Kenza eBookz

Baqeer complete - Chapter 6

Baqeer complete - Chapter 6

Baqeer complete Chapter 6: Baqeer complete Chapter 6. Kai kawai Baqeer ya kauda daga inda Salim yake zaune yana ƙoƙarin kai mishi abinci bakinshi, hannu…

3,232 words

Kai kawai Baqeer ya kauda daga inda Salim yake zaune yana ƙoƙarin kai mishi abinci bakinshi, hannu yasa ya amshi cokalin da hanunshi na dama, faɗuwa cokalin yayi saboda karayar dake hannun, sake ɗauka yayi nan ma spoon ɗin ya faɗi, gaba ɗaya Baqeer tsoron abinda ke faruwa dashi ne ya sake kamashi, nan da nan yasa hannun hagunshi ya ɗauki cokalin yana jin wani irin zafi da raɗaɗi na sake dabaibaye mishi zuciya, shi kanshi Salim tausayinshi ne duk ya rufeshi, nan Baqeer yayi spoon ɗaya wanda yake jin abincin ya koma mishi tamkar maɗaci saboda ɗaci, da ƙyar ya haɗiye na bakinshi sannan ya maida cokalin ya ajiye kafin ya rufe ido. Addu'a kawai ya samu kanshi dayi akan Allah yasa duka waɗannan abubuwan dake faruwa dashi su kasance mafarki ne ba gaskiya ba. Sallamar Bello ce tasa ya sake runtse idanunshi, yana ji Bello na yiwa Salim magana akan halin da Baqeer ɗin ke ciki yace "Salim ashe abinda ke faruwa kenan? Ni ina can Kaduna ban san aminina na cikin wannan halin ba? Wallahi ranar da muka kawoshi asibiti washegari na tafi Kaduna akan akwai wani aikin zane da wani yake so za ayi wai na decoration ne za'a saka a hotel din daya buɗe, Baqeer ne ya haɗani da mutumin saboda shi ya fara nema shi kuma sunata shirin tafiya Baba baya so yayi nesa da gida, sam zuciyata bata kawo abin ya kai girman haka ba." Cike da jimami Salim yace "Ayya!" "Amma dai ba da gaske bane kafafun Baqeer sun samu matsala ko?" Bello yayi tambayar cike da tsoro, Salim gaba ɗaya kasa amsa mishi yayi sai dai kawai ya girgiza mishi kai alamun babu magana "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Kawai Bello yake faɗa gaba ɗaya ya kasa iya cewa komai, meke faruwa da aminin nashi haka? Mutumin da future ɗinshi a shirye take taya wannan mummunar ƙaddarar zata afka mishi? Da ƙyar ya jinginar da kanshi jikin bango yana maida ajiyar zuciya, ya daɗe a haka kafin yace "Amma dai babu abinda ya samu hannunshi ko?" Salim ya sake girgiza kai yace "Wannan karaya ce kawai sai dai matsalar warkewar ba yanzu ba." Hankali a tashe Bello ya matso kusa da Baqeer cike da wani irin mugun tausayi, zuciyarshi na wani irin harbawa na tsantar tausayin abinda ke faruwa da abokin nashi. A hankali Baqeer ya buɗe ido ya zubawa Bello dake tsugune kusa dashi, idanunshi sun yi jaa sosai, da ƙyar ya iya ƙaƙalo wani wahalallen murmushi wanda iyakacin sa leɓensahi cike da jimami yace "Baqeer wannan wani ibtila'i ne ya samemu?" Kai kawai Baqeer ya girgiza dan baya jin ma bakinshi zai iya furta wani abun. Bello ya cigaba "Ɗazu Yallaɓai ya kirani ina hanya akan yana ta nemanka bai sameka ba idan ya kira Baba kuma sai yace mishi baka gida, wai yana sin ku haɗu gobe akan maganar tafiyarka, yanzu ya zamu yi da wannan ƙaddarar?" Idanun Baqeer ne suka cigaba da kara kaɗawa suna yin jaa sosai, babu shakka shidai kam rayuwarshi ta ƙare, da ace babu karayar hannun nan ma da watakila abun yazo mishi da sauƙi, ina zai kai burin daya ɗauka akan gasar nan? Auren da zai yi fa? Ƙannenshi daya yiwa alƙawari zai taimakawa su samu jarinsu mai ƙarfi fa? Mahaifinshi da yake jira ya faranta mishi da kyautar daya samu fa? Nan da nan ya shiga jin wani abu na harbawa a saman ƙirjinshi, nan ya fara fitarda numfashi da ɗan sauri da sauri, da sauri Bello ya riƙeshi yace "Baqeer ya isa haka nan, dan Allah ka rufa mana asiri kar wani abu ya sake samunka." "Allah gani nan a hanunka, ka ɗauki raina kowa ma ya huta da wannan wahalar da nake shirin ɗaura musu, ni ban faranta musu na sauƙaƙa musu ba gashi ina ƙoƙarin sanyasu cikin uƙuba." Abinda Baqeer kawai ke faɗa a cikin ranshi kenan, cike da tausayi Bello ya ajiye ledar dake hannunshi ya kalli Salim yace "Bazan iya zama anan ba zuciyata sai ta buga saboda tausayin Baqeer inda wani abin ka taimaka ka kıranı ka sanar min zan dawo gobe In Allah ya kaimu." Yana kaiwa nan ya fita da sauri bai tsaya ba sai a cikin motarshi, shiru yayi yana nazari dan ko motar ya kasa kunnawa, can ya ɗauki waya ya kira Asiya. A lokacin tana kwance akan gado ranta duk a ɓace, Habi na zaune a ɗakin tana gugar kayansu da suka bushe dan tun sassafe tayi wanki, Asiya sam bata wankin kayanta in har Habi na gida a ganinta ita babbar yarinyace mai karatun degree wacce tasan ƴan dabarun daɗin bakin da take tasa Habi tayi mata komai. Habi ce ta kalleta tace "Asiya kin kira kinji ya jikin Baqeer ɗin kuwa?" Tsaki tayi tace "Habi dan Allah ki bar maganar nan, kema kin san bazan kira ba kin san taurin kaina." Ajiyar zuciya tayi dan tasan halin yayar tata, wayarta ce tayi ƙara ta ɗauka ganin Bello ne bata san me zai ce mata ba saboda har yanzu a ƙasan ranta tana skn Baqeer. Tana ɗauka suka gaisa yace "Asiya kin je duba Baqeer kuwa?" "Naje amma ban shiga ba." Ta faɗa tana kauda kai, cike da zargi yace "Me yasa? Ko tausayi?" "Umm" kawai tace tana ƙoƙarin kauda maganar da cewa "Kaje Kadunan?" Daɗi ne ya kamashi ganin yau ta tambayeshi abinda ya shafeshi yace "Naje, kuma Alhamdulillah na samu kuɗi sosai sannan sun ce zasu sake kirana saboda sunji da ɗinaikin da nayi musu." Kai ta jinjina tace "Congrats Allah ya ƙara buɗi ni zan kwanta." Da sauri yace "Baqeer har da hannunshi suka karye fa?" Cikin sanyin murya tace "Na sani, sai da safe." Tana kaiwa nan ta kashe wayar, Bello ne ya dafa kanshi yana jin wasu tunanuwa na ɗarsar mai a zuciya, waya ce ta shigo wayarshi, ganin sunan Yallabai yasa yayi ajiyar zuciya ya ɗauka cikin fara'a suka gaisa sosai Yallabai ne yace "Wai ku haka ake abu? Taya zan yita neman amininka wayarshi a kashe? Ko wayarce ta lalace ai zai iya kirana ta wurinka ko ta wurin Babanshi, menene kuke yi haka ne? Bayan kun san jibi zamu je ganin Deputy Gomna akan tafiyar mu." Bello yayi ajiyar zuciya ya kasa magana, ran Yallabai a ɓace yace "Bana son iskanci fa, wani abun kuke ɓoye mini ne?" Bello ya sake ajiyar zuciya yace "Yallabai ka kira Baba ka tambayeshi ni tsoron yin magana nake yi." A fusace yace "Kenan dai wani abun ya faru? Da kaina zan je gidan gobe." Bello yace "To Yallabai in dai da taimakon da kuke buƙata ku sanarmin." Kashe wayar yayi ya fara wani tunani kafin ya tada motar ya bar wurin.

****** Washegari da safe Baba da kanshi yazo yace sai an sallami Baqeer, duk yanda ake lallaɓashi akan yayi haƙuri ya barsji ya ƙara samun sauƙin bai yarda ba, haka nan suka sakashi a keken guragun da Baban ya siyo suka turashi zuwa mota shi kuma ya tsaya ya amshi magungunan da aka rubutawa Baqeer ɗin ya fito don shi dai ba zai bari su ruguza mishi shirin da suka daɗe suna yi ba. Da ƙyar Bashir da Salim suka cicciɓeshi sakashi a cikin motar. Salim ya kalli Baba yana son yace zai bisu amma yasan halin faɗan Baba da rashin son yaga Baqeer da abokai. Baba har yaje zai shiga mota sai yace "Kai da mota kazo?" Da sauri yace "A'a adaidaita na shigo." Ya sani sarai magana Baban ya faɗa mishi tunda shi dai ba motar nan ce dashi ba, alamu Baba yayi mishi da kanshi akan ya shiga baya kusa da Baqeer, hakan yasa Salim shiga, duk wannan abinda ake yi Baqeer na zaune idanunshi na kallon window yana hango satin daya gabata fa yazo duba Auntyn Asiya asibitin nan ta haihu suka zo tare suna tafe suna ƴar soyayyarsu, cike da farin ciki da annashuwa, wai yau gashi sai dai ya kalli waje ta window amma babu damar ma ya taka? Yana jin Salim ya shigo har suka fara tafiya babu mai magana a cikin motar, can Baba ya kalli Bashir yace "Kai kuma yaushe zaku koma makaranta?" Da mamaki Bashir ɗin ya kalli Baban dan tun wancan wata aka koma ya sanar da mahaifin nasu amma yace bashi da kudi ya jira in an biyasu kuɗin tafiyar Baqeer zai bashi yayi registeration ɗin, da aka turo kuɗin ya sake yi mishi magana sai Baban cewa yayi ya jinkirta yaga nawa Baqeer ɗin zai bukata sai ya duba ragowar in zai isa a bashi yayi registration, shima tun daga nan bai sake bin Baban da maganar makarantarshi ba, a rayuwa har mamakin Baba suke yanda bai damu da kowa ba a cikinsu banda Baqeer din, bai damu da rayuwar da suke yi ba sai ta Baqeer wanda hakan yasa kiyayyar Baqeer ta gama shiga zuciyoyinsu kaf ɗin su babu mai sonshi har kuma wannan lokacin babu mai tausaya mishi, su ganin hakan ma suke yi da Allah ne yayi musu sakayya. Yawun bakinshi ya haɗiya yace "Baba ka manta nayi maka maganar tun kwanaki?" "Ka shirya gobe ka sake yi mini magana sai kaje ka biya, dan naga kai har yanzu ba hankali kayi ba baka san abinda ya kamata ba, karatun nan shine gatanka." "Toh" kawai ya iya cewa don bai ma san me zaice ba kuma, a ƙofar gida suka sauka, haka suka kinkimeshi da ƙyar aka saka shi a keke sannan suka turashi ciki.

**** Suna zaune a tsakar gida, Abu dake sana'ar maganin mata tanata dafa tsumin ta a gefe, tana zaune akan kujera irin ƴar tsugunno ɗin nan, ita kuma Jamila tana gefe tana tsince shinkafar da zata yi girkin rana dashi dan yau itace da girki, suna yi suna gulma da habaicin Fatima wacce ke zaune a cikin ɗakin ta tasa carbi a gaba tana addu'a, ita dai kawai addu'a take Allah ya sassauta musu, ta sani jarabawa ce daga Allah sai dai tana fatan Allah ya basu ikon cinye jarabawar. Kamar daga sama taji muryar Abu tana tafa hannu tana salati, Jamila hankali a tashe ta riƙe haɓa tace "Yau me zan gani? Duwawo ya mutu ya bar zani? Baqeeru? Ya ka fita da ƴan ƙafafunka zaka dawo mana a kujerar guragu? Yau ni naga abinda zai kasheni? Wai abin nan dai da gaske ne ashe?" Abu ce ta ɗaura da salati tana ajiye ludayin da take tuka tsumin dashi tana cewa "Baqeeru? Wannan wani ibtila'in ne ya samemu?" Baba ne ya kauda kai yace "Ku shiga dashi ɗakin shi." Salim dake tura keken ne ya cigaba da turawa suna shiga Fatima ta taho da gudu ta zubawa Baqeer ido wanda ke zaune akan kujera kai baka ce yana magana ba, kallon komai na wurin kawai yake yi, idanunshi ne suka sauka gun Umma dake jikin ƙofa tana ganin yadda aka dawo dashi gida bayan bai ko gama warkewa ba. "To sannunku ku fita." Baba yayi maganar yana kallon Salim, fita yayi jiki a sanyaye, Fatima tana ƙoƙarin shiga ɗakin Baba ya ɗaga mata hannu sannan ya maida ƙofar ɗakin ya rufe, cak ta tsaya a bakin ƙofar cikin tashin hankali dan ita kam tasan ba ƙalau ba. Baba ne ya maida idanunshi kan Baqeer wanda ke zaune akan kujera, turashi Baba yayi zuwa gaban table ɗin da yake zane, da mamaki Baqeer ke kallonshi, Baba ya cire takardar kai yasa sabuwa, ya saitashi yadda ya kamata, pencil ɗin da yake amfani dasu ya ɗauko ya miƙa mishi yace "Bismillah!" Daga waje kuwa Abu ce ta kalli Fatima tace "Me kike yi a tsaye a bakin ƙofar ki shiga mana?" Fatima ta kalli ƙofar ba dai abinda take tunani bane yake faruwa a ciki? Nan da nan zuciyarta ta shiga bugawa, ya zata yi? Ga tsoron Malam take balle ta kwankwasa ƙofar ɗakin. Jamila ce tace "Ba dai yaron da aka kawo daga asibiti bane za'a sashi aikin da aka saba?" Abu ta sake tafa hanu tace "Ai shine ma, yo dama daga sun shiga ɗaki sun kulle ai kowa yasan kwanan zancen." Nan da nan Fatima ta ƙara jin hankalinta ya tashi, Baqeer ne yasa hannun hagu yana neman amsa, a fusace Baba yace "Dama zaka saka, ko ka taɓa yin zane da hannun hagu ne?" Baqeer ya kai hannun damanshi sai dai yana kaiwa ya amshi pencil ɗin yaji yatsun hanunshi sun kasa riƙewa sai jin pencil ɗin kike a ƙasa, Baba rai a ɓace ya tsuguna ya ɗauko ya sa hannu a saman kafadarshi yace "Ka manta kai wanene a gareni Baqeer? Ka manta abubuwan dana sadaukar saboda kai? Ko kuwa ka manta duk wani burina a duniyar nan akanka yake? Naji ka rasa ƙafa zan iya hakura da hakan amma banda hannu, dole ka cikamin burin nan nawa, kai kaɗai ne wanda nake ganin abinda ban yishi ba zaka yi mini shi, kafi kowa sanin hakan, saboda kai har mantawa nake yi ina da wasu ƴaƴan, saboda kai mahaifiyarka ta samu girma da daraja a gurina, idan har ba so kake yi duk abubuwan nan su ruguje ba ka ɗaga hannu kayi abinda na saka ka, dan har yanzu mutane nayi mini kallon shashasha saboda na dage akan zanen da kake yi ina nuna musu shima sana'a ce ana ganin rashin sanin ciwo kai na da nuna ban san me ke faruwa ba, na dage har kazo ka kai wannan matsayin da zaka wakilci garin mu sannan muna sa ran ka wakilci ƙasa shine zaka ce wai karaya ta hanaka amfani da hannu? Kai har ka isa ma? Baqeer hannunshi na rawa idanunshi sun cika taf da kwalla ya kai hannu cike da dauriya wanda bai taɓa sanin ma yanada ita ba, sai dai me? Yatsunshi ne suka sake yarda pencil ɗin. A tsorace ya kalli Baba wanda yanayinshi kaɗai zai sa kasan yana cikin tsananin ɓacin rai. Fatima dake waje tana jiyo kalamanshi sama-sama hawaye kawai take yi, ita kam tasan ko kowa zai amshi kaddarar abinda ya faru tasan banda Malam, yanzu ya zasu yi?

(To wannan lamari mu kanmu kallon juna muka yi dan tuni tausayin abinda ke faruwa ya gama mamaye mu, me kuke ganin zai faru?)

*ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU.

*BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar

*KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu

*AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce

*MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari

*KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan

Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500

VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k

NORMAL GROUP 500 VIP 1000

ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130

KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730

Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336

Umm Asghar Ce Da Ayusher Muhd

BAQEER NA UMM ASGHAR DA AYUSHER MUHD

RUBUTUN TAGWAYE SHAFI NA TAKWAS

{8}

Yanda ya da ka mishi tsawar itace ce ta ƙara gigita shi yace "Ɗauki mana, ka tsaya kana yin wani abu salalo-salalo kamar mara jini a jiki, kana ganin idan baka dage ba zamu kai ga cimma nasara ne? Maza ɗauki pencil ɗinnan ka fara tun raina bai gama ɓaci ba, kuma so nake yi ka ƙure basira wajen yin zane mai kyau mai ma'ana." Hannunshi yana rawa ya ƙara ɗaukar pencil ɗin ya riƙe da ɗan ƙarfi wai don ya samu ya zauna a hannun sai dai wata irin azaba da yaji ta ratsa shi har tsakar kanshi ya sakashi sakin pencil ɗin jiki na rawa, wasu hawaye ne masu ciwo suka sulmiyo daga idanunshi, ɗaga kai yayi ya kalli Baban daya kirne fuska ya sha kunu tamkar ba shine wannan Baban mai yawan so da tattalin shi ba, kwata-kwata yanzu babu tausayi a cikin ranshi sai fatan cikar burinshi kawai da yasa a gaba. Da ƙyar ya iya buɗe baki yace "Wallahi Baba ba zan iya ba, hannuna bai gama warkewa ba ko yaya nayi ƙwaƙƙwaran motsi dashi ba ƙaramar azaba nake sha ba." Babu zato yaji Baba ya sauke mishi wani irin gigitacen marin daya gigita shi har ya kusa faɗowa daga kan wheel chair ɗin cikin taimakon Allah yasa hannunshi mai lafiya ya riƙe hannun kujerar wanda ya taimakeshi bai kai ga faɗowa ba.

Cikin hargagi da masifar da Baqeer ya saba jin shi yana yiwa ƴan uwanshi da iyayensu mata sai dai bai taɓa katarin an sauke mishi shi ba ya nuna shi da yatsa yace "Wallahi ba zaka so ganin kalar ɓacin raina ba idan har baka ɗauki pencil ɗin nan kayi zanen nan ba, kana nufin duk uban kuɗin dana kashe da lokacina dana ɓata a kanka sun tashi a banza kenan? Baƙin ciki kake yi min ne Baqeer? Ganin ina daf da cika burina na shekara da shekaru, inace akwai ƴar baƙin ciki a tsakaninmu dama?" ya karashe maganar yana ji kamar ya saki kuka ko yaji sauƙin damuwar data cunkushe a zuciyarshi, ta yaya sai da yake daf da ganin cikar burinshi Baqeer zai nemi ya watsa mishi mafarki da burin da ya ɗauka gaba ɗayan rayuwarshi yana ginawa. Hawaye kawai Baqeer yake yi don yafi Baba jin baƙin cikin wannan ƙaddarar data sameshi sai dai baya da yadda zai yi don a yanzu dai a irin ciwon da yake ji a duk lokacin da ya motsa hannunshi yasan babu abinda zai iya ko yana son yin zanen bare ma baya cikin nutsuwar da zai iya yin wani zane a yanzu, ƙunci da damuwar dake danƙare a cikin zuciyarshi baza su bari ya iya yin komai ba.

A fusace ya fito daga ɗakin ya buga ƙofar da ƙarfin da sai da ya girgiza ginin ɗakin, wani irin wulaƙantaccen kallo ya watsawa Fatima data kasa matsawa daga ƙofar ɗakin tun bayan da Baba ya korosu waje ya rufe ƙofar ɗakin da Baqeer a ciki, yana wucewa tayi wuf ta faɗa ɗakin sai dai halin da taga ɗan nata a ciki ya ƙara sanyayar mata da gwiwa, kuka yake yi irin mai cin zuciyar nan wanda baka jin sautinshi sai dai kaga zubar hawayen kawai, tunda take bata taɓa ganin Baqeer cikin wannan yanayin ba, itama bata san lokacin da kukan ya suɓuce mata ba sai dai tayi saurin saka hannu ta toshe bakinta tana ƙoƙarin hana kanta yin kukan sai dai tausayinshi da take ji ba zai bari ba don duk sadda ta kalleshi sai taji wani irin rauni ya lulluɓeta. A haka taja jiki ta ƙarasa gabanshi ta tsugunna, hannayenta tasa ta kamo hannunshi mai lafiyar ta riƙe a cikin nata duka biyun, wani irin rauni ne ya lulluɓeshi ganin da yayi wa mahaifiyarshi a tsugunne a gabanshi, tausayinsu gaba ɗaya ya kamashi har bai san lokacin da ya fashe da kuka ba "Umma" kawai yake ambata muryarshi na rawa. Sai da suka yi kukansu ya ishe su sannan ta haƙurƙurtar da zuciyarta tasa hannu tana share mishi hawayen tace "Kayi haƙuri Baqeer da duk abinda zaka gani a yanzu, dole sai ka koyawa zuciyarka haƙuri ka koyi ɗauke kai daga al'amuran mutane ka koyi haƙurin zama dasu a yadda suka zo maka don ba kowa ne yake baƙin ciki da ƙaddarar data sameka ba, wasu har cikin ransu murna suke yi da abinda ya sameka ba dai zasu fito su nuna bane kawai, Allah ya baka lafiya ya ƙara maka haƙuri da danganar karɓar sabuwar ƙaddarar data shigo rayuwarka a yanzu."

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull