aiki shekara uku da suka wuce a matsayin lauyan mai xaman kanta wacce ta fito daga chamber din AL 'AMIN MEMORIAL CHAMBER. Itace ta qirqiri chamber din ta xuba lauyoyi irinta kwararru a qoqarinta na tunawa da babanta. Kowa yasanta akan aikinta sunanta yayi fice ne sabida tsayawarta wajen kwatowa yaran da akaiwa fyade haqqinsu da kuma matan da maxa kan saki su barsu da wahalar yaya, wanda ta haqiqance wayan sakin aure shike maida yara marayin tilas daga nan kuma yasa yara kwarara kota ina suna nemanrwa kansu abinci hakan kuma ke kawo yawaitar fyade. Duk wanda yasan maryam yasanta da sanyin hali da nutsuwa, amma in irin wannan case din yaxo gabanta babu mutunci Sam tsayawa take ta fafata tayi ragargaxa harsai anwa wanda aka kama sukunci. Barrister Mimi kenan, lauyan kare yara da mata kuma lauyan mijnta SULAIMAN A AZEEZ, domin a komai nasa na dukiya itace take tsaya masa.

Ta shigo falon a gajiye, ta cire rigarsu ta lauya, sanye take da suit riga da skirt ta dora Baby hijab a wuyanta. Ta rage kayan jikinta ya rage daga ita sai shirt da skirt. Ta nufeshi yana xaune akan carpet yana latsa system as usual. Yana ganinta ya dauke system din kan cinyarsa dan bawa Mimi maxauninta ta hau ta dare shi, yana cewa "hannu da xuwa my luv, ya shariar taku? Nasan kinyi nasara kamar yadda kika saba" ta zare glass din idonsa tana shafa gashin bakinsa da yatsanta kana ta kwanta akan qirjinsa ta kewaye hannunta a qirjinsa shima ya kewaye qugunta yana shafa gashinta tace "ya Bature munyi nasara kam, amma nasha wuya fa lauyan da gayen ya dauka yana da wayo amma qarshe Allah ya dorani kansa" yace "mashallah tashi muje wanka dama kenake jira" ta miqe ya dauketa suna dariya suka shiga bed room.

Sai da mima ta shekara biyar sannan Mimi ta samu ciki, watan haihuwarta na tsaya ya dau hutu itama ta dauka, Germany yakeson kaita ta haihu dan yace baxata qara haihuwa a 9ja ba tunda ta sha wahala a wancan karon. EDD dinta ya nuna saura 9 dayz ta haihu su kuma saura 7 dayz su tafi kamar yadda yake a visarsu. Suka wuce kano dan tanan zasu tashi.

Tunda sukaxo Kullum da daddare yan uwansa da matansu na kusa kan shigo bayan isha a hadu duka a babban falo aita hira sai goman dare suke watsewa.

Yauma sun hadu dukkansu, anata hira kamar yadda aka saba, Mimi na gefe guda ta baje ta tasa robar pop corn dinta agaba tanaci, wanda ya xama shine abincinta yanxu Kullum sai anje kwari an siyomata shi me madara. Cikinta yayi wani irin mugun girma wanda ake ganin kamar yan biyu ne. Tun jiya take jin ciwo amma tana sharewa dan tasan wasa farin girki haihuwar mima da haka ta fara amma sai data kwan ta wuni sannan ta haihu. Yanxu ma wani azabar ciwon kwankwaso takeji ko sauraran hirarsu batayi. Farida ta dubeta tace "besty yaya? Ko jikin ne?" ta kalleta itama da nata cikin dan kusan tare suka samu tace "a a ummu jidda (haka take kiranta yanxu) babu komai inason xuwa toilet ne" Bature ya miqe da sauri yaje ya dagata, dan inta xauna bata iya tashi saiya dagata, in kwanciya tayi bata iya juyawa saiya juyata sabida girman cikin. Xai rakata tace ya barshi yanxu xata fito fitsari xatai.

Ta wuce bedroom ta tsuguna akan gwiwarta tayi gofo dan baxata iya tsugonon fitsari ba. Wani masifaffen fitsari takeji amma ta kasayi sai nishi take.

Acan falo sukaji shirun yayi yawa yasmin ta tashi ta bita. Ta dawo da gudu tace da mutanan falon "wlh haihu xatai" Bature yayi wuf ya shige dakin, Audu kuma ya kira Faty a waya yace tai maza tazo mimi na labour.

Lokacin daya shiga kan Baby ya fito, ya gigice ya rasa yadda xaiyi tace "ya Bature ka zaremun Babyn" yace "to ya akeyi maryam?" tace "kunnansa biyun xaka dafe ka zaro" yayi yadda tace ai kuwa saiga qaton da namiji akan tiles din bandaki. Sunanan ahaka mahaifa bata fado ba, ita kuma sai ajiyar xuciya take yana mata hannu duk sun dame cikin jinin haihuwa, Faty ta iso, ta shiga ciki tasa safa ta taimaka mahaifa ta gado, baby ya cika gida da ihu. Faty tace "ya Bature dan fita ka bamu guri in gyarasu" ya watso mata harara yace "da Allah uwar iyayi kiyi mata abunda xakiyi mata kawai, ni dana karbi haihuwar?" tanajin haka tace "to riqeta in kwarfe mata jini" ya riqeta ta kwarfe jinin, Mimi ta kalleta tace "ya Faty sai anmun dinki ko?" tace "a a Mimi baki qaru ba, Allah ya baki da sauki."

Mama da mumy sukaxo a tare Audu ya kirasu ya fada musu, mama ta karbi gyara Mimi, mumy kuma ta yiwa Baby wanka. Cikin qanqanin lokaci sukai fes gida ya dau turaren wuta, aka fito da Baby su yasmin anata dauka da sauran mutane farida kuma cewa take yadda besty batasha wuya ba nima baxan sha ba ko ya ishaq? Sai yace mata eh maman jidda. Sai sha biyun dare suka watse, ya shigo bedroom din dauke da Mima a hannunsa tana tamai surutu. Su mama duk suna ciki, ya nemi gefen gadon ya xauna inda Mimi keshan tea.

Mima ta dane cinyarsa tace "ABBA wai kaine Dady na, Maman Abuja kuma mamana?" ya sumbaceta yace "eh mana ai shiyasa nake ce miki my lovely mumy, amma waya fada miki?" tace "yaya Dady ne" Bature yace "kinga wannan Babyn kuma qaninki ne" tace "to Dady na" ya dakko Baby yana kallonsa, kamarsu daya dashi sak, duk da yaron jaririne kamarsu da Bature bata buya ba. Ya miqe ya kwanta akan gadon yasa Mima da Babyn a tsakaninsu da Mimi sukai baccinsu, mama da mumy suka fita suka bar musu dakin.

A taqaice dai Germany din daba ajeba kenan, tunda abunda xai kaisu Allah ya kawoshi cikin sauqi. Ranar suna yaro yaci sunan "AL AMIN" Mimi tayi murna da sunan da babanta da yasa tana kiransa ABBA.

******* ****** *********

Rayuwa ta tafi, Mimi ta xama attajira sosai, ko aikinta ya isa ya riqeta balle business dinta wanda ya zama gagarumi ita kanta batasan adadin dukiyarta ba. Duk sanda ta fidda xakkah asibiti take xuwa ta gaida marasa lfy a fito mata da wadanda suke da lalura babu kudin magani kona aiki ta biya musu kuma dama ta dade da wannan buri tun tana qaramarta, sai kaga mutum ya rasa ransa ko ya nakasa akan kudin da basu taka kara sun karya ba, shiyasa take xuwa can takai zakkah.

Gidan Baffa kuwa tuni Al amura sun dai daita, abunda kuwa yasa hakan shine; anty tayi wani zazzabi mai zafin gaske wanda yasata sanqarau daga baya kuma tayi jijjiga tasha wuya sosai kamar baxata tashi ba, Allah yayi da ragowar shan ruwanta a gaba. Ana ganin abun ya warke amma ina dan saidata shekara biyu cis tana jinya komai sai anmata. Ansha wahala tun yayanta nayi har abun yayi tsaho suka dakko mace matashiya tana kula da ita dan babu manya duk sunyi aure sai qanana guda biyu. Mimi itace kan gaba wajen nemawa Anty magani da yawon asibitoci manya na kudi duk da yayanta sunayi amma ita tafisu hidimar kudi. A qarshe dai ta warke ragal, abun dadi kuma sai Anty ta shiryu ta wannan hanya, ta nemi gafarar mama da Mimi da duk wanda taiwa mugun abu. Ta kwantar da kai sosai dan yanxu ko magana bata dameta ba saita wuni batace komai ba, sai dai ka ganta da casbaha. Umma ganin abokiyar burminta abunda Allah ya aiko mata, itama tayi saurin watsar da makamanta ta nemi yafiyar kowa aka xauna lfy. Girman da Baffa yaso taja a matsayinta na uwargida taqi ada yanxu ta dakkoshi ta dorawa kanta. Ta riqe gida sosai tsakaninta da kowa girmamawace. Mama itace qaramarsu kuma duk tafisu sauqin kai ta basu hadin kai gida yayi dadi Yayi kyau xaman lfy ya samu xama daram.

Mimi itace attajira a gidan, kowa yasan haka babu wanda ya kai ko rabin dukiyarta, in biki ya tashi takansa aje shagonta na sai da furnitures a debowa amarya kaya iya girman gidanta. Ta daukewa Baffa wannan nauyin, in kkuma namiji ne xata hado lefe na kece raini ta kawo. Tuni ta qara gyara gidan ta saka AC taiwa su mama kayan daki iri daya sak. Ta dakko masu girki wanda itace ke biyansu in sun gama wacce take da girki aikinta kawai rabo.

Baffa kuma aikin hajji ta biya masa yaje, ranar har kuka yayi yace "abunda na gaxa yi miki yau kinmun Maryam Allah ya jiqan mahaifinku Aminu" mama ta kama qasa sosai itama har private skul Mimi da Faty suka bude mata anan Hotoro bayan layinsu bayan tayi retire a aiki.

Baffa ya kance "fadima haihuwar yaya mata tai miki amfani, yayan da ake miki gori akan baki haifi namiji ba gashi sun cika miki daki da jikoki maxa (Faty yayanta 4 duk maxa) wannan shi ake kira da "Goran duma me yado" kai madallah da haihuwar ya mace" duk sanda ya fadi haka sai jikin su Umma yayi sanyi dan sunsan da su yake. Mamace tace Dan Allah ya dena tuna musu tunda sunyi nadama.

Wannan karon shekarar Abba 3 Mimi tai wani cikin dan Bature cewa yayi gara suyi su gama karsu jera dasu mima. A cewarsa aure xai mata tana qare secondry skul zai aurawa Dady, jidda kuma yar ishaq xai aurawa Adil dan Audu. Ya hadasu ya kaisu jamiar Madina suyi xamansu can suna karatu da aurensu.

Cikinta yana 7 months sukaje yawon bude ido qasashe daban daban ita dashi da mima da Abba. Dubaice ta qarshe daganan xasuyo gida.

A Dubai sun fito xasu wata shago sanye take cikin doguwar riga baqa me duwatsu farare hannu da gaban rigar ta nade kanta da mayafin rigar tayi kyau sosai ta qara haske sabida jin dadi tana riqe da hannun abba shi kuma Bature yana dauke da mima yar 9 years wacce tai bacci a kafadarsa suna tafiya suka hadu da Badaru.

Suka tsaya aka gaisa, yayi qiba sosai ya dunqule, Mimi tai mamakin ganinsa nan dan tasan a singa yake kasuwanci to meya kawoshi Dubai sarin Kaya kamar yadda yace. Shima a nasa bangaren dubanta yake, har abada bazai daina danasanin sakin maryam ba. Tace "ka koma saida kayan mata kenan?" yace "eh tun da dadewa amma wancan kasuwancin ma ban barshiba ina tabawa" ya shafa kan ABBA yace "mashallah wato Maryam tsautsayi da kuma rabon wadannan kyawawan yaran da xaki haifa ya rabamu" tayi murmushi ta kauda xancen da tambayar yayansa nawa. Yace "guda bankwai ne" tace "bakwai?" cikin mamaki. Yace "eh ai bayan Nafee na auri wata yar abokin abba, to ita tana da biyu Nafee tana da 5" tace "Allah ya rayasu" yace "amin" mama ta tashi daga bacci ta juyo tana kallonsa yace "yan mata ya sunanki?" kamar ankunna radio ta fara xuba "ni sunana HALIMA SULAIMAN AZEEZ. Mumy ma sunanta Halima sulaiman, mutane na kirana MIMA. Amma Anty little da friends dina a skul suna cemun preety , ABBA kuma yana cemun ya mima, Dadyna kuma yana cemun my lovely mumy" Mimi tai mata tsawa tace "stop it Mimi, u talk too much" Abba kafin a tambayeshi sunansa yace "ni kuma sunana AL AMIN SULAIMAN, ana cemun Abba mamana tana cemun abbana ya mima na cemun broda. Mama tace nima innasami qani zai dunga cemun ya Abba" ya fada yana taba cikin Mimi. Kunya ta kamata ta ture hannunshi. Badaru yace "mashaallah Allah ya rayaku ya baku ilimi mai amfani yasa kuyi koyi da kyakykyawan halin mahaifiyarku" Bature yaja hannun Mimi sukai gaba yace da Badaru "amin amma kyakykyawan hali sukam sun tsotsa a nono, so ko bakai musu addu a ba suna dashi." Badaru ya bisu da kallon shaawa yaran ko yace family din sun burgeshi.

Mimi sunayin gaba ta kalli Bature tace "meye hakan da kayi kenan?" yace "Mimi luv ban taba ganin mutumin da yayimun abu na kasa mantawa dashi ba irin Badaru, ina jin tsanarsa innna tuna shiya fara saninku diya mace sannan kuma ya azabtar dake shiyasa na kasa yafe masa" ta fuskanci kishi ke damunsa, ta sanyaya murya tace "amma ai kai kuma kaina fara so a rayuwata" ya juyo yana kallonta ya hadata da yayansa ya rungume yana jin qaunarsu.

***** ************* ******

Xaune suke kaf dinsu cikin qaton falon gidan mumy, birthday din Dady ake yau na cikar shekarunsa 75 a duniya wanda Mimi da yasmin suka shirya kuma suka dau nauyi.

Cikin yayan mumy babu wanda babu har Anty mami dake nesa taxo. Mimi tana kusa da mama da mumy a xaune tana fama da qaton cikinta suna aikin hada kayan rabo a qatuwar jakar takadda me dauke da photon Dady wacce xa a raba in anjima da yamma. Abba kwance akan cinyarta, Mima ta tsallako taxo itama ta kwanta akan cinyarta. Abba ya hau ture kanta wai saita tasan mai a cinyar mamansa. Mimi ta daga mima a jikinta da cewa "ke tasar mai a cinyar babarsa, haka kawai ki hanamun babana sakewa" Anty mami tace "mima taho kinji mamana, kema in banda nuna qoqon usuli meye na xuwa jikinta ki kwanta keda kike da iyaye da yawa, dan tsabar gata ma ke kakanninki iyayenki ne" mama ta dubi Mimi tace "Mimi anya baxaki dena runquma dannan a cinya ba kina fama da qaton ciki" tana shafa kan abba tace "haba mama! Babana ne fa, kuma duk kunfison mima shi bamai yimun kara akansa shiyasa nake lelen abina" tace "ai shikenan"

Audu ya shigo ya kallesu Cikin shaqiyanci yace "mumy, gaskiya ke kyakykyawa ce, abu daya yayi miki cikas, kedin gajeriya ce. Da ace duguwa ce wlh sai dai shugaban qasa ya aureki" tayo masa daquwa tace "Dan ubanka haka ubanka ya ganni da gajartar ya aureni kuma na haifi dogo kamarka" aka kwashe da dariya, ya kalli yasmin yace "honey babu magana?" ta harareshi kawai dan haushinsa takeji dan yayi mata wayo taje ta cire robar planing yayi mata ciki wanda ita bata shirya masa ba. Rabonta da haihuwa tun Adil. Ya kada kai ya fita, mumy ta riqe haba tace "oh ni halimatu, tun kana haifar danka saika haifi jikanka. Audu ya maidani kamar kakarsa" aka kuma kwashewa da dariya, Faty tace "wlh mumy ya Audu da Lubna halinsu daya, sun iya shaqiyanci."

Bature ya shigo shima ya kallesu duka ya xauna kusa da mumy ya dafata yace "my lovely mumy, ina alfahari dake" tayi murmushi tana shafa kansa. Ya dubi Mimi yace "Mimi luv" ta bashi amsa "yaya luv" akaci gaba da hira can ya kuma kallonta yace "Barrister MARYAM" ta kuma bashi amsa "ENG SULAIMAN" ya tashi xai fita har yakai qofa ya juyo yace da Mimi "Haj mairo" a karo na uku ta kuma bashi amsa da cewa "Mal manu" ya xaro ido yace "lallai ma yarinyar nan ni kike cewa Mal manu😳" tayi far da ido tace "nima yaya meyasa kacemun mairo 🙄?" aka kwashe da dariya ana kallonsu cikin burgewa, mumy tayo musu daquwa tace "🖐🏻 kunga yara muna zaune xai fadar sunan iyayenmu suke" Anty mami tace "yi haquri mumy Romeo da juliet ne suke soyewa a gabanku" aka kuma dariya gaba daya.

Anty mami ta bisu da kallo, suna burgeta. Bata yadda true luv yana existing saita dubi BATURE da MIMI.

Kamar yadda mumy tai hasashe adalilin kusancin yasmin da Mimi, yasmin ta koyi wasu halayen Mimi. Kuma Mimi tasan yadda tayi ta shirya Anty mami da yasmin suka dawo kamar da aka koma xaman lfy. Lamarin yayiwa Audu da mumy dadi tunda kowa nasu ne cikin yasmin da Anty mami.

Ina miqa godia ta musamman ga

Maman Khairat Maman shukra Anty sis Sadnaf Maryam Baita usman Hudallah (mrs JH) Huraira Yabo

(wanda da taimakonsu ne da kuma qarfafa gwiwa na ida rubuta wannan novel)

Ban manta da kuma ba Maryam (besty na) Wasila (saqonki ya isoni) Maryam sani mani Diyar khatibi Da duk wata maryam(my maryams)

Godiya ta musamman ga daukacin yan grp din

Hudallah and Rahmatullah novels Fahimta novels Hausa novels S A AZEEZ Novels (maman khairee)& FANTASTIC START WRITERS (F S W)👍🏼

Ina godia ga daukacin masoya fans din AL 'AMARIN MARYAM, wanda na samu damar ambata da wadanda lokaci bai barni na fada ba. Masu bugomun waya da masu yimun text harda masu biyoni in box. Dafatan ni da ku gaba daya xamuyi koyi da kyakykyawan halin "MIMI LUV"😊

Tammat bihamdulillah.

Sai munhadu a sabon novel dina in Allah ya kaimu 2018.

Ms Hajia 😊

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull