Kenza eBookz

Baccin so complete by m shakur - Chapter 31

Baccin so complete by m shakur - Chapter 31

Baccin so complete by m shakur Chapter 31: Baccin so complete by m shakur Chapter 31. Ya fito nan falon sama ya tsaya chak saiya kalli Saleem dake kwance…

4,179 words

Ya fito nan falon sama ya tsaya chak saiya kalli Saleem dake kwance awajen idanunsa rufe saiyahau fuzar da ijiyan zuciya first dukan dayama Saleem he regretted it koba komi Saleem yaci darajan Abba, and deep down he understands Saleem pains, shima lokacin da yadauka da Saleem za'ayi auren ko kallon fuskan Saleem baya iyayi sabida kishi, ayanda yakeji yanzu idan yace zai taba Saleem zai iya masa kisan gilla har lahira so calm Marwan calm, yafadi yana dukan kirjinsa yana fuzar da ijiyan zuciya saiya sake tsallake Saleem yashiga dakinsu wayansa yadauka number Abba yaciro yayi dialing wayan ruwan yaji akan fuskansa dasauri yakai hannu ya share ringing daya Abba yadaga kafin yayi magana ahankali Marwan yace "Abba kana ina?" Dan jimmm Abba yayi jin yanayin muryan Marwan, kai tsaye yace "meya faru? I'm close" ahankali Marwan yace "Abba dan Allah kazo gidana yanzu" Abba yace "menene Marwan" ijiyan zuciya ya fuzar zaiyi magana yakasa ya katse wayan kawai ya jefar da wayan ya runtse idanu yana dunkule hannu yana karanto ayyoyin Allah, Allah kabani ikon controlling zuciyata, Allah kabani ikon controlling zuciyata, saiya tashi yawuce yashiga closet yaciro jean yasaka yasaka t-shirt fara kirjinsa kawai dukan uku iku kawai yake yakasa believing baiga Amirah dasuke kwance tare ba, saiya sake fitowa yadauki wayansa number Mami yayi dialing just to be sure kaman Mami bazata dauki wayan ba tadaga tai shiru, cikin muryansa data karkace sosai yace "Mami dan Allah Amirah na wurinki"? Muryansa kadai Mami taji tace "meya faru? She's not here" gabansa bugawa yayi rasss, da kyar ya tattaro kuzari yace "don't worr…." "Marwan I said what happened?" Kaman bazaiyi magana ba ahankali yace "banga Amirah bane Mami" cikeda tashin hankali Mami tace "mene? Bangane bakaga Amirah ba"? Dasauri yace "ina zuwa Mami kaman ga Abba nan yazo" Mami tace "Abba?" Kawai tamike tadauki hijabi tazura tafito, saukowa kasa Marwan yayi Abba dake tareda driver nasa dake takasa yabude bayan motan yashigo gidan yana kallon Marwan yace "meke faruwa" Marwan bai basa amsaba yacigaba da tafiya yashiga falo Abba ya bisa yace "meke faruwa? Why did you call me here you look so scattered?"Kallon Abba Marwan yayi yabude baki zaiyi magana saiga hawaye hannuwansa biyu yadaura akan idanunsa yarike sAbida yahana hawayen zuba wlh bashi yake kuka ba kawai hawayen zubowa suke daidai Mami na shigowa falon sanye da hijab ta tsaya turus itama tana kallon Marwan yanda Abba ke kallonsa, dasauri ta matsa takai hannu ta kama kafadan Marwan cikeda so tace "kai Marwan, menene?" Zare hannuwansa yayi dagakan idanun ya goge fuskansa tasss yamaida glasses dinsa yasaka yakalli Mami da Abba yace "jiya bayan sallan isha'i dana ke dawowa gida i saw Saleem anan kofar gıda" yay shiru bai fadi maganan giyan ba dudda shi Abba dazai shigo gidan yaga kwalban gida daya fashe awajen kuma wlh saida zuciyabsa takawo masa Saleem, ahankali yace "we had little disagreement dai nashigo na kulle gidan nashiga falo shima na rufe na kashe komi as usual nawuce sama" yayi shiru Abba yace "saime yafaru?" Ahankali Marwan yace "bansan ya akayi ba he got the key na gidan nan yashigo har sama thankfully nasa key a kofarmu na bedroom saisa key dake wajensa couldn't work" Abba yace "Innalillahi wa innailaihi raji'un"Mami tace "I saw him jiya da daddare nafito daga kitchen yana saukowa daga bene I was trying to talk to hi…….." ahankali Marwan yace "Mami" shiru Mami tayi suka kallesa, ahankali yace "this morning mun tashi dagani har Amirah munyi salla mun koma bacci, yanzu na farka ban ganta ba!" Atare daga Mami da Abba sukace mene?". EPISODE 8️⃣7️⃣

Saiga hawaye yasauke kansa kasa yace "babu inda ban dubawa agidan nan ba banganta ba Amirah is not in this house" Abba yace "Innalillahi wa innailaihi raji'un!" Yashiga ciro wayansa Marwan ya goge hawaye yace "idan Saleem zaka kira he's still here yana sama" Abba yace "what! Yana sama? Anan ya kwana?" Gyadamai kai Marwan yayi yana lumshe idanu, Abba yawuce yayi sama azuciye Mami tabisa Marwan ya tsaya yabisu da kallo kafin shima yabisu saman. Turus Abba ya tsaya dayakai karshen stairs shi dayaji ance yana sama yadauka yasami wani daki yama shige ya kwana ne but no Saleem na kwance akasa gaban master bedroom gaban dakin ma'aurata, kirjin Abba dukan uku iku kawai yake ganin kanninsa na jini ciki daya, uwa daya uba daya yake abun nan, Mami itama just found kanta in a situation da sai tama kasa magana ta tsaya itama, Abba yakai minti daya tsaye awajen saiya yunkura cikeda karfin hali yakarasa gaban dakin hannu yasa yawani fizgo Saleem din zaune shuuu yabiyosa Abba ya kauda kansa sabida wani warin giya dayaji yanayi, saiya dawo da kansa ya kallesa still bacci yake ya bubbuga fuskansa "Saleem, Saleem, Saleem" amman ina shiru sakinsa Abba yayi yakoma sharap ya kwanta Abba yatashi yashiga kalle kalle nan falon saman ya hango bottle water akan table yatashi dasauri yawuce yaje yadauki daidai Marwan na zuwa saman, Abba yana zuwa yabude ruwan yashiga tsayayawa akan fuskan Saleem da afirgice yatashi dan ruwan sanyi sabida AC ya yunkuro yatashi ya zauna daman tsabagen maye ne yasa since yakasa motsi kaman mai paralyzed idanunsa sunyi jajir ya shiga fuzar da baki yana yatsine fuska yana kakkabe duwan daya kama wanke fuskansa da wuyansa some har kunnensa yana kakkabe kunnensa Abba ya duka gabansa strictly yace "Saleem" dago jajayen idanunsa Saleem yayi yakalli Abba yahade fuska sosai, strictly Abba yace "ina Amirah? Saleem banson tashin hankali? Kokai mayene yakamata ka hakura tunda an daura mata aure dawani bayan ka gudu, Marwan yatashi this morning baiga Amirah ba, she's nowhere to be found, nasan somehow you have something to do with it, kafadamin inda Amirah take ko wlh zan mikama hukuma kai amaka hukuncin daya dace dakai, for the last time Muhammad Saleem ina Amirah?"Tunda Abba ke maganan Saleem ke kallonsa Allah yasani baisan ina Amirah take ba amman da Abba yafara maganan yaga damuwa kan idanun Abba wannan da neman Amirah yasa har an kura Abba yasan plan din Daddy yafara aiki ashedai tsohon nan shegen duniya ne, wow ya kwana da bakin ciki but is as if Abba yabasa golden news that just make his morning, kawai saiyaji wani farin ciki ya lullubesa, Abba kawai yaga Saleem na murmushi sosai. Kai Ya Allah! Wannan wani kalan tashin hankali ne wannan? Saleem wani kalan mutum ne wanda baisan mutunci ba da alkhairi? Wani kalan butulu ne Saleem? Wani kalan mara imanine Saleem, Mara Imani kuma da kaddara? Yanda zuciya yakawo ma Abba wuya baisan sanda yakai duka hannayensa gaban wuyan rigan Saleem ba yace "ina ka kaima Marwan mata Saleem? Eh? Tell me now Kona maka dan banzan duka"? Kawai Saleem yabushe dawani kalan matsiyacin dariya dayasa azuciye Marwan yataho zai wuce Mami ta taresa tareda girgizamai kai, she knows abinda Marwan keji but ko mutuwa na kunyan mahaifiya, Abba shine yayan Saleem shima yana iyakan kokarin sa akan yaron, cin fuska ne Marwan yahau dukan Saleem agabansa kowani abu, mutunci da karamancin Abba shine Marwan yayi hakuri ya danne zuciyansa yabar yayan da kanninsa suyi magana batare da sun shiga ba, dukan Saleem Abba yashigayi Saleem yana wani kalan dariya na dadi da gidan ke amsawa sosai Abba saima yagaji yadena yana haki gwanin ban tausayi, Saleem dake dariya sosai yace "wait harka gaji Yays? Dan Allah cigaba da dukana kaninka ai yazama punching back na kowa, har kasheni aka kusan yi bakace komi ba, kaima yinaka yanzu" yamikama Abba kansa, Abba ya tsaresa da idanu, Saleem dake dariya yace "kome zakamin yau I promise you bazan taba fushi ba cus I'm the happiest man alive today" yayi murmushi saiya dena yakalli Abba ido cikin ido yace "nine kanninka! Nidakai mun fito daga cikin mace daya, the same blood ajikina shine the same blood ajikinka amman in order ka faranta ma wanda baka hada komi dashi ba ka gwammace nayi rayuwa haka miserably, pathetically ,kana kirana da bunsuru, kana Allah wadai dani, meanwhile kana kyautatama kanin matarka, kana nan nan dashi, kana kiransa danka sabida yayarsa nashan maganin mata tana baka gindi kanaci……." "Saleeeem!". EPISODE 8️⃣8️⃣

Abba ya dauramai mummunan mari jikake tassss! Abba na huci yace "don't you dare disrespect my wife!" Saleem yashafa inda Abba ya mare yadan cije lips nasa yanama Abba wani kallon rashin kunya, saiya fashe da dariyan keta sosai, yace "you know I finally get wani point na wata karin magana da jama'a keyi, wato daka haifi gwanma gwara ka haifi Matar gwamna, look at me kanninka, look at him kannin matarka"yanuna Marwan dake kallonsu Mami ta taresa tahanasa komi, Saleem yace "you gave him better education than me, yanada masters, harda PHD, a Dr, kasamamai aiki da NGO ana biyansa in dollars, komi ka kawo Marwan, abubuwan ka shi kakesa yana duba maka yana managing maka, nasha ji kana praising nasa wajen abokanan ka kan idan baka raye shikakeso ya jagoranci gidanka da iyalinka, Marwan is your everything while ni kaninka I'm just a photo daka tsana, I have just LLB na law shikenan, no masters, no NGO job, nothing, absolutely nothing" Abba yadade yana kallonsa cus duka abinda Saleem yake fadi are lies, pure lies, ahankali Abba yace "Saleem bantaba banbantaka da Marwan ba, same school kukayi, kun gama same university, he proceeded with his masters kaifa? Kakiyi, kwanakin baya karyama kamin kaje dubai masters nan kana club, your entire life you choose clubbing da bin mata while Marwan is here working his ass off to be a better person to earn his own source of living not depending on my money, he established kansa da kansa, I only recommended him to the NGO tunda psychiatrist Dr suke nema, sunba Marwan aikin base on his merits, sun gansa sunka what he's capable of, sunga resume nasa, i didn't get him this job, he earned it, banda haka bazan iya tuna the last time Marwan yaci 5k tawa ba, he does everything for kansa, kona basa baya karba, kaiko you live and breathe on my money with my credit card nike maka komi, Marwan baida credit card from me ko guda daya, all this things baka gani ba Saleem?" Saleem nawani murmushi yace "saikuma kayi, karya kake Yaya, you always show me and show the whole world Marwan kakeso, ko baki kayi daga kasashe shi kakeson nunawa not me, abin yakaiga yarinyar danake so nake kauna kadauka ka aura masa just sabida kasa matarka dashi farin ciki ni ina cikin bakin ciki, baka taba tunanin for once how i will feel ba, and you think yau Amirah data bace I will not be happy?" Ya kwashe da dariya yace "bari nagaya maka wani abu Yays, inhar banda peace of mind kaima bazaka taba samin peace of mind ba same goes for the entire family, baka auramin Amirah ba shima bazai taba zama da itaba, kodai ni na aureta kokuma dukanmu nida shi muhakura inba hakaba wlh wlh bazan taba barinku ku zauna lafiya ba dukanku"saiya juyo da kansa yakalli Marwan dake kallonsa Mami ta taresa tareda kama shoulder nasa idanunsa kadai ya kalla yasan yayi kuka yayi murmushi yace "remember rannan nace maka you will go to Mami and be crying like a Baby? Trust me bakama fara kukan ba wait for the things that await you, nizaka kwana kanacin yarinyar nan ina……" Saleem! Abba ya fizgosa yana daka masa tsawa, Saleem shima azuciye yadakama Abba yace "dalla chan Yaya kabarni mana dakai nake eh yane, ahhh ka kyaleni fa mutumin nan ko zan sassaka maka hannu" zuciyan Marwan tafarfasa yashigayi jin yanda Saleem kema Abba rashin kunya sosai, zai wuce Mami tasake rikesa tace "Marwan!", Abba ya tsaya turus kawai yana kallon Saleem da idanunsa suka juya kaman zai rufesa da duka, Saleem ya nunasa da yatsa yana ihu kaman zai daga gidan sama yace "Yaya after abinda kamin kafifita kanin matarka kan ni I loose all respect for you, girmanka yazube a idanuna Yaya! Kahanani wacce na keso kuma akan idanunka zan aureta, sannan ka tattara gadona kabani abuna na barka har abada, kabani share na na company kokuma I will go to media saina ci maka mutunci, saina tozartaka nasa kayi loosing respect akan idanun duniya and this our gold company will come crumbling right before your eyes, you hurt me I will not hurt you amman idan baka bani gadona da share dina ba wlh I will hurt you in the most painful way, kuma da yardan Allah amanata da Baba yabaka baka rikeba saita kamaka! Saika wulakance Yaya……." Saleeem! Mami takirasa da karfi jin abinda yake gayama yayansa dayake matsayin uba a hannunsa, he's just 3yrs old Abba yadauki Saleem, Saleem yajuyo yakalli Mami yace "baruwanki dani makira!" Fizge hannunsa Marwan yayi zaiyi kan Saleem cikin tsananin fushi Mami tace "inhar kataba sa Marwan ban yafe makaba wallahi!" Chak Marwan ya tsaya yana nishi da zafi zafi yana kallonsa, Saleem shima yakallesa yace "you all will pay for betraying me wlh! Da wanchan mutumin dakakema kallon mahaifi zan fara dayaci amanata, saina wulakantasa na wulakanta sunansa aduniyan nan, saikasan ni kaninka ka yar kaja kanin matarka a jiki ka maidasa da"kaman ance Mami ta kalli Abba hannunsa tagani yadaura akan kirjinsa yanadan kyafkyafta idanu dan mugun jiri yake gani bana wasaba saiya fara tangal tangal zai fadi dasauri Mami tace "Alhaji! Alhaji" tai wajensa da gudu Marwan yayi wajen da sauri Abba nawani kalan nishi he's finding breathing so hard and difficult Mami tafashe da kuka tana kiran sunansa tana kamasa, dudda Abba na in that condition Saleem yake kallo dakemai mugun kallo, Saleem yaki shiru yana kallon Abba in the eye yace "ko mutuwa ce in sha Allahu you will not die in peace! Sai Allah yasakamin abinda kamini!" Yana maganan yajuya abinsa yafice. EPISODE 8️⃣9️⃣

Gidan sukakai dake bayan gari daga sama Daddy yaji karan motan mikewa yayi yaleka ta window daidai an budema Amirah kofa tafito ahankali jikinta bari kawai yakeyi tashiga dafa motan tana tafiya ahankali da kyar chan ta tsaya sabida zafi zai kasheta, mutumin yace "ke dallah jamuje" tsorata tayi bashiri ta gwale kafafun tashiga tafiya tanajin radadi ahaka da taimakon Allah suka shigo dakin ana bude kofa ta hango Ammin ta kwance a daddaure, baki a rufe hakan yasa tawani kwala ihun kiranta ahaukace. "Ammiiiii…………" dauketa akayi da mari da saida taga stars guda uku ajere suna blinking, tawani zube akasan wajen takai hannunta dasauri tadaura kan kumatu tana wani kalan sauke ijiyan zuciya da duka jikinta marin ya shigeta, Daddy yashiga yarfe hannunsa dahar zafi yake mai sabida yanda yazuba mata marin yana jan tsuki yace "nonesense kin dauka nakawo ki nan ne dan kimin ihune mahaukaciya, nasara da rayuwan GRA yace I hate noise and tantrums" ahankali Amirah tadago rinanun idanunta takalli Daddy dake yarfe hannu yahade fuska hannunta na kan kuncinta ta tsaresa da kallo tana kallonsa da manyan idanun nan nata, bude idanunta Ammi tayi dan ihun Amirah har kasan zuciyanta tajisa abinda yasa ta farka kenan kanta na sarawa, tabi ko'ina da kallo da yanda aka daddaureta dakuma Amirah data gani zube akasa tadafa kuncinta tana kallon Daddy da jajayen idanunta ga gardawa adakin saita fara yunkurin tashi zaune tana motsi sosai trying to talk so bad tace "uhmmm…..uhmmmmm" dasauri daga Amirah har Daddy suka juyo, dasauri Amirah tace "Amm,i Ammi na, Alhamdulillah Ammi kin tashi" ta yunkura zatai wajenta, kafa Daddy yasa yawani tokare mata kirji saida tiles yaja Amirah kiiiiii ta buge da bango, Ammi tawani zaro idanu tareda mirginowa zata tashi takasa hawaye nafitowa daga idanunta tana uhnnn uhnnn ganin kalan haure Amirah dayayi kaman ya haure kwallo da ba'aso, Amirah felt kaman zata mutu her chest got congested from yanda Daddy ya tokare ta, ko numfashi balle kuka saitama kasa tama kasa wani motsin kirki, Daddy dako ajikinsa yawuce Plastic chair yazauna yadaura kafa daya kan daya batare daya kalli Ammi ba yanuna Amirah datake ayanda take da yatsa kaman yana nuna kashi yace "ku dagota ku kawomin ita nan gabana"gardawa biyu suka wuce hannu sukasa suka dago Amirah sharap ta biyosu suka kawota gaban Daddy suka ijiye yadaka mata tsawa yace "kalleni nan ko angaya miki yanzu zamanın dakikemin haukan nan ne" kallonsa Amirah tayi ahankali da jajayen idanunta dasukai laushi gwanin ban tausayi, Abba yakalli agogon hannunsa saiya kalleta yace "I don't care ko ke mahaukaciya ce koba mahaukaciya ba, if there's one language danasan kina understanding aduniyan nan shine mahaifiyarki dan haka yanzu ma we are using her as mode of communication, kalli mahaifitarki yanuna mata Ammi dake uhmmm ummm tana kiciniyan bude hannu ko kafa wlh duka takasa, idanun Ammi sunyi jaaaa Amirah ta tsare Amminta da kallo dake struggling in pains taji abu ya tsayamata a kirji, Daddy yadaka mata tsawa yace "kalleni nan!"Kallon Daddy Amirah tayi ahankali, yace "you have one hour idan bakison mahaifiyarki ta mutu, inba hakaba kasheta zanyi!" Amirah tashiga girgizamai kai zatai magana yadaga mata hannu yace "you have exactly one hour dot za'a maidake gidanki, I don't care kome zakiyi, kome zakiyi kije kiyisa ki tabbatar kinsa Marwan ya sakeki!" Wani kalan kallon Daddy Amirah tayi da sauri kanta nawani dundummm! Dum! Dum, Ammi tazaro idanu tace "uhmm, uhmmmmm, ummmmm" Daddy daya tsareta da kallo ganin yanda take kallonsa just makes him realize tsaf tagane abinda yake cewa kuma tagane menene saki, sai taga yakalli daya daga cikin yaran kawai saitaga yawuce yashiga wani daki Amirah tabisa da kallo saigasa yafito da bulalan inji doguwa sharbebiya a hannunsa ya tsaya gefen Ammi, wani bugawa kirjin Amirah yayi tama kasa kallon Daddy sai mutumin dayake tsaye gefen Amminta da dorina zuciyanta na racing kaman zai fito, Daddy yayi wani murmushi cus ya karanci Ammi da diyarta kaman me, strictly yanajin kansa yau kaman sarkin duniya mai power da babu wanda zai iya takasa yace "yima uwarta shegen duka kai Goro!" dawani kalan sauri Amirah tazare muryanta dabaya fita kawai yafito tagama kidimewa tace "Daddy, Daddy, Dady dan Allah dan Allah………" Pauuuuu! Kawai taji karan an zubama Amminta dake adaddaure bulalan injin Amirah ta kalli Ammi datai wani mikan bankara na tsantsan azaba da radadi ga ba bakin kuka, Ya Ilahal Alameen! Wuyan Amirah harwani girrrgirrrrgirrr yakeyi ganin yanda mahaifiyarta keyi agabanta in pains, tawani fashe da kuka wanda tunda aka haifeta bata tabayin kalansa ba harda majina, koda Marwan yake cinta ba irin kukan nan datake yi yanzu takeyi ba, tama haukace gabaki daya tawuce zatai wajen Ammi, Daddy ya fizgo hijabinta yajawota gabansa gardin yasake zubama Ammi bulala na biyu ihuuuu kuka Amirah tayi tana hada hannayenta biyu. "Daddy dan Yarasulullahi kadena dukan Ammi na, na rokeka da girman Allah kudena, ni kumin dukan amadadin Ammi na, na rantse da Allah zanyi kome kakeso, Daddy Kamin rai, ni ku dakeni kudena dukanmin Ammi na, Daddy nika daken, dukanku ku taru akaina ku daken, Daddy wlh wlh kome kakeso zanyi, zance ya sakeni kudena dukan Mamana"now this is abinda yakeso ta tsorata har tsakiyan jinin jikinta, kuka harda majina har baki, tsawa Daddy yamata yace "bacewa nayi kice yasakeki ba kisa yasakeki, you have one hour zaki dawo wajen nan da takardan sakin sa, idan kinason mahaifiyarki araye inba hakaba kasheta zanyi babu abinda aka isa amini ke kin sanni, kinsan waye ni" ahaukace Amirah tagama kidimewa tana magana tana kuka tana waigen Ammi tace "toh, toh, naji, wlh saiya sake, Daddy stop hurting Ammi na dan girman Allahhhhhhhhh" yanda take kuka kaman zata shide, Ammi dudda she's in pains jikinta namata radadi saida taji wani karfin hali da dakewa yazo mata, she needs to be her daughter strength, cikin karfin halin son yin magana tace "Amirah kibarsa ya kasheni ban yarda ki kashe aurenki ba"amman ina Amirah bataji, Daddy yace "kina dawowa da sakin zan aura miki Saleem shin zaba miki, do this and I will let mahaifiyarki leave in peace, saikuma gargadin dazan miki wlh wlh kika wuce hour daya, ko kika sanar da wani ga abinda ke faruwa na rantse da wanda ke busamin numfashi yaune rana na karshe dazakiga mahaifiyarki aduniya, idan kina tantaman hakan ki gwada yi kiga" Daddy yabuga kafa akasa irin buna mata he's serious Amirah ta tsorata har karshen zuciyanta yace "tashi kutafi" tashi tashigayi mance ciwon tayi tayi wajen Ammi tawani rubgumeta tana shafa bayan Ammi da hannunta inda taga bulalan yasauka tana wani irin kuka, Ammi taji jikinta zafi kaman wuta, Amirah ta kankameta tace "Ammi ina sonki na yarda narasa komi na duniya bandake Ammi na, kene rayuwan Amirah, I will save you kinji Am….." fizgota gardin yayi yajata Amirah na kuka suka wuce suka fita tana waigen Ammi tana share makinan hancinta da hijabi hankalinta yatashi na fitina yau.

BURA'UBA NOVEL NA FIRE 🔥

A GANINKU MARWAN ZAI YARDA YA SAKETA???

A GANINKU AMIRAH ZATA YARDA KAR MARWAN YASAKETA??

JAMA'A I THINK AMIRAH WILL DO KOME ZATAYI TA TABBATAR MARWAN YASAKETA SABIDA TA CECI MAHAIFIYARTA AMMI KO???

KUSA KANKU A SITUATION NA AMIRAH KUBATA SHAWARA MEYA KAMATA TAYI YANZU TAKOMA GIDA???? EPISODE 9️⃣0️⃣

Tashi Daddy yayi yawuce ya tsaya jikin window saida yaga tashiga mota sannan yajuyo ya tsare Ammi da idanu da harga Allah baiso an dakaba but yasan idan baiyi hakaba bazai taba ruda yarinyar nan ba Amirah, Ammi nawani kalan kallonsa da idanu tanaso tai magana yashiga tahowa yana kallonta yazo har gabanta saiya duka yana kallonta sosai gabansa na faduwa batare daya cire tape na bakinta ba yace "me kikeso ki fadamin Amaryata" saiya daga hannunsa yakai kan bakin Ammi yaja tape din yacire bala'in zafi saida Ammi ta runtse idanu Daddy ya tsaya ya tsareta da idanu yanda ta runtse idanun kaman yacemata sannu amman saiyayi shiru yana kallonta bude idanunta Ammi tayi cikeda fada da tsananin masifa kaman ba Ammi ba tace "what do you think you're doing? Kana tura yata taje tacema mijinta ya saketa what are you up to? Meke damunka Baban Baby? Are you sick? Kai wani kalan mara Imani ne azzalamu eh?" Tunda Ammi take masifan kallonta yake bayako kyaftawa saida tagama yace "wai tayaya ma akayi na sakeki eh kinyi fresh sosai" yadaga hannunsa zaikai jikin Ammi, Ammi tace "wallahi wallahi inhar hannunka yataba jikina koda this is the last ting dazanyi aduniya saina gille maka hannu sannan zan rasu? Why are you back in my life? My y'ata tamaka dakake cutar da ita kake azabatar da ita" kallon Ammi yake sosai saiyadan sosa kai yace "bari na gayamiki asalin wanda yaga mahaukaciyar yarki yanaso Saleem ne, Saleem kanin Akhaji Gold ne uwa daya uba daya, Marwan ba dansa bane, kanin matarsa ne dasuka daura dun yana dan shakara daya sabida iyayaensa sun rasu ya girma hannunsu, Daleem akaso har gidana nemawa aure ba Marwan ba muka sa Rana, rannan daurin aure something happens Saleem bai hallara ba kawai aka daura da Marwan bayan sunsan Saleem ke sonta, to sai bayan wata daya yadawo shima ashe aşırı wata yarinya tamai, yanzu ni Saleem nakeson bata" Ammi na kallonsa tace "sabida yabaka kudi" kallon Ammi yayi irin tayaya kika sani, Ammi tace "Baka taba abu dan Allah, bazaka tana zuwa this limit hannu banza ba yabaka kudi shine kake kokarin bata auren yar kaninka, kasan Amira marainiya ce bata da mahaifi and a sick girl kake azabtarmin da yarinya haka? Wani washe baki Daddy yayi yace "ai naga ta warke" Ammi tai shiruuuu tana wani kalan kallonsa saitai jimmm tace "deep down ada nakance duk abinda kamin nayafe kaddara ne, somehow I feel rashin soyayya yasa kamin duk abinda kamin da yarana, amman yanzu mun rabu dudda haka bakabar diyata tahuta ba, bakabar kwakwalwanta yahuta yasami sukuni ba" Ammi tai shiruuu ta lumshe idanu saita bude ta kallesa tace "abu daya nasani shine inhar auren Amirah da Marwan yarabu daman Allah yariga ya kaddara rabuwansu ya zone amman kai baka isa karaba abinda Allah yahada karubuta ka ijiye nina fada maka maganan nan" Daddy yafashe da dariya yace "zako kisha mamaki, diyar nan naki is ready to do the impossible for you baki sani ba, zakisha kallo nagaya miki" Abba yana maganan yajuya yana wake yana tafiya Ammi tace "Baban Baby" chak Daddy ya tsaya saiya juyo ya kalleta yaga idanun Ammi sunyi jajir cikin murya mai masifan ciwo Ammi tace "Ya Allah kace aduk sanda wani ya zalunceka kai addu'a zaka amsa Ya Allah wannan bawan ya azabtar da rayuwana dana diyata da batasan komiba, he torture diyata tun tana yarinya har yau bai bartama, Ya Allah ina rokanka ka amsa bakina na uku ka azabtar da bawan nan kwatankwacin yabda ya azabtar da yarinyana marainiya, Ya Allah ka sakamata da gaggaw……." Kafa Daddy yasa yatokare Ammi batare daya bari tagama maganan ba yace "ke bakisan Allah yace anemi kudi ba that is simply what I'm doing kisan nawa yaron nan yabani kuwa? Kinsan bandır bandır na dollars guda nawa yakawomin kuwa?" Gardawan biyu dake dakin suka kalli juna sai Daddy yajuya rai abace yace "kurufe nata baki" yawuce yazauna zuka o wajen suka yaga tape suka kara mannawa abakin Ammi dake kallon Daddy idanunta yayi jajir. EPISODE 9️⃣1️⃣

Readers Also Read