Auren katin kasa complete - Chapter 1
Auren katin kasa complete Chapter 1: Auren katin kasa complete Chapter 1. ✍️✨***Auren Katin Kasa ***✨✍️ (Unexpectedly falling❤️🇦🇪)
4,360 words
✍️✨***Auren Katin Kasa ***✨✍️ (Unexpectedly falling❤️🇦🇪)
Story and written by: QueenMarh👸🏼
Paid book 📚
Chapter46-47
Washe gari Sunday salima na zaune itada salim suna ninke kayan su da suka wanke saiga ya Ibrahim kamar an wulloshi, yana sanye da riga da gajeran wanda da dan iskan askin nan nashi, kallonshi sukayi gaba dayan su kafin su gaishesa ''ina wuni yaya?'' …baiko amsa masu ba ya kalli salim yace ''kai fita anan''.. sum sum salim ya fuce shikuma Ibrahim ya juyo yana kallon salima sannan yace ''ke wato karamar mara kunya ce ko, nasan abinda kikayi jiya'', dam kirjin salima yayi, anatse ta tattaro jarumtar ta tace ''me nayi yaya?" dariya Ibrahim yayi sannan yace ''dan ubanki kinsan me kikayi, basai na fada maki ba, yanxu dai akwai abinda zan sakaki idan har kika bujire min to zan tona maki asiri kuma wallahi daddy cin ubanki zaiyi bama shi kadai ba harda mummy dani ma''… salima kam ido ya raina fata hankali atashe tace ''mey zan makan?''.. dariya yayi irin ta yan manyan yan iska sannan ya fara lashe bakinsa daman tun bayan ya dawo ya fara kwadaituwa da ita dukda yaga babu wani abun arziki ajikin ta amma zatayi zaqi sosai, gyara tsayuwa yayi sannan yace ''kizo dakina da karfe goma akwai abinda zan fada min akan abinda zakiyi min, and Idon har kikaqi zuwa tofa kisan cewa watan cin ubanki ya kama'' yana kaiwa nan ya fuce kamar iska, …da kyar ta iya zama gefen gadonsu hankalinta atashe, wannan wace irin masifa ce, itafa duk wani abu da zai sanya ta Magana da ya Ibrahim ma bata so, haka dai ta cigaba da ninke kayansu duk babu nutsuwa a tattare da ita, bayan sallar magrib kuwa abinci ma gagarar zama abakinta yayi, tunani kawai take idon taje tasan babu arziki idan ta zauna ma cin ubanta zasuyi, haka yasa ta yanke zuwa kawai taji mai zaice mata.
Karfe goma daidai ta zumbula shirgegen hijabin ta sannan ta kalli salim wanda bacci har ya daukeshi, bargo ta jawo mashi sannan ta gyara mashi kwanciyarsa ta fuce, lokacin data hau stairs har an kashe fitilun wajen, anatse ta lallaba ta tsaya daidai part dinshi, tana zuwa gaban kofar ta saita natsuwarta sannan ta kwankwasa kofar, bata karasa kwan kwasawa ba ya bude kofar, kallonshi tayi , yana sanye da towel fari ah qugunshi, matsawa yayi donta ta wuce ciki sannan ya rufo kofar, tunda ta shiga gabanta yake faduwa, warin taba duk ya cika dakin, kallonta yayi sannan yace ''wuce muje mana'', anatse tadanyi taku biyu sannan ta tsaya, shiko zama yayi har gaban gadonshi sannan ya kalleta ''ke ki saki jikinki fa, zaki bani ne ni kuma na rufa maki asiri'' afurgice ta dago ta kalleshi sannan tace ''yaya ka fada min abinda kace zaka fada min dare nayi inason naje na kwanta sbd gobe Monday akwai school''…mikewa yayi yana cewa ''okay ashe har kin qagu sosai,'' yana kaiwa nan ya tsaya gabanta ya janyota gaba dayanta zuwa jikinshi, arazane ta Gwalo ido, ganin abinda yake shirin yi yasa ta saurin bude baki zatayi ihu , charap ya tsoma bakinshi cikin nata, lokaci guda ta rikice, yaqushi bugu babu wanda batayi mashi ba, shiko tsabar mugunta da karfi ya dunga fusgarta, farke hijab din jikinta yayi sannan ya tsagaita, tana dagowa kuwa ta wankeshi ta hannunta, dagowa yayi azafafe yace ''ke lallai yarinyar nan kina wasa da rayuwar ki, aiko yanxu zan nuna maki karfi'' haka ya dunga janta tana tirgewa, karshe dai harda duka, kuka ihu babu wanda salima batayi ba, ido rufe Ibrahim ya soma neman kece mata mutuncinta, saida ya rabata da komai ya danneta, anan kasa ganin babu sarki sai Allah kuma idan ta tsaya haka nan zai cuceta abanza yasa ta tattaro dan kuzarinta ta hankada shi gefe, ta fara Jan jiki tana neman hanyan fuce wa, tangal tangal yayi zai fadi ya dago ya kalle ta idonshi cike da masifa, da gudu ya biyota da kyar ta fara rarrafawa gaban kofar dakin ko kayan data shugo dashi bata bi ta kansu ba, ganin tana neman guduwa yasashi jawota da karfi ya dunga bugunta akan tiles, saida yayi mata jina jina sannan ya tsagaita ya fara kicinyar kwace towwl din jikinshi, gadan gadan yayo kanta, ahankali ta fara bude idanunta da suka kumbura tsabar bugu sannan ta yunkura, idonta ne ya fada kan wata kwalbar shisha agefe, da kyar ta rarumo kwalbar ta daddage yana karasowa ta kwada mashi akai, nan take ya fadi wanwas akasa, tana ganin haka ta zari hijab dinta daya farka mata shi ta sanya sannan ta fara kiciniyar bude kofa lokacin wajen karfe 12 saura,tana fitowa sukayi kicibus da hilma wanda ta tunkaro dakin nasa, ganin salima afurgice yasa ta kallonta zatayi Magana Kenan salima ta gifta ta gefenta ta wuce kasa da gudu, ganin haka yasa hilma wucewa cikin dakin tana bude kofar kuwa taci karo da ya Ibrahim akwance, kamar matacce hankali atashe ta karasa gabansaa tana kiran sa, amma ina ko motsi haka ya furgitar da ita, da sauri ta jawo towel dinshi ta daura mashi sannan ta fuce, direct dakin daddy ta wuce, lokacin yana zaune gaban wasu papers yana karantawa, jin knockin ya sashi cewa waye, jin muryar hilma ya sashi mikewa, ya kalli haj labiba wadda bacci ya dauketa sannan ya wuce bakin kofar yana bude wa ganinta afurgice ya soma Magana ''ke menene meya faru'', kyarma jikinta ya fara tana nuna dakin Ibrahim tace ''yaya…yaya yam utu ta kashe shi'' jin haka yasashi jawota sosai yace ''ke waye yamutu, waye wani yayan?'' hannunshi ta jawo har gaban daki Ibrahim, nan ya kutsa kai, ganin Ibrahim kwance ya sashi saurin karasawa sannan ya fara tattabashi, jin pulse dinshi kadan yasa shi saurin cewa ''dauko ruwa'' hankali atashe ta fita domin dauko ruwa nan tayi kicibus ta haj lalbiba mamanta, ''ke ina babanku, meya faru?" batako tsaya kallon mummyn nata ba ta wuce kitchen, ganin haka yasa labiba bin inda ta fito, tana shiga taga daddy zaune, ya daura Ibrahim akan cinyarshi, hannunshi har kyarma yake, yana ganinta ya soma ihu ''ina hilmar take ina ruwan ne''? da sauri hilma ta karaso ciki tace gashi na kawo, yayyafa mashi ruwan yayi kusan sau biyu jin shuru yasa hankalinshi tashi, qara zuba mashi yayi nan yayi wata doguwar ajiyar zuciya sannan ya fara bude idanunshi akan daddy, afurgice ya zauna yana kallonsu daya bayan daya… kallonshi dady yayi sannan yace ''ibrahim what's going on here, menene ya faru haka''?... shuru Ibrahim yayi yana tunanin mai zaice, don yasan yanzu idan ya fada masu to fa tashi ta kare don dady ya fada mashi karya sake ya kuma mu'amala da mata acikin gidan shi, ganin haka yasa hilma saurin cewa ''daddy salima ce, wallahi itace, akwai ranar da muna zaune ta samemu tace wallahi saita ga bayan kowa na gidan nan bama ni kadai ta fada ma haka ba ka tambayi khady itama ta taba fada mata shine tazo yaya yana bacci ta buga mashi abinnan'' jin irin karyar da hilma ta fado yasashi sauke ijiyar zuciya yace ''yes daddy haka ne, jiya na sakata gyara min daki tayi min rashin kunya shine na mareta, nan take tace wallahi saitaga bayana, dazu ina fitowa daga toilet ina cikin shirin bacci naji an bude daki na, na dauka mummy ce kawai saiji nayi an kwada min kwalba akaina'' yana kaiwa nan ya dafe kan nashi..jinjina kai daddy yayi sannan yace ''kuje ku kwanta zamuyi maganan gobe'' anatse kowa ya miqe ya wuce daki, labiba wadda tayi suman tsaye don duk abubuwan da hilma ta fada tasan karya ne don tana kallon fuskarta tasan cewa karya take, daddy na wucewa daki itama hajiya labiba tabi bayan hilma, tana shiga dakin harta kwanta cikin bargon ta don tasan tabbas mummy saita biyota don jin ya akayi ta san duk haka kuma mai yakaita dakin Ibrahim din alokacin har tasan cewa an bugeshi. ✍️✨***Auren Katin Kasa ***✨✍️ (Unexpectedly falling❤️🇦🇪)
Story and written by: QueenMarh👸🏼
Paid book 📚 Chapter 48-49
Haj labiba na shugowa ta tsaya gaban gadon ta fara Magana ''kiyi gaggawar fitowa daga cikin bargon nan kafin ranki ya baci'' da sauri ta yaye bargon tana sunnar dakai,,,kallonta mummyn nata tayi sannan tace ''fadamin, ubanme ya kaiki dakinshi at this time?"…shuru ne ya biyo baya kafin hilma tace ''haba mummy kidaina irin wannan abubuwan dan ALLAH, yanxu mai kike tunani zanje yi dakin nashi, ehe??...ina kwance ya kirani awaya yace don allah na hada mashi coffee yanajin ciwon kai shine ta tafi nakai mashi" tana kaiwa nan ta fara kwallar munafunci, ganin haka yasa haj labiba jin rashin dadin tuhumar yarta da take, bata kuma cewa komai ba ta fuce zuwa dakin dady tana fucewa kuwa hilma ta share kwallar sannan tace ''kai mummy kin fiye binciken kwakwaf wallahi'' sannan tayi kwanciyar ta.
Ibrahim kuwa yasha alwashin saiya lalata rayuwar salima wannan alqawari ne ya dauka duk runtsi duk wuya, sannan ya kwanta.
Baiwar allah salima kuwa kwana tayi tana kuka, kukan bakin ciki, babu abinda take fadi sai ''ka cuceni ka cucueni matsiyaci, insha allah, ALLAH saiya sakamin,''… jikinta duk ya kumbura yayi tsami,dakyar ta samu tayi wanka sannan ta kwanta.
Washe gari da safe kuwa da kyar ta tashi tayi wanka, gadan gadan wannan ciwon cikin nata ya dawo don jiya bugun da yayi mata harda cikin nata, tasha kuka sosai a bandaki kafin ta futo nan ta tarar da salim yana breakfast, saida ta shirya sannan itama taci kadan sannan tadan kwanta, karfe sha biyu dai dai taji buqowar dakinsu, hankali atashe ta miqe da kyar, ganin daddy yasa ta sunkuyar da kanta '' azafafe yace ''fito parlor'' Ahankali ta soma takowa tazo har main parlor inda suke zazzaune, daddy ne da mum kareema azaune kujera daya sai Ibrahim da hilma kujera daya sai kuma haj labiba agefen kujera daya sai khady wadda batama son maganar me akeyi ba atsaye. Kallon hilma daddy yayi sannan yace ''fadi abinda kikace jiya'' nan ta maimata abinda ta fada tass tana gamawa ya kalli khady wadda gaba daya ta kasa gane zancen kuma an fado sunan ta aciki, kallonta dady yayi sannan yace ''da gaske ne abinda hilma ta fada cewa kema salima ta fada maki hakan"…jin haka yasa tayi wannan murmushin mugunta sannan tace ''kwarai daddy, sau biyu tana fada min haka, ban dauki zancen nata serious ba shiyasa ban fada ba''……..daddy najin haka ya kalli salima yace ''wato yau na tabbatar jinin badaru na yawo ajininku na munafurci da cin amana, yanxu duk abubuwan da nake maku, cin ku shan ku suturarku, makarantarku da abinda zaku saka min Kenan".. salima wadda tama kasa cewa komai, adake ka a hanaka kuka, nan take ta fashe da wani matsanancin kuka,..daka mata tsawa haj kareema tayi tace ''dan uwarki kashe min da kikaso kiyi sai Allah ya tona maki asiri, to wallah kotu ce zata rabani daku''… jin hakan yasa daddy saurin cewa ''kareema kiyi min shuru anan kece zaki yanke hukunci koni'' shuru duk sukayi kafin dady ya soma Magana ''duk wani abu dana dauka nauyin yi akanku na gama daga yau, daga kan school da komai, abinci ne kawai na umarci kuci, sannan banason na kara ganin ku, ku zauna agidan nan amma kuyi zaman da kamar ba'a gidan kuke ba, sannan salwantar da ran dana da kikaso kiyi zaki biya ne don baza kici banza ba''..jin haka yasa kareema washe baki tace ''kayi min daidai alhaji wannan hukunci yayi daidai… daddy na gama maganar yace kowa ya watse, nan kowa ya tashi, salima kuwa baqin ciki yayi mata yawa, ga duka ga mari, daki ta koma wunin ranar ko ruwa bata saka abakinta ba, ganin shuru shuru yasa mama rabi lekowa don ganin ko lafiya, ganinta duk a wahalce yasa ta taimaka mata tai wanka ta bata abinci taci sannan ta kwanta.
Wannan ne dalilin da yasa sukayi shekara babu zuwa school, wanda tun suna damuwa har suka daina, sannan basu fitowa koda kitchen ne, kullum suna daki kamar prisoners kuma babu mai leqo su mama rabi ce kawai ke zuwa kawo masu abinci, daman ishaq ne maidan damuwa dasu to shima yagama secondary school kuma ya tafi eygypt karatu wannan dalilin yasa amra bata samun shi awaya kwata kwata.
Amra kam damuwan qannenta ya fara damunta da yawa, kullum cikin kuka take babu damar samunsu, akwai ranar da ta kira mrs abida, itama wayan bayayi kwata kwata wanda ita kuma daga bangarenta wayanta ne ya bace, koda ta saya sabo Sai ta rasa numbers din mutane da yawa ciki kuwa harda amra wanda ta damu sosai akan suyi waya don ta fada mata cewa su salima basa zuwa school, akwai wata rana data shirya zuwa gidan, koda taje mai gadin ya fada mata cewa basa nan sunyi tafiya wanda haj kareema ce ta bada umarnin fadin haka idon har an tambaya yaran.
Yau ta kasance weekend babu abinda amra keyi, tana nan zaune ta tapka tagumi, tunanin qannenta ya dabaibaye ta, jin karar knocking yasa ya miqewa, saida tazo dab da kofar sannan tace waye, jin muryar haifa yasa tayi saurin budewa, kallonta haifa tayi fuskarta dauke da murmushi tace ''babe nida hammam ne, munje yawo ne sai nace yadan tsaya mu gaisa, babe badai damuwa har yanxu kike ba akan siblings dinky, amra na fada maki ki kwantar da hankalinki, duk inda suke suna cikin qoshin lafiya kinji''..samun waje haifa tayi ta zauna, kitchen amra ta wuce ta kawo mata ruwa da croissant da tayi order da safe ta aje mata kan center table don tasan haifa da son cin croissant, zama tayi kusa da haifa sannan tace ''babe bazaki ganeba, ni abunnan damuna yake, sai yanxu nayi regretting aje number wani daga cikin gidan mu a waya na, hatta daddy ma saidai naga alert dinshi, haifa hankalina ya soma tashi sosai, over a year now fah babu wanda ya nemi yaji lafiyar jikina, gashi ni bama wannan ba qanne na ne matsalata, bansan a wani hali suke ciki ba, bana samun ishaq awaya, bana samun mrs abida, bana samun su salima, kullum sainayi kuka sbd nasan cewa akwai matsala wallahi inaji ajikina something is wrong haifa''..tana kaiwa nan ta fashe da kuka, rungumeta haifa tayi sannan ta kwantar mata da hankali, ba karamin dadin zuwan da haifa tayi mataba taji, don taji damuwarta ta ragu, basufi 30mins ba hammam ya kira haifa akan ta futo ya sauketa gida, nan ta sanyo hijab dinta har qasa don vest ce daman ajikinta sai wani flau skirt wanda yayi mata kyau sosai kamar baby doll, tambayar haifa tayi akan tayi mashi maganar last time da yayi ignoring dinsu, nan haifa ta shaida mata abinda tayi hasashe dai akan cewa office dinsu basu son any string relationship indai ba aure ba, hakan yasa yayi ignoring dinta amma yanxu ya fahimtar da ita komai.
Suna sauka qasa suka tarar dashi cikin motorn shi Lambo red color, gaisawa sukayi shida amra daganan tayi masu sallama suka wuce itama ta wuce cikin apartment dinta.
Washe gari ma dai babu abinda tayi banda wankin kayan sawanta, bayan ta gama kuma ta fara workout, daman tun lokacin da basit yayi mata wannan iskancin bata kuma sha'awar zuwa gym ba saidai tayi acikin gidan hankalinta kwance. Koda yamma tayi futa tayi zuwa mall don anyi masu payment din housemanship din da suke wanda hakan yasa ta yi planning ta sayama kanta abubuwan amfani don halaliyarta ne, mall ta wuce ta saya set of abayas da English wears masu kyau, riga da wando riga da skirt dasu English gown, sai flat shoes sbd tana qaunar flat shoes sbd tana da dan tsayi ba laifi, sannan ta saya hills suma masu kyan gaske, saida tayi ma kanta shopping sosai sannan ta wuce wani hadadden restaurant mai tsada, zama tayi sannan tayi order platter na special dishes dinsu, tana nan zaune tana jiran order taga giftawar mutun zai shiga restroom, da sauri ta qara dubawa don tabbatar da wanda idonta ya gane mata, kafin ta dago kuwa ya wuce ciki, sharewa tayi sannan ta maida hankalinta wajen kallon wajen don tasan cewa mutun kamar wannan ba lallai yazo waje irin wannan ba don kamar middle class restaurant ne dukda yana da tsada. Anatse amar ya bude tap din ruwan restroom din ya fara wanke hannun rigarshi wanda wata waitress tayi mashi splitting juice ajikin hannun rigar nashi, saida yagama tukunna ya danyi drying hannun, babu abinda yake tunani sai dada wato mahaifinshi, lokacin da yana raye wannan ne favourite restaurant dinshi shiyasa dukda ba standard dinshi restaurant din yake ba yanason zuwa don yana tuna mashi happy moment dinshi da mahaifinshi da mahaifiyarshi, murmushi kawai yayi ya fuce, ya koma seat dinshi mai dauke da kujeru biyu kachal, anatse aka fara aje mashi different dishes din da yayi order wanda duk favourite dinshi ne shida dada, anatse ya soma tsakuran kadan yanaci cikin jindadi, chan wayanshi yayi ringing yana dubawa yaga m-5 ne yana ganin haka ya daga hannunshi waiter yazo, card dinshi ya basu sannan yayi payment ya miqe, amra kuwa tana nan daga gefen wajen inda ya zauna hankalinta nakan abincinta wanda ta saya, saida taci tayi nak sannan ta bada payment dinta da cash anatse ta mike da paper bags dinta da tayi shopping niki niki sannan ta juya zata wuce, idonta ne karaf ya sauka kan na amar wanda yake shirin fita, tana ganinshi kuwa ta bude baki zatayi Magana shiko yayi kamar bai taba ganinta baya wucewar shi, mamaki ne ya cikata na irin wulaqancin general dinan, don saura kiris ta gaishesa don da tayi hakan da saidai ya jizgata awajen, haka yasa sumi sumi ta wuce abinta aranta tana ayyana irin isa ta mutumin.
Shiko amar sarai ya ganta saidai baiyi tunanin zatayi Magana ba don ba wani kusanci ne yake dashi ba da staff din headquarters shiyasa baimabi ta kanta ba kuma shima yayi mamakin ganeta da yayi domin its hard for him ya gane mutane don shi bai fiye shiga sha'anin mace ba.
Washe gari Monday shirinta tayi sosai cikin wata Lebanese gown red wanda tayi mata kyau sosai, rigar tana da adon flowers ajiki, ta zauna dam ajikinta, fuskar nan tata fayau babu komai saidan kwalli data sanya wanda ya kara mata wani irin kyau sosai, anatse ta dakko dan vine flat shoes dinta shima red ta saka sai yar channels hand bag dinta maqale ah kafadarta, anatse take tafiya harta shiga motorn datayi requesting, tafiyar minti ashirin sukayi suka iso headquarters tana sauka cikin asibiti ta wuce, tana zuwa ta tarar da haifa zaune ah office dinta, gaisawa sukayi kafin suka shirya cikin lap coat dinsu suka fara ward rounds, saida suka duba patients din da sukaje last operation tukunna suka dawo office nan suka tarar da hafiza tana ta sassarfa hankali atashe, kallonta amra tayi sannan tace ''sis hafiza is there anything wrong''…ko kallon inda take batayi ba ta fuce..nan take ran haifa yabaci tace ''babe wallahi idan da nice nake zaune da wannan wallahi wataran sai an raba dambe, she's so rude bata da mutunci ko kadan''..dariya kawai amra tayi sannan tace ''haifa wallahi she's nice, idan kin ganta acikin wannan mood din to fah lallai an tabo mata inda yake mata zafi ne''…dariyar mugunta haifa tayi sannan tace "wai har yanxu ita nan son general din take? Haha gaskia tana cikin matsala indai wannan zata so''…jin haka yasa amra kallonta fuskarta dauke da tambaya tace ''why did you say that''…..gyara zama haifa tayi tana fuskantar ta tace ''kinga wannan general din idan bazaki manta ba kin tuna lokacin da mukaje flower garden park dake har muka hadu da hammam''? girgida mata kai amra tayi alamun gamsuwa.. sanan haifa ta cigaba ''idan kin tuna ay tare yake da wani guy wanda kikeji nace besfriend din mu, toh ay shine general din''…tabe baki amra tayi tace ''oh no wonder inata tunanin inda na san shi ashe shine, kai haifa mutuminnan badai wulaqanci ba, jiya fa naje shopping ah mall saina tsaya yin launch ah t&t restaurant na ganshi, I was so surprise banyi tunanin ganinshi ba'', murmusawa haifa tayi sannan ta cigaba ''toh nima dai haka nace amma hammam yace min he's easy going fah, kawai dai baya shiga sha'anin mata kwata kwata kuma yana da zafin zuciya sosai shiyasa it's hard to live with him'''………..saida suka gama tsegumin amar tukunna sukayi sallama kowa ta wuce office dinta. ✍️✨***Auren Katin Kasa ***✨✍️ (Unexpectedly falling❤️🇦🇪)
Story and written by: QueenMarh👸🏼
Paid book 📚 50-51
Hankali atashe hafiza ta karasa office din amar,ahankali ta kutsa ta shiga ciki, yana nan zaune da army uniform dinshi kamar kullum amma yau ya cire rigar sama sai yar ciki wadda white top ce mai kyau wadda ta amshe shi sosai faffadan qirjinshi wanda ya cika rigar ya futo tsam, arms dinshi kamar zasu farka hannun rigar tsabar murdewa fuskarnan kuwa kamar kullum ahade babu ko alamun murmushi saidai kyawun fuskar ya rinjayi hade rai da yayi, ahankali ta tako gaban table dinshi tace ''good day sir, I'm mss hafiza from hospital''..baiko kalli inda take ba yana latsa waya yace ''why have'nt I received my last medical report,? Management team dinku basu fada maku qa'ida na ba?duk wani medical report dina office zaku kawo min?..yana kaiwa nan ya buqi table din gabanshi da karfi. Girgiza kai ya fara, duk shekarun daya yayi a headquarters wannan ne karo na farko da yake samun matsala da health care team, da zarar yagama abinda ke gabanshi zaisa asake recruiting sabbin medical staffs cause wadannan suna saka mashi ciwon kai sosai''…hafiza wadda cikinta ya duri ruwa da sauri ta soma koro mashi bayana ''sir I'm so sorry, last time kace karna sake zuwa yi maka blood test so I send my assistant to.." baima bari ta karasa ba ya kalli m5 yace ''get her now'' da sauri m5 ya fuce don shima ta shafesa. kallon hafiza amar yayi ataqaice yace ''you're excused''..da sauri ta fuce, shiko tabe baki yayi kamar yaga kashi sannan ya miqe yana shafa few suman kanshi da tafin hannusa ya tsaya gaban view din office din don curtains din abude suke, hannunshi ya sanya cikin aljihun kakin jikinshi kamar maiyin nazari, mamaki gaba daya ya cikashi da takaici don wannan ne first time da akayi delay wajen kawo mashi medical report dinshi wanda tunda ya samu daukaka sosai baya ajewa a files room sbd yana da enemies da yawa har acikin office wanda zasu iya using health issue dinshi as his weakness don su ci galaba akanshi dukda yawanci a report din baya bari sunayin test din abinda ya shafi mazantakar shi kwata kwata.
Cikin hanzari m5 ya shiga cikin asibitin, nan yasa aka kira office din su amra. Amra wadda tunda suka dawo daga salla itada haifa ciwon kai ya dameta ya sa ta dan kwantar da kanta kan table dinta, jin knocking yasa ta dago da kanta, idonta harsun fara jaa sbd ciwon kai da damuwa data sakama kanta gashi ta fara jin zazzabi kadan kadan, anatse ta dago ta kalli staff din tayi mata murmushi tace ''yes'', kallonta matar tayi sannan tace ''ana nemanki a reception''.. fita matar tayi nan amra ta bi bayanta, ganin soja a tsaye yasa gaban ta faduwa da kyar ta dan nutsar da kanta sannan ta karasa gaban m-5, tana isowa yace ''are you mss hafiza's assistant?..jin haka yasa ta girgida mashi kanta tace ''yes I am''.. juyawa yayi ya fara tafiya sannan yace ''follow me now'',.. hankali atashe ta fara binshi, gaba daya sai taji wani irin zazzabi ya taso mata gadan gadan, tana nan biye dashi har suka karaso gaban office din general ganin haka yasa ta fara qoqarin saita natsuwarta, bude qatuwar kofar m5 yayi sannan suka shiga, gaban wajen guest chair ta tsaya while m-5 ya tsaya abayanta don jiran order daga oganshi, jin tsayuwar mutun abayanshi yasa ya juyo ataqaice sannan ya kalleta wanda zan iya cewa kallo na biyu Kenan da yayi mata na qurulla, anatse ya fara takowa dan gab da ita sannan yace ''where's my last medical report,?'' Ganin yanda ya tsaya dab da ita yasa ta daburce lokaci guda turancin nata ya kubce tama rasa me zata ce mashi, chan dai ganin kamar zata bata mashi lokaci ya sashi calming voice dinshi don yaga kamar tana da masifaffan tsoro, haka yasa ya kuma maimaita mata tambayar cikin harshen bahaushe..anatse ta dago ta mashi kallo daya ta sauke kanta qasa tace ''Na kaishi file room''…..runtse idonshi yayi da sauri, wani irin balbalin masifa yana taso mashi, furzar da huci yayi sannan yace ''what the hell…jin haka yasa m-5 saurin ficewa direct 4th floor wajen file room, ahankali ya fara dubawa har yazo kan wani green box wanda ake aje health report files na manya manyan sojoji, anatse ya zaqulo na amar sannan ya fuce,…bangaren amra da amar kuwa kamar yaqi don fitar m-5 da wuya ta zube qasan gwiwoyinta, ta fara kuka, tama rasa me zatace don kwata kwata ta kasa gane menene ainahin laifinta, shiko oga kallonta yake cike da mamaki, yama rasa mai zai mata, ganin kukan nata ya fara cika mashi kunne yasa yace ''get the hell out of my office now, kuma na baki 5 minutes kije ki kawo min file dinnan yanxu, and karkiyi tunanin haka zan barki, purnishment dinki yana nan yana jiranki'' yana kaiwa nan ya wuce wajen table dinshi ya zauna, amra kuwa baiwar Allah da sauri ta miqe ta fara neman hanyan fita hartana harde qafafunta, batama tsaya bin lift ba ta wuce stairs ta fara hawa matattakalar har takai 4th floor, tana shiga ta wuce wajen inda ta aje report din nashi, ahankali hawaye ke zubowa daga idanunta, zuciyanta sai faman harbawa takeyi da zafi, kamar mahauciya haka ta dunga fidda files din daya bayan dama hankali atashe.
Bayan fitar amra kuwa kifa kanshi yayi akan table din, kanshi yana mashi wani irin zafi, kukanta har lokacin yana jinshi cikin kwakwalwar shi, babu abinda yake fado mashi aranshi face Amma shi, idan yaga mace na kuka itace kawai take fado masa, sbd irin kukan da takeyi akan aman wanda shi kuma baya so kwata kwata ko kadan.