Kenza eBookz

Auren huce haushi complete - Chapter 3

Auren huce haushi complete - Chapter 3

Auren huce haushi complete Chapter 3: Auren huce haushi complete Chapter 3. Dan Jim tayi har Saida Ammah tace "kina jina?" "Eh inaji Ammah duk muna tare…

4,330 words

Dan Jim tayi har Saida Ammah tace "kina jina?" "Eh inaji Ammah duk muna tare dasu, muna Nan gurin Zahra Bata Jin dadi ne Amman da sauki yan haka barci take". "Wane irin zance ne wannan kamar Bata Jin dadi Kinga Hasana fadi min gaskiya yanzu kina Ina?". " Muna F.M.C wlh jikin da sauki sosai kawai sunce ana dai San ta huta ne, kada ki tada hankalin Dan Allah". "To Allah ya kyau Amma Ina hankali ze kwanta". Waje Aunty Hasanar ta fito gurin su Baba tabawa da sajida tace "Baba tabawa Dan Allah kuje gida da sajida tasan inda aka aje abubuwan da zasu bawa kawayensu tunda yau zasu wuce sai ki fad'a musu tana gida gurin Abba, ta kalli Sajida ke Kuma duk tmbayar da saying Miki kice Baki Sani ba mu barsu a haka". Kudi ta mikawa Baba tabawan sannan ta karasa gurinsu Inna maimuna da Hajiya kaltume, Suma bayi tayi musu na Kiran Ammah tace suje gidan Dan hankalinta ya kwanta.

********* Da kyar Amma ta Bari akayi sallar magariba ta shiga bangaren Alhaji Jafar ta same shi da Hassan da Abdul Hakeem suna magana akan Zahra Hassan Yana ta mitar meyasa Abban yayi haka ai da hakuri kawai akayi har lokacin da Allah ze kawo Mata wani. Dan murmushinsu na manya yayi Yana "fadin wannan ma in Sha Allah Babu Dana Sani a cikinsa ni nasan nagartar Dana gani tare da yaron yasa na bashi, Kuma ko bayan Raina zakuce na fad'a muku". Jiki ba kwari Amma ta gaishe da Alhajin tana Masa ban gajiya tare da godiya. Sannan ta Dora da fadin "Dan Allah ko zaka Bari naje Naga jikin nata?" Tsai yayi Yana kallon ta "da kinyi hakurin zuwa Suma da anjima zasu taho gida yanzu ma daga cen muke ko zuwan mu Bai isar ba?" Cikin Jin nauyinsa tace "A'a ya badatar" Ta tashi ta nufi kofa da kallo Abban ya bita ita kanta tausayi take sashi da gani zuciyar ta ba Dadi. Da sallama suka shiga dakin lokacin Aunty Hasana tana sallar insha'i ita Kuma zahra farkawarta kenan tana kokarin tantance Wai inane ma Nan din inda ta gani idan dai ba gizo idanunta ke Mata ba kamar asibiti. Sallamar ce ta katse Mata tunani ta Dan dago kanta kadan sukayi arba dashi Ido cikin Ido da sauri ta runtse idanunta zuciyar ta na wata irin bugawa tana ambaton Allah a zuciyar ta, meya kawo wannan dodon nata gurinta, Kara rufe idanun tayi it fa wallahi zata iya rantsewa Allah duk duniya ba idanun da suke figitata kamar nasa.

💋❤️ AUREN HUCE HAUSHI 💋❤️

Strory & Written By MAMAN FATIMAH

Page five 📖🖋️ _______ Shiru dakin ya dauka har zawan lokacin da Aunty Hasana ta idar da sallar. Dan juyowa tayi kadan tana fadin "wa'alaikumus Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, sannunku da zuwa Bismillah ga kujeru nan ku zauna". "To mun gode Aunty" Sameer ya fada. Cikin ladabi da mutuntawa suka gaishe ta tare da tambayar Mai jikin, ta amsa musu da sauki, sai kuma dakin ya Kara daukar shuru Zahra dai tunda ta rufe ido Bata Kara gigin budewa ba, ita ji take duk ya cika dakin ita tun ganinta na farko dashi a duniya ya birkita Mata lissafi, Kuma saboda Allah meya kawo shi gurinta asibiti duk da tasan mutumin Ya Abdul Hakeem ne Amma sai taga kamar ba sai yayi Masa Kara ba, ko Kuma yazo wata sagbar ne asibitni ya Sami labarin shine ya shigo ya dubata. Magaji ne ya shigo dakin da sallama sai Kuma ya Dan tsaya baiyi tunanin ganinsa ba Sam da fara'a ya karaso Yana fadin "Ashe Kuna Nan ai tare muke da Ya Abdul Hakeem ma". "Ok" abinda Mahmud ya fad'a kenan Shi Kuma Magajin ya karasa gurin Auntyn Yana gaishe ta. Abdul Hakeem ne ya shigo Yana rike da wayarsa a hannu da sauri ya karasa gurinsu Mahmud din Yana fadin "A'a angon ne da kansa" Yana Mika masa hannu. Saroro Aunty Hasana tayi ita wace iri ce kawai dai taga sun shigo sun gaisa wallahi Sam Bata kawo ba ita da akace Mata Alamajirin Baba malam ne ai ta dauka irin wannan gaddawan ne, yo ta Ina wadannan sukayi wani Kama da kolaye ai ita zallar ilimi ta gano da wayewa a tattare dasu. Hanyar wajen ta nufa tana janye da hannun magaji duk sai taji kunya ta kamata Ashe sukanta ne. Ita kuwa Mai gayya Mai aikin ai tana jin an ambaci ango ta bude idonta girjinta Yana wata irin dokawa "ango a nan to waye a tsakaninsu da suka shigo tare? Abdul Hakeem ne ya kalli gurin gadon Yana fadi. "Masha Allah! Ashe kin tashi, ya jikin?" Ya fad'a Yana karasawa jikin garon Sameer ma Dan matsawa yayi Yana dubata Kai kawai ta gyada musu, tana kallon Ya Abdul Hakeem din, kallo irin na neman Karin bayani. Yi yayi kamar Bai Gane ba ya juya yana yiwa Sameer magana suka fita. Har suka fice Bai dago ba Yana ta faman tab'a waya sai da ya Mula Dan kan shi sannan ya tashi ya tunkari gadon. "Ya jikin?" Ya fad'a Kai tsaye, Bai Kuma jira ta amsa ba Dan ko kwakwkwaran motsi ta kasa sai tunanin da yake Mata Kai komo. "Badai wannan bane ake nufin an daura min auren dashi Amman da Naga ta kaina". Shine ya katse tunaninta. "Ki kwantar da hankalinki ki daina saka damuwa a ranki da kannan shekarunki, ki kuma dagawa Ammah í nata hankalin, idan nine bakya so ba damuwa Nima kusan hakan take. Amma kada mu watsawa iyayen mu kasa a ido Mana tun yanzu gara ki nutsu ki kwantar da hankalinki daga baya sai a duba Mai yuwuwa tunda nasan bazaki so Zama da almajiri marar karatun boko mai zurfi, ga karqncin wayewa ga rashin madafa ta yau da kullum, Nima kasada ce tasa na yarda da tayin da akayi min tunda Naga nema ake a tozarta min da iyayen a kunyata su a idon duniya aci mutuncin su". Ita da'i ko motsin kirki ta kasa da gaske gani take duk ya cika dakin, ga wani fitinan kamshinsa duk ya cika Mata hanci.

A bazato taji ya Dan shafi gefen fuskarta idan ba kunnenta ne suka jiyo Mata ba da'i dai ba sai taji kamar yace "my previous" a hankali sannan ya Mike Yana fadin "Bari a kawo maganin ki saimu wuce gida tunda doctor yace zamu iya wucewa, Amman yace ki rage yawan tunani Yana haddasa cututtuka".

Har dakin Amma Abdul Hakeem ya raka Zahra lokacin duk yawancin bakin sun tafi sai 'yan uwan Amma na Mubi Dana Jimeta sai Kuma Aunty Hasana da take dakon dawowar su, ai tunda magaji ya Kara Kora Mata bayani akan Mahmud ta tafi daga asibitin tunda Mai dungurungum din yazo ita bataga ta Zama ba. Saida ta matsawa Zahrar tayi wanka Tasha tea da magungunan ta kwanta sannan tayi haramar wucewa gida.

Sai wurin karfe Tara sannan Hajiya mama ta shigo dakin tana fadin "wallahi daga idar da sallar ta barci ya dakeni sai Dana tashi zilai Mai wanke wanke take fad'a min an dawo da Zahra har sun shigo sun duba ta". "Wallahi kuwa ai jiki da sauki yanzu Tasha magani ta kwanta" "To Allah ya Kara lfy, Wai Hajiya wanene mijin yarinyar Nan ne naji ana fadar Wai cikin Almajiran baba Malam ne, shine nace haba yaushe Alhaji zeyi wannan danyen aikin ya rasa bazai bawa aure Sai a cikin Almajirai". Inna maimuna ce tace "ai mu Hajiya ko waye Alhaji Jafar ya aurawa Fatima wallahi mun karba da hannu biyu mun gode tunda mun San har abada Babu cutarwa a tsakanin Asama'u da dashi da ita Fatiman da abinda ya Haifa bamu taba ganin banbanci ba, Dan haka mun karba da kyakykyawan niyyarsa Allah ta tabbatar Mana da Alkhairi". Gaba daya suka amas "Amin" Hajiya mamar ta Dan jima a dakin kafin ta koma dakinta. Bayan Zahra tayi sallar Asuba ta gama Azkar dinta komawa tayi ta kwanta har lokacin kanta Yana Mata ciwo kadan kadan, sai gurin takwas da rabi Inna maimuna ta tasheta tana fad'a Mata tayi maza ta kimtsa Abbansu Yana nemanta. A gurguje tayi wankan ta fito lokacin an kawo Mata kunun gyada da fanke, kunun gyadar kawai tadan Sha kadan ta shafa lotion dinta ta saka doguwar rigar atamfa ko dankwalin Bata daura ba ta fito cikin takunta na nutsuwa Wanda da yawa mutane ke gani a matsayin yanga da jiji da Kai. A tsakar gidan suka rinka gaisawa da tsirarun yan uwansu na Mubi da sauran ma'aikatan gidan Mata. Da sallama a bakinta ta shiga falon Abban nasu, tayi mamakin ganin kusan duk 'ya'yan Abban suna Nan sai su Ammah da Inna maimuna da kanwar Abban Maman lafia.

"Zo nan kusa dani Uwata". Abban ya fad'a Yana murmushi, itama murmushin tayi ta karasa kusa dashi ta zauna nata fadar "Abbana Ina kwana?". "Lafiya kalau Alhamdulillahi Uwata". Sannan ta juya tana gaishe da jama'ar gurin. Said Kuma dakin yayi shiru. Abban ne yacewa Imam "Mai sunan Malam ayi Mana addu'a". Ya jima Yana addu'a sanan aka shafa. Sannan Abban ya Dora da cewa. "Alhamdulillahi ala kulli halin, dole ne mu godewa Allah s.w.a a cikin kowane Hali mutum ya Samu kansa, kowa yasan yanda lamarin Auren Uwata ya ringa kasancewa a baya abune ba Mai dadin maimaitawa ba, to wannan karon ma tarihine yaso maimaita kansa Amma na yanzu sai yafi sauran tada hankali ni Kuma Naga a wannan gab'ar bazan Kara bada wata kafa ba wadda za'a dunga walagigi da rayuwar yarinya karama ba kamar Uwata. Sunanta Ya kira Fatima dago ki kalleni, cikin girmamawa ta dago kanta kamar yanda yayi Mata umarni. Hannunsa yasa ya nuna kansa yace kina ganin zan iya zaluntar k?" Da sauri ta girgiza Kai hawaye na zubo mata. Yace "To Fatima na daura Miki aure da bakon yaron Nan Mahmud na wajen Aminina Malam Bukar". Duk da taji haka daga bakinsa a jiya Amma Bai hanata kara shiga rudu ba saboda wannan taji daga bakin da bazeyi Mata karya ba, Nan da Nan ialahirin jikinta ya shiga rawa wallahi ita a jiyan jinsa kawai take gani take kamar almara ce kawai. Muryar Abbansu ce ta Kara katse Mata tunani "kiyi hakuri Uwata kowa da irin jarabawar da ubangji yake Masa ki dauka taki jarabawar kenan, ki yadda da kaddararki sai Ubangiji ya jibinci lamarinki wannan ba hadin kowa bane hadin Allah ne, kiyiwan mininmi biyayya in Sha Allah zakici ribar rayuwa, ki cire yaron Nan Musbahu daga zuciyarki ki rungumi abinda Allah ya baki. Allah yayi Miki albarka yanda Kika yi min biyayya Allah ya Baki 'ya'ya Wanda zasuyi Miki biyayya kema, Allah ya albarkaci aurenku ya tsone idon makiya da mahassada".

Hajiya mama ce ta fasa Kuka tana fadin "Haba Alhaji wannan wane irin danyan hukunci ne? ya zaka dauki 'yar marainyar Allah ka baiwa Wanda ba'asan asalinsa ba, ai duniya saita zage ka Dan Allah ka janye maganar Nan da wannan ba gara kaba salmaun gidan Hajiya Dago ba tunda ya jima Yana son yarinyar Nan Amma ka Hana shi" Kowa a falon kallonta yake ba Wanda ya tofa sai danta Hamza yace "haba mama menene haka kikeyi Dan Allah kiyi shiru da wannan maganar salmanun me Allah ya sauwake me za'a da wannan zuri'ar". Hannu Abban ya dagawa Hamza Yana fadin "ya Isa haka tunda ka Bata amsa basai nace komai ba, Amman ki rubuta ki aje in Sha Allah sai wannan auren ya Zama abin kwatance Kuma abin alfahari duk Wanda ze zageni ya Dade Bai zageni ba, Kuma duk Mai ganin zalunci ne yasa na aurawa Fatima Mahmud na barshi da Allah wallahil Azeem ban taba kallon Uwata a matsayin 'yar wani ba kullum Ina Mata kallon 'yata malak malak a makaranta ne kawai ban saka Mata sunana ba shima nayi haka ne Dan tasan nata mahaifin ta rinka Yi musu addu'a". Addu'a Abban yasa Imama yayi yaba kowa izinin tafiya Amma yace Ammah ta tsaya ita da Hajiya mamar da Inna maimuna da Maman lafia.

Aunty Hasana ce ta kamo hannun Zahra zuwa dakin Ammah tana kuka, yarinyar tausayi take Bata kamar yanda Abban ya fad'a ana walagigi da rayuwar ta. Cikin bed room din Ammah suka wuce, bayan sun zauna ne Auntyn ta riko hannun Zahrar "kiyi hakuri kinji Allah Yana sane da halin da kike ciki, Dan Allah kad'a ki watsawa Abba kasa a Ido ki bijirewa auren nan wallahi irin wanna auren Yana albarka fiye da tunanin". Wasu sabbin hawayen ta goge. Cikin shashhshekar kuka tace "wallahi Aunty nifa tsironsa nakeji idan muka hada Ido wani Abu nake gani a idonsa". Sororo Auntyn tayi kafin tace "ban Gane ba tsoronss kamar Yaya, Daman kinsansa ne runtuni?. Kai ta gyada Mata alamar Eh. "Allah ya kyauta" kawai Auntyn tace. "Ko meme ma dai wannan tsakaninku ne kin gyarota can". Ta Mike tana fadin "Bari na koma gida sai zuwa an jima zamu shigo da Sajida da Amatu itama Bata tafi ba jiyan.

********Tun bayan suka dawo daga sallar Asuba Mahmud yake ta faman aiki a cikin laptop dinsa, Yana kallon Sameer Yana kwasar barcin gajiya. Bai gama aikin ba sai kusan karfe takwas na safe, kai tsaye toilet ya nufa ya jima a ciki kafin ya fito daure da towel a kugunsa karami Kuma a hannunsa ya goge sumar kansa me baka sidik Mai laushi Saida ya shirts cikin wani farin yadi filtex marara nauyi ya feda turarensa Alburaq sannan yaje gefen bedside ya dauki wayarsa ya kunna. Abinci ya bukata a kawo musu, yana Gama wayar Kira ya shigo sunan Habib ya gani, ya daga da sallama daga cen Habib Fara fadar. "Habe Dan Allah dukka tadawa Baba malam hankali baka kwana a gida ba abinda baka Saba ba Koda wasa duk dare zaka dawo Amma jiya daga Bari kaje ka dawo shi kenan kayi layar zana Kuma ka Kama ka kulle waya". Dariya yayi Yana cewa "kana tunanin Kona bi dare nayi Gudun auren dole ko?" Shima Habib din dariyar yayi. "Ka Gudun Mana idan ka Isa mai wannan tsaleliyar Ina zaya ya barta koka gudu ka dawo da kafarka, kawai da malam ne ya matsa yaji kana ina". "Ok shi kenan Bari na kira shi Dan hankalinsa ya kwanta Ina Nan tare da Oga Sameer shine ya rikeni nayi Masa wani aiki". Yana kashe wayar ya nufi sofa ya zauna yana janyo stool din da aka Dora abincin. "Oh ni Sameer yaushe na rikeka? ka rikeni dai ka Hanani tafiya ka barni da kame kame ga madam can tana fama da kanta ba mataimaki gaskiya yau in Sha Allah sai kano". Ya fad'a yana nufar toilet shima. Can hayin bankin suka Fara zuwa gurin masu aikin gidan Masha Allah aikin yayi nisa kamar ba jiya aka Fara ba Sam an canzawa gidan fasali kamar bashi ba, duk abinda ake bukata Sameer ya danka shi a hannun Binya. Sannan suka nufi cikin gari. Wani mall suka shiga Mahmud ya jido kayan fruits dasu kayan tea sai chocolates dasu farm fresh yogurt da fresh milk. Leda uku aka cika manya Saida suka dauki hanya Sameer ya kalli Mahmud yana fadin "wadannan kayan fa yallabai na waye". "Dubiya zamu saika Bata tunda ni dai kowa yasan bani da kudin sayansu.

💋❤️ AUREN HUCE HAUSHI 💋❤️

🔷 Page six🔷

P📖🖋️

________Sun jima a gurin Baba Malam Yana yiwa Sameer godiyar dawainiyar da yasha akan wannan lamarin, sannan yayiwa Baba Malam din sallama akan zai wuce sai hutu ya Kare zasuzo da mutanen su suna son su kawo wasu ayyukan da za'ayi. Har gurin mota Malam dasu Habib sukayi Masa rakiya, Baba malam Yana fadin "Bari muyi addu'a". Nan yaja doguwar addu'a akan Allah ya tsare hanya, har Sameer ya shiga mota ya fito ya nufi Malam Wanda har ya Fara tafiya, sai Kuma yaja ya tsaya Yana jiran karasowar Sameer din. Dan risinawa yayi Yana fadin "ko za'a samu Wanda ze rakani na Kara dubo jikin wannan yarinyar?" Wani kallon kasan ido Mahmud ya bashi dashi "Wai yarinya". "To! To! Masha Allah ai sai kuje da Mahmud din da Habibu kuga jikin, ai wannan tunani ne Mai kyau.Nima na shiga da safe gurin Alhajin naji yata kwana". Har cikin harabar gidan Sameer ya shiga da motar, Abdul Hakeem Habib ya Kira kafin su shigo ma ya fito Nan Harabar gidan Yana jiransu. Shi yayi musu jagora zuwa falon Abban, yayi murna sosai da ganinsu sun gaisa sosai sun masa godiya sosai da karamcin da yayi musu, yaji dadi sosai Dan har ya ringa tsokanar Sameer Yana fadar "wato tunda kazo gabatar da aikinku ban sake ganin kafarka ba a gidan Nan sai yau dana baku Mata ko? Dan na lura baka da aminin daya wuce Mahmud a garin nan. Masha Allah, Malam ya fada min duk Fadi tashin ku akan lamarin Allah ya saka da Alkhairi yabar zumunci". Suka Amma da "Amin ya Rabbi". Mahmud Alhajin ya kalla Yana fadin "kayi hakuri fa Mahmud munyi maka nauyin kuka". Kai ya gairgiza Yana fadin "ko daya wallahi ba komai nagode, Allah ya saka da Alkhairi ya Kara lafiya Nisan kwana Mai albarka" "Allahumma Amin. Allah yayi Albarka, ya baku zaman lafiya ya baku zuru'a Mai Albarka, sai ayi ta hakuri da lamarin Mata fa. Abdul Hakeem ku shiga ciki su gaisa da Iyayen nasu".

Wannan shine shigar Mahmud na biyu gidan, na farko lokacin da magaji yayi accident da mashin suka shigo shida Abdul Hakeem da Hamza ya duba shi a dakin Ammah, dan ma lokacin ba kowa a gidan sunje gaisuwar mutuwa. Directly dakin Hajiya Mama Abdul ya nufa dasu, Zilai Mai musu wanke wanke ce tayi zuruf ta shiga dakin Ammah. Tana fadin "Ammah Ina Jin fa ga mijin Zahara'u Nan sun shiga dakin Mama shida Abdul Hakeem da wasu inaga abokansa ne". Ta juya ta fita. Gyalen Inna maimuna Ammar ta dauka dake kusa da ita ta yafa a jikinta. Da sallama Abdul Hakeem din ya shigo Yana fadin Bismillah ku shigo Mana, a nan kan carpet a kasa suka zauna suna gaishe dasu Ammar tare da tambayar Mai jikin. Abdul Hakeem ne yace " Inna mijin Zahra ne da ubangidansa suka shigo duba ta shi yau ze wuce shine yace a rako shi ya Kara dubata da jikin nata".

"Kai Masha Allah an gode madallah Allah ya saka da Alkhairi ya maida ka gida lafiya". Inna maimuna ta fada sannan ta kara da cewa "to waye angon nawa Dan nice ta karfe ita wannan Farafarar ba wani abun azo a gani zata iya ba ni kuwa ko banza na tuka maka tuwon dawa da man shanu ko ba haka ba?" Ta tambaye shi tana kallonsu. Duk dariya sukayi Amma shi gogan Dan murmushi yayi kadan Yana basarwa. Abdul Hakeem ne ya nuna Mahmud Yana cewa. "Ga angon naki nan nagama kamar kunyarki yakeji" "A'a! Masha Allah tubarakallah Mai gidan nawa wanke hannu daka taba ne, kaga dago ka kalleni ni Kaka ce kada kaji wata kunya ta". Kara sadda Kai yayi shifa duk jinsa yake wani iri Wai shine a zaune a dakin surukai Ashe da gaske ana jin kunyar shi wallahi da ji yake kawai fada ake ba wani nauyin da akeji Saida ya same shi yanzu yake gaskata hakan. A kaikaice Ammah ta kalleshi "Masha Allah" ta fada a zuciyar ta, ita bataga wata makusa ba a tare dashi Kuma idan ba idon tane yake Mata gizo ba sai taga duk cikin Wanda zasu auri Zahrar a baya bataga Mai nagarat wannan yaron ba. Albarka da nasiha dai ya Sha ta gurin Inna maimuna. A haka suka fito daga dakin har suka fito compound din Abdul Hakeem Bai fito ba sai duba agogo Sameer keyi Yana mita. "Nifa bana son nayi Rana a tafiyar Nan gaskiya, Naga alamar kuma neman kuke kusa nayi yamma ma". Kafin Mahmud ya bashi amsa Abdul Hakeem din ya fito da sauri da key a hannunsa Yana fadin "kuyi hakuri key din ne ba'a gani ba da wuri ku karaso ciki kafin Zahrar ta fito ku gaisa". Mahmud ne yace "Kai haba da an kyaketa ta huta ita da Bata da lafiyar kirki". Karamin falo ne da kujeru masu kyau sosai da kayan kallon alama an tana deshi ne saboda Yara Mata na gidan da Kuma dai dai kun Baki. Bayan fitar Abdul Hakeem, Sameer ya kalli Mahmud. "Dan Allah my man yaushe idonka ya koyi kunya? Naga sai wani sadda Kai kake, nifa lamarinka ya Fara bani tsoro na rasa wace alkibla ka kalla kazo garin mutane ka Mike kafa kana wata irin rayuwa a takure nace zan dauki mataki ka aje min sharadi, da kasan bazan it's tsallakewa ba, yanzu Kuma Rana tsaka a tarko aure Kai kadai kamar marar gata sai walagigi kake alhalin kana da madafa". Tsaki yayi " kana da matsala wallahi ko me zance fada maka bazaka Gane ba, amma idan lokaci yayi zaka fashinmta,yanzu duk bayanin da zanyi maka ba fashinmta zakayi ba, kawai mu bar maganar kawaai" Kanshin turaren ne ya alamta musu zuwanta. sallama tayi cikin siririyar muryarta. Sameer ne ya amsa Mata sallamar a zahiri Dan shi Dan gogan a saman lebensa ta amsa sallamar. Sameer din ne ya Dan Mike Yana fadar. "Masha Allah jiki yayi sauki kam, "Bismillah". Yana nuna Mata kujerar gefen Mahmud. Kai ta dangirgiza Masa tana dan murmushi kasa kasa. A Nan kan carpet ta zauna daga gefe tana gaishe da su a jimlace. "Lafiya kalau" Sameer ya amsa Yana fadin "ya jikin naki?" "Alhamdulillahi" ta amsa masa. Sai Kuma duk sukayi shiru, ganin lokaci Yana qurewa Sameer ya Mike tare da kallon Zahra Yana fadin " To madam bako zeyi halinsa Allah ya bada zaman lafiya. Amma fa sai kina hakuri da halinsa gaskiya ba kirki ya cika ba Ina son idan na dawo Naga canji na zahiri a tare dashi, sunan Sameer Sa'ad koko, zeyi miki cikakken bayanin koni waye a gurinsa Allah ya bada zaman lafiya da zuri'a mai..albarka Allah yasa next year by now muna bkin suna" Da sauri Mahmud ya kalli Sameer a zuciyarsa Yana fadin "Allah ya shiryeka Sam baka girma".

A hankali tace " Mun gode kwarai Allah ya tsare ya kiyaye hanya". "Amin" ya amsa Yana kallon Mahmud. "Ni zan wuce saina sake shigowa ayi kokarin ganin aikin Nan ya kammalu". Ya fada Yana nufar kofar fita. Sai lokacin Mahmud din yayi magana "pls ka jirani minti biyar Dan Allah".

"Idan ya wuce haka Kam...."

Ya fice ba tare daya karasa fada ba.

Tunda Sameer din ya fita take wasa da karamin zoben da yake hannunta. Bata dagon kalle shi ba shi Kuma Bai tofa tasa ba amman idonsa Yana kanta, Kare Mata kallo yake Yana fadar "Masha Allah tabarakakkahu ahasanil kaliqin". Tsam ya taso daga inda yake ya sauko kasa inda take zaune. "Ya jikin naki?". Ta tsinkayi maganarsa kusa da ita daf Sam bataga lokacin daya taso ba. Cikin daburcewa saboda kusancin nasu yayi matukar yawa ji tayi kamar ma iskar gurin ta tsaya sai munfashinsa take shaqa kawai. A mamakance taga yasa hannunsa ya dago fuskarta suka hada Ido hudu dashi. Da sauri ta runtse idanunta zuciyarta na wata irin bugawa. "Bude idon Kona Baki mamaki". Marmar ta Fara da idon tana budewa a hankali Amma taki kallon nasa idon. "Ya jikin?". Ya Kara maiamaitawa, a hankali ta bude bakinta tace "da sauki" Gamshin Lister mint ne ya daki fuskarsa. Banda Yana daf da ita ba yanda za'ayi yaji abinda ta fada. "Allah ya Kara lafiya". "Ameen" Ta fada. Hannunsa ya cire daga fuskarta yana Dan furzar da iska daga bikinsa ya Mike tsaye, a hankali ta sauke wani numfashi. A bazata taji yace "bani wayarki" Ba musu ta Mika masa, aljihu taga ya saka Yana fadin "ki shiga gida ki kwanta kiyi barci sosai kada ki yawaita hayaniya ki samu hutu sosai, zan tambayi magaji idan bakya hutawa yanda ya kamata ni Ina da inda zan kaiki ki samu isolation, tashi muje ki shiga gida ana jirana". Saida ta shige ciki kafin ya juya ya nufi gurin da Sameer da Abdul Hakeem suke suna Hira.

Lokacin data shiga dakin ta Samu Aunty Hasana dasu sajida sunzo har da yaran duka. Da guda ta karasa cikin suka rungume juna da Sajida Nan da Nan sai hawaye itama sajidar kukan ta fara. Ammah ce tace "Naga abinda ya isheni meye haka zaku tasa mutane a gaba Kuna kuka, to kukan maganin me ze muku aikin Gama ai ya Riga ya Gama Saida hakuri da addu'a kawai". Uwar dakin Ammah suka shige. Magaji ne yayi sallama ya shigo da manyan ledoji guda biyu niqi-niqi da kaya Auntyn Hasan na tambayar"daga Ina?" Ya fice da sauran Yana fadin "ina zuwa Aunty" Wata ledar ya shigo da ita Yana fadar"kayan dubiya ne aka kawo Mata" ledar daya kawo daga karshen ya bude rafar 'yan dari bibiyu hura biyu ya dauko daga saman kayan, Aunty Hasana ya Mikawa yana fadar "gashi nan inji abokin mijinta Wanda suka shigo dashi dazu". Godiya su Inna maimuna sukayi tayi kamar Yana nan a gurin suna ta Saka albarka.

********* Bayan tafiyar Sameer can gurin aikin gidan suka wuce, ba karamin mamaki Habib yayi ba har ya kasa hakuri ya tambayi Bilyaminu lokacin Mahmud Yana ciki. "Dan Allah wane irin kudi gayen Nan ya bada haka Nan da Nan gidan ya juye ya Zama kamar daukowa akayi daga wata kasar". "Wallahi Nima bazance ga abinda ake kashewa ba, iya kudin aiki Dana abinci kawai suke a hannuna, bakaga wash bakin fuska ba su biyu?' "Eh nagansu" Habib ya fada. "To ai tun jiya sukazo da komai na aikin bakaga Nata'ala ba shima lebura ya koma kaga ai da malam shi yasa a Kira saboda 'yan gyare gyaren amman da masu iyawar sukazo shima yaronsu ya koma". Ya fada Yana dariya. "Wallahi Bilya sai a kyaleka Kai kowama sai ka tab'a". "Gaskiyar kenan ni wallahi burgeni ma yayi tunda baiyi zuciya ba ya tafi, ko banza nasan Yana lure da koma Dan gyaran nasa aikin".

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull