Babban goro complete novel - Chapter 17
Babban goro complete novel Chapter 17: Babban goro complete novel Chapter 17. Mami da Shahida ya tadda a falon, ya zauna bisa kilishi suka kara yiwa juna…
3,198 words
Mami da Shahida ya tadda a falon, ya zauna bisa kilishi suka kara yiwa juna ta'aziyya, sannan ya ce da Mami, "Ko za mu iya tafiya yanzu? Gobe litinin ina son ta koma makaranta gobe". Mami ta ce, "Hakan ya yi, Shahida kirawo ta su tafi". A yadda Shahida ta gansu face-face da hawaye ya taba zuciyarta, 'yan kannen nata sun sanya ma ransu damuwa mai yawa. Basu taba bata tausayi ba sai yau. To ai gara su suna da Mami da za su rika gani su ji dadi, su kuwa fa? Ta juya musu baya tana dauke nata hawayen da 'yan yatsunta ta ce. "Marwah fito ku tafi mijinki na jiran ki". Da kyar ta shiga toilet ta wanke fuskarta da sabulu ta fito ta tadda su a falo cikin shirinta rataye da jakarta. Zahraddeen ya riga ta fita, bayan ya yiwa Mami sallama ba tare da ya iya hada ido da Marwahn ba, saboda shi yanzu matsanancin tausayin su yake ji, duk wasu makaman yakin day a tanada don dai-daita sahun matar tasa, ya nemesu ya rasa, yadda suka shaku da mahaifinsu har ya fi shakuwar su da Mami. Mami ta daga ido ta kalle ta, idanun sun yi jawur sunyi luhu-luhu, duk da wanke sun da ta yi da sabulu. Ta yi mata kallo na zuciya da zuciya, wato kallon kauna na da da mahaifi. Suka yi sallama ta bi bayan Zahraddeen. Mami ta kasa ce mata komai. Banda "agaida Hajiya Binta". Yana cikin motar kafarshi daya a waje yana danna wayarshi ya hangota ta fito, ya mika hannu ya bude mata gaban motar ta shiga ya rufe suka dau hanya. Tunda suka hau titi babu mai uhm, babu mai umh-umh a tsakaninsu. Da shirun ya ishe shi sai ya danna sautin Sudais cikin suratul An'am. Tafiya suke sannu-sannu, domin Zahraddeen baya gudu sosai. Ya kara karfin A.C din motar ya rufe tagogin motar wadanda suke bakake wulik (tintic), ba mai iya hango mutanen da ke ciki. Duk wasu kudurarrika na batanci da yake dasu a kanta, sai ya neme su ya rasa, sai tausayin ta da yake ji kamar-kamar me, zuciyarshi tayi laushi da yawa, yana tuna lokacin da shima ya rasa nasa mahaifin (the same feeling…). Karo karatun ma ya fasa, zai tabbata a serbant din Alh. Aliko Dankasa muddin rayuwarshi. Zai kula da diyarshi duk da cewa ba ta son shi, ya ji ya yarda ya amince (shi yaron Babanta ne) kamar yadda take ikirari. Sai me? Yana yin 'parking' cikin garejin shi ta dauki Jakarta ta fice ba tare da ta ce da shi komai ba, ta wuce cikin gidansu ainahin sassan Inna ba flat din su ba. Bata taba shiga ba, bata san hanyar ba, sa-kai kawai tayi. Ya kashe motar ya fito rike da hularshi a hannu da briefcase ya doshi dakin Innarshi, ya sha mamaki ganin Marwah a dakin Inna suna yiwa juna ta'aziyya. Da kuzarin shi ya shigo, amma ganin Marwah yau a dakin mahaifiyarshi sai ya ja ya yi turus a bakin kofa yana kallon ta, don bai san da wacce ta zo ba. Inna ta ce, "Ka zo ka tsaya mana kerere a ka, in shigowa za ka yi ka shigo, in fita za ka yi ka fita". Ya saki fuska sannan ya juya ya fice ya nufi sassansu zuciyarshi ta yi mishi sanyi a karo na farko tun zuwan ta gidan. Ba mamaki mutuwar mahaifinta ta fara ladabtar da ita. A yau sai ya samu kansa da zama a falon, don kawai yana son ya ga gilmawar ta, daga shi sai singileti da wandon shan iska (short niker) samfurin Adidas, ya jona kettle ya hado ruwan gahwa (coffee) a kofin tangaran ya zauna cikin kujera yana kurba kadan-kadan yana duba wayar hannunsa, amma a zahiri hankalinsa baya kai, yana kan kofar falon. Da an dan jima sai ya dubi kofar shigowa ko za ta shigo, amma shiru. Shi kanshi ya kasa gane kanshi a kwanakain nan, matarshi yake ji sosai cikin zuciyarshi tun bayan rasuwar Alh. Aliko. Can sai gata ta shigo rike da mayafinta da jakar hannunta. Ya daga shanyayyun idanunshi a hankali yana kallon ta yana kurbar coffee. Kallo daya ta yi mishi ta kau da kai, don ji ta yi kunya ta kama ta, don bata taba ganin namiji haka ba. Amma shi din bai gane hakan ba. Ko kuma ya gane din ba damuwarshi bace. Ta zube shirgin hannunta ta yi kicin don ta samarwa cikinta abin da zai ci, don Inna danwake ta yi mata tayi ta ce a koshe take, don ba za ta iya jefa wadannan lunkuma-lunkuman abubuwan a bakinta su wuce makogwaronta ba. Yana nan zaune duk kamshi ya cika masa hanci, Marwah rainon Mami ce ta fuskar girki na zamani kala-kala, ba wanda ba ta iya ba. Inda ta sha bamban da Safah kenan, ita sai karatu da son tsarge jarrabawa. Ta debo danyen nama a firiza ta zuba a na'urar nika nama ta markade shi sannan ta juye a frying fan ta sanya albasa, maggi da tafarnuwa da curry ba tare da ta zuba ruwa ba, ta sa wuta kadan sannan ta kawo green beens kofi daya ta zuba ta rufe. A gefe ta kwaba fulawa ta yi falle-falle da ita ta hau gashin pita-bread wanda za ta ci da sauce din. Cikin Zahraddeen in banda kugi ba abinda yake, ga wani irin kamshi ya cika shi. Shiru-shiru ba ta fito ba ta barshi sai hadiyar miyau yake, dama muguwar yunwa ta sa shi shan gahwar, tun karin kumallon da yayi a Kaduna bai kara sanyama cikinsa komi ba. Can sai gata ta fito da plate a hannunta da robar lemon Mountain Dew za ta wuce dakinta, sai ya sha gabanta. Ta dago ido ta dube shi sai ya rausayar da kai gefe ya lumshe lumsassun idanunsa, sannan ya budesu ahankali a kanta a lokacinda ita kuma ke ta kokawar kawas da ido daga gareshi. "Ni baki bani ladan ganin ido ba!". Harara ta zabga mishi ba tareda ta yarda ta dubeshi ba. Sannan ta ce, "Ban girka da kai ba, ko da ni nake baka abincin?" Ya yi murmushi ya karbe 'plate' din hannunta, ya bata hanya ya koma kujerar tsakiyar falon hankalinsa kwance ya soma cin abinsa. Karshen kulewa ta kulu, ta juyo ta koma kicin ta juyo sauran a wani 'plate' din ta zauna nan cikin kichin din tana ci, kada ya sake kwacewa wahalarta ta zama haramiyarta, sai gashi ya shigo. Daga bakin kofa ya tsaya hannun shi daya ya sanya jikin kofar kicin din, ya rike fankon filet dinshi da hannu daya....... ya mika mata plate din, fuskarsa dauke da wani kayataccen murmushi wanda ya fitar da annuri mai yawa akan fuskarsa, da sabuwar soyayyah dankare cikin kwayan idanunsa. Kamar almajiri yana bara; "I'm asking for more....Maa!!!"
Yadda ya yi maganar cikin kwantaccen sauti, duk sai ya bata dariya, yana iya hango siririn murmushi, a siririyar fatar bakinta, amma ba ta ce da shi komi ba, har ya saki kofar ya karaso ya tsugunna a gabanta, kamin ya zauna sosai ya sanya hannu cikin 'plate' dinta suka ci gaba da ci tare. Wannan girki dai, bata koshi ba ko kadan. Itama yunwar take ji dole dai ta hakura ta kyaleshi. Don bata son magana ta tsawaita a tsakaninsu don ta lura yau dai neman shiri yake. Ta kowacce fuska alamu sun nuna. Da suka kammala hannunta ya kama ya wanke mata a cikin 'sink', bai cika hannun nata ba, janyo ta ya yi da hanzari suka nufi bed room dinta. Ta ce, "To cika ni guduwa zan yi ne?' Ya sassauta rikon da yayi mata amma bai cika ta ba. Zama ta yi a gefen gadonta ta kwace hannunta, ya jawo stool din madubi ya zauna a kai daf da ita yana fuskantar ta. Ya ce, "Bayan rashin SO, girl,… sai mene ne matsalarki a zama dani?" Yadda yake magana kadai ya saukar mata da kasala, balle yadda hucin sassanyan numfashinsa ke dukan fuskarta. Ta samu kanta da rikicewa ta kasa amsa mishi tambayarshi. Ya ce, "Ke nake sauraro?". Tareda daga girar shi sama kadan, alamar sauraron. A hankali ta dago ta dube shi, abinda ta gani cikin kwayar idonshi ya sanyata kokonton anya Zahraddeen ne? Kwayar idanunshi ta nuna wani mutum da ke fama da azabtacciyar soyayya da kauna mai yawa, (yet he's not weak), amma dai kamar ba Zahraddeen din da ta sani ba, mai ji da kai da rashin son wargi. Sai ita ma ta yi cooling, gwiwoyinta sun sage, ta ce, "Ni na ce bana sonka?" "Kwarai kin ce ba kya sona, saboda ni yaron Babanki ne. BABBAN GORO SAI MAGOGIN KARFE koh? Ko ba haka kika ce ba? Kunnuwana suka jiye min, ba wani ya taso ya gaya min ba". Za ta yi magana ya katse ta. "…… Ba na kalubalantar ki, not eben a little, na yarda na amince in cigaba da zama YARON KI (serbant), kuma MIJINKI, (husband) mahadin rayuwar ki (life-mate) kamar fiyayyaen halitta da Uwargidansa Nana Khadijah Bint Khuwalid, idan har za ki bani wannan gurbin, zan samu Marwanatuh?" Kunya ta kama ta. Kamar tace da kasar ta tsage ta shige. Magana zarar bunu….ta riga ta fita. Wannan ba itace tarbiyyar da mahaifin su ya dora su akai ba. Ta tuno dukan mutuwan da Daddy yayi mata a lokacin da tayi wannan furuci. Ashe Zahraddeeen din ma ya ji. Sai ta soma kokarin yin repenting. Ta yi murmushin yake ta ce, "Idan ni na ce bani son ka, kaima ai bani kake so ba, Safah kake so, aka lika maka ni, don haka bai kamata ka ga laifi na ba. Soyayya ba lallai ta faru a sanda aka so faruwarta ba. Ita wata irin aba ce da ba ruwan ta da lokaci, matsayi da dangoginsu. Abu ce wadda ke faruwa a duk sanda ta so, ta gudanar da tunani ta sarrafa gangar jiki (duba littafin ALHERI). In hakane kenan banida laifi don nace bana son wanda na san ba so na yake yi ba". Ya ce cikin murmushi, wanda ya kara kawata kyakkyawar fuskarsa. "in haka ne, we habe the same problem, sai mu kirkiro SON mu taru mu rufawa juna asiri, ta hakan ne kadai zamu sanya marigayi farin ciki a kushewar sa. Auren mu babu rabuwa, (mutu-ka-raba ne). In haka ne kenan dole mu mance baya (past), mu fuskanci gaba (future), mu yi gini a kan sabuwar rayuwar da muka tsinci kanmu (present), ba tare da waiwaye ba!". Ba ta amsa ba, amma zuciyarta sanyi take, haka fuskarta ta nuna sassauci. Soyayyar mijinta na kutsawa har cikin bargo da kasusuwanta. Ashe wannan shine ZAHRADDEEN din da take kalubalantar Safah a kan ta so shi? Ashe ita soyayyar baka saninta sai ta zo kanka? Ashe Zahraddeen din ba'a sonsa ba'a saninsa sai an dan yi kyakkyawar mu'amala dashi, koda ta dan lokaci ce? Ashe wannan itace SOYAYYAHr da Safah ta dandana, amma take ganin bekenta akan rashin alkawari??? Zata iya fassara tata soyayyar a yau da 'definations' da yawa, wadanda neither Safah nor Zahraddeen edperienced it. Sai ta sunkuyar da kanta, ta kasa hada ido da Zahraddeeenin….… wanda ke kallon yanayinta, yana binta da ido, da zuciya, yana karantar weakness dinta; tana da karfin hali, tanada tsiwa, tanada son aji (class) amma bata da power a fannin soyayya (abin nufi, bata iya fin karfinta bata da juriya a fannin ta, mijin aurenta zai iya gane hakan, zai iya yin amfani da hakan ya cutar da ita batareda ta kare kanta ko ta ankara da hakan ba), irin su ne ake cewa da wuya su fada a soyayyar, amma in ta samesun, ko ta zo kansu, to basu iyata ba, suna yin ta ne (wholeheartedly). Murmushi yayi, murmushi mai mika bukatar miji zuwa ga matar sa….kowanne sassa na zuciyar ta da gangar jikinta na kaduwa, kaduwa mai ban mamaki irin wadda bata taba ji a rayuwar ta ba. Kamar yasan abinda take ciki, (kodayake ya sani din), zai iya cewa nashi ya fi nata, tunda ita mace an halicceta da kawaici da alkunya, wanda shi baya dashi. Sai ya mika hannu ya kama hannunta biyu hagu da dama, ya mikar da ita tsaye. Dukkansu dogaye ne tsayinsu daya, fadin kirji kawai ya fita. Lokaci na farko da ya jata cikin jikinsa, a hankali ya rungume ta. Ya sanya hannu cikin sumar kanta cikin wani salo na kwarewa da sanin weakness din duk wata lafiyayyar mace. Banda karkarwa da bari ba abinda take yi cike da tsoro, fargaba da razana na rashin sabo. Sai dai duk wata gaba ta jikinta ta amshi sakon da Zahraddeen din ke aikawa ta cikin gashin kanta zuwa sassan jikinta. To such an edtent that, lamarin ya zo wani 'limit beyond her capability to ignore….' (ya zo wani mataki da bazata iya hanawa ba). Karo na farko a rayuwarta da ta tsinci kanta a wata duniya ta daban, da bata taba tsintar kanta a ciki ba.
****"Kalli 'ya'yan hutun, da hutun bai sa su sun kaucewa tarbiyyah ba! MADALLAH da wannan Uba nagari. Allah Ya nuna maka aikin ka har makwancinka.". Haka Zahraddeen ya fada cikin zuciyarsa, yana rungume da amaryar tasa, wadda yake kallo tana barci sadidan cooly, ta hasken farin wata wanda ya ratso ta cikin shara-sharan farin labulan dakin barcin ta. Ya rungume matarshi sosai, cike da so da kauna, hadi da godiya ga Allah tare da yiwa Alh. Aliko addu'a. Wannan ta mallaki duk abinda yake so matarshi ta kasance tana dashi. Koma fiye. Ya yarda soyayyah is not the most important thing in marriage (ba itace abu mafi muhimmanci a cikin aure ba). Akwai wasu abubuwan da yawa bayan ta; neman zabin Allah a duk sanda maganar aure ta taso, albarkar iyaye, bin shawarar na gaba (musamman Uwa), da rashin nuna gaggawa akan abinda mutum yake so. Ta yi juyi a hankali ta bude idanunta wadanda ke cike da barci da gajiya, suka hada ido kunya ta kama ta, Zahraddeen din sai ya kara lumshe mata idanun, ta sunne kanta cikin yalwatacciyar sumar da ta cika kirjinsa. Zuciyarta fal da so da kaunar mijinta, wanda ya siye duk wata soyayya da Allah Ya halittawa dan-adam cikin zuciyarsa a dare daya kacal. Ta ta lumshe ido, hawaye suka zubo, zuciyarta cike fal da so da kaunar mijinta da ya mamaye 90% na zuciyarta, cikin dan lokaci kalilan. Bayan ta gama wanka ta yi sallah ba tare da ta cire hijabin sallar ba ta cimmasa a kicin yana ta kiciniyar sama musu abin karin kumallo, yana sanye da wasu 'pj's' ruwan makuba. Kanta a kasa ta shigo kicin din ta ce, "Da ka bari zan yi". Ya aje dankalin da ke hannunsa, ya iso gareta ya zagaye ta da hannayensa ya kwantar da kai a kafadunta. "Ya zan dora miki gajiya the whole night (a tsayin daren bakidayansa) kuma in dora miki aiki? Hakan zai zama injustice (rashin adalci)" cikin matsananciyar kunya tace "Na hutasshe ka. Ka je zan karasa. Wannan ba aikin ka bane. Ban taba ganin Daddy yana taya Mami aiki a kicin ba, ni nake tayata, nida su Dije" dariya ta bashi amma bai bata ba, kallonta kawai yake yi, sai tasa hannunta cikin nashi ta karbi wuka da dankalin dake hannun shi. Ya harde a gefe yana kallon yadda take girkin ta cikin kwarewa, mamaki fal ransa, don bai zaci ko kicin tana shiga ba. A yadda yake kallon takunta, ya kuma fassarata. Don ko sanda suke off campus ya lura Biola take sawa tayi mata komai. Ya cigaba da kallonta cikin yin obserbations masu yawa akanta, kamar wani 'psycho-analytist' koko 'behabioural analyst……..'. Ta juyo suka hada ido, har zuwa lokacin ya kasa dauke ido a kanta. Cikin shagwaba ta ce, "Ni dai don Allah ka tafi, idan kana kallona haka sai kasa na kone ko na yanke". Ya yi dariya ya juya zai fita yana cewa, "Na fita,your edcellency!" (Wato ranki shi dade). Shower ya je ya sakar ma kanshi, sannan ya fito ya shirya cikin kananan kaya na Hilfiger, yana tazar sumar kanshi ta shigo dauke da katon tray, ta ja tebir ta dora tana satar kallon shi ta gefen idonta. Ba karamin burge ta Zahradden dinnan yake yi ba, wajen dressing, ba tun yau ba, tun sanda yake zuwa zuwa gidansu na makaranta, domin mutum ne da ya san sirrin dressing na western ne ko namu na Hausawa. Duk irin dresing din da ya yi kuma, karbar jikin shi yake ya dace da zubin halittar shi, kara juyawar nan da za ta yi suka yi ido hudu tayi saurin dauke idonta. Da sassarfa ta juya zata fice, ya riko gefen mayafinta, batareda ya juyo ba. "Ba inda za ki sai kin gaya min me kike kallo?". Cikin sauri da sarkewar murya ta ce, "Ni ba abinda nake kallo…". Sai ya rungume ta, yana kwaikwayon 'yar muryar ta yace "….da abinda kike kallo. Zahraddeen kike kallo. Kuma shi din mijinki ne, mahadin rayuwar ki na har abada! Babu laifi a cikin hakan. Kalleni ki more, nima tube wannan zurmemen hijabin in kalleki cikin hasken safiya in more……, wata rana irin yau na zuwa da zaki bude ido ki ga kin cika gidannan da 'ya'yan Zahraddeen har ki aurar dasu ki goya jikokinsu. To wace kunya ce ma ta rage afterall abinda ake ma kunyar Zahraddeen ya kawar dashi gabadaya jiya.??? " Ya fadi, tareda juyowa gabadaya, domin da ya juya mata bayane rike da gefen mayafin nata. Kamar ta rafsa ihu don kunya. Alkunyar ta na burge shi. Ya janyota ya rungume gabadaya. Ya soma kissing karan hancinta da bakinta yana gaya mata kalamai masu nauyi da suka fi karfin biro ya rubuta. Sai bayan wani lokaci ne ya bari suka yi kalacin tare. Ta koma kicin ta dauko fulas din da ta zubawa Inna don Rabi'a ta koma makaranta, ta je ta kai mata har dakinta ta gaishe ta. Ba karamin jin dadin hakan Inna Binta ta yi ba, don dama ita bata dauka da zafi ba, bata sa mata ido ba, tunda tasan yadda auren ya kasance. Ramar da Zahradeen ke ta yi a lokacin ita tafi damunta, ita da kanta ta lura yarinyar ta sauko don kanta. Ta janyo kula cike da kosai da soyayyen dankalin hausa tace ko zata diba, tace "na koshi Inna, amma bari na kaiwa Yayan Rabi'a ko zai kara" ta debi kadan a filet ta rufe. Ta sanar da ita yau za ta koma makaranta. Inna ta yi musu addu'a mai yawa, ta koma sassanta, ta tarar da Zahraddeen ya gama shiryawa ita kadai yake jira. Ta dauko jakarta da mayafi da wasu takardu cikin file ya janyo kofar, suka yiwa Inna sallama bakinta ya ki rufo da ganin sauyukan da ba ta zata cikin dan lokaci ba. Tabbas mutuwar mahaifinta kadai yasa ta shiga taitayin ta, ita kanta Marwah yanzu duniyar tsoro take bata, saboda rashin tabbas na rayuwa da ta gani. Shi ya taya ta ta gama registration dinta na sabuwar shekara, duk da a makare ta zo, ya maida ita gida. A ranar ya juya Kaduna, don yana da aiyukan dake jiran shi a ofis masu dimbin yawa, ya bar mata motarsa daya don zuwa makaranta.