Bakin ruhi complt by mrs sadauki - Chapter 25
Bakin ruhi complt by mrs sadauki Chapter 25: Bakin ruhi complt by mrs sadauki Chapter 25. Ta ja wata ajiyar zuciya kafin ta ce "tun bayan tafiyarki…
4,489 words
Ta ja wata ajiyar zuciya kafin ta ce "tun bayan tafiyarki abubuwan da aka saba yi suka ci gaba da tafiya har ma sai da aka samu ƙari.Kusan kullum sai iyayenmu maza sun yi meeting akan wannan ranar wacce za ki dawo,sun yi mata tanadi na musamman don sun sha alwashin naɗa ki sarautar kuma shugaba,sai dai al'amarin da ya faru yasa komai ya rogaje komai ya tsaya cak.A jiya na ji Kawu Hamza na cewa ke ce tushen wannan matsalar ,ko ma mene ne to ke ce sila don haka ko kin zo sai kin bar gidan nan don zamanki a ciki tamkar maido da zaren saƙa gadarsu baya ne, macce-maccen da ake yi sun ɗan tsagaita saboda dukiyar da BAƘIN RUHI ya musu sakayya da ita sai dai fa suna kawo mutanen da ba a cikin ahalinmu suke ba.Haule duk yaron da ya kuskura ya shigo gidan nan to fa ba zai fita ba,in kuma mace ce yadda kika san ana cire ciki daga mahaifar uwarsa haka suke cire budurcinta su miƙawa dodonsu.Gangar jikin kuma in ta yi rai za su haukata ta ko kuma su sa ta bar garin.
A kwanakin baya wani mutum ya zo nan gidan kwana ɗaya yayi kacal aka soma shirin bikin Mardiyya.Manufar auren nasu don ƙarfafa ginin matakin tsaron ɗakinsu na sirri da suka ɓoye dodonsu,kuma sarai iyayenmu maza sun san da cewa ahalin mijin an barranta su saboda yanayin tsafinsu da kuma uwar shirkar da suke yi.
Ita kuma baiwar Allah ta yarda ne tana ta murna saboda kawai ba ta taɓa aure ba,HAULE in da kin ga mijin Mardiyya bai brush haƙoransa yadda kika san masarar yin tuwo haka suke,ba shi ɗaya ba har da family ɗinsa amma a haka ta yarda ta yi auren da bai da amfani kawai don ta gaji da gori.Tun bayan auren hankalin iyayenmu maza ya tashi,saboda ƙofar da ta rage wacce ake iya kutse ta nan har zuwa lokacin ba ta haɗe da juna ba,hakan na nufin Mardiyya ba ta yi abin da ake so ba" shiru Hassana ta yi ,ni kuma na ce "ta ya aka yi kika ga duk abin da ya faru alhalin babu ido a tattare da ke?"
Ta saki wani murmushi kafin ta ce "saboda a baɗini ni ba makauniya ba ce,matar da ta yi mini aikin idon nan ta saka mini wani abu na musamman sannan ita ce ta toshe bakina don kar na yi magana.Kuma na ga amfanin haka don na ji sirrin iyayenmu maza wanda wanzuwata a wuri bai hana su yin hira"
Ban ƙara cewa komai ba ,sai formula da na karanto domin jawo ƙwayoyin idanun Hassana da Papy ya bani.Babu jimawa suka bayyana a tafin hannuna,na buɗe ƙyallen kafin na ɗauki ido ɗaya na saka mata shi ma na biyun haka.Jini ya soma zuba kafin kuma ya tsaya,sai ta dube ni tsakiyar ido ta saki murmushi tana mai cewa "Haule kin ƙara kyawu fa"
Na ce "Yanzu dai je ki kwanta,kuma gobe duk abin da zai faru kar ki fito daga cikin ɗaki ki zauna kawai zan zo gare ki" ta jinjina kai alamar ta ji ta ɗauka,na tarwatse katangun da na yi kafin ta kama gabanta ni kuma na shiga ɗakin Innarmu.
A kwance na tarar da ita kan sallaya tana bacci ,a hankali na taka na je na yi zaune kusa da ita ina mai ci gaba da kallonta kafin .Na kai hannu na shafi gefen fuskarta,cikin baccin ta furta "Haule?"
"Na'am Innarmu " na amsa,tarau ta buɗe idonta ƙila don jin muryata ne. "Haule ke ce ko kuwa mafarkin da na saba yi ne?"
"Ni ce da kaina Innarmu"
Da sauri ta tashi zaune tana kallona kafin ta kamo tafukan hannuna,hawaye ta soma yi suna ɗiga kafin ta soma magana cikin taushin murya "alhamdullah! Na gode ma Allah da ya nuna mini wannan rana,na jima ina tsamumaye sai yau Allah yayi nufi .Ina shi mijin naki?"
Na ɗan murmusa ina tunanin ko yaya MAHEER zai ji in ya duba bai ganni ba? Ko wane hali zai shiga a tsawon kwanakin da zai yi ba tare da ina kusa da shi ba? "Fatan dai yana lafiya ko?" Inna ta katse ni.
Na ce "eh lafiyarsa lau.Innarmu ashe shi ma Fahad ya rasu?" sai kuma hawaye suka ciko idona,Innarmu ta yi wani murmushi wanda ya fi kuka ciwo kafin ta ce "na ga rayuwa Haule amma yanzu ai komai ya zo ƙarshe tun da ga shi kin zo,shawarar da nake baki dai ki sa a ranki girman al'umma ya fi komai kar ji tsoro ko tausayin kashe wanda BAƘIN RUHI ke a cikin gangar jikinsa ko da kuwa Abbanki ne"
"Abba kuma Innarmu?"
"Eh yana ɗaya daga cikin makircin esprit sai su yi wasa da hankalin mutane su shiga a jikin wanda ba za ka iya ɗaukar mataki ba a kansa"
"Amma Innarmu..." da sauri ta katse ni tana mai cewa "zo ki kwanta HAULE " ban musa ba na tashi na kwanta kan shimfiɗarta,ido na lumshe ina jin wani daɗi na luluɓe ni yayin da kuma wani ɓangare nake cike da kewar mijina.Tunaninsa na yi ƙoƙarin lalubowa amma abin mamaki na kasa,ban san dalili ba kuma a haka dai na samu bacci ɓarawo ya ɗauke ni.
★A can ɓangaren MAHEER kuwa yana fitowa daga toilet ya ga babu HAULE ,tamkar wani mahaukaci haka ya soma duba ko ina na ɗakin amma babu ko da inuwarta ne.Cikin azama ya fito ya dinga dube-dube,sai dai kaf cikin asibitin ba ta nan.Ji yayi kansa na mugun sara masa,dakyar ya iya fita can harabar asibitin inda ya aje motarsa ya shiga yayi mata key sai gida.
A buɗe ya tarar da falon hakan yasa ya kutsa kai yana mai faman kiran sunanta amma shiru sai Hajiya ce ta fito take tambayarsa lafiya.
"Queen ce Mama ban gan ta ba,ba ta asibiti na duba ko ina fa"
Hankali ya yi wani mummunan tashi,murya na rawa ta ce " ban gane ba ta can asibiti,to ina za ta je? Bari na dubo ɗakinsu" Hajiya ta faɗa tare da shiga can amma iya su anty Bahijja kawai ta gani a kwance suna bacci har za ta fito sai ta ji motsi a toilet sai ta ce "Haule? Haule ke ce a toilet?"
Ambaton sunan HAULE shi ya tayar da Aliya daga bacci,yayin da kuma Lubna ta fito daga toilet daidai nan kuma MAHEER shi ma ya iso ɗakin duk da kuwa dare ne bai kamata a ce ya shigo ba.
Yadda duk kowa ya tayar da hankalinsa aka shiga duba Haule ta ko ina yasa Ikilima wacce ke can ƙumshe da baƙin ciki ita ma ta ji hayaniyarsu har ta fito,ba ta tambayi kowa meke faruwa ba amma yadda ta ga kaf ahalin su MAHEER waɗanda suka kwana a nan su ma sun tashi kuma hankalinsu duk a kansa yasa ta samo bakin zaren.
Ƙarin daɗa kuma fa da ta ji MAHEER na cewa "duk wanda ma ya san inda take gwara ya faɗa kafin na yi masa abin da bai yi zato ba" da sauri Ikilima ta bar wurin ta koma ɗakinta ta ɗauki waya ta kira Umma, ita kuwa sokuwa duk a tunaninta aikin da boka ne yayi mata ya ci sai kawai ta saki baki ta soma yin magana "to gobe tun da safe ki zo mu je mu yi masa godiya,ladar bayansa shine ki basa haɗin kai sannan ki tabbatar dai yau MAHEER ya kusance ki .Maganin da na baki ki ɗauke shi ki turara shi"
"Amma Umma ba shi ɗaya ba ne a falon ba"
"Babu ruwanki da sauran mutane ,ai iya shi ɗaya kawai maganin zai shafa"
Ita kuwa Ikilima jikinta na rawa ta ɗauko gawayin nan na zamani ta kunna ashana bayan ta tabbatar ya kama sai ta fita falo inda suke ta neman mafita.
Aliya na tsaka da cewa "Oga ni a tunanina mu je can asibitin mu duba Camera tsaro,in ma dai sace ta aka yi za mu gani in kuma Camera ba ta yi ba to...to ..to" tari ne ya hana ta ƙarasa abin da take son faɗa sakamakon hayaƙin da ya turniƙe wurin,duk kowa ya shiga yin tari banda MAHEER da ya kafe Ikilima da ido ita ma shi take kallo da idonta da suka yi ja kamar na tsohuwar mayya.Jikinta na ƴar kyarma ta ajiye mangal ɗin turaren,tana shirin yin kisisina don jawo hankalin MAHEER ta kai shi can ɗakinsu kawai ta ga yayi ball da mangal ɗin yayi sama tare da bugun fuskarta kafin ya faɗo ƙasa.
Ransa a mugun ɓace ya nufi ƙofar fita tare da cewa Aliya "zo mu je" da sauri ta bi bayansa ,suka shiga mota suka isa asibiti.
Camerorin tsaro ya shiga dubawa musamman na ɓangaren ɗakin da Haule ta kwanta,a hankali suka ga ƙofar ta buɗe amma babu kowa wanda ya fito haka suka dinga kallon yaɗa ƙofofi ke buɗe kansu da kuma rufe kansu amma kowa,da aka zo harabar asibiti ne suka hango idon magen da ta ɗauki Haule shi ma iya idonta ne kawai waɗanda suke ƙyalli.
Aliya ta ja ajiyar zuciya tana mai cewa "ta tafi gidansu"
MAHEER ya dube ta ya ce "ta ya aka yi kika gane?"
"Ga idon Roza nan na gani,magen maɗaukakiyar FARIN RUHI ce.Ka kwantar da hankalinka babu abin da zai same ta,yanzu tana da ƙarfin iko sosai wanda take iya tunkarar kasada kowacce iri" Sai a lokacin MAHEER kawai ya ji hankalinsa ya ɗan kwanta.
★ HAULE
A cikin baccin da na soma ne na soma jin wani irin yanayi,yau shi ne farko da na ga ruhina ya bar gangar jikina zai yawo a cikin doron duniya.Balaguron ruhi ne,haka na fita daga gidanmu na bar gangar jikina a kwance a ɗakin Innarmu.
Gidaje na ƙetare har na isa can gidan Anty Mardiyya,tun a cikin soro na ci karo da ƙaton kai na Saniya an rataya masa layu sun fi kwano biyu sannan ga wasu rubuce-rubuce a bango da tambarin aljanu.A nan take duk na wargaza komai na ƙona su,hakan ya jawo hankulan ƴan gidan waɗanda kallo ɗaya za ka yi musu ka ga yadda tsafi da shirka ke yi musu ƙawa.
Duk iya shegensu ba su iya hango ruhina ba,haka na soma bincikar gidan har Allah yasa na ga baƙar rijiyar da suka jefa anty Mardiyya.A hankali na buɗe murfin sannan na shiga ciki,wurin baƙi ƙirin yake,amma shiga ta a ciki farin ruhina ya haskaka shi.Ban sha wahala ba na hango ta a zaune a ɗaure da wasu igiyoyi,tuni ta fice hayyacinta ni ce na cece ta na fito da ita daga cikin rijiyar.
Muna dab da fita na ji wata murya na tsayar da ni,na juyo muka haɗa ido ban san ma ta ya aka yi ba har ta iya ganina ba.
Ba tare da na tambaye ta ba ta soma bani labarin kanta wanda yasa na fahimci cewa ashe ba iya family ɗinmu ba ne kawai suka ƙware wurin tsafi ko kuma ɓoye wani sirrin,tabbas kowanne ahalin dai yana da wani sirri.
"Ina buƙatar taimakonki,ina tsakanin rai ko mutuwa nan ɗin gidan Uncle ɗina ne .Amma ni a yanzu ban san taƙamaimai ni wace ce ba,amma zan sanar da ke labarina duk da yana da tsayi amma zan sauƙaƙa shi ta hanyar gajarce shi .Tun lokacin da aka haife ni aka sayar da ruhina ga duniyar ɓoye,an yi ƙoƙarin kashe ni ta kowacce siga saboda a cikin family namu akwai wani mai ɓoyayyar fuska,ko kuma na ce mutum da rigar aljan wanda yake sayar da ƴaƴan ƴan uwansa domin samun ƙarfin iko da kuma arziki.Wannan mutumin ba kowa ba ne sai Kawuna,mugun mutumin nan yana ɗauke da wata baƙar takardar mai jerin sunayen rayukan da ya ɗauka,a samanta kuma ni ce ta gaba wacce zai kashe .Yadda nake mai riƙo da addini ne yasa har yanzu ya kasa kai ni ƙasa,amma duk da haka ya toshe hasken taurarina sannan yana yi mini izaya ta hanyar turo mini fatale suna firgita ni,duk inda zan je kuma sai sharrinsa ya bi ni wani sa'in sai ina tsaka da tafiya sai na koma mahaukaciya na cire duk suturar jikina,haka kuma duk dare na Allah haka ruhinsa ke zuwa yana amfani da ni da na gaji da yawo shi ne na zo na tare gidansa kamar yadda ya buƙata tun farko babu laifi ya bar yi mini izaya sai dai fa ban iya fita daga gidan"
"In kin fita daga nan za ki iya gane gidanku?" na tambaye ta,ta bani kuwa amsa da eh kawai sai na kamo hannunta muka fito.Sai a lokacin na rufe duk wata hanya sannan na cillawa gidan wuta ,na yi amfani da furicin Aliya ne a ranar da ta kashe matar nan da ta kashe ƴaƴan kishiyarta,tabbas akwai mutanen da in an samu dama kawai kashe su shi ne ya fi zama alkhairi.
Ita kuwa Anty Mardiyya sai da na zo tsakiyar gidanmu sannan na kwantar da ita na wuce ɗaki,na tarar da Innarmu a tsaye gaban gangar jikina tana tashe ni.Da sauri na mayar da ruhina a ciki kafin na buɗe ido na ce "na'am Inna"
"Tashi ki yi alwala " shi ne kawai abin da ta faɗa ,kamar yadda ta ce haka ɗin na yi na je na yi alwala na yi sallah bayan mun gama muka soma taɓa hira ina ta bata labarin su Lubna da Aliya .Can kuma na sauya zuwa na MAHEER ina jin zuciyata na yin sanyi,muna tsaka da nishaɗi aka turo ƙofa Abba ne fuskar nan tasa tamau babu annuri kafin na yi yunƙurin furta kalmar gaisuwa sai cewa yayi "ki zo ke da ƴarki a ɗakin hukunci" yana gama faɗa ya fice yayin da kuma na ga hankalin Innarmu ya tashi sosai,har ya kai na tambayi kaina a zuci 'yaushe kuma aka yi wani ɗakin hukunci ban sani ba? Me ake yi a can ɗin me kuma ya ƙunsa?????"
🌻🌟🌻🌟🌻⭐🌻⭐🌻⭐🌻🌟🌻🌟
*_GYARA SHINE MACE_*
*_shahararriyar Mai Saida kayan Matan nan maman Yusuf likitar mata sokoto kuma CEO ta SOKOTO TOP 3 KAYAN MATA SOKOTO mai gyaran mata ciki da waje ta sake zo maku da zafafan Kayan masu kyau da inganci don farincinku a kullum shine burinmu* 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*Ina uwargida da Amarya ina masu shirin yin aure budare da zawarawa , ina masu son su zama taurari ✨🌟ababen alfaharin mazajensu , ina mata masu kishiyoyi da ake ci masu zarafi ake wulakantasu akan kishiyoyin su ina wacce keshan wulakancin namiji , ina matan da sukeson burge mazajensu da zallan ni'ima da dandano ??? Ina matan fake fama da rashin ni'ima , budewar gaba wadan da suka faru sanadin ciyon sanyi kokuma haihuwa , ko wadda Ke fama da k'arancin ni'ima da karancin sha'awa , ?? To saurara kiji*✋🏻✋🏻✋🏻
*Ko kinsan Maman Yusuf Dr mata kuwa ?? Hmmm akace in bakasan gari ba to ka saurari daka*,💃🏻💃🏻 *Namu na dabanne kamar yadda salonmu yake daban ingantattun kaya ne da basuda wata illa ajiki sannan ba boka ba malam zaki mallaki mijinki da dandanonki sai yadda kikayi dashi*
Duk abunda kk so a bangaren kayan mata zaki samu hajiyata daga gyaran ciki harma Dana waje
Munada ingantaccen maganin sanyi na maza Dana mata hakama maganin Basir
Maganin nono Dana hips Maganin kiba dakuma maganin rage tumbi da kibar, Maganin gashi
Sabulun wanka na gyaran jiki Sabulun dilka na amare Dilkar amare
Kwallin mallaka (daga ni sai kai) Maltinar mata Bobintan mata Set na lalata gindin kiahiya Set na ukku bala'i Set na rantse bakida kishiya,
Kalolin gumba Kalolin gari Kalolin matsi Kalolin sabulan tsarki Zumar mata Zumar ridi Zumar goron tula Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin sabon budurci Tsumin kankana Tsumin tabaje Tsumin makalemata Shayin mata Sirrikan mallaka Dan goshi da mahadinshi Dan goshi na Mara Kyallen al'ajabu Rakumi da akala Bita zai zai Dahuwar kalolin kaza zabo zakara Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar zuciya Dambun nama Dahuwar yan shila Yajin mata Yajin maza domin Karin karfi
*Hmmmmmm in nace sai na lissafamuku zafafan kayan nan sai in wuni ina typing shawara daya zan baki uwargida in har baki jaraba kayan mmn Yusuf ba to ki garzaya ki saya da kanki zakizo kina godiya , 😉😉😉😉😉😍 wadan da suka San ya kayan suke kuwa. Basa bukatar wani Karin bayani , Domin Neman Karin bayani kokuma ganin kayan da nake dasu Ku tuntubeni ta wannan number 07069711327 call or WhatsApp mmn Yusuf mai kayan mata🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰
Ina bada sari ina sokoto ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah , Don Allah in baki shirya siyaba to kibari sai kin shirya sai muyi magana🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 My book is only 500 via
2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank
DM +22795045822.
🔞In kin san ba ki biya ba kar ki karanta min book,yin haka babban kuskure ne don cin haƙin da ba naki ba ne.Kuma Allah ba yafe haƙin wani akan na wani,don haka kar ki raina girman haƙi komai ƙanƙantarsa.
__________________________________________________ *PAID PAGE*
38
Yadda na ga hankalin Innarmu ya tashi sosai yasa na tambaye ta "yaushe kuma aka yi wani ɗakin hukunci? " ba ta iya bani amsa ba ,sai miƙewa da ta yi a dole ni ma na tashi .Tana gaba ina bin ta a baya har muka isa wani ɗaki,duk iyayenmu maza suna a zaune kowanne ya ɗaure fuska kamar tsohon kashi.
Innarmu ta zube ƙasa kan jan capet ɗin da ke malaye a ɗakin tana mai furta,"ko ma dai wanda irin hukunci ne za ku yi mata ni na ɗauka ku yi mini madadinta " da sauri na je na kama kafaɗun Innarmu ina son miƙar da ita,amma Kawu Hamza ya daka mini wata irin tsawa yana mai cewa "nan ɗin ni ne mai magana da kuma bada izinin kowanne motsi don haka ki zube gwiwanki ƙasa" a yadda na fahimta yayi haka ne don ganin shin ina da ƙarfin ikon ko kuwa dai su ne suke hasashe .Rawar jikin ƙarya na ɗauka kafin na zube kamar yadda ya ce ɗin,sai na ga suna ƴar kallon-kallon tsakaninsu.
"Tsawon shekarun nan kina ina ? Muna saurarenki muna son jin inda kika je ba tare da kin waiwayi gida ba" Kawu Hamza ya sake faɗa .
Idona ya kawo ruwa na soma kyarma tare da soma basu haƙuri,ganin haka yasa ya ce mu tashi mu fita.Innarmu ta fara miƙewa sannan ni,haka muka baro ɗakin muka dawo nata.Muna shiga ta tsure ni da ido kafin ta ce "ya aka yi kika iya sarrafa su? "
"Babu komai Innarmu kawai dai gaskiya ce ke son yin aikinta "
"Ya kamata ki gaggauta aiwatar da abin da ya kawo ki kafin su gano gaskiyar "
"Zan yi Innarmu amma sai zuwa dare" haka muka dinga yin hira har hantsi yayi muka yi wanka muka fito,sai a lokacin ƴan gidan suka san da na dawo yayin da kuma lokaci zuwa lokaci suke taɓo zancen gidan surukan anty Mardiyya ya ƙone ƙurmus Allah yayi mata awon arziki ita ba ta ciki.
Kan dianing masu aiki suka jera abincin breakfast,sai na ga abin banbarakwai don saman tabarma muka saba ci.Tashi na yi na ɗauki plate na zuba kafin na nufi ɗakinsu Hassana,tana kwance tana kallon sama na yi mata sallama ta amsa kafin ta tashi zaune.
Kusa da ita na zauna muna kallon juna muna murmushi kafin mu soma cin abincin,na ce "Hassana a cikin moments ɗinmu na baya wanne ne ya fi burge ki wanda yanzu kuma gidan nan ba a yinsa?"
Ta ce "cin abinci a faranti guda bayan mun gama kuma a yi gatana"
"Ni kuma ɗebo ruwa a rijiya,saboda a can ne tushen samo bakin zaren da muka yi a yanzu ya fara."
"Ba ki bani labarinki ba ,ya kika ji lokacin da kika bar gida har ta ya kika iya zama a wurin da babu Innarki?"
Na ɗan murmusa kafin na bata labarina a taƙaice,ta waro ido bayan ta gama ji ta ce "yanzu nan kina da aure Haule? Kam! Na so in ga mijinki kuwa"
"Kyakkyawa ne kuwa irin sosai ɗin nan, kuma inda kin ga yadda yake mugun sona "
Hassana ta ja numfashi kafin ta ce "ke ma ai kina sonsa sosai ,a yadda kike zuba wannan fara'a"
"Eh yanzu ma ji nake kamar na gansa a gabana "
"Da zarar kin yi aikin da kika zo ai shikenan "
"Wane aiki?". Goggo Lami ta faɗa wacce shigowarta kenan. Duk shiru muka yi muna kallonta,ba zan taɓa mantawa ba shekarun baya ma ta taɓa rutsa mu muna hira.Ban ɗauki tsawon lokaci ba na yi amfani da power na juye mata tunani akan abin da ta ji,sai kuma ta saki murmushi kafin ta ce "ah Haule ashe nan kika shigo?"
"Eh abinci muke ci " na bata amsa,ita kuwa fita ta yi ta bar mu nan.
Hassana ta ce "Haule mene ne kika yi a yanzu? Na ga idonki sun koma sak na mage"
Na ce "ina tsoron ta je ta sake faɗawa wani hirarmu shi yasa,amma ban yi don cutar da ita ba"
"Haka ne,yanzu yaushe kike tunanin shiga can?"
"Tare za mu je ai" na bata amsa nan kuma muka ci gaba da tattaunawa.
A can ɓangaren su Kawu Hamza kuwa sun gwada Haule ne kamar yadda ta yi tunani,sai dai fa ba wai sun bar ta ne ta tafi ba wai don sun gamsu ba a'a idonsu na kanta.
Kawu Laminu ya ce "hum! Kana ganin idon Haule ka san ba ita ce ta farko ba"
Kawu Hamza ya ce "tsorona dai guda kar a je wajen guje-gujen barin gida a ce sai da ta yi yawon ta zubar don kamar a cikakkiyar mace nake hango idonta,in kuwa haka ne kun san halin Maitama ba zai yarda ya zubar da makaman yaƙin ba kamar yadda ya faɗa lokacin da ya nemi a aura musu Haule "
"Ni kam Ibrahim ya na ji ka yi shiru? Fatan dai ba za ka bamu matsala ba in muka tabbatar Haule ce matsalarmu"
Ibrahim wanda ya kasance mahaifin Haule ya ce "kar ka manta na fi ka sadaukar da ƴaƴana duk don na ga Baba na ci gaba da rayuwa da runhin BAƘIN RUHI, sannan in maganar tsoro ce ka san ba na cikin sawun maza masu faɗuwar gaba.Ko yau aka tabbatar da Haule ce tushen matsalarmu ku yanke mata hukunci kai tsaye"
Kawu Hamza yayi wani murmushin jin daɗi jin abin da ɗan uwansa ya ce,ba banza ba yake ganin mahaifinsu ya zaɓi Aliyu matsayin Jagaba ba komai ya kawo hakan ba sai don sanin Aliyu daga tsatson Ibrahim ya fito sannan ita kanta Haulen abin da yasa suka fi zurfafa zatonsu kanta don sun ga ita ce taƙadiriya wacce ba ta da tsoro a kaf ƴaƴan shi Ibrahim ɗin, sannan tana da taurin kai da kafiya akan abin da ta sa gaba.
"Muna tsumayen ganin gaskiyar abin da kake faɗa" Kawu Laminu ya faɗa saboda a duniya yana jin takaicin Haule a tunaninsa ta dalilinta ne Hassana ta rasa idonta, sannan muƙamin da ke hannunta ya so a ce ƴarsa ce ke da shi.
Haka suka ta yin hira wacce babu abin kirki a cikinta kafin kuma su miƙe don yi wa sabon ginin tsafinsu ban ruwa.Yatsunsu suka tsaka dukkansu kafin su je gaban wata ƴar randar ruwa su dinga ɗiga shi,nan take ɗakin hukunci ya ɗauki wani hatsabibin duhu .Duk yadda suka so su sada da mahaifinsu abu ya cuttura saboda yana can a takure yana zaman jiran farmaki sai kakarin mutuwa yake . Ganin haƙarsu ba ta cimma ruwa ba suka haƙura ,ɗakin ya dawo normal .
★ Da dare bayan duk an ci abinci an kwanta ni da Hassana muka fito ta yi mini jagora zuwa ɗakin sirri ta ƙofar baya.Kamar yadda ta faɗa luluɓe yake da matakan tsaro ta ko ina illa ƴar siririyar hanyar da ba a toshe ba wacce dama alƙaluma sun nuna ta nan ne zan bi.
Na dube ta kafin na yi mata alama da ta tafi,ba ta musa ba ta juya yayin da ni kuma na bi na ratsa na shiga ciki dakyar.Tamkar wutar murhu haka ɗakin ya ɗau wani irin ja sosai yayin da kuma muke ƴar kallon-kallon ni da Kakana Nalado wanda yake cikin siffar mutane sai gumi ke yi masa tsiyaya kamar wanda aka bai wa gashin nama.
A halin yanzu in ban fi shi ƙarfi ba to za mu zo daidai,don kuwa ƙarfin ikonsa bai fi nawa ba.Da a ce kamar can baya ne da MAHEER bai tura mini nasa ƙarfin ikon ba,da tabbas Nalado ya soma azabtar da ni.
"Maitama ban san dalilinka na son kai ni ƙasa ba,kar ka manta tsawon shekarun da muka ɗauka ni da kai muna fafatawa a tsakaninmu amma ba ka taɓa yin nasara a kaina ba" shi ne abin da Nalado ya faɗa.
Yana dire furicin sai na ji tamkar har da esprit da ruhin Maitama suna cikin gangar jikina haka kuma duk rayuwar da yayi a baya ta dawo cikin kwanyata ta zauna daram.Wata irin dariya na yi kafin na ce " a'a Nalado kar ka yi ƙarya,ka tuna ni ɗin mai yin nasara ne kullum a kanka,in ba ka manta ba duk inda ka yada zango don yin mugunta ni ne nan ke haskaka wurin don mutane su farga"
"Duk da haka dai ga shi zaman doron duniya yayi maka wuyar zama ta sila ta,ka ga ka kama gabanka ka bar ni na yi rayuwata yadda nake so"
"Ba zan taɓa barinka cikin doron duniyar nan ba Nalado sai ka koma inda ka fito,zan mayar da kai duniyar matattu don can ne ya fi dacewa da kai " na furta ina mai yin tsalle na kai masa farmaki,na kumburtsi fuskarsa yayin da shi kuma yayi cilli da ni na faɗi gefe amma na yi saurin miƙewa muka ci gaba da gwabzawa.
Sai da na jigata shi sosai sannan ya fara rikiɗa cikin siffar da dama ita nake jira ya ɗauka.Da farƙo ƙashin bayansa ne ya fara kumbura ya faso fatarsa ya fito ya bayyanar da wani doro,kafin kuma wasu ƙahonni biyu su fito masa a kai zuwa can kuma harshensa ya zazzalo yana ɗigar da wasu yawu masu ɗohi da harshen yayi amfani wurin ɗaure ƙafata kafin ya ida rikiɗa ya dawo sak BAƘIN RUHI .
"Hahaha! Ka ha'inci abokinka ka haɗa jininka da jininsa a wuri guda don kawar da ni sai dai ka sani wannan shi ne babban kuskurenka zan fara cire ɗan jinjirin cikin mutumin da ta fi so a duniya kafin na kashe ta" ya faɗa cikin wata irin murya,daidai nan tunanina ya dawo jikina sai hankalina ya tashi jin wai ina ɗauke da cikin MAHEER amma zai cire shi.
Azabar da na ji ta huda cikina ce yasa na farga na tuna tashin hankalin da nake fuskanta,idona suka fara rufewa tsabar azaba ina jin yana ɗalasiman tsafi da niyyar cire cikin jikina.Dakyar na iya motsa bakina na furta harufan da nake amfani da su,nan wuƙar da muka fitar cikin dutsen nan ta bayyana a hannuna ban ɗauki lokaci ba kuma na daɓa masa ita tsakiyar baya.