Kenza eBookz

Baccin so complete by m shakur - Chapter 32

Baccin so complete by m shakur - Chapter 32

Baccin so complete by m shakur Chapter 32: Baccin so complete by m shakur Chapter 32. Tunda suka shiga mota kan Amirah juyawayake, kanta na sarawa, amai ma…

4,429 words

Tunda suka shiga mota kan Amirah juyawayake, kanta na sarawa, amai ma tashigaji yazo mata wuya dasauri tabuga kujeran driver da kyar tace "Malam kayi parking" dayake su biyu ne mazan juyowa sukayi suka kalleta dasauri ganin yarinyar dake kuka since tadena tana musu magana adake, cikin wani kalan dakewa da ihu Amirah tace "nace kuyi parking! Ba guduwa zanyi ba, Mamana na hannunku, kunsan gidana, park the damn car" Yanda sukaga hannunta awuyanta da yanda tamusu ihu kaman mahaukaciya dayan yama driver alamu dayayi parking gangarawa gefen hanya sukayi sukai parking, ruwan data gani a tsakiyansu gaban motan tasa hannu tadauka tabude motan dasauri suka bude suma harda dan gudunsu irin karta gudu dinnan, wani matsayicin kallo Amirah ta musu zuciyanta yagama konewa kawai ta taka kafanta cikeda dauriya da jarumta tawuce dab da kwatan kwalbatin ta duka takai hannayenta biyu tadaura saman kanta tareda lumshe idanu zuciyanta na tashi tanason tai aman takasa sai ijiyan zuciya kawai take saukewa, takai one minute ahaka taji zuciyanta na kwanciya iska nasa tanajin tashin zuciyan na raguwa saita bude idanunta tadauki goran ruwan tabude tazuba a hannunta ta kuskure bakinta ta zubar sannan tadena ta wanke fuskanta tasss hancinta yayi jaaa saida ruwan yakare sannan ta jefar da goran tasa hannu tadauka sharce fuskanta tanajin wani confidence da dakewan zuciya da karfi da jarumta kalan wanda bata tabaji ba arayuwanta, ahankali tace "Ammi i will save you kinji, just wait for me Ammi na, whatever it takes me to do, I will do it to save you" tana maganan tamike tasa hijabin ta goge fuskanta tasss ko kallon gardawan batayiba ta taka kafanta for the first time da kyau tana danne azaban ciwon datakeji tawuce kawai tashiga motan duka mutanen sukabi Amirah da kallo ganin something in her just changed, sauke glass na motan tayi ta kallesu cikin wata kalan murya kaman ba tataba tace "idan bazaku kaini gidaba zan iya sauka na shiga dan sahu i have less than an hour yanzu" kallon juna sukayi suka kara kallon Amirah sai suka wuce suka shiga motan sukaja Amirah bata maida glass na motan ba tanajin saukan iska kan fuskanta tana kallon hanya tana kiran sunayen Allah taki yarda tai tunanin wani abu kawai, ahaka har sukakai layin motoci biyu tagani kofar gidansu da batasan nawaye ba but probably maybe motan su Mami ne cus tasan hankalin Marwan zai tashi ba'a ganta ba da sauransu, parking sukayi kofar gidan takallesu anatse tace "kujirani karkuyi nisa" duk atare suka waigo suka kalli Amirah cikeda mamaki ganin tama daina kukan datakeyi that time tabude kofa tafita taja tafiya straight tabude kofa tashiga gidan tawuce direct tabude kofan falo tashiga babu kowa a falon, but taji muryan Abba dawani magidanci Abba nacewa zaisa case din a police magidancin na cewa is a family matter hawa staircase tashigayi ahankali, Marwan dayake tsaye tuntuni yakasa zama yana sauraran şu Abba yahango inuwa mutum a bene da sauri ta tashi daga jikin bango kirjinsa na bugawa dumdumdum kaman daga sama idanunsa suka sauka kan Amirah dake hayowa benen walking perfectly, tana sanye da maroon hijabin daya samata this morning tai salla dashi, her eyes are a bit swollen yanda dai suke this morning sabida kukan daya sata tayi, her nose tip is reddish, sai yaga kaman bangaren haggu na fuskanta is looking swore sannan yadanyi jaaa, dawani kalan sauri yace "Babybear, Amirah, wife" yawani taho da sauri yan dakin na juyowa jin sunan wanda ya ambato Marwan na karasawa wajen daidai tana karasa hayowa staircase din baiyi wata wata ba kawai yayi wani hugging nata yana sata ajikinsa ya kankame ta yana sauke ijiyan zuciya abayyane kaman yayi shekara bai ganta ba yana fadin. "Oh Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah!" Har sau uku Amirah could hear the way zuciyansa ke bugawa, wani kalan karaya taji zuciyanta yayi kaman zata fashe da kuka amman takara dakewa bamatason taji wani feeling for him sai kawai tasaka hannunta biyu ta turasa Marwan yadan koma baya kadan, tafita daga jikinsa saita kalli Mami datazo wajen su Abba ma duk sun tsaya Marwan nawani kalan kallonta, Mami tace "Amirah daga ina kike duk hankalinmu yatashi bamu ganki ba"? Kallon Mami Amirah tayi she needs to do something that will make them hate her, kai tsaye tace "ni yarinya ce dazaku taru anan sabida baku ganni ba, banda right nafita ne?"

Wani kalan kallonta Marwan yake jin abinda tafadi hakama Mami dasu Abba, juyowa tayi takalli Marwan dake kallonta bayako kyafta idanu tace "inason magana dakai Marwan!"sosai Marwan yake kallonta kawai yasha jinin jikinsa, he knows something is happening, gabansa sai faduwa yake, hannunsa yayi folding a kirji yana kallonta da kyau especially daya lura she's also talking fine, acting fine, babu wasa atattare dashi sounding like a man yace "maganan dazakiyi dani can wait, first I need to know daga ina kike? Ina kikaje all of us anan were worried because of you? Ina kikaje"? Atsanake Abba yace "eh daughter Amirah ina kikaje daga ina kike eh? I was about nakira Inspector nace we have a missing person report, where are you coming back from daughter" Cikin kakkausan murya Amirah tace "where I'm coming back from ko where I was is non of you guys business, kaikuma" tajuyo ta kalli Marwan dake kallonta tace "tunda you're not ready mu kebence muyi maganan danazo yi dakai, then let's have it here sauri nake I have somewhere to be"kowa na dakin ya girgiza harshi Marwan infact yanda take maganan ma bazaka yarda Amirah can talk like this ba dan yawanci maganan ta shagwaba ne, shirme da sauransu, Marwan kallonta yake kawai, wani juya idanu Amirah tayi na tsantsan rashin kunya da rashin ganin girman mutum tace "Yayarka was there with me rannan dana sami lafiya kin fadamai?" Takalli Mami dake kallonta saita kalli Marwan tace "bayan naga yanda kaman Poor Saleem dukan kisan kai you know I feel agabanka amman ka tsallakeni kawuce abinka, bayan an kaini hospital I woke up fine, but you were too angry and ignorant to noticed na warke, anyways that's by the way ba maganan nan nakeso nayi ba"tafadi maganan saita daga kafanta ta tako few more step to gaban Marwan ta tsaya dab dashi takalli kwayar idanunsa dake cikin glasses kaman yanda yake kallonta bayako kyafta idanu tace "Marwan aurena dakai was auren da akayishi bana cikin hayyacina! Banda kai! Banda lafiyan sanin menake so, mene banso, meya dace dani menene bai dace dani ba, sanda aka aurar dani ina hauka lokacin but yanzu I'm well, nasan banbanci mai kyau da mara kyau, I know d difference between right and wrong, I know what I want da wat I do not want, also I know the kind of man danakeso nai rayuwa dashi da wanda banason nai rayuwa dashi"tadanyi shiriuuu saikuma tadaga hannunta tanuna Marwan daga kasa zuwa sama tace "you're clearly not kalan namijin danake so a matsayin mijina!" "Amirah" Abba yakirata da sauri kawai saita juyo takallesu tace "please can you all allow me nayi magana da mutumin nan da akace shine mijina and stay out of this" jar'uban chan har ransa Marwan yaji zafin yanda tama Abba magana anatse cikin kakkausan murya yace "can you stop being rude to my parents" juyowa tayi takalli Marwan tace "then tell your parents dakai nake magana sudena samin baki please!!!"

Wani kara kallonta Marwan yake kaman yaune yafara sanin Amirah ganin a very very total different person ba that girl da aka taba shigo da ita office ta chukuikuyi hijabin Mamanta ba bata yarda takalli kowa ba, goshinta Amirah tadan sosa sounding and acting so disrespectful tace "yauwa as I was saying" tadauka hannunta daga goshin takalli Marwan sosai tace "baka jam'in kalan mazan danakeso Marwan!" Tadanyi shiru tana kallonsa zuciyanta na zafi tanaji kaman bazata iya cigaba da magana ba saita tuna Amminta hakan yasa ta kallesa tace "bakakai namiji a idanuna ba!" Tadanyi shiru tadake tace "baka min ba ko kadan!" Tadanyi shiruuu sai chan tace "bana sonka at alll!" Wani azaba Marwan yakeji azuciyansa, strictly tace "da bazan dawoba but I actually come back sabida nazo ka sakeni kowa yakama gabansa, dan haka Marwan ka sakeni!"Wani kallonta kowa na dakin yakeyi, babu wanda yayi magana, takara kallon Marwan sosai tace "ka sakeni Marwan!" Marwan yadade yana kallonta na kusan one minute kaman yanda take kallonsa saiya sauke ijiyan zuciya kana ganinsa kasan he's hurting, anatse yace "waya aikoki da sakon nan?" Faduwa gaban Amirah yayi jin abinda Marwan yafadi amman saita daure ta dake tace "ban gane ba!" Cikin kakkausan murya Marwan yace "whoever sent you wajena yace kicemin na sakeki tell them bazan taba sakinki ba! In this family bama sakin matanmu, so kome zakiyi kinyi kadan kisa nasakeki, ko da zan tabayin hakan zanyi ne base on my decision not because ke kince nayi"yana maganan yawuce yajuya zai wuce daki sabida zuciyansa dake tafarfasa kaman ruwan zafi hankalin Amirah yatashi duka duka she has less than 20min yanzu kafin şu kashe Ammi, she needs big point abu dazai batamai rai sosai tahau tunani dawani kalan sauri tace "Saleem nakeso!" Chak Marwan ya tsaya gabaki daya yaga duhu ya lullubemai idanu, yanda maganan ya chaki zuciyansa kawai sai jikinsa yahau rawa yashiga juyowa yana kalllonta dishi dishi sabida duhun dayake gani, kunensa na maimaita Saleem nakeso! Saleem nakeso! Saleem nakeso…!

Tunda take bata taba ganin idanun mutum na komawa ruwan tokaba tsabagen fushi sai yau ga jijiyoyi sun fiffito a goshinsa idanunsa nawani kalan kyalli na hawaye zuciyansa na tafarfasa sabida wani kalan kishi da zuciya, now is perfect time Amirah tafadi aranta tana kokarin tuna abubuwan da taji Saleem yafadi jiya da daddare, cikin wani kalan rashin kunya Amirah tace "ka kalli Saleem ka kalleka Marwan?" Tai dan shiru tace "Saleem embodied the qualities of namiji dayakai akira namiji ba kaiba kanin mata!" Mata takara kallon Amirah data juya idanu tace "Saleem shiya fara cewa yana sona, bantaba ganin namiji as handsome as he's ba, ga jarumta, ga haduwa, he loves me he keeps fighting kowa to have me this is kalan namijin danake so that's ready yajuya duka duniya for me, I love Sal………" Ameenatu!!!!! Marwan yakirata azuciye saida gidan ya amsa, awani zuciye Amirah ta taho gabansa ta tsaya dab dashi itama tai ihuuuu tace "I said Saleem is a better man than you are, yafika komi, yafika class, da kyau, yafika aji, Marwan I'm saying it to you face look at me, Saleem nakeso! Masakeni na aure Saleem!, Saleem nakeso! Saleem nakeso! Shinake kauna, shi nakeso nayi rayuwan aure dashi na haifamai yara, Marwan I said Saleem nakeso!" Duk yanda Marwan yaso yarike yakasa saiga hawaye sharrrrrrrr sun fado daga idanunsa dawani majina yafito daga hancinsa duka sun sauka akan lips dinsa yana kallon kwayan idanun Amirah sosai, Amirah tayi wani dariya na danne kukan datakeji ganin the way she's hurting Marwan sosai tace "you see kasakeni ka tsaya kana kuka kaman mace abinda Saleem dina bazai taba iyayi ba kenan, I forgot to tell you something kasan ranan nan dana rungume Saleem a stairs?" Tasake kallon kwayan idanun Marwan dake kallonta tears na saukowa daga idanunsa tawani lumshe idanu cus she can't anymore tadaure tace "ina kara tuna ranan ayanzu, that day was the best day of my lif…….." "Ameenatu!!!!" Dasauri Amirah tabude jajayen idanunta ta kallesa tace "I made sure rannan yaga komi na jikin…a……" "NA SAKE K…….. " Marwan yayi magana da sai next episode zakuji….😓😓😓😩😩😩

AMIRAH REALLY HURT MY MARWAN WLH😭

ALLAH SA SAKI UKU NE MA YAMATA!!!! EPISODE 9️⃣2️⃣

NA SAKEKI SAKI……. Atare daga Abba, Mami harda Alhaji Hamza dake wajen suka hada baki sukace. "Marwan!" Muryoyinsu kaman zai fasa gidan, Amirah har wani jiri jiri takeji kaman zata fadi amman tadake, numfashinta har wani karkacewa yake kaman mai shirin suma tana haki kaman irin wacce tai awa daya tana serious gudu dinnan, but tsabagen taurin kai da karfin zuciya tace "idan ka isa ka karasa sakin" Mami ne tazo wajen ranta abace amatsayinta na uwa ta fizgo Amirah batai wata wata ba ta maketa a kafada cus she loves Amirah so much dabazata iya marinta ba, tasake maketa a shoulder tana ihu tace "meke damunki Amirah? What's wrong with you today dakikema mijinki rashin kunya haka? Meyayi zafi? Menene? Do you think akwai matsalan dazaki shiga dabazamu iya magance miki iya karfinmu ba? I'm right here tell me Baby menene eh? Menene tell me Amirah na" Mami takai hannayenta biyu cikeda so tai cupping fuskan Amirah trying to get her to talk, wani kuka Amirah taji yazo mata yanda Mami tamata maganan was so touching, kallon Mami take asanyaye, sotake tama Mami rashin kunya but data kalli kwayan idanun Mami saita kasa wlh, hawaye suka soma tsatso mata a idanu kawai tacire hannayen Mami daga fuskanta tajuyo dasauri takalli Marwan da kawai saiya juya yawuce daki zata bishi saitaji takasa sai kafanta yahau rawa duk yanda taso ta tadaure tadake saita kasa kawai saita daura hannunta abakinta tadanne tana hana kuka kufce mata hawaye suka shiga saukowa daga idanunta kaman pampo kowa na dakin kallonta yake babu wanda ya iya magana, she wants to follow Marwan takasa, bata taba sani haka matan aure kejin kalman saki ba and bamatasan saki nawa bane kawai tadaiji yasaketa ita takasa binsa ita takasa ma komi kawai brain nata froze gabadaya in everything har ta bangaren tunanin Ammi, tana wajen taji karan an bude kofa karfi ne yazo mata dasauri tasa hannu ta share fuskanta tassss takalli wajen kofan Marwan ne ke fitowa yashare fuskanta tass kaman baitaba kuka ba kawai dai fuskansa yayi jajir ne, ga paper a hannunsa Abba yawuce wajensa gadan gadan da fushi yace "angaya maka idan mace tace asaketa ana biye mata ne? Wannan wani kalan shirmene? Meke damun yaran yanzu da basajin magana? Kuna yanke shawara bakwa neman shawaran manya, agabanmu iyaye muna tsaye anan zaka tapka shirme haka"? Tsayawa chak yayi yakalli Abba saiya kalli Mami dake kallonsa itama ranta a masifan bace da Marwan, yasauke ijiyan zuciya yace "duk macen dazata bude baki tama iyayena rashin kunya batada space arayuwana Abba, kuyakuri but har abada nahakura da Ameenatu" yana maganan yawuce Abba ya wuce gaban Amirah ya tsaya yakalleta yamika mata takardan, tunda aka fara bala'in nan sai yanzu Amirah taji takasa kallonsa saikuma takasa mika hannunta takarbi takardan, yakai kusan 20secs yana bata takardan envelope din kafin strictly yace "take" dan kallonsa tayi da wasu kalan eyes yake kallonta kaman he doesn't have a single feelings for her, mika hannunta Amirah yayi daya shiga rawa dudda tana kokarin bada hannun amman rawa yake kowa kallonta yake takai kusan 15seconds sannan tasa hannunta ta karba tajuya aguje tai stairs tawuce tafita, kowa na dakin jikinsa yayi la'asar they're in such a shock da babu wani mai iya magana ganin aure just die in front of them just now, wayansa yaciro batare daya kalli Abba ba yace "I'm calling the Police Abba, I'm following her she's under threat" cikin wani kalan mugun masifa Mami tace "kasan da haka kasaketa, duk wanda yasan Amirah yasan ba hannu daya tayi abinda tayi ba, akanme zaka saketa" kallon Mami yayi shima yace "I'm her husband, her life partner, her soulmate, kowani situation take ciki we can solve it together we are one me and her, inhar zata iya samin kanta awani situation tamin abinda tamin yau, nan gaba tashiga wani situation daza ace taje takasheni she will kill me without hesitation, Mami, duk macen dabata daukeni Abokin rayuwanta that they can fight anything together with ba, ba mata bace ta gaskiya, is true abinda tace ni da ita aren't compatible, taji sauki let her explore life and find a husband situable for her dream, duk wanda takeso ta aura she's free" yadanyi shiru yace "oh tama samu, anyways I'm going" yawuce Abba yace "wait wait ina zaka yanzu"? Yana sauka staircase din yace "there's tracker at the envelope and ina kiran police" Alhaji Hamza dasauri yace "bari nakira" Abba yace "kwarai gwara kai kakirasu general yanzun nan zaka gansu sunzo" Alhaji Hamza yashiga kiransu duk suna fita suka shishiga mota, Mami kadai aka bari agidan takasa motsi.

Allah yasani tagaji da rigiman Saleem tasan he has something to do with this entire thing amman yanda Marwan yasaki Amirah yamata ciwo kaman taitai kuka, bakin ciki takeji aranta sosai da bacin rai wanda tadade bataji kalansa ba kaman yar cikinta aka saka haka takeji.

Shifa Saleem baisan meke faruwa ba so koda yafita motansa yashiga yaja yana gudu a titi amman shima sai tunani yake ina Amirah taje? Zuciyansa na basa Daddy has something to do with it, sai kawai yadaga wayansa yashiga kiran Daddy wanda ringing daya biyu yadaga kai tsaye Saleem yace "Yohh Pops kana tareda Babe dina ne ba'a ganta ba fa" Dan dariya Daddu yayi yana kada kafa yace "banace kabani nan dariya 3days ba, but I think I will finish this job today cus right now she's on her way going to gidanta tasa yasaketa" Saleem yazaro idanu yana mamaki yace "me kayi hakane eh"? Dariya Daddy yayi yace "zamuyi magana anjima go and have fun zan kiraka anjima na nuna maka takardan sakinta" wani ihun Daddy Saleem yayi yace "love you Pops Inlaw" Daddy ya fashe da dariya, Saleem ya katse wayan yawani kunna wakan mota yana zuba gudu a titi yana rawa. EPISODE 9️⃣3️⃣

** Amirah na fitowa da gudu motan tabude ta shiga bamata tsaya rufe kofan ba kawai ya kwanta ta kifa fuskanta a kujeran bayan datake tafashe da kuka Ya Rabbi! Kuka take with all her heart and soul mai karfi, jikinta na rawa tana shesheka, mazan suka kalleta sai driver yabude motan kawai ya sauko ya kulle kofan bangaren ta yadawo yashiga motan ya kunna yasha motan. Amirah kuka take kaman ranta zai fita bata taba sanin this is the feeling da mace keji idan aka saketa ba, for the first time in her life saitaji inama ta mutu kawai bayan ta ceci Ammi she wants to die, sabida nothing will make sense again, tayaya zata cigaba da rayuwa babu Ya Marwan ciki eh? Saleem she just mentioned that one name sabida yasaketa amman Saleem tama tsani kallon fuskansa haka nan kawai baitama ba at all, kawai Marwan sai dawo mata yake azuciya tana tuna the first day data fara ganinsa a asibiti daya bata chocholate, after Amminta Marwan was the second kind person data taba sani a rayuwanta He takes care of her he protects her he pampers her yanzu shikenan sun rabu? Bazata kara ganinsa ba?

Har sukakai gidan kuka take parking akayi, driver yabude mata kofa yace "fito" tasowa tayi daga kwancen datake saita mike tafito daga motan idanunta sunyi suntum tafito ta tsaya saita daga hannunta ta kalli takardan daya bata that was folded tana hadiye wani abu hawaye na gangarowa daga idanunta, namijin yace "let's go" tafiya tafarayi jikinta ba karfi suka wuce sama azaune taga Ammi bakinta arufe amman idanunta na nuna tashin hankali tana kallon Amirah data kalleta tana göğe hawaywn fusknata.

Kirjin Ammi yashiga bugawa dum dum dum tadaura idanunta akan envelope dataga Amirah tarike a hannu sai kawai ta runtse idanu da karfi tareda juyar dakanta, Daddy baya dakin hakan yasa Amirah ta taho wajen Ammi dasauri tazauna gefenta tace "Ammi nadawo everything will be fine kinji I will save you" tai maganan tana tsare Ammi da kallo dataga taki juyowa ta kalleta kawai zuciyanta ya idasa karyewa gabaki daya gane cewa wani kalan mummunan fushi Ammi takeyi da ita bana wasaba kawai saita fashe da kuka sosai har wani kalan shesheka take kaman zata shide wlh hakan baisa Ammi tajuyo ta kalleta ba ayanda take fushi ayanda ranta ke baci, tasan waye Marwan mutum ne mai hakuri da hankali duk abinda zai kaisa daya saki yarnan bakaramin abu Amirah tayi ba maybe taje tamusu rashin hankali.

Daddy all this while yana bayi fitowa yayi daga bayin yanda yaga Ammi tajuya ma yarinyar dake kuka sosai baya yasan fushi Ammi take da yarinyar yawani kwashe da dariya yasami kujeransa yazauna yakalli Amirah yace "ke zo bani takardan nagani" tasowa tayi ahankali tazo wajen saita duka tabasa Daddy yasa hannu ya amsa yana murmushi yadaga wayansa yashiga kiran Saleem yana warware letter yace "Hello" Saleem yafadi, Daddy yace "Na sakeki saki daya! Harda signature da date da sunansa yarubuta" Saleem yadanyi shiru yace "maisa ba uku ba" Daddy yace "as long as mun sami dayan ma Alhamdulillah" Saleem yace "to kuna ina nazo kadaura mana aure"? Dasauri Daddy yace "Haba Saleem wani daurin aure, ai saitayi idda ya kake abu kaman bakaje islamiyya ba kusan wata biyu da auren su fa kenan" cikin fushi Saleem yace "nidai kadauramin aure da ita yau I don't care" Daddy shima yace "to ai shikenan kaika sani hado balance dina ka kawomin da share dina sai na daura muk………" "everyone raise your hand above your head!" Daddy yaji muryan yan sanda, tsabagen rudewa saida yasaki wayan kasa, kwata kwata abinda bai luraba Amirah nabasa envelope din zata yayi tabasa takardan taciro takardan taga dan wani bakin abu dabatasan menene a envelope din ba ta share yan sanda tagani sun shigo falon kusan şu goma chan saiga Marwan yashigo yana tafiya kaman zaki wani tsaresa da kallo tayi tana ganin wani haske na binsa tana kallon fuskansa dasauri taga yayi wajen Mami baiyi wata wata ba taga yadaura hannuwansa biyu akan kafadan Ammi cikeda kulawa yace "Ammi are you okay?" Yashiga kwance igiyan daurin hannuwanta dana kafafunta, saiyakai hannunsa bakinta yashiga cire salatef din ahankali sabida zafi Ammi ta runtse idanu, saiyakai hannunsa yakama hannayen Ammi dayaga shatin bulala banda sign na daurin igiya, daga wajajen guiwan hannunta akwai shatin bulala wani rawa jikinsa yafara saiya kalli shedan bulalan injin dake hannunsa strictly yace "who beat you like this Ammi?" Murmushi kadan Ammi tayi tace "Dan bugewa nayi" idanun Marwan na komawa ja yace "is that man right?" Kafin Ammi tai magana kawai yasa hannu yadauki bulalan yatashi azuciye yawuce inda yan sanda ke kama Daddy dake zuba turenci karaf Marwan yaji an rikesa, saiya juyo Alhaji Hamza ne girgizamai kai yayi yace "ba huruminka bane dukansa kana auran diyarsa let me do it with him man to man, inspector ku sakesa" yafada with so much command and authority, atare sukace "Yes Sir"kawai sai suka saki Daddy suka matsa gefe, Daddy ya kallesu da sauri yana mamakin waye mutumin, Alhaji Hamza yashiga nannade hannun rigansa, he was once a soldier retired yayi yafara business bazaka taba cewa yanada shekaru ba, wani kallo Daddy yamai yace "and who are you?" Yana linke hannun rigansa yace "I'm the man that's is willing to go to any limit to protect that young woman you just tortured, yau zan gwada maka you don't mess with abinda tsohon soja keso!" Dago idanunta Ammi tayi takalli Alhaji Hamza dan bata sansa ba bakuma tasan waye ba, Abba yadanyi murmushi yana sunnar dakai kasa ganin Abokinsa na playing hero lines. EPISODE 9️⃣4️⃣

Ammi bata taba ganin Alhaji Hamza ba, amman shi yasha ganinta har unguwansu Abba yakaisa yanuna masa gidan da Ammi take kullum saiyaje ya tsaya a waje just ya ganta, yagayama Abba saita gama idda zai fito ya nemeta amman Allah yadaura masa son Ammi sabida yanda yaga she's so religious shi addini yakeso ajikin mace, Daddy jin abinda yafadi wani kishi yarufe sa yace "kar har ka isa? Wayekai har yanzu Matata ce ai ance saki uku a Lokaci daya saki daya ne, kumadai bata gama ba saura 3daya, abamu fili mu fafata" Alhaji Hamza yayi wani murmushi yace "ai an bamu bakaga sun matsa ba taho" yanuna yan sanda Daddy yashiga linke hannun riga Alhaji Hamza yace "yau zan maka dukan da bazaka kara kwadayin dukan wata mace ba a tsawon yan shekarun rayuwan dasuka rage" cikin kunfan baki Daddy yataho zai naushesa haba kama hannun Alhaji Hamza yayi da hannu daya kawai yajuya Dady Daddy yajuyu kaman muciya yasa kafansa ya kwashesa saiga Daddy akasa on his knees hannunsa twisted sosai yayi wani kara. "Wayyyoooo hannuna zaka karyamin hannu" har yanzu dorinar I Jin na hannunsa Alhaji Hamza yadage ya zubama Daddy dorinar wani burgima Daddy yayi. "Wayyooooo Allah na officer zai kasheni" yashiga soda jikinsa kaman zararre yahaukace ashe haka zafin bulalan inji ke zarar da mutum, kunga yanda Alhaji Hamza ke dukan Daddy da wayan Daddy na ihu kowa na dakin kallonsu suke especially Amirah da Ammi, Ammi tunda take bata tabajin abu yamata dadi azucuya kaman yanda taji dadin yanda taga Daddy na ihu in agony ba Hamza na dukansa har Abba babu wanda yace yadena, soja baida imani saida Alhaji Hamza ya farfasamai jiki da bulalan dan kana ganin jini jini a rigansa sannan ya jefar da bulalan yasa hannu ya fizgo Daddy dake nishi kaman zai mutu yajasa keeeee yakaisa gaban Ammi yadagasa yakamo habansa yanunama Ammi shi hancin Daddy har jini yake fita lips dinsa sun kumbura yadaku, Hamza yace "bata hakuri"Daddy nada rudewa sosai ya tsorata ganin mutumin babba ne kuma kaman Ogan yan anadan ne dan babu wanda yahanasa arude yana magana yace "kiyakuri dan Allah kiyakur………" tasssss! Ammi tadaukesa da mari da saida yaga tauraro Alhaji Hamza yace "good" yasakesa yana clapping for Ammi yana kallonta, Ammi takara kai hannu tadaurama Daddy mari jikake tassss! Saida bakin Daddy yashiga dalalar da yawu, hawaye zai fito daga idanun Ammi cikeda wani kalan tsantsan kauna Alhaji Hamza yace "don't cry for him dagayau bazai kara ganin hawaye ki ba, baikai ba sannan bai isaba, he's a nobody" kallon Alhaji Hamza Ammi tayi idanunta fal da hawaye amman basu zuboba, gyadamata kai yayi yace "it's okay, he will never hurt you again or your children, i will make sure he spends the rest of his life in prison, you're a strong woman karki karamai kuka instead trash him nabaki bulalan"? For the first time dan murmushi kadan Ammi tayi ta girgixa kai alamun a'a wani sanyi Alhaji Hamza yaji aransa, saiya daga Daddy ya wurgama yan sandan shi yace "make him pay for bullying kidnapping molesting them" yan sandan suka saramai aka jasa aka wuce dashi dasauran boys dinsa, Abba yaduka yadauki wayan dayaga Saleem bakan layi yakai wayan kunne yace "saura kai duk inda kake sai an nemota you are also going to pris…." Katse wayan Saleem yayi dasauri Abba yakalli Amirah data kasa tashi daga inda take saiya duka gabanta ya kalleta asanyaye kasa magana tayi kawai saita fashe da wani kalan kuka tana rerasa agaban Abba, ko kallon inda take Marwan baiyiba sai kawai yajuya yafita.

Readers Also Read