Kenza eBookz

Auren huce haushi complete - Chapter 45

Auren huce haushi complete - Chapter 45

Auren huce haushi complete Chapter 45: Auren huce haushi complete Chapter 45. Cikin abinda Bai wuce minti talatin ba suka shiga Asibitin office din doctor…

3,931 words

Cikin abinda Bai wuce minti talatin ba suka shiga Asibitin office din doctor suka nufa tunda ya bukaci ganin mahmud saboda ze cike wasu forms ze Kuma yi signing a takardun da za'ayi aikin. Basu Dade ba suka Gama da office din doctor suka nufi dakin da Baba Malam din yake. Suna tafiya kawai Habib kallon mahmud yake ya rikide ya juye daga mahmud din Baba Malam ya koma wani na daban Mai wani irin kwarjini da cikar Kamala ko Zama sukayi Hira irin ta da yanzu sai Habib yaji baze iyaba sai fa mahmud ya matsa Masa sannan yake Dan sakewa, ga Abubakar wanda shine babban guard dinsa Amma sukayi basaja ba Wanda ya gane, ga wani Karin abin mamakin Wai Bilyaminu ma yaran mahmud ne. Har suka karasa dakin yana ta faman tunanin abun. Masha Allah ba karamin Dadi sukaji ba da ganin yanda jikin Baban yake. Sallamar su ya amsa Yana sakin murmushi tamkar ba Mai lalura ba, gani ma sukayi har wani haske ya Karayi duk da Daman farin mutum ne Shi, Yana kwance sandam da sauri mahmud ya Karasa kusa dashi Yana fadin. "Masha Allah! Baba jiki ya Fara kyau Alhamdulillahi, ya kaje jin jikin naka?". "Alhamdulillahi Mahmud jiki ya Fara kyau ko yanda nakeji da banbanci akan kwana ukun baya, sannunku da kokari Allah yayi Albarka yasa afi haka". "Allahumma Amin". Suka amsa su duka, Abubakar da Habib ne suka matso suna gaishe da shi da tambayar ya jikin nasa. Ya amsa musu da sauki suma yayi musu godiyar dawainiyar da suketa faman yi dashi. A Nan suka zauna har dare suna dauke Masa kewa mahmud ya cika Alkawari ya kirawo Bilyaminu video call yace ya Kaiwa iya Abu zasuyi magana da Malam, taji dadin yanda taga jikin nasa Dan sun Jima suna Hira har su mahmud sukaje suka Kara dubo Alhajin su Faisal. Sai wurin goman dare na agogon kasar suka wuce daga asibitin, ba gida suka nufa ba, Abubakar ke driving sai Habib dake zaune a gefensa sai Kuma oga kwata-kwata dake baya yana ta cinkunar wayarsa. "Sir ina zamu Fara zuwa?" Abubakar ya tambaya cikin ladabi. Saida ya Gama duba results din club dinsa real Madrid, sunyi Wasa lokacin suna Asibiti shine yanzu yake duba results din wasan. "Wuce Africa Avenue kawai na gama ganawa dasu sai mu shiga Taj idan lokacin be Qure ba". "Ok sir Leela palace kenan?". "Eh a can nace musu zamu zauna"

"Ok." Akalar motar ya canza daga hanyar da yake bi, shi dai Habib nasa ido ne Dan fadan da yafi karfinka sai ka mayar dashi Wasa. Ganawa ce mahmud din zeyi da managers na different companies dinsa ya Dade Basu hadu ba sai dai ta Internet kawai, shine yayi amfani da wannan damar ya tarasu duk da yaso sai Nan gaba to wata kura ce ke neman tasowa shine yayi musu Kiran gaggawa.

Habib yaso fita mahmud ya Hana shi, ba karamin abin al'jabi Habib ya gani ba yanda yaga manyan mutane daga different countries suna Masa aiki a Nan Indian shifa har tsoro ya Fara kamashi waye Mahmud ne Wai? Yanda yaji managers da Accountant suna bada lissafi saida jikinsa ya dauki tsuma, basu suka baro Leela palace ba sai kusan Daya da rabi na dare. Suna shiga gidan Mahmud ya wuce bedroom, requesting coffee kawai daga gurin Mr Ajey. Su Habib dai sunci Abinci sannan suka wuce, kowa ya shige nasa, tun jiya aka hada dayan dakin Habib ya koma ya barwa Abubakar wanda suka Fara sauka.

A gajiye mahmud ya shiga bedroom dinsa wayar da eyeglass din ya aje a Kan bedside ya wuce toilet. Lokacin Daya fito Mr Ajey ya kawo masa coffee dinsa. Saida ya saka pyjamas dinsa milk colour mai haske sannan ya zauna Yana sipping din coffee a hankali yana Jin dadin yanda yake ratsa Masa makogwaro Yana gangarawa. Kira ne ya shigo wayarsa yasan ba previous bace har ze share sai ya dauka ya duba Sameer ya gani. "Sameer" ya ambaci sunan a fili sannan ya daga Kiran. Daga can Sameer din ya Fara magana. "Sir Naga sakonka, wallahi da kyar na samu visar madam yau Amma sai Monday zata taho in Sha Allah gara nima dai na huta". Ya fada Yana dariya. "Au dariya ma kakeyi ko? wallahi idan tace na mayar dakai China da Zama Allah saika koma can,Kuma Banda madam zaka tafi, sai bayan wata shida zaka ringa zuwa Kuna gaisawa shima sai ta amince, idan Bata amince ba sai dai once in year". "Tuba nakeyi gani nayi ka kasa hakurin rashinta a kusa da Kai tun yanzu to Yaya idan labarin yasha banban"?". Ya fada Yana dariya irin ta shakakikan friends. "Allah ya shiryeka badai abinda zakaji Dan saka Ido kawai, ka aje komai jibi ka wuce Nigeria Kai da kanka zaka kawota min ita Kano". "Ok. In Sha Allah". Sukayi sallama,wayar ya aje yana tunanin ko ya kirata ko Kuma ya kwanta ya huta.

** *** **

Barci sosai Zahra tayi Bata tashi ba sai kusan la'asar toilet ta shiga ta sake gyara jikinta. Alhamdulillahi Abun ya Fara sauki sosai, amma dai ha lrokacin Yana Zuba over, Saida ta shirya ta nufo parlour tana rike da wayarta, ba kowa a ciki sai kamshin turaren daki da tureren wuta. A hankali ta ratsa ta nufi dining Abinci ta gani kala biyu coconut rice ce sai danbun shinkafa da yaji vegetable a ciki, dambun ta Zuba kadan taci kadan ta tashi ta dawo parlour ta zauna. Aunty Hasana ta kiya har sau biyu ba'a dauka ba saita tura mata text, Aunty Safiya ta Kirawo lokacin suna makaranta dalibai na Exams, dauka tayi tana amsa sallamar zahra tana fadin. "Kaga Mrs Dange, ya kanon?". 'yar dariya zahra tayi. "Kaji dai Aunty Safiya, to Ina Azare Kuma kusa dake ma". "Ahhh haba Dan Allah....!" "Wallahi Ina layi na biyu bayan layinku". Dan Jim Aunty Safiyar tayi tana tuna wani gida data gani lokacin da taje barka layin Wanda "yan layin suke ce masa gidan Dan America, masu aikin ginin ne da wani ya tqmbayesu gidan waye sukace Mai gidan Yana America shikenan suka sakawa Masa gidan Dan America. "Kamar nasan gidan naje barkar haihuwa kwanaki baya Naga wani sabon gida akace mai shi baya kasar Ina shine gamu Nan zamu shigo da Amatu in Sha Allah". "A'a kice na tashi na shirya abin tarba, Ina jira, Dan Allah kuzo da wuri".

Aunty zilai ce ta shigo fadin. "Wallahi daga na Dan kwanta na huta barci ya daukeni". "Ai Rai dangin goro ne hutu yakeso, Ina laifinki sannu kema ai jiyan yanke Miki barci akayi shi Kuma ba'a cin bashinsa sai an biya" "Haka ne Kam ai anyi ta barka dai tunda na rabu da wannan kaddararren ciwon cikin gaskiya duniya da magani waye ze taba kawo masoro zeyi irin wanna aikin?". "Gaskiya dai Kam". Zahra ta fada. "Amma dai uwar dakina kin Kira Hajiyar makwarari kiyi Mata albishir ko?". Kai zahra ta girgiza alamar bazata kirata ba. "A'a ba'a haka,ki kirata ki gaisheta ki fada Mata magani yayi aiki kiyi Mata godiya ai zataji dadi'. "To shikenan na kirata anjima saina fada mata, yanzu me za'a Karayi Mai sauri zanyi Baki ne abokan aikina da muka zauna a Inda nayi service".

"Akwai samosa da nayi dazu na saka a fridge sai a soya Musa tunda da abinci da drinks ina ga ai ya Isa ko?". "Eh hakan yayi". Kitchen Aunty zilan ta koma ita Kuma zahra tabi lafiyar kujerar. Aunty Rukayya ta kirawo.

Bata kusa sai mommy ta dauka cikin ladabi zahra ta gaisheta mommyn ce tace Mata. "Ai kuwa Rukayya na gidan Hajiyar makwarari dazu ta tafi ta manta wayar a gida garin sauri". "To mommy Baki na Kira da layin Hajiyar na gode". "To nagode Allah yayi Albarka, ya wajen Mai jikin Kuma Sameer yace sun wuce indai ko". "Eh suna can da sauki". "Allah ya bashi lafiya yasa ayi aikin a sa'a". "Allahumma Amin nagode". Sukayi sallama. Akalar Kiran ta juya ga Hajiyar makwarari cikin sa'a wayar na hannunta ta Gama amsa wani Dan uwanta Malam na Dala Kiran zahra ya shigo. Dauka tayi tana fadin, "Salamu Alaikum, waye yake Kira?". "W/slm, Hajiya nice zahra". Dan Jim tayi tana tuna Ina tasan muryar Nan. "Zahra wace ce kenan? Ko Zahara,un Hajiya Fateen lalloki?". "A'a ba ita bace". Sai zahra ta rasa me zata ce Mata ne, tace zahrar mahmud abokon Sameer, sai taji da nauyi ta fada Mata haka. Rukayya ce ta shigo da cup din kunun tsamiya data damawa Hajiyar a hannunta. "Wa Kika Sami haka naji kina ambatar zahrar lalloki". "Ungo kiji ko wacece tayi shiru batayi min bayani ba ke kiji ko zata fada Miki". Wayar Rukayya ta karba tana mikawa Hajiyar kunun a cup. "Aunty Rukayya". Zahra ta Kira sunanta. Take ta dauki muryar zahrar. "Au kice min amaryar big bro ce ai bayani Zaki yiwa Hajjaju, kince zahra Ina zata gane". "Hajiya matar Ya Mahmud ce mutuniyar ki da Kika Gama maganarta dazu to gata 'yar halak ta kiraki". "Ga Hajiyar ku Gama gaisawa Dan ba barina zatayi muyi hirar kirki ba idan Baku gaisa ba tunda nazo take you min zancenki". Wayar ta mayar Mata ta nemi guri ta zauna. " 'yar Nan Daman kece ki kak'i yi min bayani dan Ashatta". Gaishe da Hajiyar tayi tana fadin. "Cewa nake Zaki ganeni fa, Daman kiranki nayi na gaisheki Kuma na fada Miki ciwon Nan na cikina ya narke yanzu babu shi". Wata zabura Hajiya tayi kamar yarinya tana fadin. "Kai Masha Allah kice nayo shiri na taho Azare na kawo Mik wani maganin saboda bibiko da Kuma aasske- sassake saboda sanyin dake Hana Yara haihuwa kinsan yanzu kuma sai a Fara shirye-shiyen haihuwa Kwana kadan ai sai laulayi, Dan ma naji labari mijin naki ya Kara yin halin nasa ya fice daga kasar wallahi sai kin jajirce kin zamar masa karfen kafa sannan zakiji dadin aure, Amma Kika zauna sanyin Nan sai kinyi tsa-tsa a banza Naga shi matan ma basa gabansa ta Neman kudinsa kawai yake, Kullum mutum na sama kamar tsuntsu to kinji dai na fada Miki". Baki bude Rukayya ke kallon Hajiyar. * AUREN HUCE HAUSHI*

MAMAN FATEEMAH.

Page 65

---------- Wayar hannun Hajiyar makwararin Rukayya ta karbe tana fadin. "Dan Allah ki daina fadin wata maganar ba girman ki bane". "To uwata saiki hanani na saita yarinya, ai gobe in Sha Allah Mahfuz ze dangana Dani Azare, yo duk abinda aka yiwa matar Mahmud ai bazamu iya biyansa abinda yayi Mana ba, Banda rashin lissafi irin naki Rakiya ke kome nace zanyiwa iyalin yaron Nan ai naki idone,kina zaune ya daukeni ya kaini wata uwa duniya aka gyara min ido da yanzu kina Nan kina min jagora ko bakya so kuwa. Tashi ki kimtsa ni ki rakani kurmi na Sami abinda bani dashi, muje agadasawa a Sami kilishi da dambun nama na tsaraba mu shiga madatai a samo gireba da su bakilawa to kinji" Ta yunkura ta tashi Tana daukar sauran kununta, ita dai Rukayya bakinta mutuwa yayi da kalaman Hajiya, tunda ta furta tafiyar nan Allah ne kadai ze kawo abinda ze hanata zuwa Amma badai Dan mutum ba, tun su Sameer na secondary tasu tazo Daya da mahmud tun Batasan Allah ze daga shi haka ba.

A nutse Amatullah ke driving dinsu, taso ta wuce gida saboda ta gaji sosai Amma jin zahra na garin Kuma babu nisa da gidan yayar mamanta da take zaune a hannunta sai kawai tayi waya ta fada Mata zasuje unguwa. Tunda suka shigo layin Amatu ke Kakabin gidan tana fadin. "Kambala'i wannan Kuma waye yayi one in town din Nan? lallai Aunty Safiya unguwar taku ta masu ido da kwalli ce". Murmushi tayi mata tana kokarin Kiran waya. "Mun shigo ki turo a shiga damu". Dan saurare tayi kafin tace. "Ok muna jira". Ta sauke wayar daga kunnenta. "Kika ce menene?". "Cewa nayi unguwar taku ta Zama ta masu Ido da kwalli". "Bakiji ranar nan muna maganar layin Dan America ba? To ai gidan ne ake cewa gidan dan America". Labarin yanda gidan ya Sami suna ta Bata. Dai dai suna zuwa kofar katafaren gate din gidan. "Dan tsaya a Nan mu jira muga ta Ina zata bullo Mai kaimu gidan". Amma ita Safiyar ta hakikance matukar da gaske MAHMUD DANGEN ne da gaske mijin Zahra to babu ko tantamar wannan gidansa ne. Saka aya a tunaninta da bude Karamar kofar gate din ya Zama lokaci Daya. Zilai Mai aikin gidansu zahra Amatu ta gani ta fito, zaro Ido tayi tana kallon Aunty Safiya. Gyada Mata Kai tayi kawai, sannan ta bude kofar ta fito. Gaisawa sukayi da Aunty zilan, sannan tace Mata. "Ko kune Bakin Uwar dakina Zahra". "Eh mune". Aunty zilan juyawa tayi da sauri ta koma ta fadawa zayyan zahra tayi Baki. Jim yayi Yana kallonta kafin ya samu zarafin fadin. "Yallabai fa ya kafa dokar kada nabar kowa ya shigo gidan nan, Amma Bari na fada Masa duk da nasan ba wadanda yake nufi bane.

Tana tsaye ya Kira Mahmud cikin sa'a ya sameshi, tun kafin ya fada masa wani Abu yace masa. "I sw everything, just open the door". Kawai ya katse Kiran Dan yana bibiyar gidan ne tun lokacin da yaga ta saka ayi wani girkin, Dan har a kitchen Saida aka saka CCTV. Gate din zayyan ya bude musu suka shigo, parking lot Amatu ta aje motar suka fito zilai tayi musu jagaba. Amatu sai raba Ido take Dan wallahi gidan ya tafi da imaninta ba kadan ba. Suna shiga zahra tayo wani tsalle tana fadin . *Wayyo Allah oyoyo! oyoyo!! Sannu da zuwan ku Amatu, Aunty safiya nagode da Kika kawo min Amah wallahi Daman Ina nemanta. Dan ja Baya Amatun rayi tana fadin. "Ni ba gurinki nazo ba Aunty safiya na rako". Hannunta zahra ta riko tana fadin. "Haba my bestie kiyi hakuri Dan Allah na tuba kowane laifi nayj kada a tona".. . dariya sukayi su duka, Ammatu dai 'yar kauye ta zama Dan Saida ta tada Kai taga yanda saman dakin yake kamar sararin samaniya Dan harda taurari da wata. Dauko wancan kawo wannan zahra da Aunty suka shiga yi, sai murna zahra keyi na ganinsu, sunci sun Sha sannan suka Dora da hira har aka Kira sallar magariba hirar yaushe gamo akeyi, cikin hirar ne Zahra ke fadin "Wai da gaske kinsan Mahmud?" Zama ta gyara tana fadin. "Wallahi ba karya har gidansu na sani sai dai shi nasan be sanni ba". Daga Nan ta tsaya itama Zahra Bata zafafa ba taja bakinta tayi shiru. Dakin kusa dana Aunty zilai zahra ta kaisu sukayi alwala, har Amatu zata Fara sallah ta tsaya ta dubi zahra. "Ya Naga ke Baki tashi kinyo alwalar ba". "To sa'i'dawa Ina ruwanki". Gurin zahra Amatun dawo ta zauna a gefen gadon in da zahra ke zaune. "Zahra Wai ya haka, ko dai planning kikeyi ne? Amma ace har yanzu babu wani labari, Ni da naganki kinyi wani sirrin kyau nayi zaton ko an Mana ajiya ne? Kuma kice Wai bakya sallah". Dariya zahra tayi tana Fadin. "Cikin lafiya? Ai ni ban isa haihuwa ba". Wata malalaciyar dariya Amatullah tayi. "Kice min 'yar yaye aka kawo masa, Wai Ina yallaban? Ko yana ciki kin Hana shi fita Dan Naga yanda Kika cika din Nan nasan baya Wasa gurin zagaya gonarsa tunda ga yabanya Nan tayi kyau da gani ana samun ban Ruwa akai akai". Ta fada tana Kara wata dariyar.

"Wallahi Amah ki daina wannan dabi'ar Baki da magana saita wannan sabgar Kinga fita ta, Ni idona da sauran kunya a cikinsa Banda tsabar jaraba a gaban Aunty safiyar kike fadar irin wanna magana, Dan tsabar gulma da kinibibi kinyi alwala Amma Kika zauna Zaki Fara zancen da ze karya Miki ita, wallahi mijinki yaga ta Kansa irin ku ne maza suke guduwa daga gida saboda halinku". Tana Gama fada ta Mike ta fice, wayar ta aje a Kan gadon. Daukan wayar Amatullah tayi tana juyawa, ba karamin mamaki tayi ba da ganin wayar dake hannun Zahra. "Wai ba zakiyi sallar ba kema Naga da alama ma kin Manta zakiyi sallar in dai lamarin gidan Nan ne bakiga kamai ba, I'm telling you in dai 'yan wannan family din ne, kinsan Allah duk wannan Wasa ne ko ita kanta Mai gayya Mai aikin Batasan wa take Aure ba, kin manta na fada Miki indai shine baze iya rayuwa da matarsa a wancen gidan ba?". Kai Amatullah ta gyada alamar haka ne, Bata iya tofa wata maganar ba saboda shigowar zahra. "Au bakiyi sallar ba kenan? Gaskiya kina Wasa da sallah". "Kema dai Kya fada Mata, gashi na baro baby na Dan ma tana cin Abinci shi yasa Honey Bai takura min da Kira ba, suna cikin gari duka gidan Baba Dan lawan". Tashi Amatullah tayi ta tayar da sallah.

Basu suka bar gidan ba sai bayan insha'i Shima Saida mijin Aunty safiyar ya Kira Dan bayan sunyi sallar babin karatu Aunty safiyar ta budewa zahrar Dan idan ta Fadi wani abun rufe Ido zahrar takeyi Amah na Mata tsinyar Wai muna furcine idan suka shige other room wata Kila ita ke Jan sitiyarin motar ai tasan ba'a banza ba tayi irin wannan cikowar tasan ta gane garin. Sai a Nan Zahrar ke fada musu mahmud din ma baya kasar Yana India an Kai malaminsu Asibiti ya samu matsala a bayansa. Sun jajanta sosai, mayuka da turaruka Zahra ta basu, Aunty safiyar tayi mata Alkawarin kawo Mata wasu kayan Mata dasu tureren mara Mai fitar da oga daga hayyacinsa duk iya yanda ya Kai ga kame bakinsa, Amma Bata fada Mata hakan ba tasan halin kayanta sai taki amfani dashi. Har gurin mota zahra da Aunty zilai suka rakosu, bayqn sun tafi ciki Zahra ta wuce wanka takeso Dan ki take kamar ya Bata Mata jiki. Basu Dade suna Hira ba Zahra taga Aunty zilai tana hamma sai tace Mata taje ta kwanta kawai tasan har yanzu da sauran ramuwar barcin a idonta.

*********

Tun karfe shida na safe Mahmud ya wuce asibitin shida Mr salahuddeen, Saida ya jira doctor din yafi son ya Gama da doctor din kafin yaje gurin Baba malam misalin bakwai da rabi doctor ya shigo office dinsa be Jima da shiga ba mahmud ya shiga suka gaisa da yarensu na indianci, sannan yayi Masa bayanin yanzu takwas dai-dai zasu shiga dashi suna tunanin zasu dauki awa goma Sha biyu suna aikin Dan ma lakkar Bata tsinke ba. sallama sukayi ya nufi dakin da Baba malam din yake. Lokacin da suka shiga har an shirya Baba malam cikin Kayan aiki. Murmushi ya fara yi da yaga mahmud ya shigo. Da sauri Shima ya nufe shi Bai taba jin karaya ba irin ta yau daya ganshi kwance sandam babu inda yake motsawa daga kugunsa zuwa kafarsa. "Sannunka jarimin namiji, ubangiji yayi Albarka Mahmud ko yanzu Allah ya bani abunda bani dashi da namiji, kayi min komai Babu abinda zance maka sai godiya, idan Allah yasa na tashi falillahil hamdu idan Kuma lokacin komawar yayi to muna rokon Allah yasa mu cika da imani, ga Zainabu Nan Dan Allah a kula da ita, ga Kuma makaranta Nan Daman yanzu ni suna ne kawai na me makaranta, Amma kune ke dawainiya da ita, to kada a kasa ko bayan Mana Nan bamu San abinda ubangiji ke nufi da kawoka gurinmu ba shiya barwa Kansa sani, a kula da ibada da Kuma riko da gaskiya, Mai gaskiya baya tab'ewa kayi duk Mai yuwuwa ka koma mahaifarka Dan girman Allah a rage fushi kaji mahmud bashi da kyau ko alama ka Zama Mai yafiya kaima Allah ya yqfe maka kaji, Nima ka yafe min Zaman da mukayi Kona saba maka, Kuma ka rokarmin sauran jama'ar da muka zauna dasu Suma a fada musu na yafewa kowa Nima su yafe min, Abu na karshen da Zan fada maka ga yarinyar nan kaji tsoron Allah a Cikin lamarin ta nasha yin istikhara Ina ganinka a Cikin wata irin wadata Wadda na kan samu kaina da tunanin abun to duk yanda rayuwa ta juya ka kula da Amana ta Fadima marainiyar Allah ce". Tunda Baba malam ya Fara Masa wannan magqngaun masu Kama da wasiyya jikinsa ke tsuma daga ciki Yana ta faman rokon Allah akan ya rufa Masa asiri kada bawan Allahn nan aikin ya Zama sanadinsa. "Idon jajur da gani kukan zuci yake ya Kara rike hannun Malam. "Baba in Sha Allah lafiya za'ayi aikin nan a Gama Kuma ka warke in Sha Allah saika taka da kafarka ka zagaya Asibitin Nan Alfarmar Manzon Allah s.a.w.w, Allah ya baka lafiya yasa kaffara ne ya bada nasarar aikin da za'ayi, ai sunce babu wata matsala Mai yawa dama mun zauna a Nigeria anyi aikin". Kafin Baba malam ya fadi abinda yayi niyya ma'aikatan da zasu tafi dashi sun shigo da gadon da zasu tura shi zuwa theater room din, lokacin da zasu canza Masa gado ya ringa fadin. "Wash!!! Allah kuyi a hankali bayana bana son ana motsani" . Da sauri Mahmud ya karaso Yana musu magana da yarensu, da sauri suka mayar dashi suka fita. Sannu kawai mahmud ke jerawa Baba malam Nan da Nan jibi ya rufe shi. Kusan mutum bakwai suka shigo suka hadu aka Dora shi a gadon sannan suka tura shi a hankali suka fice daga dakin mahmud na biye dasu, har kofar karshe mahmud ya raka baba Malam Bai tsaya ba saboda dauriya kawai yakeyi Amma Yana Daf da zubar da hawaye.

Guri ya nema ya zauna Yana kallon yanda manyan doctors manya da kananu suke Kai kawo kafin time ya cika suka rufe kofar. Yana Nan zaune har kusan one hour sannan Kiran Habib ya shigo Masa. Cikin dari dari Habib ya Fara fadin. "Yallabai ya maganar zuwa Asibitin ne munji shiru baka fito ba tun bayan da muka dawo daga sallar Asuba". Tsaki mahmud yayi dama duk ransa ba dadi ga wani sabon salon da Habib ta tarka Wai yallabai. "Wallahi ka Kara kirana da wani yallabai sai munyi uwar watsi a kasar nan da Kai,ba dai ba barci kuzoyi ba sai kuyi tayi, yanzu Baba malam ya samu good one hour a dakin tiyata, zaka wani ce min maganar Asibiti,kaima wallahi inaga saina kaika Inda zaka Kwana a tsaye kana aiki ko Abinci sai dai kaci a tsaitsaye sannan zaka fashinci namiji Allah yayi ka, ka fadawa dayan ya kawo ku yanzu Ni tun shida Ina nan". Ya yanke Kiran ya dafe goshinsa da yake Sara Masa.

* *

Karfe bakwai da rabi dai dai Mai a dai daita ya sauke Salma a kofar katafaren gate din gidansu,kudin dake hannunta ta Mika Masa ta wuce da sauri ta shige ciki, ba kowa a harabar gidan ko Mai gadi ma ya shiga sallar insha'i. Wuf tayi ta shige part din Mama cikin sa'a babu kowa a cikin parlourn directly master bedroom dinta ta wuce, can ta hango Mama ta Zuba tagumi tana zaune duk tayi zumu ba wannan gayun da kwalisa, tunda ta rasa tudun dafawa a Kan sakon da za'a kaiwa Zahra ta shiga halin ha'ula'i tunda Saida aka gindaya mata sharadi ta amince gashi kuma kwabarta na neman yin Ruwa. Ganin shigowar Salma ko sallama babu yasa Mama ta wani zabura ta taso tana fadin. " Ke!!! Salma lafiya? Daga Ina kike da wannan tsohon daren? Ina Hameeda Kuma?". Zama tayi a gefen gado tana sadda Kai kasa tayi shiru. "Wai ba magana nake Miki ba Dan ubanki kin mayar Dani banza". Kuka ta fasa Mata Mai cin Rai, Wanda ya firgita 'yar sauran nutsuwar Mama. *AUREN HUCE HAUSHI*

Naman Fateemah

Page 66.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull