Kenza eBookz

Auren huce haushi complete - Chapter 69

Auren huce haushi complete - Chapter 69

Auren huce haushi complete Chapter 69: Auren huce haushi complete Chapter 69. A cikin sati daya Zahra da Mahmud sunyi wata irin shak'uwa ta ban mamaki,Dan…

4,336 words

A cikin sati daya Zahra da Mahmud sunyi wata irin shak'uwa ta ban mamaki,Dan Daya ji yake baze iya rayuwa ba Saida dayan Zahra ta Zama 'yar gari sai tsula shagwaba take Masa shi Kuma duk ya susuce a kanta, ga wani irin fresh da sukayi dan dole idan ka kallesu ka kara, Saida hankalinsa ya nutsu sannan ya zauna dasu Salis da Bashir ya nemi shawararsu akan idan suna ra'ayin aiki dashi to suyi Shawara da gida akan Nan gida suke son Zama suyi aikin ko a waje sannan ya bawa kowa gida a acan Azaren Saida ya fada musu inda gidajen suke Salis yayi murmushi Shima Mahmud din yayi wani Abu suka tuna, lokacin da Mahmud yaja Salis din sukaje ana yiwa gidajen pop Salis ke tambayar ko gidan waye haka sai Mahmud din ke fadin na wani abokin Sameer ne yasa shi ya dube Masa har yake cewa Salis din ko gidan ya burgeka ne Naga kamar kana sonsa? Dariya lokacin Salis din yayi Yana fadin wa zeba Dan rogo rumfa? ai irin wannan gidajen sai wadanda sukaci suka tada Kai. Dariya kawai lokacin Mahmud yayi baice komai ba kawai dai yace Masa ya Taya shi a duba abinda baiyi ba Mai gidan ne yace ayi hakan Nan Salis din ya zage Yana ta fadin Nan kaza ya kamata ayi nan ayi kaza haka suka zagaye gidan har suka Gama bada gyaran, haka suka shiga dayan ma aka rubuta komai, to sai yanzu da yake fadar inda gidajen suka Salis ta tuna da abun, sunyi godiya kamar su Ari Baki Dan Dadi Bashir baisan lokacin da hawaye ya zubo masa sai gani sukayi Yana share hawaye, saboda Tunda ya Gama Karatu Bai Sami aiki ba gashi Dan Mai karamin karfi kullum Yana yawo neman aiki sauda yawa Mahmud Kan fada Masa yayi hakuri da lokaci, in dai aiki ne Saiya zab'a, a lokacin jinsa kawai yake Ashe da gaske yakeyi saiya zaba din tunda gashi ya Basu options na zabar Ina suke da muradin yin aikin. Dariya sosai Mahmud ya ringa yiwa Bashir ganin yanda yake shafe Ido kamar Mace. "Haba bash meye haka be strong mana Dan Allah, kuka kuma? To in banyi muku ba suwaye Zan yiwa kun riqeni Amana lokacin da bakusan daga wace duniyar nake ba, kun ciyar Dani kun dinka mun suturar sakawa, kun bani kudin da kuka nema da karfin jikinku, kun tsaya a gurin jinyata lokacin dasu Habib ke yinta ga abin Hawa an sakar min babu shamaki duk inda zani, an bani Mata kunyi uwa kunyi makarbiya gurin hidima da jikinku da aljihunku to ni kuwa ai bani da abinda Zan biyaku dashi sai dai nace Ubangiji ya biyaku da madaukaliyar Aljanna wallahi tuni na cireku daga abokai kun zamar min 'yan uwa yanzu ga wannan" ya mikawa Bashir Daya fi kusanci dashi E.passport ne yace su saurari visa Sameer ze kawo musu ta umarar Azumin nan Mai kusantowa, yace Kuma kowa ya duba akwai sako a wayarsa, sunyi tsaraba ya Kuma fada musu tickets dinsu na zuwa Bauchi Yana hannun Sameer, bakin godiyar ma rasawa sukayi Dan wata kyautar tafi gaban godiya, Dan ya gigita musu lissafi ba Dan kadan ba. Sameer ne ya shigo da sallama lokacin kwanansa biyu da dawowa daga Egypt gurinsu Mama Dan Saida akayi Mata aiki sannan ya juyo ya barosu a can, Mama tayi kuka tayi kuka akan wautar datayi a baya na nuna hassada da ganin kyashin yarinya marainiyar Allah wadda aka mutu aka Bari ko kanta Bata sani ba Amma shedan yayi Mata katutu a zuciya ta dunga kulle-kullen mugun Abu Tunda masu dubanta suka barbasa Mata yarinyar tana tare da wata irin sa'ar rayuwa duk sai ta rude tana ganin ta Yaya hakan ze faru gata Mai kyau na ban mamaki sannan ace sa'arma tatace tun daga lokacin zuciyarta Bata huta ba, to gashi Alkawarin Allah ya tabbata gata a gadon asibiti a wata k'asar tare da ciwon zuciya Wanda bakin ciki da hassada sukayi sanadinsa, ga Kuma wadda take abun a kanta taje inda Ubangiji ya nufa taje din,tunda Alkawarin Allah baya tashi ga shi Kuma mijin da taketa kangewa kada yazo gurinta shine ya Zama silar samun waraka ga ciwonta, ga mijinta Tunda sukazo bai Kira ba ya bawa banza ajiyarta Bata Kara Jin ko duriyarsa ba tun lokacin da yaje sokoto tana barcin Allura batasan yaje ba,yau ga dan 'yar uwarta Mai ingizata tayi komai Dan Hana Allah ikonsa itace Dan cikinta ya yiwa yarinyar ta cikin shege. Da kukanta share-share ta ringa fadawa Sameer ya nemar Mata yafiyar Zahra akan abubuwan data yi Mata. Kusa da Salis sameer ya zauna ya gaishe da Mahmud sannan suka gaisa dasu Salis din, sannan ya dauko musu tickets dinsu na jirgin Sha biyu da rabi na Rana, godiyar dai suka Kara yi musu har Mahmud na fadin "wallahi idan ya Kara Jin godiyar na zasu bata.

**

Ranar da suka cika kwana goma sha biyu Mahmud tun dare ya fadawa Zahra ta shirya da safe ze kaita gidan Ammi shi kuma zeje Lagos wani aiki, Bai barta tayi barcin kirki ba a Daren,dan daga baya ma cewa yayi ta shirya ta raka shi suje su wuni su dawo, da kyar ta samu ta lallabashi da kalamai sannan ya hakura Amma Saida ya Kara rage tafi. Tun asuba zahra ta Kira Aunty zilai suka Fara aikin dabun kaji dasu cake sai da sauran tarkacen snacks Tunda su duka gwanayene kafin takwas da rabi sun Gama hada har breakfast, sama Zahra ta koma lokacin Mahmud ma ya farka Dan nine thirty flight dinsu ze tashi daga sokoto zuwa Lagos. Tare suka fito sukayi break sannan yace ta dauko gyalenta su tafi ya ajeta ya wuce, fada Masa tayi tare zasu tafi dasu Aunty zilai, waya ya yiwa zayyan ya saka wani ya kaisu Aunty zilai can family house nasu, lokacin da akace su fito sai gani yayi ana ta fitowa da manyan warmers ana sakawa a boot din mota, Bai nemi Jin abasin menene ba itama Bata fada masa ba. Su suka Fara yin gaba sannan suma suka fice daga gidan, sunzo wucewa ta kofar gidansu Dr Haseenah ya Dan shafo cinyarta, tsuke fuska tayi tasan abinda yake nufi. "Komu shiga ku gaisa tana garin har yanzu Tunda Nima Ina garin kinsan lokacin da Ina Nan ai a Nan take aiki Saida nabar garin ta koma Kano da aiki Tunda daman a kanon aka riketa kuma masu fada aji ne, jiya da har zatazo ku gaisa sai tace sauri takeyi gurina kawai tazo wani lokacin ida ta dawo ta shigo ku gaisa". Hade Rai tayi ta hade gabas da yamma tayi kicin-kicin duk yanda yaso ta kulashi tayi banza dashi har sukaje gidan. Abbie baya k'asar yaje Benin republic akan wasu Kaya nasa da aka rike a can. Direct part din Ammi suka nufa duk yanda yaso ta saki ranta abun ya faskara Dan da gaske ya Bata Mata rai ita fa ta tsani matar Nan ba kadan ba shi Kuma ya kasa ganewa. Yana tsayawa tayi wuf ta fice Bata tsaya ya fito ba ta wuce Abinta tana ayyana itama ai Amminta ce bazata tsaya shi ba,Amma kafin takai ga kofar parlourn ya cimmata. "Ke meya faru Wai kike ta hade min Rai haka?".kauda Kai tayi tana jin zuciyar na Mata zafi. Janyota yayi ya rungumeta a Nan da sauri ta dago tana rarraba idanu. "Dan Allah ka sakeni kada wani yazo ya ganmu a haka wallahi ba komai,Dan Allah ka Bari kada ace bamu da kunya plssss...." "Baki San anyi min tambarinta ba a gidan Nan wannan ai ba wani Abu bane,nida kace nayi abun a gidan Nan ko kin manta?". "Ai sharri ne wancen, wannan Kuma gamu in reality ne". "To shine me? Ai ba haram bane ko.....," Bai karasa ba yaji alamun za'a bude kofar da sauri ya saketa Dan bazeso kannensa ko Ammi su gansu a haka ba,ko maid din Ammin sai girma ya Fadi. Sahalatu ce 'yar Babban yayansu Abdallah da Afnan da hannunta suka fito, ai yarinyar na ganin Zahra ta Fara zillo tana dariya, itama zahrar dariya tayi Mata ta nufesu da sauri ta karbeta daga hannun sahalatun tayi wuf ta shige tana amsa gaisawar yarinyar. Ammi ce dasu Aunty Aishat a parlourn farkon sai Aunty zilai daga gefe a zaune bintar dai Bata gurin Zahra batayi mamaki ba Tunda ita 'yar gida ce, gaba Daya suka amsa sallamarta cikin nutsuwa Zahra ta karasa kusa da Ammin ta tsuguna har kasa tace "Ammy Ina kwana?". Ammi wadda bakinta yaki rufuwa saboda farin ciki ta amsa Mata "Lafiya kalau Zahra ya gidan naku?". A kunyace ta amsa "lafiya kalau Ammy". Ammin sai hamdala take yiwa Allah Daya azurta danta da irin wannan matar, a Nan Kan carpet ta zauna duk yanda Ammi tayi akan ta tashi ta zauna kiyawa tayi sai hakuri Ammin tayi. Zahra tayi mamakin Ina Kuma ya tsaya Bai shigo ba? Saida ta Jima da Zama sannan ya shigo ta baya Yana amsa waya taji Yana fadin "ka sayi ticket din online yanzu" Tunda ya shigo Ammin taga ya wani Kara girma da haske ga cikar Kamala da taga yayi da gani ya samu kwanciyar hankali. Kusa da Ammin ya zauna Yana gaisheta suka gaisa da Aishat wannan su batool suka gaishe shi, tashi su batool sukayi suka koma wani falon Aunty zilai ma kitchen ta nufa Tunda ta Saba tana Taya masu aikin aiki a Dan zaman da tayi kafin ta koma gidan Zahra. Parlourn ya rage daga Ammi da Yan biyunta sai Zahra da Afnan hira suka Fara a junan su Zahra na Zaune tana yiwa Afnan wasa, hira Mahmud yakeyi Amma 100% hankalinsa na Kan Zahra har dai Aishat ta gaji ta jefa masa tambayar data bashi mamaki. "Waini bros ko dai laifi kayiwa madam ne Naga ka kasa nutsuwa sai kafeta da Ido kakeyi irin na neman sulhu din Nan". Dan murmushi yayi Yana Dan shafa gefen sajen fuskarsa. "Ko Daya kawai burguni sukayi ita da Afnan yanda suke kaunar juna tamkar sun shekara da sanin juna, ki karbeta ma tafiya zamuyi". A tare Zahra da Aunty Aishat suka kalleshi Bai kalli zahrar ba Aishat ya bawa attention dinsa .. "Zuwa Ina kuma mobile?". "Lagos zamu". Ai Zahra Bata San lokacin da bakinta ya subuce ba tace. "Kaiiii..meu amor bafa haka mukayi da kaiba, kace fa wuni zamuyi a Nan Kuma yanzu zaka ce wai tare zamu Dan Allah ka barni na zauna a Nan din plssss...." Saida ta Kai Aya ta Farga da inda suke sauri tayi ya rufe fuska da gyalen dake jikinta. Yau taga ta kanta ita wace iriya ce. Dan murmushi Ammi tayi kawai tasan da wata a kasa saita basar Aishat ce ta shiga maganar "a'a kuyi tafiyarku kawai ba wani wunin da zakiyi Tunda kukazo kafa ya kafa ai nasan tafiyarku Daya idan yayi niyyar ki wunin ai ke kadai zakizo amma fa su binta suka Fara zuwa". Sai lokacin Ammi ta tuna an kawo musu abubuwa ganinsu ya shagaltar da ita. "Zahra munga sako fa. Allah ya saka da Alkhairi mun gode kwarai da gaske". "Meta kawo ne haka Ammi?". "Ina ruwanka ku tashi ku tafi kada kuyi missing flight". Narai narai Zahra tayi da fuska kamar zatayi kuka. "Tashi kuje kinji Tunda haka yakeso Allah ya tsare gobe ma Rana ce sai kizo ki wunar min din kinji". A kunya ce ta tashi tana fadin " To Ammy nagode mun tafi sai mun dawo". Har gurin mota Aishat ta takasu tana mitar Bai Bari zahrar ta shiga sauran parts din gidan ba. "Bari kawai da anan zata wuni sai Kuma ta nemi ta hanani sakat idan na tafi ma babu nutsuwa Dan yanzu ta birkice min a hanya ai gara muje tayi min bayanin abunda nayi Mata, idan tana Nan ai wallahi aiki baze yuwu ba zuwan banza zanyi, nifa Naga alama sai yanda Hali yayi Dan yarinyar Nan..., Ki bari kawai sai mun zauna". Hannu Zahra tasa ta dafe kirjinta, tana mamakin furucinsa. "Wallahi Aunty fada kawai yake ni babu Abinda nayi masa kawai dai bana son Yana min maganar wannan doctor din shi Kuma Koda yaushe sai ya yi ta yi min maganarta ni Kuma banaso". "A'a gaskiya tayi ma hakuri idan nice saina maka yaji wallahi kawai ka tasani gaba kana min zancen wata ai baka taki gaskiya ba" ."Hummm kinsan abinda yarinyar nan tace Mata Ranar dana nuna Mata sabon gidansu?".. Girgiza Kai tayi alamar a'a. "Cewa fa tayi Wai mace ba gaba ba baya" Aishat Bata San lokacin data fashe da dariya ba. "Well done, wallahi ba karya tayi ba to Kai karya ta fada?".Kiran wayar da akayi masa ya katse maganar da sukeyi. Abinda aka fada masa yasa yayi saurin duba agogon dake daure a hannunsa. "Bari mu wuce lokaci yaja kada muyi late". Karfe Sha daya har sun karasa gidansa na Lagos Tunda tsakanin gidan da airport din babu nisa sosai nan ma Aljannar duniya ce dan Sai taga kamar yafi kowane gida kyau ma, dan daya wuce wurin meeting kasa Zama tayi a kowane parlour, bedroom ta koma ta rufe kanta dan abin yafi karfin tunaninta, to Dan Allah shi wace irin dukiya ya mallaka haka da kananun shekaru irin nasa? ita fa tana Jin tsoron irin wannan dukiyar a gurin matashi kamarsa gaskiya. AUREN HUCE HAUSHI. Maman Fateemah

09062432330 08055362975

Page 96

________Karfe shida da kwata su Mahmud suka shigo gidan shida Sameer da zayyan dake driving dinsu, Basu tab'a tunanin zasu Kai wannan lokacin ba a gurin meeting din, suna cikin meeting ne kiran gaggawa ya shigowa sameer injinan sabon kamfanin hada Madarar gari da 'yar Amana condensed milk suka karaso Wanda za'a bude a Azare,tunda tuni an Gama ginin gurin, to dole suka nufi deport can tincan island, Saida sukayi clearing din komai suka baro gurin, sai Kuma goslow ya rikesu. Mahmud na sauka Shima Sameer ya sauko zayyan ya wuce da motar ma'adanar aje motoci, ciki suka shiga shi Kuma zayyan ya wuce nasa masaukin dake wani bangare na gidan. Shiru parlours din duka babu alamar dake nuna da mace a gidan Dan da alama ko abincin dake saman table ba'a tab'a ba, jakar laptop dinsa Sameer ya aje Yana fadin."Bari naje ba watsa ruwa naji Kiran da madam ke jera min lokacin muna meeting kasanta Bata da hakuri yanzu haka danta ne yake Zazzabi Dan dazu da safe take fada min wai taji jikinsa da dumi ga Kuma mura". Kallo daya Mahmud yayi Masa Mai nuna alamar baka da hankali. "Meya faru kuma?". Coat dinsa ya cire ya nufi ciki ba tare Daya tanka Masa ba, Dan murmushi Sameer yayi yasan halinsa na son Yara da tattalin mace wato yayi laifa kenan. Shima juyawa yayi ya fice Yana ayyana idan oga yayi nasa yaran ko Yaya, yasan dole ya Basu kulawa fiye da tunaninsu dan Sam baya Wasa da Lamarin Yara Allah ya jarabce shi da son Yara matuk'a. A kalla Saida ya shige parlours biyar sannan ya haura steps ya shiga corridor Wanda aka kawata shi da wani irin mirror Mai shegen kyau irin Wanda ake ajewa din Nan a corridor,bedrooms hudu ne biyu na facing din biyu, Wanda ya barta a ciki ya nufa, ya gaji iya gajiya, Kati ya saka ya bude kofar, can karshen gado ya ganta a takure kamar Mai barci, da sauri ya karasa Yana fadin. "Menene precious?". Shiru tayi Masa Dan yau dai tayi dana sanin biyo shi Lagos yafi sau shurin masaki, Dan wuni tayi da yunwa ga fridge din dakin ruwa roba biyu ne kawai a ciki sai tarin lemukan gwangwani irinsu Pepsi da Coke ita Kuma ba kukanta Nan ba. Zama yayi kusa da ita Yana dago da fuskarta, ba zato yaga ruwan hawaye suna bin Kumatunta. "Subhanallahi! Previous meya faru?pls fada mini, baki da lafiya? Me yasa Ina ta kiranki Baki daga ba?". Babu amsa Daya data iya bashi sai kwantar da kanta tayi a jikin gwiwuyinta. "Ya subhanallah! Wai fushin ne har yanzu ba'a huce ba? Kiyi min magana Dan Allah kada ki sakani a damuwa mana, to Bari na Kira Miki Ammi ko Ammah wata qila su ki fada musu Abinda yake damunki". Ya fada Yana kokarin Kiran wayar. Da sauri ta karbe wayar tana fad'in. "Ni wallahi tsoron gidan nakeyi tunda ka tafi ko kofar dakin Nan kasa fita nayi Ni dai ka mayar Dani sokoton gara can da nan, kace wuni Daya zamuyi gashi har dare ya kawo jiki muna garin babu alamar tafiya, Kuma nifa gaskiya hankalina ya kasa kwanciya da abubuwan da nake gani a tare da Kai,Wai kana nufin wannan mahaukacin gidan ma naka ne, idan haka ne to sai dai idan kana da wata sana'ar a boye wadda ba kowa ne ya sani ba" . Mahmud tsayawa kawai yayi Yana kallonta, bil haqqi da iya gaskiyarta take maganar, tsura Mata idunusa yayi Yana Kara nazarinta, yama rasa Abinda ze ce mata. Saida ya hadiye wani busashshen yawu Daya kalato daga bakinsa ya hadiye sannan ya Sami zarafin yi Mata magana. "Kice ko abinci Baki fita kinci ba kenan? To me kike tsoro a gidan Nan Dan Allah? Gida da jama'a a kalla sun Mutum talatin Amma Kika takure kanki? Na fada Miki yanzu ma Zan Kara fada wallahi babu Abinda ze sameki sai ikon Allah Amma Dan mutumci dai Kam kafin ya cimmiki ya Kai kasa da karfin Allah,wayarawa an zo a duba min ke ance bakya Nan a duk parlours din gidan, sera tace Sam throughout Bataga ko gilmawarki ba,na shigo Mai makon special we'll come sai bacin Rai harda hawaye ga zirgina da kika Bari shedan ya sauwala Miki a zuciya, kina zargin ko Ina kauce hanyar Allah a gurin nema na ko? To Bari nayi sallah na dawo nayi Miki Abinda Ina ganin kamar ze gamsar dake". Ya tashi tsam ya wuce toilet ya barta tana shefe hawaye. A gurguje yayi wanka ya fito baibi ta kanta ba ya Dan shafa lotion ya zura jallabiya ya baza turarensa ya wuce masallaci. Itama shiga tayi tayo Alwalarta Bata bukatar wanka Dan wurin biyar da rabi tayi nata da taji wani Abu Yana fita daga jikinta, ita abun harya Fara damunta ita kadai sai tayi ta mutsu mutsu. Bai shigo ba sai kusan takwas da kwata Dan harta kwanta suna chart da sajida da Amatu a group da suka hada mujiba ce Bata online sai Dan biki suke mata data fada musu suna Lagos, Dan caaa sukayi Mata suna fad'in lallai a samu musu Dan Legos ladar meeting. Kusa da ita ya zauna Yana Dan leken wayar boyewa tayi. "Inyeh kice na zage dantse kenan, da Ina Shirin mubi flight din seven thirty,kice na fasa booking din mu kwankwaje a nan tunda bestie ta zabar Mana nan'. Shiru tayi masa kamar kurma. "Ke! Wai Dan Allah me nayi da zafi haka ne? Ki rufa min asiri kada na kasa gane komai, wallahi kinji na rantse Miki duk abinda Kika gani da Wanda Baki gani ba duk halaliyata ne idan Ina wata sana'ar da take haramtacciya ko Ina wani Abu daya sabawa shari'a Ubangiji ya....... Da wani irin hanzari ta toshe bakinsa da tattaussan tafin hannunta tana girgiza Masa Kai, idanunta sun cicciko da hawaye. "Wallahi ba Ina zargin kana sabawa Ubangiji bane kawai abun ne Yana bani tsoro, naganka yaro da Kai Amma ka mallaki Abinda yafi karfin tunanin mai karamar brain irin tawa, amma kayi hakuri bazan sake maka tambaya irin wannan ba Naga kana niyyar debo rantsuwa kawai Dan kaga Ina fushi,na fa maganar Dr din Nan ce banaso, Allah da gaske bana sonta har zuciyatw wallahi". "Sorry my previous na daina har abada kada ayi min tawaye a gudu Jordan kamar yanda akayi niyya a can baya saboda ita, da yake Allah ya tarfawa garina nono yasa a ranar naji kamar ana ingizoni na taho da yake Allah Alhakimu ne Saida aka nemo min ke da tsohon dare danma a lokacin ba wani caring kawai dai gani Nan ana kallona Ina ragaita ba'a nunawa kurciya baka ba, tashi muje ki Samar min Abinda Zan saka a bakin salatina kafin nayi aikin bada hakuri kada ayi min nak'i". Ya fada yana dariyar Nan tasa Mai sakata shagala da kallonsa.

Itama dariyar tayi tana kokarin tashi tana fad'in "yau dai anyi abun kirki babu 'yan.." Bata karasa tunanin ba taji saukar hannunsa a jikinta, Batasan lokacin Daya furta "Ashe ba'a yabon dan kuturu Saiya shekara da yatsu". "Gaskiya Kam ai kena gani kamar kina bukata ta a kusa dake ko ba haka bane?". Shiru tayi Masa idan ta biye Masa zeta Bata kunys ne kawai, ta rasa ta Ina ma ya ganota. Basar da maganarsa tayi. "Tashi muje kaci abincin kaji meu Amor,.nasan kana Jin yunwa ko?. "A'a muci dai kema ai bakici ba, tun break din safe". Tare suka fito Yana manne da ita. "Wai me kike tsoro a gidan nifa tsoron Nan naki Yana damuna kinga duk gidajen ki haka suke sai dai idan abokiyar Zama kikeso to wannan fa sai ta ringa debe Miki kewa yanda zakuna Jin motsin juna ai hakan yayi Miki ko?". Da sauri ya raba jikinta da bass kamar wadda huta ta yiwa shocking. "Kishiya Kuma? Har ka gaji Dani Nan da Nan haka? Daman abunda kake fada min ba gaske bane harka Gama Dani Kuma sai wata? Na shiga Tara, Dan Allah Dame na kasa maka ko ba irin type din da kakeso nake ba".. Sai hawaye sharrrr..... "Ya salam.! Previous meya hau kanki ne Wai tsakanin jiya da yau? Wace iriyar magana ce wannan marar dadin saurare, kece na gaji dake? koko ba irin type din da nakeso ba? Wallahil Azim ban tab'a son wata mace ba kamarki tunda Allah ya halicceni idan Kika cire uwata to ba'ayi ba Kuma Ina ganin har abada babu wata mace da zata samu matsayi irin naki a wannan zuciyar, kin Dade da mamayeta tun ban gama Zama mutum cikakke ba, maganar type Kuma ai ni har kin wuce sanina wato so kike na nuna Miki true colour dina a wannan fannin ko? Naga alama kema jirgi Daya ya dauko mu, Bari ki bani abinci mu gani daga Nan zuwa asuba ko mun Kai ga inda muka dosa inaga da tsarabar Lagos zamu koma SKT, da alamar ma Nan gaba kadan saina Fara service gaskiya". Sunne Kai tayi a kirjinsa tana fad'in a'a wallahi bada fa wani Abu na fada ba cewa fa kayi Wai zaka kawo abokiyar Zama ai kowa yaji yasan banyi maka dai dai bane shi yasa zaka karo Aure". "Ya salam! Previous yaushe Mika zama haka Dan Allah? To Bari na fada Miki kinyi min fiye da tunaninki wato Naga kin Zama sai a hankali ko? Kada fa na Fara guduwa da kafata kisa ace min ragon miji".

******Tunda su Ammah suka tafi Salma ke aikin kuka, bakin ciki goma da ashirin gana wannan wulakantaccen Auren gana Makarram ga Kuma uwarta Mai daure mata kugun itama tana wata uwa duniya da tata lalurar,ga mijin da aka Bata Wanda ta rainawa ajawalin shima ko kyeyarsa ma bataci arzikin gani ba har karfe Daya na dare ga unguwar irin sabuwar Nan ce wadda Bata da cikowar mutane, barci dai sai barawo Dan sai ana Kiran sallar asuba ta farka, haka ta wayi gari kamar mayya ita kadai a gida, sai wurin takwas taji ana buga gate din gidan da farko banza tayi Saida taji bugun Yana damunta sannan ta fito sai lokacin taga yanda gidan yake Dan Sam Bata fito ba, Data bude daga cikin kannensa ce mata, ba laifi ita da sauki Bata da halin sauran, murmushi ta yiwa Salma itama murmushin ta mayar Mata duk da zuciyar ta babu Dadi. "Sannu da zuwa". Salma ta fada tana Bata hanyar shiga. "Yauwa sannu Aunty salma". Kofar Salma ta rufe suka juyo cikin gidan ba laifi ya tsaru dai dai misali self content ne sai wani Dan karamin part Kamar boys quater. Basket din hannunta ta aje ta zauna tana fad'in ga abincin break Nan inji Umma tace a gaisheki Kuma kada kiga Ya Anas baizo ba Aunty Bara'atu ce bata da lafiya tunda aka fada Mata Ya Anas din yayi Aure ta Kama Aljanu a kanta aka kwana yanzu ma zasu tafi gumau can Toro local government gurin mai Magani ance dai ko kwana akeyi a can din yace dai sai sun dawo ze shigo Nan gurinki yace na zauna na tayaki Zama zuwa dare". Tunda Hafsa ta Fara rattabo Mata bayani taking wani tashin hankali ya rufeta sai gumin goshi takeyi, wulakanci dai ta tabbata a Nan ya Gama nunawa duniya ita ba komai bace ita da banza duk daya, Bata tab'a Jin tayi nadama ba sai yau, duniya tayi Mata juyin waina, ba haka ta shiryawa rayuwa ba taci buri kala-kala amma karshe ga yanda ta kare, Nan da Nan taji idanunta sun cicciko da hawaye Bata damu ba da Hafsa da take Zaune kuka ta fashe dashi tamkar wadda aka aikowa da sakon mutuwa, bare data tuna hotunan da magaji da mujiba suka Dora na bikin Zahra da irin gidajen da taga ana sabgar a ciki da Kuma gidan da majiba ta Dora hutunansu tana gani tasan shine gidan Zahra Dan taga magaji ma yayi hotuna a cikinsa. Hakuri Hafsa da dinga bawa salma Dan ko ita abun yayi touching din ta Dan ance ciwon 'ya mace na 'ya mace ne. Abincin dai kasa cinsa tayi Dan dankalin Hausa ne sai kunun tsamiya da jallof din taliya, abunci dai gashi nan tasan da gangan akayi Mata shi Dan kada ace ba'a kawo Mata ba. Har dare ya kawo jiki ba Ango ba labarinsa ko Kiran wayarsa babu, Amma dai zuwan Hafsa sai yasa Salma ta Dan ware suna Hira da Hafsa din tare suka dafa abincin Rana tunda babu Abinda Abba baisa anyi Mata ba haka Ammah ma tayi nmijin kokarin hada Mata duk Abinda uwa takeyi, ganin dare ta Fara yasa Hafsa tafiya a tabar salma ita kadai.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull