Kenza eBookz

Bakin rijiya part 1 complete novel - Chapter 3

Bakin rijiya part 1 complete novel - Chapter 3

Bakin rijiya part 1 complete novel Chapter 3: Bakin rijiya part 1 complete novel Chapter 3. " Boo mie banfa karyaba" hannunshi ya kuma saqalawa a kugunta "…

4,241 words

" Boo mie banfa karyaba" hannunshi ya kuma saqalawa a kugunta " Bazaki iya girka komai bane da kanki sweetest?" gyad'a masa kanta tayi cikeda shagwab'ar da sam bata karb'eta ba tace " Ni kasanfa jiya baka wani barni bacci ba na gaji kuma chips nake sanci with liver sauce" kallonsa ya maida kan Hafsat "kulele kije ki hada mata breakfast dinnan datakeso sannan bayan kin kammala ki daura lunch kinsan kuma banaso ya wuce 1:00" murmushin yaqe tayi batare datayi magana ba ta wuce su zuwa inda take saaran nanne kitchen din sabida kula da tayi komai na tsarin gidan irine dayane da nata kayane dai ta kula kowannensu da irin nashi,taje ta had'o breakfast din ta kawo dinig ta ajiye sannan ta juya zuwa daura na rana,zuciyarta tana mata suya sosai a daddafe ta kammala girka musu chinese rice da veg pepper chicken and mock champagne drink,a dining ta jere su bayan ta kammala had'a colslow sannan batare data d'ibi komai aciki ba,ta juya zuwa part d'inta,wanka tayi ta sauya kaya sannan tayi kiran umman yaa shaam ta asali akan a aiko mata abinci,da wannan umman ta kira shaam akan yazo ya karb'a wa hafsat abinci,da mamaki yafito parkor din gidanshi ganin kayan abinci a jere ya sanyashi mamaki amma batare da wani dogon nazariba yafita yaje ya karbo ya dawo, da iya karfinsa ya banko kofar gidan ya shigo a parlor ya sameta kwance ta daura wayarta asamn flat tommy d'inta tana tunanin data saba wannan shigowar da yayi a haka be sanya tako motsa ba sabida ta shiryawa kanta tarb'ar duk wani bakin ciki dazezo mata bama yanzu ba har nan gaba,a kanta ya tsaya "Wane munafuncinne ya sanya dakika girka abunci baki ebi naki ba sekika kira sabida ke ba Allah aranki burinki kawai kiga kin had'ani da mahaifiyata,shegiyar yarinya me munafuncin tsiya wlhy kika kuma mun haka sena illata miki fatar jikinki kuma inji zancen nan gidan agidan daddy ko gidan Abba ko hmmm rahbb wlhy nida kene,kuma zanyi baqi da dare kiyi girki a nan part d'in" Harya gama fadan shi ko motsi batayiba a haka ya juya be jima da fitaba sega su huda lokacin kuwa har 3 ta gota ba karamun sanyi tajiba atake huda ta tayata suka hada girki me yawan gaske basu suka zauna ba se 6, wanka hafsat ta sakeyi sukayi sallah sannan suka kule d'akin hafsat kallon ta huda tayi tace "Qawata nasani kina cikin damuwa me tsananin yawa kuma na fahimci hakan tun zuwana,nasani bakyaso ki tattauna matsalolinki da kowa amma ki sani hafsat kin burgeni matuka lallai kinyi hankalin da ban zata kuma inaso naja hankalinki akan abu d'aya,karki kuskura ki sanar wa iyayenki irin zaman da kike acikin gidannan,ke bama suba kowa harni,duk sanda kikeda wani matsala kimun matsal ki gayamun sabida yawan barin abu a zuci yana sanya ciwon zuciya,karki yadda da kowa se kanki,kuma bawai rashin fad'a ba hadda nuna wa dan Allah yar uwata kina daure wa kuma kina jure duk wani wulaknci da shammaz ze miki,kiyi zaman aure me kyau kindaiga ke qaramar yarinyace idan kika biyewa waccen tsohuwar matar wlhy wahala zakiyi sosai sabida nisam ban yarda da ita sabida haka ki kiyaye kinji" se a sannan taji wani kuka ya qwace mata rungume huda tayi ta dinga kuka seda ya isheta sannan ta sake huda ta mata suka yi sallama akan washe gari zasu dawo.......

Mom Nu'aiym [1/21, 7:15 AM] Mmn Sadeeq: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅

Love story 2018

Billy galadanchi

*HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)

Wattpadd@68billygaladanchi

*Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*

09 Da darema haka ta zauna zaman jiran yaa shaam amma shiru kakeji tamkar an aiki bawa garinsu,haka ta kwana ranar kam tana rusar uban kuka,tana idarda sallan asuba wayanta ya soma ringing tana dubawa tagan sunanshi gabanta ya fadi, jiki ba kwari ta d'aga kiran,yace da ita "Karfe 9 zanyi baqi saga abuja zasu sauka a lodge su uku ne ki hada break fast before 8 sabida nafiso su taradda shi suna zuwa" to kawai tace ta ajiye wayan tana sharar kwallah,ga ciwon kai sabida kuka da rashin bacci ga azabar aiki sekace jaka,a daddafe ta hada musu finger sandwitches da sultan chips fried chicken and jello,se 8:15 ta kammala,tana shirin fitowa kitchen d'in ya shigo da sauri taja baya ta durqusa har qasa "yaa shaam barka da kwana" harara ya wurga mata

"ke jakar gidan uban waye wai? Bance dake before 8 ki kammala ba yanzu karfe nawa?" sadda kanta tayi kasa wani qututun bakin ciki ya tasoma mata ta kuma rasa dalilin daya sanya sam bata iya kuka idan yaci zarafinta sedai zuciyarta ta dinga wata suya me azababben rad'ad'i,da k'yar ta lalubo kalmar "kayi hakuri" tsaki yaja "Dama mana kullum kece ayi hakuri,idan kin isa gobema na sakaki aiki na baki lokaci ki wuce time d'in wlhy zaki d'and'ana kud'arki a hannu" batace kanzil ba taje ta dauko warmers d'in data zuba abinci aciki ta sakosu acikin wasu cute baskets guda biyu ta ajiye a gabanshi ta juya zuwa d'akinta cikeda qunci,tana zuwa tayi kiran umma akan zancen yarinyar dasukace zasu kawo mata me tayata aiki,sabida a yanda ta gaji yanzu bataji zata iya girka lunch and dinner kuma taga har haleemah tafara fita aiki tun jiya,bayani umman ta mata akan an kawo yar aikin khairiyya zatazo ta kawota anjima kadan......

*Bayan wata biyu*

Rayuwa a haka taci gaba wa hafsat cikeda qunci da wahala,gashi duk k'wak'war mutum be isa yasan abunda ke damunta sabida dama batada jiki balanta na kace tayi rama,sannan kuma bazaka gane a fuskarta,tana zuwa school yanzu 200l suke kullum huda cikin bata shawarwari na kwarai take akan tayi hakuri kasancewar itace kadai aduniya tasan meyake damun hafsat,kuma har wannan lokacin shammaz baya kwana gidan hafsat indai abubuwan more rayuwane da kudade sedai ta baiwa wani amma sam ba magana me dadi a tsakaninsu wasu lokutan sam ko gayar dashi tayi baya amsawa,yau agajiye ta dawo daga skul tana fitowa wanka wayanta ya soma ringing,d'agawa tayi ganin sunanshi yace " Yanzunnan ki kawomun abinci yunwa nakeji" cikin takaici tamkar zatayi kuka tace

"yaya yau ba abunda naci wlhy yanzunnan na dawo daga skul ko sallah banyiba dan Allah kace Aunty haleemah ta baka mana" wani mirmurshin mugunta yayi da har tana jiyo sautinsa yace " Ita d'inma yunwa takeji kuma yauma agajiye ta dawo ke muke jira ki bamu abinci kuma 1 hour kawai na baki" yana kaiwa nan ya ajiye wayar,cikeda takaici taje kitchen ta dafa musu sphagetty bolognese da orange juice tafita kaimu su haushi tamkar ta had'iye zuciya ta mutu,da sallama tashiga parlor din amma abun mamaki se numfarfashi take jiyowa juyawan dazatayi tagansu akwance suna kissing junansu shaam se shashafa leemah yakeyi yana mamatsa breast dinta kai abubuwan data gani sam bazasu fad'uba,wani takaicine ya taso ya tarnaqeta a wannan lokacin ji hafsat keyi tamkar ga kashe kanta har lahira,da kyar tayi karfin halin zuwa dininga tabajiye kayan ta juya,abunda yafi bqanta ranta shine yanda sukayi tammar basu ganta ba kuma sarai ta sani dukkaninsu ba wanda be sanda zuwanta ba wani abin ma har da gayya suke yinshi,wanda sosai ta kula Aunty haleema wannan surutun datakeyi danta gantane,a wannan ranar kuka hafsat ta kwanayi ko abunci bata iyaci,Allah sarki qaramar yarinya akace ana wata ga wata domin kuwa tun daga sanda hafsat ta gansu a haka se wani azababben sha'awa yake taso mata gashi wannan lokacin ne tashen balagarta seta rasa yanda zatayi a haka take danne zuciyarta tana adu'a Allah ya kawo mata d'auki...

Ranar wata juma'a bayan sallan isha tashiga part din haleemah sabida tanasan ganin yaa shaam akan zancen bikin huda dayake wani satin za'ayi tana zuwa kofar d'kin tajuyosu suna iskancin nasu dasuke ihu sekace wasu maguna,juyowa tayi cikeda takaici anan taci karo da abinda tangamemen tv n dake parlor din ke haskawa wato BF,gabanta ne ya fad'i ganin me akeyi take taja baya se kuma wata zuciyar tace kindaiji ana labari amma yaune ganinki na farko,jeki ki kalla...da wannan ta tsaya ta kurawa tvn idon tana kalon masha'an da ake tafkawa rashin kunya iri iri,dakyar ta dakatar ta juya zuwa part d'inta jikinta har rawa yakeyi wasu abubuwa takeji suna mata yawo kasa haqura tayi da tambayoyin da zuciyar ta ta gaya mata ta zari key na motarta zuwa gidansu huda......kallon huda tayi bayan sun zauna a d'akinta tace bayan ta tattare nutsuwarta zuwaga hudan

" friend mene ne sha'awa? Yaya kakeji idan kanajin sha'awa?" kallon mamaki hudan ta mata tace "Ban fahimcekiba?" sosa kanta tayi ta labarto mata tun farkon ganinta dasu shaam dakuma abu da ta gani ayau,ta qara da cewar "Huda wasu lokutan sena kasa bacci kinga har kuka nakeyi sena ringajin ina matukar sanjin abinda Aunty leemah keji tana sambatu idan yaa shaam yana mata wannan abun,kuma kinga yau danaga turawannan suna wannan abun sena ringa jin dadi sosai nima inaso kuma naji na rage yawan sha'awa shine nakesan siya nakuma ana yawan cewa haramun ne kallon wayannan abubuwan kuma yana saurin kashe ido?" cikeda tsoro huda tace

"kinga hafsat wlhy ki kama kanki,inake ina kallon wannan abun?? Masu siyarwa ma karuwai kad'ai suka san inda suke masu browsing a waya kuma wlhy duniya tana kallonsu sosai da sosai,sa'annan na kula kinada karfin sha'awa sabida haka wlhy kine ki samu mijinki kice dashi kina buqatarsa inba haka ba wahala tana ganinji,kuma wlhy idan nakuma jin wai zaki siya wayannan mugayen films senaje na fadawa momy,ki barsu yaa shaam matarshi batada maraba da karuwa wlhy ni sunaso su b'atamun ke,wainikam ma tukunna tsaya sanar dani kina yawan adu'a da tsayuwar dare?? Kuma kina azkhar?" dan sosa kanta tayi tace "Gaskia bana,wani yi ina dai adu'a"

"Toki riqayi akan mijinki da duk wata damuwarki kinji huda,adua yana da kyau da kyautata ibadu yawan yin azumin nafila da sallar nafila dakuma azkhar,kina yiwa qananan yara sadaka tunda baki rasa ba kinji,ki cire ranki da wannan mugun kallon indai ba wuta tsundum kikeso kije ba,kuma masu san kalllon wannan ma idan suka saba basa iya denawa,sekiga idan ba namiji a tare dasu suna yiwa kansu abubuwa da hannu kuma wlhy masifa ne Allah ma yayi alkawari. Azabtar da masu irin wannan mugun aikin,seki kiyaye kinji qawata" gyada kanta tayi alamar gamsuwa sannan tamata sallama tabar gidan,huda se tausayinta takeji matuka.......hafsat se tunanin rayuwarta takeyi da abubuwan ban mamaki datake ta faman gani arayuwa,a haka ta isa gidan cikeda damuwa,a harabar ajiye motocin gidan taci karo da yaa shaam tamkar bashiba,bashida niyyan koda kallonta ne balantana yamata magana,da sauri ta qarasa gunshi

"yaa shaam ina wuni?" "Lapiya" ya amsa a taqaice yana shirin shigewa motarsa takuma kallonshi tace " yaa shaam magana nakeso muyi" batare daya kalletaba yace "Enhmm"

"Dama nikam wai yaya banida wani haqqi a gidannan ne koda na kwana a part dinane yanzu kusan watannina biyar agidannan amma koso daya baka taba kwana bangarena ba atare dani" wani kallo ya wurgo mata ya murtuke fuska sannan yace

"Idan tunanin kike kinada wani haqqi a kaina to kuwa kinyi babban kuskure domin nidai,ni shaam wlhy nafi kardinki sam *Bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane* bakida wani abu ajikinki ko a fuska daze gayyaceni kwana sashen ki,sa annan kuma bakida wani diri na ya mace dage gayyaceni zuwa shimfidarki,wlhy Hafsat bakida banbanci da namiji awurina,iyayenki sun cuceki domin nidai bazan taba iya furta kalmar saki agarekiba kamar yanda bazan taba iya makwanci dakeba sabida haka idan ma mafarki toki farka samni kam bana san mace sekace tsinken stintsiya se dare kamar wani daren yunwa,kuma me harma kinyi girman dazaki tareni da wani haqqinki wlhy kika kuma mun irin wannan maganar sena tattaki mara kunya fitsararriya haqqin uban wahe dake a hannuna sekace da yunwa take kwana a gidan" batare datace komai ba tayi ciki aranta tace "Nice ma bankai mace ba,nice ma ban isa yasoni ba,nice banida banbanci da tsinken tsintsiya" ko wannan daren hafsat kasa bacci tayi kuma se zazzab'i me zafi ya rufeta Allah ya taimaketa ta kammala exams nata gaba d'aya........washe gari yayi kiranta wai tasan haleemah nada juna biyu bata iyacin abinda ta girka ta kawo mata abunci,tace dashi "yaa shaam nima a kwance nake ko bacci banyiba wlhy banida lapiya" tsaki yaja yace wai mintuna talatin yabata ta kawo kalacin....

Mom Nu'aiym [1/21, 7:15 AM] Mmn Sadeeq: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅

Love story 2018

Billy galadanchi

*HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)

*Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*

*Wannan shafin nakine maryam Abdullahi gumel,nagode da qaunarki agareni*

10 Tunda hafsat tashiga gida take rusar uban kuka daganan tayi alqawarin ficewa sha'anin yaa shaam koda kuwa soyayyar sa zata hallakar da ita har abada.....da wannan ta mayarda hankalinta akan karatunta matsalar fa d'aya tsananin sha'awar dake damunta kullum ba dare ba rana,ta rasa yanda zatayi da kanta kuma tayi alqawarin koda huda bazata sake sanarwa da duk wata matsala tata ba zata qalubalanci rayuwarta ita daya, amma fa sam bata acikin walwala.....yau dai shirin zuwa gidan momy tayi sabida sunday ne ba school,harta shiga mota yaa shaam ya tsaidata "Kije ki dafa mana abinci sabida Babyn shaam bata da lapiya kin kuma sani sarai tanada juna biyu bata iya cin abinda ta girka" tamkar zata yi kuka haka ta ji amma seta daure batace komai ba tafito zuwa cikin gidan,a bangarenta ta girka komai sannan ta shirya ta dauka takai bangaren haleemah,tana zuwa ta ajiye a dining ta sanar musu,seda haleemah ta kalleta sannan tace,cikeda sigar rarrashi "Dan Allah hafsat kiyi hakuri wlhy bazan iya cin komai ba se indomie,ki daure ki taimaka ki girkamun" kallon mamaki tabita dashi sannan batare datace komai ba ta juya zuwa ktchn din a gurguje gani karfe uku ta gota momy se waya take mata akan bata zoba ta dafa ta kawo mata,har takai kofar barin parlor din tajiyo karar daya bata mamaki "Nashiga ukuna ni haleemah,wlhy boo me baran iya ciba yaji ne aciki sosai ga kuma magi yamun yawa" wani mugun kallo shaam ya wurgawa hafsat

"muguwar yarinya dawo nan ai kinsan muguntar da kika kullah me baqar zuciya,dan ubanki da dakikasan bazaki iyaba meya hanaki kanki tsaye kice bazakiyiba,wato wannan cikin na jikinta shi kikeso ki kashe ko? Muguwar banza muguwar wofi wlhy yau bama inda zaki,kin dinga girka mata indomie kenan se sanda kika girka mata kalan wanda tace ya mata" kan tayi magana kuka ya kwace mata se kuma wayanta ya soma ringing,dagawa tayi tana me hadiye kukan lokaci daya ta qaqalo murmushin daya baiwa shaam mamaki takuma saisaita muryanta

"Momy dan Allah kiyi hakuri,wlhy Aunty Haleema ne batada lapiya inaga kamar bazan samu damar shigowa ba yau,kinga ita kadaice bazan barta haka ba" murmushi momyn tayi tace "Eyyah Allah sarki Allah ya bata lapiya ki gaida ta kinji,yanzu se yaushe??"

"gobe sha biyu nake qare lectures inshaa Allah daga school se gidanki momy karki damu" "To Allah ya kaimu hafsat Allah ya miki albarka kinji" Ameen kawai tace ta ajiye wayan sannan ta juya zuwa kitchn din,dafa wani tayi bata saka yaji ba ta kawo,ai loman farko ta zubar aqasa ta kalli yaa shaam fuskar nan harta soma kawo ruwa "Yaa shaam kaci kaji wlhy ba taste yanzu fa ko d'an green pepper ta saka man amma haka tayishi,Allah ni bazan ciba kuma" Tsaki hafsat taja bada shirinta,dama fa hafsat gwanar rashin kunya ce kurin tsoron yaa shaam ne ke durqusar da ita,yau kam ta cika fam

"Gaskiya Aunty haleema bansan ya kikeso na miki ba na dafa wancan kince bazakiciba na dafa wannan indomie kince yaji,na kuma dafa wani kince ba yaji ni kije ki dafa da kanki,ko aikin bauta nazo na muku wlhy ko zaku kasheni bazan dafa muku wani ba" kallon mamaki shaam ya mata domin shi har tasoma bashi tausayi ya matso kusa da ita yace "Jeki kitchen ki dafa mata me abunda takeso" tsayuwa tayi a wurin taqi koda motsi,saukar wani kyakyawan mari taji seda ta ga wasu taurari na musamman,yace "ina wasa dakene? Nace kije ki dafa mata wani" kamar yanda batayi magana ba haka bata koda motsa ba da wannan ya shaam ya soma dukanta tamkar wani mahaukaci baji ba gani seda haleemah taga tayi lilis sannan ta saka kukan muna furci tazo tana qwatar hafsat "shaam dan Allah kayi hak'uri,idan ka illatar da qanwarka ni za'aga laifina kuma kaga ai tama gaji ni dama ba ina nufin ta dafa wani bane,nama ji na qoshi tea ma ya isheni,miqewa tayi tsaye ita kuwa tayi hanyar waje har wannan lokacin bakinta be mutuba tana kaiwa kofa tace "kuma wlhy ko zaku kasheni na dena muku girki kenan har abada" bebi ta kanta ba ya dawo wurin haleemh da rarrashi......

Bayan magrib tana d'akinta tana rusar uban kuka abinta shaam ya shigo,zama yayi kusa da ita da yace "Hafsat ni kikewa baqar magana??" bata kulashiba yace "Kinaso na ci gaba da lallasaki kenan?" budar bakinta se cewa tayi

"ka lallasanin ai akwai Allah,kuma wlhy duk wanda yaci zalina Allah ya isa" mamakin kalamanta yakeyi "waye yake koyar dake rashin kunya hafsat?" nurguda bakinta tayi sannan tace

"Wanda suke cin zalina kullum kuma Allah ya isa" miqewa yayi yace "hafsat kin janyowa kanki zaman bakar uquba a gidannan sabida kinga ina miki wasa shine kikemun wulaknci san ranki ko? Wato ke kin isa lallai kuwa zakisha baqar wuya a hannuna" bata kulashiba taci gaba da kukanta yayi ficewarshi yana mejin tsananin tsanar hafsat,tundaga wannan ranar kuwa shaam komai qanqantar laifi idan hafsat ta masa se duka har yakasance daga dazan ya sanyata abu jikinta ze soma rawa,kuma da sauri takeyi,sedai kwanakinnan batada lapiya ko kadan, da wannan ta sameshi tace dashi "Yaa shaam kwanakinnan da zazzab'i sosai nake kwana ko zakaje dani clinic dinka a dubani" kallon ta yayi ya rufe jaridar dake hannunshi " A matsayinki nawa zakijemun clinic? Kinga nawa clinic ma na masu matsalar zuciyane,sabida haka kije wani asibitin kawai" batace masa komai ba taje gun huda daganan suka wuce wurin mijin ta dayake shima likitane,binciken farko ya fito da tambarin heart problem ajiki,sosai sadeeq ya shiga cikin shock,huda ya fara kira a gefe yace

"Baby wai anya qawarki ba kashe kanta takeso tayi akarin banza ba @kan soyayya kinsan kuwa ciwon zuciyane da ita,fisa bilillah @her age gaskiya bance ba'a samun irin wayannan cases dinba sabida yanzu irin wayannan cutukan sun yi yawa a wurin yarama harda hawan jini,amma ni tausayi take bani gaskiya me take sakawa a zuci har haka,jininta mafa hawa yakeyi" dafe kai huda tayi tace dashi "Hubby kasanme har fa dukanta yakeyi sannan ko kwanciyar aure bayayi da ita,ga school ga problem dinshi girki mafa ita kewa matarshi ko sau daya betaba kwana a bangarentaba,ga hafsat da zurfin ciki tacika barwa kanta abubuwa ni wlhy har naji kaina yana ciwo ma,yanzu meye solution?" dafe kanshi yayi yace "Amma gaskiya shaam ya bani kunya wane irin sakarai ne qanwarka guda daya matar da iyayenta suka nuna maka so tamkar sune suka haifeka shine tsabar mugunta yarinya ko 17 bata hada ba zaka hadata da ciwon zuciya mugun banza" wurin hafsa suka koma dakyar sadiq ya tattaro nutsuwarsa ya shaidawa hafsat komai cikeda rarrashi da nuna mata hanyoyin dazatabi tunda abin beyi nisaba,sosai hafsat tayi kuka sannan ta nuna musu su rufa mata asiri karsu sanar wa kowa,hakan dai aka bata magunguna ta koma gida da damuwa me dinbin yawa wacce ta ninka tada,tundaga wannan lokacin hafsat ta dawo sukuku sam bata walwala gashi batada lapiya a haka har Haleemah ta haifi yaro namiji,wanda bataje wankan gidan ba kuma tanayin 40 days aka maidashi kwana wurin hafsat,komai wahalar khaleefa hafsat keyi baji ba gani, harma ya saba sedai yasha madara wasu lokutan idan ya tashi a bacci da dare ya saka kuka setayi ta rarshinsa idan yaqi itabdinma seta saka mar kuka suyitayi se me aikinta tazo ta karb'eshi.......a haka har khaleefa yayi wata hudu a duniya,san suniya shaam ya dauka ya daura akan yaronnan bama a san ranshi yake barinshi kwana acan ba,danma bayason bacin ran haleema na......

Ranar wata juma'a Cikin dare khaleefa ya tashi da wani irin ciwon da hafsat ta kasa gane na menene,kuka yake tayi tamkar me yana zabure zabure,hankalin hafsat ya tashi ta dauki wayarta tayita kiran shaam baya dagawa,takira haleemah akayi rejectin call din sannan kuma aka kashe ma wayar gaba daya,shaam yaga ta kuma kiranshi yace "Haleemah lafiya kuwa? Kodai in daga inji menene dalilin kiran naga bata taba yin hakan ba?" wani narkewa haleemah tayi tace "Boo me dan Allah manta da ita,nasan kuka khaleefa ke mata shiya sanya kaga ina ce maka akaishi acan kar ya hanamu walawa" biyeta yayi sukayita har kofar gidan tazo ta bubbuga suka mata banza,koda ta koma yaron baya motsi lokacin ma karfe biyar na asuba,da kukanta takira shi again be daga ba,ta aika masa message "Yaa shaam nayita kiranka inaga fa Khaleefa ya rasu" yana fitowa daga gun alwala yaji aran message yaje ya duba a rude ya gayawa haleema da salla be dameta ba tana baccinta aibhar ture juna sukeyi sabida tsabar gidi mewa,banka kofar sukayi suka sameta rungume da gawar tana uban kuka,

"yaa shaam kunga illan rashin daga waya ko? Shine inata kiranku yaron nan se zabura yakeyi amma kuka qi dagawa wlhy kungani ya mutu" ta sake fashewa da kuka,ai shaam na dubawa yaga da gaske ya mutu ya soma jibgar hafsat

"yanzu tsabar bakida mutunci shine kika kashemun yaro,dama wannan qiyayyar taki akanshi ta wuce tunani wlhy kema sena kasheki,jibgarta ya hauyi baji ba gani haleema se kuka takeyi ta dauki gawar se jijigawa takeyi,dakyar yadena dukanta yace dan ubanki kije na sakeki saki d'aya ki barmun gidana........yana kaiwa nan yabar dakin yana me karbar gawar yana kuka,wayanta ta janyo da kyar ta kira Abba haris,yana dagwa dak'yar tace "Abba kazo ka daukeni yaa shammaz ya sakeni kuma so yakeyi ya kasheni da duka,banama iya tashi".............

To jama'a kunjifa yanda ta kasance,anya kuwa shammaz yanada hankali? Anya kuwa wannan halin nashi asirine kawai kodai har da qiyayya da wulaknci? Yaya rayuwa zata juya masa?

Mom Nu'aiym

*Don't forget to vote and comment,ur votes and comments are more important to me than anything plsss do vote for me*

[1/21, 7:15 AM] Mmn Sadeeq: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅

Love story 2018

Billy galadanchi

*HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)

*Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*

Wattpad@ 68billygaladanchi

11

Sosai ran Abba haris yake a b'ace sanda yazo gidan,kai tsaye part d'in hafsat ya wuce ya tarar sabuwar yar aikinta dasuka saba sarai ta tasata agaba tanata kuka ko motsi batayi,da hancinta da bakinta duk jini,sosai ya tsorata bema wani damu shaam sabida bashida abun ce masa ya sakata a mota itada sarai suka nufi asibiti.....waya yayiwa matarshi da dama ya barota hankali a tashe tana salallami akan driver yazo dasu Uduth suna can,Dr. Sayyeed hamid Ali shine dr d'in da ya duba Hafsat sunkai kusan awanni hud'u akanta kafin ta farfad'o,zuwa yayi ya kira Abba haris a office d'inshi ya kalleshi sosai sannan yace

"Sir wannan yarinyar shekarunta nawa ne?" dubanshi abban yayi yace cikin damuwa "shekarunta sha shida inaga nanda watanni biyar zata cike sha bakwai" jinjina kanshi yayi sannan yace "Amma yallab'ai kuna zaune da qanqanuwar yarinyabhar ciwon zuciyata da hawan jini su mata yawa haka,ni fa a gaskiya nasan is very rare kagan yara masu qananun shekaru irin nata suna fama da wannan cutar,sa'annan wannan uban dukan da kuka ce mijinta ya mata kyautuwa ma yayi ku kaishi gun hukuma sabida kuwa ya tab'a wa yarinyar kai, yanzu haka idan ta farfad'o gaba daya bamusan a wanne halin zata tashiba,sabida jini ya taru mata a k'walwarta,rayuwar yarinyar abar tausayi" dafe kai abba haris yayi tare da zare ido waje cikeda kad'uwa yace "wane irin ciwon zuciya da hawan jini kuma likita? Anya hafsat tamu kake magana kuwa?" nisawa Dr. Sayyeed yayi cikeda tausayawa yace 'Alhj wlhy itan kuwa,kana nufi kenan bakusan tana fama da wayannan cututtukan ba? Bincike ya nunar mana cewa har magungunan take sha" A zuciye ya miqe yace "wannan azzalumin mijin nata ya sani sabida kuwa shikeda asibitin zuciya sukutum wacce itace k'wallin k'wal agarinnan,kuma shine babban likitan zuciya" kallonshi sayyeed yayi cikeda mamaki yace "Alhj Karkace dani Dr. Shammaz kake nufi sabida a iya sanina shikad'aine ya mallaki asibitin zuciya me zaman kanta,bazan amince ba idan har kace dani wai shine da kanshi yayiwa matarshi irin wannan dukan" kallonshi Abba yayi cikeda takaici sannan cikin d'acin zuciya ya furta "Amma zaka iya yadda cewar nine mahaifinsa na asali na haihuwa,yayinda mahaifin wannan yarinyar da yayiwa wannan dukan shine mariqinshi shine ya zamto gata agareshi harya kai wannan matsayin dayake kai a yanzu,amma shine tsabar yana butulu ya aikata wa yarshi wannan mummunan ta'adin" sosai wannan maganar ta girgiza Dr.sayyeed ya zare madubin idonshi ya dawo kujerar dake kusa data Abba ya zauna sannan yayi abba nuni da daya kujerar akan shima ya zauna ya ce

"Amma nayi mamakin jin wannan maganar,sabida da badan kai bane mahaifinshi wlhy da bazan yarda ace wai Dr. Shaam ne yayi wannan aikin ba,sabida sanin dana masa mutumin Kirkine kuma kamili,Allah yamana tsari da sharri shaidan,yanzu dai bazamu sanar daku komaiba se yanda bincike ya nuna mana,sabida haka ku bamu nanda yamma seka dawo nan muji koma meye" Godiya Abba haris ya masa sannan ya fice kai tsaye gidan Daddy ya wuce ya tarar ana jajen mutuwar khaleefa,a fusace ya kalli jama'ar dake parlor kasancewar duk yan gidane se daddy da shaam,idonshi yayi jajir tamkar gaushin wuta

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull