Kenza eBookz

Baƙin ruhi complete by mrs sadauki - Chapter 8

Baƙin ruhi complete by mrs sadauki - Chapter 8

Baƙin ruhi complete by mrs sadauki Chapter 8: Baƙin ruhi complete by mrs sadauki Chapter 8. Ina ɗaga kiran ya ce "ki je ƙaddamar da aikinki na gaba,ki kawo…

4,481 words

Ina ɗaga kiran ya ce "ki je ƙaddamar da aikinki na gaba,ki kawo mana jinin jariri sabuwar haihuwa za mu yi amfani da shi don sabunta soyayyarki da Fahad " cikin kuka na ce "ni na fasa ! Ban so ka daina aikin haka nan ya isa haka,ka faɗa min kuɗin aikinki sai na turo ma son aikin da ka yi ya wadatar tun da ka raba su ni dai ko bai aure ni ba to babu komai tun da duk mu biyun mun rasa"

Wata irin dariya yayi kafin ya ce "kin kuwa yi kuskure ,don mu Family ba ma taɓa yafiyar member duk wanda ya shigo to ya shigo kenan ba zai fita ba,in kuma kika yi kuskuren ƙin yin abin da muka ce to ki kuka da kanki " yana gama faɗa ya kashe,ni kuma na buɗe murfin wayar na cire batirin tare da ɗaukar niyyar ba zan taɓa kunna ta ba sai ko kafin in ajiye ta ƙarar shigowar ssƙo ya shigo wayar.Saƙo ne mai ɗauke da bayanin dokokin abin da zan yi, ninkin tsorona ya lunku sau ba adadi saboda na fahimci suna da power sosai tun da har suka iya aiko min saƙo a wayar da babu batiri ciki.

Abin da suka sharuɗa min abu ne mai tsanani,ba komai suke buƙata ba sai jini.Jinin na ɗan mutum, wannan ya haifar min da zazzaɓi mai tsananin da yasa sai da aka kai asibiti kwana biyu na yi a can mafi haɗari don kuwa a can na gano cewa asibiti na ɗauke da wani ƁOYAYYEN SIRRI(MRS SADAUKI) wanda ta ɓoye iya masu ido uku kawai suke da izzar ganinsa.Bayan mun koma gida na samu shimfiɗa na yi bacccin da rabon da na yi shi har na manta,a cikinsa ne na yi ga ƙawata Fa'iza a zaune kusa da wata ƙorama tana kuka yayin da ni kuma ke ta yin dariya ban bar dariya ba har sai da na farka kuma tun a lokacin na soma jin canji a jikina.Da farko ƙaiƙayi na soma ji,da zarar na sosa sai ƙurji ya fito tun ina ɗaukar abin wasa har na soma yin jinya don kuwa haka gashin kaina duk ya siɗe kamar yadda kike gani ,duk wani kyawuna kuma ya ɓata na dawo mummuna.Amma dai hakan bai sa na yi abin da suka ce ba saboda tsoro ba zan iya kashe jinjirin yaro ba" tana kawowa nan da labarin ta ƙara ƙaimi wurin kuka,na ce "ita kuma ƙawarki Fa'iza ta samu lafiya ne?"

"A'a har yanzu tana kwance ita ma tana jinya" ta bani amsa ,sai a lokacin na maido hankalina ga Aliya,ban ɓata lokaci ba kuma na yi mata bayani bayan ta gama saurare ta ce "kamar yadda ta faɗa ɗin baƙin tsafi ne aka yi wa ƙawarta,ba za ta taɓa warkewa ba sai ranar da aka cire baƙar kazar nan da ta jefa salanga.Ita kuma maganinta banda labarin yadda za a yi ta warke,ke ce za ki faɗa"

A bayanin Aliya na fahimci cewa a dole dai ni ce zan samo mafita,sai dai kuma a zahiri ban san ta yaya ne zan yi ba don warkar da ita.Aliya ta miƙe tsaye ta ce "zan je na buɗe dakalin salangar da ta jefa kazar na fito da ita,ke kuma ki aje hankalinki da kyau ki yi tunani na tabbata za ki samo amsarki tun da ina ji a jikina tamkar ɗazu da muka je AOKIGAHARA wato dajin sirri an isar miki da saƙo sai dai cikin biyu ne ko dai ba ki fahimci me yake nufi ba ko kuma kin yi shiru ne"

Kalaman Aliya sam ba su sa na ji a raina cewa ai fuskata da ta Maheer ita ce ainahin saƙon da aka isar min ba,abu guda kawai na ce mata shine zan yi tunanin.Bayan fitarta sai hankalina ya kawo kan sarƙar wuyan da na ɗauko,na saki murmushi kafin na kai hannuna cikin riga na shafo ta tare kuma da riƙe ɗan dutsen tsakiyar da aka yi wa ado.Tamkar yadda in aka saka gogagen kaset yake rawa bai kawo hoto mai kyau to haka aka soma kawo min kilishen hotuna da bidiyoyin wasu lamurra da suka shuɗe na tsofin ƙarni da kuma na yanzu.Wani irin ɗaukewar numfashi ne ya riske ni yayin da nake kallon komai ido rufe,ban fahimci komai in aka cire hoton farar yarinyar da na gani tana leƙena a saman bene a ɗazu da muka je can gidan Alhajin da ya cuci Meeel.

Ganin matashiyar yarinyar nake tana gudu tana waiwaye haɗi da kuka tana kiran sunan Daddy,tana dab da faɗowa daga saman bene wani farin maciji wanda yake sak kamar irin launin fatarta ya zo ya tare ta daidai nan kuma na ji shiga tsinin allura a muscul ɗina da sauri na buɗe ido sai na ga Maheer ne yake jawo jinina cikin kwararon allura bayan ya gama ja ba tare da ya nemi izinina ba sai shi ma ya zuƙi nasa,kafin ya je daidai gadon Ayush mai siɗaɗen gashi ya zuba rabin jinin cikin ledar ƙarin ruwanta sauran kuma ya saka shi a aljihu ban san uwar me zai yi da shi ba. Nan take ita kuma ta soma yin wani fizge-fizge tana huci can kuma sai ta soma yin bacci mai nauyi.

Maheer ya ɗan juyo ya kalle ni,a cikin kallon nake hango takaicina a cikin ƙwayar idonsa sannan kuma da wani abu mai kama da gargaɗi.Daidai nan Dr Muhamud ya shigo,direct wurin gadona ya zo ya ce " Haulatu ya jikin naki?" ban amsa ba sai ma uban masifafu da nake kallo,shi kuwa Dr Muhamud ci gaba yayi da cewa "mu je ki yi wanka ki canza kayan jikinki,zuwa ƙarfe tara na dare za a shiga da ke ɗakin tiyata don ciwonki na buƙatar ɗinki"

Wani miskilin murmushi na ga Maheer yayi wanda na ji sam ban yarda da shi ba,sai na cewa Dr Muhamud "a'a ban so ni dai a bari ba sai an yi" ina gama faɗae haka sai ya juya ya kalli Maheer kafin ya ce "kar ki wani damu kin ji,zan tsaya har sai komai ya kammala sauko kin ji"

Dauriya na aro na gyaɗa kai kafin na ziro ƙafafuwana ƙasa,dakyar nake takawa Dr Muhamud na riƙe da hannuna muka bi ta gaban Maheer muka fice .Nurse Jamila ya kira ita ta kai ni toilet ɗin da zan yi wanka,bayan na cire sutura ta haka na daure na yi wankan har na gama ina tambayar kaina mene ne ma'anar murmushin da Maheer yayi.Rigarsa na wanke masa tasss,yayin da kuma nurse Jamila ta miƙo min wasu riga da buje ƴan kanti na saka.

A dadafe na fito ina bin bango,duk yadda nake jin rauni da idona ya sauka kan Maheer riƙe da hannun nurse Fatee sai da na ji kamar in arta a guje na je na raba su,dakyar na samu dai na kawar da kaina ina kuma sake maido dubana sai na ga ya shigar da ita wani ofis. Maganar Lubna ce ta dawo min a tunani ' ai shegen son matan tsiya ne da shi' tsabar tsiyar gumi yasa na fara takawa har na isa bakin ƙofar ofishin kunnena na kai jikin ƙofa don jin wainar da ake toyawa,muryarta na ji ƙasa-ƙasa tana yi masa magana cikin magiya "don Allah kar ka yi min ban so ,wancan karon ma da ka yi min kasa bacci na yi don zafi haka na kwana na wuni wurin na ta yi min zafi "

Saura ƙiris zuciyata ta buga jin wata lukutar masifa,na dafe ƙirji ina jin maduban idona na yi min gargada haskensu na ragewa. "Kina da zama ne tare da Dr Maheer?" na ji wata murya,dakyar na iya ganin mamallakinta wata haɗaɗiyar budurwa ce ta ci uwar kwalliya,kai na girgiza mata.

Ta ce "to me kike yi bakin ofis ɗinsa?"

Murya na ɗan rawa na ce "na zata na Dr Muhamud ne"

"Shi ga ofis ɗinsa can,mu je na kai ki" ta faɗa tare da kama hannuna,dakyar nake ɗaga ƙafata sam ban san idona na zubar da hawaye ba sai da na ji muryarsa yana cewa "Kuka kuma Haulatu? Kwanta mu ga ciwon" sai yanzu ma na farga da mun iso ofishin nasa.

Kallon tsanake na yi wa fuskar Dr Muhamud,fari ne irin mai haɗi da ja.Fuskarsa tana da ɗan faɗi,ta samu kuma albarka dogon hanci mai ɗan kauri,bai da saje sai dai bakinsa kewaye yake da gashi wanda shi ma salon gayu ne.A takaice dai shi ɗin mai kyawu ne,zuciyata na ji tana raya min ' me zai hana ki mayar da dukkan hankalinki a wurin da ake yinki? ' can kuma wani sashen ya ce min 'to mene ne ma abin damun kanki a lamarin Maheer? Ko dai sonsa kike?' ban samo amsa ba na ji muryarsa yana rarrashina.

"Ki yi haƙuri ba wani jimawa za a yi ba in an shiga ɗakin tiyatar,kuma fa na faɗa miki zan tsaya har a yi komai gabana "

Kai na jinjina masa,sai ya ja kujera ya umarce ni na zauna sai da ya taimaka min.Waya ya shiga yi ,na dai ji yana Dr David kafin kuma ya ce yana jiransa bayan ya gama kuma sai ya ƙara kiran nurse Jamila ta zo ta kai ni wani ɗaki ta saka min ƙarin ruwan da suka saka ni bacci.

Ban farka ba sai a ɗakin tiyata,dukkan likitocin mata ne sai namiji guda wanda nake kyautata zaton shi ne Dr David.Babu jimawa kuma aka fito da ni ,da fuskar Dr Muhamud na fara cin karo cikin waɗanda ke zaman jirana sai kuma Lubna da Meelat har da Hajiya .Aliya ce kawai a ban gani ba,Hajiya tana hawaye ta zo ta shafa kaina kafin ta ce "ya jikinki Haule?" ban iya cewa komai ba sai murmushi,na dubi Meelat wacce na gan ta cikin ƙoshin lafiya da dukkan alamu ita ma an yi maganin matsalarta wani sanyi na ji a raina haɗi da wata nutsuwa,ina shirin lumshe ido aka shigo da wani yaro yana fitsarin jini daidai nan ita ma Aliya ta shigo tana yi min ƙyaf-ƙyaf da ido alamun isar da wani saƙo..... My book is only 500 via

2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank

DM +22795045822.

🔞In kin san ba ki biya ba kar ki karanta min book,yin haka babban kuskure ne don cin haƙin da ba naki ba ne.Kuma Allah ba yafe haƙin wani akan na wani,don haka kar ki raina girman haƙi komai ƙanƙantarsa.

__________________________________________________ *PAID PAGE*

14

"Duk ku fita waje don Allah "cewar Dr Muhamud nan duk suka fice,sai a lokacin ya matsa kusa da gadon yaron ya samu auduga ya shiga goge masa jinin haɗi da ƙoƙarin tsayar da shi amma tamkar ma ƙara jawo shi yake yi haka ya zubowa,wasu nurse ɗin tuni sun shigo.

"Ko a kira Dr Maheer?" wata ta tambaya.

"In Dr David bai riga ya tafi ba kirawo shi" cewar Dr Muhamud.

Da sauri ta fita sai ga shi sun dawo da Dr David ɗin wanda nake kyautata zaton shi ne wanda Lubna ta bamu labari,kana kallonsa kuwa ka ga kirista saboda sarƙar Cross da ke manne a wuyansa.Nan kuma na ga wani ikon Allah yadda yaron ya soma yin kuka da ya gansa yana wasu suratai,Dr David ya ɗan murmusa kafin ya cire sarƙar wuyansa ya mannata a goshin yaron a hankali ya fara rage sautin kukansa.

"Ina mahaifiyar yaron? Ku ce mata ta shigo don ciwon nasa ya haɗa da harakar sprituality "cewar Dr David ɗin,gyaran murya na yi sai Dr Muhamud ya juyo da ido na yi masa alama sai ya zo inda nake.

Murya ƙasa-ƙasa na ce "ina son ganin idon yaron,ka san na ƙware a harakar bayar da maganin gargajiya" yayi ƴar dariya kafin ya tura gadona kusan na yaron.

"Me sunanka?" na tambaye shi,a hankali ya juyo muka haɗa ido kuwa.Cikin shashekar kuka ya ce "Amar"

"Ko za ka faɗa min me ka gani kafin ka fara yin fitsarin jini?" ina yi masa wannan tambayar sai duk tsoro ya bayyana a fuskarsa,hannuna na kai na taɓa jikinsa nan take jinin ya tsaya daidai nan kuma mahaifiyarsa ta shigo tana hawaye.

"Amar faɗa min me ka gani?" na sake tambayar shi,cike da tsoro ya soma yin bayani "wata...wata mace mai fararen kaya,fuskarta baƙa ƙirin tana da dogayen faratai da kuma manyan ido ita ce ...ita ce... Ta kama ni tana sha min fitsari,shi ne na yi ihu da na ji zafi na ce wayyo Allahna Ya Wadudu sai....sai ta yi saurin saki na ta ɓace kuma sai na ga jini"yana kawowa nan yayi shiru tare da ƙoƙarin zuwa wurin mahaifiyarsa amma Dr David ya tare shi yana kallona kafin ya ce "ke kuma wace ce?" ban basa amsa ba na dubi Mamar Amar na ce "a cikin ƴaƴanki wa kika fahimci canzawar halayensa ko kuma kika ga wani abu na daban a tattare da shi?"

Shiru ta yi tana nazari kafin ta ce "babu .. am Akwai ,kwana biyu na ga Nadiya duk ta canza min kullum a tsorace take sannan kuma tana yawan yin tashin dare"

"A kirawo min ita"

"Ai tare muke da ita,bari na kirawo ta" ta faɗa tare da ficewa,babu jimawa sai ga shi sun dawo ita da matashiyar budurwar da duk ta yi gudu ba za ta haura shekara goma sha shidda ba,fara ce tasss mai kyau sai dai kukan da take yi ya hana a ga kyawun idonta don sun yi ja sosai.

"Ina buƙatar don Allah a bar mu ni da ita da kuma mahaifiyarta "na faɗa ,Dr David ne ya cewa nurse ɗin su fita amma shi da Dr Muhamud ƙin fita suka yi.

Na dubi Nadiyar na ce "ga ki dai ƙaramar yarinya amma kin tsoma kanki cikin haɗari me girma,mene dalilin da yasa kika sayar da ruhin ƙanenki ga aljanai?"

Ida firgicewa ta yi,dama can a tsorace take da farko ta so nuna ma kamar ba ta gane abin da nake nufi ba don har da rantse-rantse babu abin da ta yi . Ji na yi kamar na shaƙe mata wuya,na ce "za ki yi bayani ko kuma ni kike so na saka ki don dole ki yi?"

"Na rantse da Allah ni ban yi masa komai ba" ta faɗa tana mai ci gaba da kuka.

Na dubi mahaifiyarsu na ce ,"ki ce ta yi bayani da kanta ko kuma na kira ƙanwata ta tirsasa mata"

Cikin rarrashi ta ce "Nadiya ki yi bayani mana kin ga halin da ƙanenki yake ciki dai ko?"

A tsorace ta soma yin magana,"dama uku ga watan Mayu ne wata rana ina suyar awara sai ..sai wata ƙawata da muka taɓa aji ɗaya da ita ta zo ita da saurayinta a mota suka saya a nan ta karɓi lambata ta saka ni wani group na ƴan mata ƴan gayu kullum sai sun aiko hotunan kansu kowacce tana gasar sutura,yayin da kuma gefe guda suke ta wayar iphone.A duk lokacin da na suna turo hotunan iphone hankalina tashi yake,don ni wata tsohuwar itel ce gare .Wata rana sai na kasa haƙuri na tambaya wayar za ta kai dubu nawa sai suka shiga yi min dariya,nan ne na ji labarin wai sama da miliyan ɗaya.Sosai na yi mamaki,amma sai wata ta biyo ni ta pc ta ce min in dai ina buƙatar iphone zan iya samu da na tambayeta ta yaya kenan ? Sai ta ce "kawai ɗigon jini uku ne za ki ɗiga a wani zobe shikenan " a lokacin sam ban yarda ba don dariya ma abin ya bani,sai kuma na share ta amma da yake ƴar fitina ce haka kullum take aiko min hotunan sabbin wayoyi da kuma kuɗi bugun Amurka tun ban damuwa har zuciyata ta kwaɗaita min kan cewa ya kamata ni ma in samu tawa.Kawai sai na tura mata saƙon "ina son samun iphone ɗin ya zan yi?" sai ta ce "ki same ni a ƙofar babbar kasuwar turaren wuta in kika tambaya da shagon J ƙamshi za a kawo ki" haka kuwa aka yi bayan na kai markaɗen awarar da zan yi sai na shiga taxi na je can shagon nata.Duk a tunanina wata babbar mace ce zan gani amma sai na tarar da wata matashiya wacce ba za ta wuce shekara ashirin da biyar ba,da murna ta tarbe ni bayan ta bani wurin zama sai ta miƙe ta ɗauko wani baƙin zobe mai kamar gawayi ta miƙo min na karɓa ina juya shi.Sai ta yi min bayani "ɗigon jini uku kawai za ki ɗiga a samansa shikenan in kin yi sai ki zo ki karɓa amma jinin cikin wani family ɗinku in kuma kina ɗa ƙane ko ƙanwa nasu ma yana yi"

Sam ban yi tunanin cewa hakan zai kawo wata matsala ba, wannan yasa da dare bayan Amar yayi bacci na tsikare shi da allura tare da ɗiga jinin nasa kuwa ga zoben,a lokacin da na yi haka sai na ga zoben ya bado wani irin haske kafin kuma ya ɗauke sai na je na ɓoye shi cikin jakata.Washegari haka na je don kai wa J ƙamshi zoben sai na karɓo wayata,amma sai ta nuna min cewa ai ba ita za ta bani ba sai dai mu je ta yi min rakiya na karɓo.

Shi ne fa ta ɗauke ni a motarta muka je can wani ƙauye ,gidan wata tsohuwa ne ba mu ma shiga ba ita ta fito ta tara min hannu na ciro zoben na bata ita kuma ta miƙa min iPhone ɗin.To tun daga wannan rana sai Amar ya soma firgita cikin dare yana mugayen mafarkai,da Mama ta tambaye irin mafarkin da yake sai na ji yana zayyano irin siffar tsohuwar nan wai tana zuwar masa a mafarki.Da farko an fara yi masa hayaƙi,to duk in an yi masa shi sai ya soma yin haɓo jini na yi masa zuba ta hanci wannan yasa aka watsar .A jiya ni kuma na soma ganin abin ban tsoro,a duk lokacin da zan ɗauki hoto sai na ga Amar a bayana yana kuka jini yau da na gwada yi ma har da muryarsa na ji yana cewa "anty Nadiya don me? Don me za ki bayar da ni ? " ina cikin wannan shock ɗin ne kuma muka ji kukansa a banɗaki da muka je sai muka ga yana kukan jini." tana kawowa nan ta yi shiru,yayin da kuma mahaifiyarta ta yi cikinta za ta dukanta amma su Dr suka hana tare da fitar da su waje.

Raina na ƙuna,zuciyata na zafi na ce a kira Aliya.Sam ban san meke damun ƴan matan yanzu ba da suka ɓace don kayan ƙyalƙyali,wasu ma ko tsarki ba su ida iyawa ba amma suna son yin ɗagawa da tunƙahon nuna wa duniya su ma wasu ne.

Bayan Aliya ta zo na faɗa mata komai,ɗan murmushi ta saki kafin ta zo dab da kunnena kafin ta ce "jininki da na Maheer ne magani,ban san haka ba sai ɗazu da na ga ya yi wa Meelat allura da shi.Hanya mai sauƙi ita ce ku yi aure ku zama abu ɗaya,amma ina ganin kamar shi Maheer ba zai iya aurenki ba shi yasa yake haɗa jininki da nasa don magance matsalar da ta shafi BAƘIN RUHI "

Shiru na yi ina nazari,kusan abin da ta faɗa sai na ga gaskiya ce.Sosai kuma na ji ciwon abin da Maheer ɗin yayi in dai tunanin Aliya ya zama daidai na bai iya aurena ne duk da cewa shi tun tuni ya san da dama wannan ce solution to tabbas zan nuna masa ni ma ƴar daba ce ta ƙarshen lamba.

Ban gama tunanin yadda zan ɓullo masa ba ya shigo ɗakin yana wani hura hanci,idona bai sauka ko ina ba sai akan farar rigarsa wacce shatin laɓa ya fito ɓaro-ɓaro duk jan baki ya ɓata ta.Na kawar da kai ina jin zuciyata na tafasa yayin da kuma amon muryar nurse Fatee yake dawo min na abin da ta ce.

'Ko mene ne yayi mata? ' na tambayi kaina a zuci,na kuma ba kaina amsa da ' me fa zai yi mata in ba iskancin da suka saba ba?'

Sai kuma na juya ina kallonsa,ƙarin ruwa ne yake haɗawa tare da sakawa yaron Dr David shi kuma uban surutu yana basa labarin abin da ya faru yayin da Dr Muhamud ya koma gefe yana hararen Masheer sai kuma na ji haushin haka har ban san lokacin da na ce "Dr Hamuuud!" ba wai Dr Muhamud ba hatta Masheer sai da ya juyo ya kalle ni ,shi kuwa David wani iri na ga yayi kamar bai tsammaci haka ba kuma bai ji daɗi ba.

Shi kuma Dr Muhamud murmushi ya sakar min yana mai cewa "Haulatu ya dai? Allurar kashe jikin ta sake ki? Kina jin yunwa ne?" na ɗan yamutsa fuska ina kallon Maheer na ce "tea kawai nake so mai zafi" da sauri ya kawar da kansa,ina jin lokacin da Dr David ke cewa "Maheer na zata ita ce Queen ɗin da kake bani labari"

Bai basa amsa ba,ya miƙa masa allura ya ce "please ɗebo jininta ka kawo min" ya karɓa ya zo ya kama hannuna ya soma jan jinina Dr Muhamud da ke shirin fita ya ce "me za a yi da jininta? Patient ɗina fa ce wannan"

Dr David yayi ƴar dariya kafin ya ce "kar fa ka manta ni na yi mata ɗinki yanzu,to ka ga ni ma patient ɗina ce" sai kuma duk suka yi dariya shi ya fita shi kuma ya kaiwa Dr Maheer jinin ya karɓa ya jawo nasa sannan ya zuba shi a cikin ledar ƙarin ruwan Amar.

Dr David ya zo ya ja hannun Aliya suka fice har da rufo ƙofa,wani irin tsoro ne na ji ya dirar min musamman da na ga shi gogan ya juyo yana yi min wani mugun kallo mai cike da tsana.Da ya soma takowa inda nake wani irin yunƙurawa na yi zan tashi amma na kasa,cikin zafin rai ya ce "mene ne haɗinki da Dr Muhamud? Ɗan uwanku ne? Kun haɗa iri da shi ne? Shishigin mene ne kike yi masa? "

Cikin tsiwa na ce "ina ruwanka to? Kai ɗan uwanmu ne da kake yi min masifa? "

Ya waro ido da alamu bai yi tunanin haka ba,a zafafe ya ranƙwafo yana mai dafa gadon da nake "ni ne masifafe?"

"Eh ɗin in banda masifa ni ƴar uwarku ce da za ka bi duk ka takura mu ni da saurayina"

"Saurayinki? Okay soyayya kuke kenan?" ya watso min tambayar yana canza launin idonsa,sai a yanzu na farga cewa fa na yi katoɓara don kuwa zargi ne kawai nake Dr Muhamud na sona amma bai furta ba.

Sam ban ga fitarsa ba sai ƙarar ƙofa na ji gammmm,na kalli ƙofar ina jin duk babu daɗi a raina.Babu jima kuma Dr Muhamud ya shigo hannunsa riƙe da kofin shayin,shi ya taimaka min na jingina kafin na sha shayin duk da kuwa ba da son raina ba nake haɗiye shi.

★MAHEER

Dogon saurayi mai cikar zati da kyawu,matashi ɗan kimanin shekara talatin da shidda.Maheer dai fari ne sol mai doguwar fuska,yana da cikar ƙasumba da sumar gashi mai santsi irin ta Hausa Fulani.Bai da ƙiba,siriri ne sai can saman ƙirjinsa da ya ɗan buɗe,manyan idonsa sune suka fi fito da kyawunsa da kuma jan hankalin ƴan mata don tamkar na mai jin bacci haka suke.Izzarsa da jiji da kai da kuma tsantsani su suka hana shi har izuwa yanzu zaɓar abokiyar rayuwa,don duk gani yake in ba macen da ta san ciwon kanta ba to ɗaiɗaiku ne suka iya wanka mai kyau.Yana ɗaya daga cikin rainin hankalin da yake yi wa ƴan mata masu bibiyarsa da sunan so ya ce su je har su iya tsarki.Duk fitinar budurwa da nacinta ba ya ɓata lokacinsa wurin tunaninta,sannan kuma yana alfahari da hakan sai dai zuwan Haule gidansu duk ta zubar da wannan ajin nasa.Tun ranar farko da yayi mata kallo ɗaya ya ji wani lantarki ya ratsa kaf illahirin jikinsa,a lokacin ma tana cikin dattinta irin na buzayen daji amma a haka ya ji ta yi masa musamman yanayin saurin bayyanar da tsoronta.Don lokacin da suka fara ganin juna ya dawo daga aiki ne a gajiye ya shigo sanye da kayan likitoci ita kuma daidai tana yi wa Hajiya bayanin duk abubuwan da ta iya amma tana ganinsa ta tsorata tare da yin shiru.A ranar da ya shiga wanka yana rufe ido ɗan ƙaramin bakinta kawai yake gani yana motsi,bai taɓa kissing ɗin kowacce mace ba a kanta ya ji sha'awar yinsa amma ya basar tare da yin tsuki yana ganin kuma me ma zai yi da ƴar ƙauye.

Sai dai duk yadda ya so hakice ta abu ya cuttura don ta samu wuri a zuciyarsa ta yi tsiron da kullum sai sabon toho yake tare da fure da ƴaƴa.Kafin ya gane ya kamu da sonta ya sha wahala,don haka kawai yake komawa gida don ya ganta tana aiki ko kuma ya tsiri kallon tv a babban falo don kawai ya ji ta kusa da shi,a cikin irin kallon ƙurillar da yake yi mata ya gano tana ƙumshe da wata baiwa wacce bai fahimci ta mece ce ba sai a ranar da ya tarar Hajiya ta sha yawunta.Tun a lokacin kuma ta ƙara samun wuri a zuciyarsa ta zauna daram,abu na farko da yayi don yi wa muguwar ƙaunar da yake yi mata adalci shine haɗa tunaninsu wuri guda ta hakan ne yake samun duk wani motsinta.

Yana jin mugun kishi a duk lokacin da Dr Muhamud ya tambaye shi ina likitar gargajiya,amma bai kai ga samo hanyar da zai toshe wannan matsalar ba shi ne ita ma Haulen ta tsiro da nata salon.Don iya shege har da guntule sunan Dr Muhamud ta mayar da Hamud,sosai abin yayi masa ciwo shi yasa ya kasa ɓoyewa yayi mata jan kunne shi ne ta yaɓo masa baƙar magana.

Yana fitowa daga wurinta dakyar ya iya kawo kansa cikin ofis ɗinsa saboda yadda idonsa ke rufewa tsabar ɓacin rai. Nurse Fatee wacce ke kwance tana baccin gajiya kan kujera yasa ƙafa ya tura ta da mugun ƙarfi har sai da ta wuntsile ta faɗi ƙasa,babu shiri kuma ta farka za ta soma yi masa kukan sangartar da ta saba ya daka mata wata mahaukaciyar tsawa ya ce "fitaaa! "

Sumi-sumi ta miƙe ta fice tana ɗingishi,Dr Maheer ya shiga watsi da duk abin da ya samu kafin ya cusa yatsunsa cikin gashinsa yana jin tamkar ya ciro zuciyarsa ya jefar ko zai huta da azalzalar da take yi.

Yana cikin wannan halin ne Dr David ya shigo ya tsaya yana kallonsa kafin ya ce "mene ne kuma duk wannan?"

Cikin masifar da ta zame masa jinin jiki ya ce "kenan ma ba ka sani ba? Ba ka ji da salon da ta kira Dr Muhamud ba? Mene ne haɗinta da shi? Ɗan uwanta ne? Babu fa dangin iya ballantana na Abba ,a gidanmu ya ganta shi ne ita kuma har ta iya kallon tsabar idona ta kira ni da masifafe "

Readers Also Read