Alkalamin kaddarata by sajeeda - Chapter 49
Alkalamin kaddarata by sajeeda Chapter 49: Alkalamin kaddarata by sajeeda Chapter 49. Ba su su dawo ba sai da karfe goma ta bada baya, domin dogon zama ne…
3,330 words
Ba su su dawo ba sai da karfe goma ta bada baya, domin dogon zama ne suka yi sakaninsu , zaman da aka yanke daurin auren NAHIDT da Malan, wanda ya nuna bukatar hakan da kansa, Mahaifinta kuwa ya nuna ya ba Dad wuka da nama, Dad ya nemi shawarar MUHAY shi kuma ya ce ya bashi, daga nan ne kowa ya nufi wajen da aka bashi masauki suka je dan hutawa
Tunda ya shigo ya ga kayan abincin da aka jera masa da irin gyaran da bangaren nasa ya dauka ya cika da mamaki sosai
Da sauri ya nufi dakinsa na barci har kamar zai ci tuntube ya shiga kunna computersa da kayan da ya boye na bincikensa Yana ganninsu sai da ya sauke wata wawuyar ajiyar zuciya sannan ya sake rufe wajen da kyau ya dan sake bin shinfidar gadonsa da kallo hakama yannayin dakin barcin nasa
Iska ya dan furzar da tunanin ko Mama ce ta yi aikin nan da kanta ne?, Dan haka sai ya tube ya shige bayi ya yarda karamin wandon nasa nan saman gado
Wanka ya yi sosai ya dauro alwallah ya fito yana shafa mararsa hadi da nufar wajen da maganinsa yake ya bude jakarsa ya ciro kwaya biyu
Da tawul din nan a daure a tsatsonsa ya fito falo dan zuwa ya hadiyi maganin nan ko mararsa dake ta dauran niyar kulewa ta warware abinta, sai dai abinda ya gani ne ya saka shi ja da mugun sauri yana kallonta, domin ta shigo kennan ne falon itama ta juya tana leke dan ta ga sun tafiyarsu ne? Ko ta iya fita ta yi tafiyarta
A hankali ta juyo jin kamar an fito ta sauke Idannuwanta a saman kansa
Ido ta kwalalo da dan karfi ta ce" A'UZUBILAHI Mina SHAIDANNIN RAJIM !"
Da mamaki yake kallonta kafin a kule ya ce" Ke ce shedaniyar ai ba ni ba , Meye kuma?"
Idannuwanta dake rufe ruf ta dan bude , sai kuma ta mayar da karfi ta sake rufe su , jikinta na dan rawa kadan ta ce" Meye me?, Wai ina rigarka ne zaka fito tsirara dan girman Allah ?"
Ido ya kwalalo da mahaukacin mamaki ya sake bin kansa da kallo, da yar dabara ya saka hannunsa ya gyara tawul din da kyau sannan ya saka abinda ya fara kumbura a matse matsin kafarsa ya dan matse kadan ta yadda ba zai ji ciwo ba yana kallonta ya ce" Ke me kika zo yi dakina?"
Kadan ta dan bude idannuwanta tana kallonsa kadan ta maida ta rufe ta girgiza kanta tana fadin" Cewa suka yi wai na zo nan a nan zan kwana, inaga ko na tare a nan dinma suke nufi? Wai dan Allah yalabai baka jin kunya jiki a waje kana tsaye gaban yar cikinka?".............
😳😳😳😳 Wollah ba luwana😳😳😳😳😳💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥 *ALK'ALAMIN K'ADDARA TA* 💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥
*The Hero writer*
*SAJIDA*
_Bismillahir rahamanir rahim_
PAGE:. 5️⃣7️⃣
*P͓̽R͓̽E͓̽S͓̽E͓̽N͓̽T͓̽*
*S̉T̉ỎR̉Ỷ ẢN̉D̉ W̉R̉ỈT̉ỈN̉G̉ B̉Ỷ*
*S͞͞A͞͞J͞͞I͞͞D͞͞A͞͞*
*T͞͞H͞͞E͞͞ H͞͞E͞͞R͞͞O͞͞ W͞͞R͞͞I͞͞T͞͞E͞͞R͞͞'S͞͞ 👇🏻*
1 *yar mahaukaciya* 2 *Banida zabi* 3 *Duk karyar kada* 4 *Baka ce* 5 *Daga tafiya daukar soja* 6 *Kutkale* 7 *Makauniya ce* 8 *Mage mai kwanciyar daukar rai* 9 *Duk nisan jifa* 10 *Dutse* 11 *Idan Ka Raina Inda Kake*. 12 *Neman Na Kaina* 13 *WATA KOKOWAR*
*The Latest Qualitative New Book ALKALAMIN KADARRATA*
*WANNAN BOOK NA KUDI NE BA FREE BANE, IDAN KINA DA RA'AYIN KARANTASHI KI GARZAYO KI BIYA KUDINKI YAR UWA ZAKI SAMU BONUS NA DUKAN LITATAFAINA CIKI HARDA NA KUDIN DA NA GAMA KWANAN NAN, KI GANE................ALKALAMI NA DORA, NA ZUBA RUBUTU......IN SHA ALLAH ZAKI NISHADANTU SANNAN KI KARU💓💓💓*
Zaku biya kuɗin ku ta wannan account numbern 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GTBank Naira 300 ne kacal zaku biya anyi araha an hana bashi.
Ko ku turo Recharge card ta wannan numbern wayar 08038856944 banda vtu hoton katin zaki ɗauka ki turo.
Sannan Sai ku tura shaidar biya ta wannan no din +22793811618
Ga ƴan Niger zaku biya kuɗin ku ta wannan layin +22793811618 katin sahelcom ko AIRTEL ta dala DARI ne ( 500 francs cefa) sai ku tura shaidar ta layin nawa sannan na saka ku a grup din
Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰
Wani mamakin ne ya kusan kume shi, har ya bude bakinsa ya kankance idannuwansa zai biyata su raba hali , sai kawai ya juya yana damke da tawul dinsa ya yi cikin dakinsa
Direct wajen kayansa ya nufa ya bude ya ciro yana waigawa kar aje ta shigo ta same shi a asalin zigidir din, domin idan da ta rufe ido yanzun bai san wani kalar tashen haukan zata nuna ba!
Dan tsaki ya ja yana jan wandon ya saka , ya saka rigar da ya janyo du yana dan dagawa yana leken kofar da ya rufe, aman ya gama sani ne yar nan bata cikin tsarin masu hankali, tana iya shigowa nan din dan wata fitinar da bai san farkonta ba bale karshenta
Neme nemen maganinsa ya shiha yi domin ya wurgar da shi wani wajen Da kyar ya same shi saman tawul din da ya cire ya dauke shi ya fita dan cin abinci da kuma shan maganin yana tunanin yadda zai yi da Mama dake son karfi da yaji sai taa hadasa masa ciwon kai da yarinyar nan
Wani idon ya sake zuba mata gannin ta zuba soyayan dankalin turawa ta kuma dora soyayan namaan kaji a sama ta koma gefe guda ta yi zaman makaranta ta fara ci
Itama kallonsa ta yi sai ta yi dan murmushi tana fadin" gani na yi da kaza a kusa me ake da gurzajiyar kubewa? Aman Mama ta dage a yi ta yiwu ta birgeku, zo dai ka dandana ka ji ta yiwu ta birgeka , ni kam Alhmdulilah walahi ga nama bana son bak'ar miya!"
Cire kansa ya yi a kanta ya karasa da dan hanzari ya dauki kopin kwalbar nan dake ajiye ya aha magungunnansa biyu ya dago ya kora da ruwa gaba dayansu kafin ya sake saike idannuwansa a kan fuskarta da ta yiwa takwaf takwa takwaf kamar a bakinta ne ya zuba maganin ba a bakinsa ba
Wani takaicin ya sake shaka na rainin wayon yarinyar nan, da wani uban haushin ya nunita da yatsarsa yana fadin" Look!, Ki tashi ki bara min falo ni bana son saka ido, dan kin raina ni sai ki ringa shigar min waje kai tsaye, kuma kika shigo waje kika gaida kowa harda namijin da saura kiris a daura maki shi kika cafe ni ga dan iska ko kallo ban ishe ki ba ?"
Ido ta kifta tana dan turo bakinta hadi da kawar da kanta gefe kadan da dan guna guni ta ce" To ai na ga ni matarka ce ko?, Kuma gaisuwar ba ta fi million ba ina maka ta waya aman ko ka nuna ka gani, hala ji kake dan soyaya ne nake gaishekan ne? Nafa san lokaci kake jira ka bani lasisin zawarci gaisuwa ce kawai irin ta musulunci"
"Ke ke me kike cewa?" Ya fada a dan tsawace domin kwarai ta rage muryarta ga cokali tana takala da hannunta kwal kwal kwal kwal kwal ya sa ba sosai ya jita ba
Dagowa ta yi tana mikewa tsaye da sauri tana kallonsa ta sake tunzuro bakinta gaba
Rigar dake jikinta ta yanza ce ya sake bi da kallo, bak'ar doguwar riga ce mai siririn hannu sannan mai rigar mama yar firit mai tsinin nan a jikinta, ta bi ta lafe a dukan wajen da ya dace ta lafe ta bada kalla abin ba'a cewa komai, da sauri ya cire idannuwansa rai bace ya sake bude bakinsa zai yi wata maganar suka jiyo ihun kuka
A tare suka kurawa junna ido , sai kuma ihun ya sake gabatar da kansa da karfin gaske na kuka wiwi ja muryar mace baba
A guje ta juya tana fadin" Na shiga uku iyayena"
Da sauri ya daga kafarsa yana fadin" Ke ke, dawo min kar ki saki ki fita wajen nan"
Ina kamar wanda ya karrawa tafiyarta iska domin maimakun ta dawo masan da ya bukata sai kawai ta bude da wani irin gudu mai hade da sauri ta nufi wajen da ta fi jin kukan da kururuwar babar macen dake yi
"Walahi walahi walahi ba adalci a gidan nan, a kan meye zaka ringa nuna min rashin adalci kiri kiri a cikin gidana?, Elhaj ka fada min idan ka gama zaman auren ne da ni ka fada min sai na dangana ai ba da kai na zo duniya ba bale nace idan na rabu da kai zan mutu, aman abinda ake mana a gidan nan ni ya kaini karshe ba zan kuma iya hakurinsa ba!" Ta karashe tana riko rigarsa da dan kwalinta a hannunta tana rizgar kuka tamkar wada aka sokawa wuka ko akaiwa wani mugun abun
Da mamaki yake kallonsu, sannan ya juya wajen sojojin dake wajen daidaiku da aikinsu ne suke yi
Da hargagin tashin hankali ya ce" Kai ku bace min a wajen nan!"
Du kamar jira suke gaba dayansu kowa ya kama gabansa da mugun sauri , kafin ya maida dubansa kan mutanen da suka fito na gidan ne ciki garda Mamansa, aman babu mahaifan su Shuwwa sannan babu su malan, ba dan basu ji bane, sun dai saurara dan su ji abinda yake faruwa koda zasu fito ba yanzun ba kam
A haukace ya juya wajen Shuwwa ya taka da wani irin sauri ya damki hannunta ya nufi hanyar dakinsa da ta fito ya bude ya tunkudata ciki ya nunata da yatsa rai bace ya ce" Ke kuma da kike jira kiris ta yi ki bale da abinda ke jikinki babu ruwanki da wa zaki iya haduwa dan rashin kamun kai da mugun sabo shine zaki fito a haka gaban kartin banza kina yawo sai ki je ki hada kayanki yau na maida ke wani gidan!"
Da bacin ran ya sake juyowa ya dawo wajen sauran du da sukai kasakai suke kallonsa yana fada ba ji ba gani ya bi sauran yan matan da suka fito da kallon mamaki ya ce" ku kuma jira kuke sai na kama sunnayenku ko zaku bace min da gani ne?"
Su dinma har rige rige suke du suka afka dakin uwar gidan nasa gaba dayansu har sunna jan kofa sannan ya fuskance su su hudu da suka rage
Idannuwansa sun fara daukan launin ja ya ce" Inaga ki karasa daga ciki zai fi Aba"
Dad da gaba daya yake jin kansa a wulakance sakamakon wannan wulakancin da iyalinsa ta yi masa dan kawai ya leko dan ya yi mata salamar sai da safe, domin yau ba aikinta bane aikin mai dakin tsakiya ne dan dare ya yi ya kuma ga yaya ta wuni sannan ya koma bangarensa dan ya saba haka yake yi kowani dare koda ba aikinki bane zai leko ki ya maki adu'ar sai da safe , shine yau yana shiga ta tada masa wasu irin magangannun da suka bashi mamaki da ciwon kai, gudun kar su ja maganar ya nuna mata su bar maganar, sai dai ta ki hakan har ta biyo shi tsakar falo tana fadin ita yanzu take so a yi maganar ba kuma zata iya barin maganar nan ba dan ta gaji, shine ya yi tafiyarsa, shine dan wulakanci da wulakantar da kai da son ta kawo wani lamari na raini ta biyo shi tana rike masa riga hadi da fasa kukan nan tamkar wanda ya kasheta ko ya mata wani mugun abu? Cike da takaici ya sake kallonta a kausashe ya ce" Sakar min riga"
Tana kallonsa ta girgiza kanta hadi da fadin" Ba zan saki ba Elhaj, ni yau sai an zauna an yi mai yiwuwa a gidan nan walahi!"
Rai bace ya daga hannunsa ya nufi fuskarya da shi yana fadin" In ban tsinka maki mari ba ki ce ni ba dan halal bane!"
Da sauri MUHAY ya tare hannun nasa yana kallonsa, a hankaki ya girgiza masa kai kafin ya kalleta, a tausashe sosai ya ce" Uma dan Allah mu je bangaren na Aba, mu je sai a yi maganar dan komai yana son sirri ai"
Sakin rigar ta yi ta fara yin gaba da sauri tana fadin" Walahi walahi mu je din, gaba dayanku ku wuce mu je domin abin ya shafi kowa a gidan nan!"
Ido ido suka tsaya yi kafin MUHYIDEEN ya nuna masu hanya gaba dayansu a sanyaye ya sake furta" Bismillah mu tafi"
Su dukansu ba baka sai hanci, dan su dai matan basu san abinda yake faruwa ba, shi din kansa MUHYIDEEN din bai sani ba, shi kuma CHIEF OF ARMY gaba daya sai yake jin kunyar a yi maganar nan haka kai tsaye domin bai san me hakan zai haifar ba na tarin kunyar da yake ji na abinda iyalin nasa take kokarin yi ya fara daga kafarsa ya nufi cikin kafin du su mara masa baya
Yana shiga ya dubeta yana girgiza kansa ya ce" zan so ki yi aiki irin na hankali, zan so ko me zaki furta a yanzu ki fara duban tarin girma da darajar mutun sannan ki tuna da abin kunya, zan so ki kasance mutun mai adalci a rayuwa , zan so ki kamanta adalci , ko me zaki ce ki sani yana iya dawowa kanki , ki kiyaye da furucinki a yanzun sannan a gaba, ki iya tankwasa zuciyarki ko zaki aikata aikin alkhairi kin ji?"
A zaunen da take ta fuskanceshi tana fadin" Ai dole ka ce haka Elhaj, dole ka ce haka, aman a yau gaskiya ni na gaji sai ka fada min Matarka ta fi mu ne a wajenka ko ita aurenta ya fi namu karfi ne a wuyanka da za'a zo gidanmu ba'a haifa ba ba'a taba yin bari ba aman an gaje mana gida har an fimu isa da takama a cikon gida an zuba mana mutane kamar mabarata an bi a gagaje komai?"
Fuskantar inda zancen ya nufa ya saka Maman Muhay kaiwa saman kujerar tana fadin" Toh Fah "
Shima MUHAY din sai ya so juyawa ya bar dakin fuskantar da ya yi kamar abin shi ya shafa, sai dai bai kai ga fita ba matar ta Dad ta dora da fadin" Ka duba ka gani yau a cikin gidan nan Madafa ta zame mana abin hange muna ji muna gani ta fi karfinmu, wai ita da uwar matar d'anta sun gaje madafa gaba dayansu sunna ta dafe dafe , an fitar da kayan abinci an yi mana almubaranci a cikin gida an watsar da komai har ana zubawa ana mikawa makota wai su a saudiya haka ake ana sadaka sosai wa makota, mu za'a nunawa sadaka ne ko so ake a nuna mana ba'a san zafin abin ba?, To gaskiya ba zan yarda ba ni kam na gaji walahi na gaji, nan Jet din dake malakinka ne yaron nan ke bulaguro a cikinsa da iyalinsa mu kuma sai dai mu bi mota mu sha wahalar zama, Elhaj kawai ka daidaita darajar kowata mace a gidan nan gaskiya"
Yadda zuciyarsa ke zafi gaba daya sai ya ringa jin har wata zufa na neman keto masa a tsayen da yake yana kallonta
A hankali matarsa ta tsakiya ta budi bakinta ta ce"💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥 *ALK'ALAMIN K'ADDARA TA* 💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥💔❤🔥
*The Hero writer*
*SAJIDA*
_Bismillahir rahamanir rahim_
PAGE:. 5️⃣8️⃣
*P͓̽R͓̽E͓̽S͓̽E͓̽N͓̽T͓̽*
*S̉T̉ỎR̉Ỷ ẢN̉D̉ W̉R̉ỈT̉ỈN̉G̉ B̉Ỷ*
*S͞͞A͞͞J͞͞I͞͞D͞͞A͞͞*
*T͞͞H͞͞E͞͞ H͞͞E͞͞R͞͞O͞͞ W͞͞R͞͞I͞͞T͞͞E͞͞R͞͞'S͞͞ 👇🏻*
1 *yar mahaukaciya* 2 *Banida zabi* 3 *Duk karyar kada* 4 *Baka ce* 5 *Daga tafiya daukar soja* 6 *Kutkale* 7 *Makauniya ce* 8 *Mage mai kwanciyar daukar rai* 9 *Duk nisan jifa* 10 *Dutse* 11 *Idan Ka Raina Inda Kake*. 12 *Neman Na Kaina* 13 *WATA KOKOWAR*
*The Latest Qualitative New Book ALKALAMIN KADARRATA*
*WANNAN BOOK NA KUDI NE BA FREE BANE, IDAN KINA DA RA'AYIN KARANTASHI KI GARZAYO KI BIYA KUDINKI YAR UWA ZAKI SAMU BONUS NA DUKAN LITATAFAINA CIKI HARDA NA KUDIN DA NA GAMA KWANAN NAN, KI GANE................ALKALAMI NA DORA, NA ZUBA RUBUTU......IN SHA ALLAH ZAKI NISHADANTU SANNAN KI KARU💓💓💓*
Zaku biya kuɗin ku ta wannan account numbern 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GTBank Naira 300 ne kacal zaku biya anyi araha an hana bashi.
Ko ku turo Recharge card ta wannan numbern wayar 08038856944 banda vtu hoton katin zaki ɗauka ki turo.
Sannan Sai ku tura shaidar biya ta wannan no din +22793811618
Ga ƴan Niger zaku biya kuɗin ku ta wannan layin +22793811618 katin sahelcom ko AIRTEL ta dala DARI ne ( 500 francs cefa) sai ku tura shaidar ta layin nawa sannan na saka ku a grup din
Sai kun zo🥰🥰🥰🥰🥰
A hankali matarsa ta tsakiya ta budi bakinta ta ce" Haba hajia, me yasa kika cika zafafa abu ne wai a rayuwa?, Yanzun wannan ai bai dace ace kece kika yi wannan abin ba kamar wata yarinya karama?, Me ya tauye mu a gidan nan? Ko mu mun ce zamu kawo bakin ne ya mana iyaka da dukan wajen da muka so ajiye su?, Ko ya taba hanna mana abinda zamu dafawa bakinmu ne? Haba hajia kece baba a gidan nan aman kuma kece mai yon wasu abubuwan da basu da dadi, kar ki manta ke ya dace ki koya mana kyawawan dabi'u fa"
Sai da ta bari ta kai karshe ta debeta da ido ta watsawa kasa ta ja uban tsaki tana fadin" Kin san ai ni ba munafuka bace da zan tsaya yin kumbiya kumbiya a kan abinda yake cikin zuciya na ringa munafuntar kaina da kaina sannan na munafurci mutanen dake tare da ni, sai ki rantse da wanda ya busa maki numfashi cewar abin nan baya ci maki tuwo a kwarya, bafa wani abin boye boye bane, abu ne na gaskiya wanda yake abin a duba, ba maganar bakin ciki sai magamar gaskiya, dan haka na kawo kukana idan zaman adalci ake yi a gidan nan a duba min"
CHIEF OF ARMY haka jikinsa ke rawa yana tsaye yana kallonta
Maman Muhay ta girgiza kanta dake kasa a sanyaye ta ce" Allah ya baki hakuri, sai da ya so ya kaisu wani wajen mune muka hanna, bamu san hakan zai hadasa wata matsala ba, aman in sha Allah idan har yayan ya amince sai su koma wani wajen, hakan ba zata kuma faruwa ba"
MUHYIDEEN ya yi dan murmushi mi ciwo yana sada kansa da hayaniyar da ake yi a hankali ya furta" Allah ya sanyaya " Sannan ya mike ya fice a falon, domin wannan dai ba huruminsa bane, koma menene zasu daidaita kansu ne tsakaninsu
Yana fita CHIEF OF ARMY ya juya ya nufi dakin barcinsa yana fadin" Idan kun fita ku rufe min kofar "
Da wani bakin cikin ta raka shi da kallo hakama sauran Sosai damuwar yannayinsa ya kama Mama, aman kuma na zata taba yin gigin zuwa a yanzu ba domin wata fitinar take ita hadasawa kanta, dan haka ta mike ta nufi bangarenta tana tunanin sanadiyarta ne ake son saka masa hawan jini ko me? In sha Allah ba zata basu damar su wulakantashi ba, in dai a kan bakin yaronta ne zata je da kanta ta gyara masu wani wajen ta kawata masu yadda zasu ji dadin zaman
MUHYIDEEN na dawowa wucewa ya yi ciki ya rufo kofarsa ya zauna bakin bed hadi da dafe gaban goshinsa
Sai kuma ya tashi yana watsar da tunanin ya dauro alwallah ya dawo ya shiga gabatar da shafa'i da wuturi dan gaba dayama ya manta da Shuwwa da barci ya kwasheta a saman doguwar kujera lulube da bargonsa, yana gamawa ya yi kwonciyarsa ya shiga neman barci
_____________________________________
Da sasafe tun kusan karfe shida Dad ya bar gidan, cikin shirinsu na kaki yau ba tare da ya nemi kowa ba sai sojojinsa masu bashi tsaro
Cen kusan karfe tara kira ya samu MUHYIDEEN daga baban ofishinsu daga shugaban kasa cewar yanzu yanzu ana nemansa, hakan ya sa da gagawa ya diro ya shiga shiryawa a gagauce ya saka kaki dinsa ya fice da mugun sauri yana dan daga mata hannu a lokacin da take fadin" Yalabai ina kwana" ya wuce ya tafi Wajen da ake kiransa