Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 13
Barrister ibrahim khalil complete Chapter 13: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 13. "Yanzu to aina yarinyan da Dad ɗin yasamo maka take?" Brr.…
4,495 words
"Yanzu to aina yarinyan da Dad ɗin yasamo maka take?" Brr. Tahir ɗin yatambaye sa
Taɓe baki Khalil yayi yace "wai ƴar Abokin sa ne, sai kace suna neman kai dani".
Brr. Tahir dariya yayi yace "kai masha Allah Allah yasanya alkhairi, gaskiya naji daɗin wannan haɗin domin kuwa idan Dad yabiye taka baza kayi auren yanzu ba".
Yamutsa fuskar sa yayi yace "kaga ni zan aje waya ina tuƙi ne sai anjima".
Still dariya Brr. Tahir yayi yace "ok zuwa a anjiman zan kira ka bye".
Daga nan ajiye wayan yayi yaci gaba da tuƙin sa.
**** ***** ****** *******
Ummi ce zaune kan Three sitter Saleema tayi matashi akan cinyan ta, gefe ɗaya kuma Abba ne zaune kan Two sitter suna hira
Abba ne yace "ƴar Baba tashi akwai maganar da zamuyi dake me muhimmanci".
Amsa mishi Saleema tayi tana tashi zaune
"Shin kin tuna Abokina Alh. Abdurra'uf?".
Kallon Abban tayi kana tace "eh Abba nasan shi, ko ba wanda ada kake yawan kai ni gidan ba?"
Murmushi Abba yayi yace "yauwa shi ƴar Baba, kinsan yaran sa ko?"
Gyaɗa kai tayi tace "nasan su Abba".
"To ki saurare ni da kyau ƴar Baba, kinsan Burin mu shine mu aurar dake ga mutumin da zai kula dake kamar yanda muke kula dake, muna Son farin cikin ki Daughter wannan dalilin ne yasaka muka yanke shawara Ni da Mahaifiyar ki mu samo miki Miji wanda zai baki duk wani kulawa, ɗan gidan mutunci wanda zai iya riƙe mana ke bisa amana, akwai ɗan sa Ibrahim Khalil shine mahaifin sa yake nema masa auren ki, Ni kuma ganin haka yasa na'amince but duk da haka sai na tambayi ra'ayin ki, idan har kin amince zai zo wajen ki don ku dai-daita, kiyi tunani da kyau My Daughter don baza mu taɓa baki abinda baki so ba, zaɓin ki shine namu".
Saleema kallon Abban nata kawai take yi har yadire maganar kafin cikin zaƙuwa tace
"Abba wai kana Nufin Yaya Barrister?"
"Eh Shi ƴar Baba".
Rufe bakin ta tayi tana waro idanu cike da wani irin farin ciki tace "Kaiiiii.."
Ummi tace "lafiya Daughter me yafaru?"
Dariya tasaki tana yarfe hannayen ta sai kuma tasake rufe bakin ta tana kallon iyayen cike da tsananin farin ciki, su kuwa kallon ta kawai suke yi suna tunanin "meyasaka ta farin ciki haka lokaci ɗaya?" Muryan ta suka tsinkaya tana cewa
"Anya Abba Yaya Barrister shine Wanda mahaifin sa ke nema masa aure na? Ina mamaki Abba taya?"
Murmushi Abban yayi yace "Ƴar Baba kenan ki dena mamaki ai komi ba yanda Allah baya nuna ikon sa, yanzu menene ra'ayin ki akai? shin kin amince ne?"
Saurin gyaɗa kanta tayi tana me tsananin farin ciki, riƙo hannun ta Ummi tayi tana kallon ta da murmushi a face ɗin ta tace
"Wai farin cikin na menene da alamun dai kina son sa kenan?"
Saleema har ta buɗe baki zatayi magana sai kuma tayi saurin rufewa don baza ta iya yin musu bayanin abinda ke ranta ba, illa tashi da tayi da gudu tanufi hanyan ɗakin su tana ci gaba da dariya, bin bayan ta sukayi da idanu cike da tsananin mamakin ta kana Abba yace
"Ikon Allah wai lafiyan ƴar Baba ƙalau?"
Ummi cike da farin ciki tace "ai inaga Abban Saleema da alamun ƴar mu ta daɗe tana ƙaunar sa ne, domin Ni sheda ne abaya sanda kake yawan ɗaukan ta kuje gidan kullum idan tadawo bata da magana sai na Yaya Barrister, Kai har dai na gaji daji don idan tazauna labarin kenan, to tun sanda tayi ciwon nan sosai aka kwantar da ita asibiti kadena kaita to ban sake jin tayi maganar ba, amma Ni ina da tabbaci son sa take yi kuma ina ganin tana cikin mamakin abun ne".
"Kai amma idan ko hakane zamuyi farin ciki sosai ai dama fatar mu kenan, burin mu shine tasami miji na gari kuma ina da yaƙini ta samu, domin Khalil be da wani matsala yaro ne me tsananin kirki da biyayya na tabbata bazai taɓa wulaƙanta mana ƴa ba, wannan dalilin ne yasaka nayi tunanin haɗa wannan auren".
Ummi jinjina kanta tayi cike da gamsuwar bayanin mijin ta kana tace "to Allah yatabbatar da alkhairi Allah yasa ayi damu".
"Ameen ameen". Cewar Abba still yana me nuna farin cikin sa
"Amma ina tunanin ba yanzu za'a yi auren ba sabida yaron zai yi tafiya, kin ga har sai ta gama school ma anan, sai kiyi mata bayani yanda zata fahimta".
"To babu matsala ai hakan yayi ma". Cewar Ummi kenan
Daga nan hira sukaci gaba dayi suna tattaunawa akan maganar. [10/30/2020, 8:51 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 37*
Tana shiga ɗakin tafaɗa kan Halwa dake barci, hakan yasaka Halwan tafarka tana kallon ta da idanuwanta da sukayi ja, cike da tsananin farin ciki Saleema tace
"Wayyo Allana yau ina farin ciki sosai kitashi ki tayani murna".
Ahankali Halwan tatashi zaune tana ci gaba da kallon ta tace "me yafaru ne Sister?"
Murmushin da yabayyana haƙoran ta tayi tace "kinsan me Abba yazo da maganar aure na Ni da ɗan Abokin sa".
Waro idanu Halwa tayi tana kallon ta, sai kuma tayi dariya tace "shine yasaka ki farin ciki?"
Gyaɗa kanta tayi tana sake washe bakin ta tace "eh mana abin ne ya matuƙar bani mamaki, ban taɓa tunanin wannan ranan ba, ban taɓa tunanin Ni Saleema ina da matsayin da zai sa ace yau zan zama matar Barrister ba, Mutumin da ko magana ban taɓa samu ya haɗani dashi ba, ada nayi burin ace Barrister ya zama nawa but ko kaɗan babu hanyan da naga yiwuwar hakan, amma yanzu kiji abin mamaki sai gashi lokaci ɗaya Allah ke ikon sa wai ni ce yau ake son haɗa ni dashi, abun sai kace amafarki wlh".
Yanda taƙarike maganar nata ne yaba Halwa dariya, sai da tadara kafin tace "to menene aciki? Ni a ganina banga Namijin da yafi ƙarfin ki ba, kar ki manta kema fa kina da kyau da haɗuwar da ko wani namiji zai yi fatar samun ki, ki dena zuzuta shi da yawa don nasan bazai fi ki da komi ba".
Saleema tace "uhmmm baza ki gane bane Sister, ko wace mace idan har tagan shi zata so yazama shine Mijin ta, ba wai don haɗuwan sa ko kyawun sa ba amma yana da nagartan da idan har kin ganshi kema wlh sai kin so shi, domin bakiga yanda mata suke rushing akan shi bane".
Taɓe baki Halwa tayi tana kallon ta tace "da alamu dai kina son sa da yawa, amma to kina ganin shima yana ciki?"
Zaro idanu Saleema tayi tace "hmm mutumin da ban taɓa magana dashi ba taya kike tunanin yana sona? I Think ko sanina be yi ba".
Shiru kawai Halwa tayi tare da tunanin Nura aran ta
"Burina a rayuwa shine in Sami Miji tamkar Barrister sai gashi shi ɗin na samu, nasan ko baya so na watarana zai ƙaunace ni domin kuwa zan yi duk abinda yake so". Saleema taƙarike maganar tana rufe fuskarta cike da farin ciki
Buɗe fuskar tayi tana kallon Halwa da tafaɗa tunani, sai tataɓo ta tana cewa "Sister lafiya tunanin me kike yi?"
Ajiyan zuciya Halwa tasauke kana tace "Babu".
Murmushi tayi tace "to faɗa min kema, menene burin ki a rayuwa?"
Shiru Halwa tayi tana kallon ta batare da tace komi ba
"Sister kisanar min mana kinji?"
Duƙar da kanta tayi tana murza ƴan yatsun hannayen ta masu tsawo da burgewa kana taɗago kanta tana kallon Saleema da murmushi a fuskarta tace "ada bani da wani buri a rayuwa sama da inyi aure in ganni gidan Yaya Nura amma.."
Shiru tayi tana kawar da kanta kana taci gaba da cewa "amma a yanzu Burina inyi karatu me zurfi in zama lauya ko dan naɗau fansar abinda Haris yayi min".
Ɗaura hannun ta Saleema tayi akan na Halwan tana cewa "meyasaka kike Son ɗaukan fansa? Meyasaka baza ki barshi da Allah ki manta dashi cikin rayuwan ki ba? Idan har kikace zaki ɗau fansa hakan na nufin kenan zaki riƙa tuna sa har zuwa wani lokaci?"
Halwa tace " Ni kaina nayi tunanin barin shi da Allah kamar yanda tun farko nabar shi, amma yanzu wani tunani yazo min arai saboda shigan ciki a gare ni, idan har nahaifi abinda ke cikina dole ne watarana yatambaye Ni "ina Mahaifin sa?" kina tunanin wani amsa zan bashi?"
Taƙarike maganar hawaye na cikowa cikin idanun ta, kana taci gaba da cewa
"Wannan dalilin ne yasaka nayi tunanin na zama lauya don nan gaba na kaisu ƙara kotu domin hakan ne kaɗai zai saka gidan su Haris su amshi abinda nahaifa, baza su taɓa amsan abinda zan haifa ta daɗin rai ba dole sai ta wannan hanyan".
Numfashi taja me ƙarfi still taci gaba da faɗin
"Burina na biyu shine in San meyasaka Yaya Nura yajuya min baya? Ina son in San dalili ina son insan meyasa?.."
Sai kuma tasaki kuka me ƙarfi, cikin rawan murya tace "na.. na kasa yarda cewa Ya..ya Nura zai juya min ba..ya, zuciyata takasa amince wa da hakan.."
Kasa ci gaba tayi da magana dole yasaka tayi shiru, rungume ta Saleema tayi cike da tsananin tausayin ta tace
"Kiyi shiru don Allah Sister ki dena kuka kinji? Ni nan zan taimake ki wajen cika burin ki, in Allah ya yarda zaki cika burin ki, zanyi wa Abbana magana zai saka ki aduk makarantar da kike so a faɗin duniya domin cikar burin ki, please ki dena kuka".
Shiru Halwa tayi tana sauke ajiyan zuciya, ɗago kanta Saleema tayi tasaka hannu tasoma share mata hawaye.
*****
*TWO WEEKS*
Khalil ne zaune ƙasar Roll ɗin parlour'n sa, daga shi sai gajeren wando fari da baƙin t.shirt, gaban sa takardu ne masu yawan gaske yake dubawa, gefe kuma Kausar ne kan kujeran da yajingina bayan sa tana ɓare maggi dake cikin Vowel
A ɗan wannan lokacin sosai suka shaƙu da juna kullum Kausar tana gidan, ita take mishi girki da gyaran gidan, su zauna suyi ta hira kamar wanda suka daɗe da sanin juna, yanzun ma hiran suke yi aciki yasako mata maganar auren sa da zai yi
Ɗan kallon ta yayi yana smile yace "kin kusa hutawa dai duk ranan da akace nayi aure, babu ke babu ɗawainiya dani".
Tsayar da abinda take yi tayi tana ɗago kanta takalle shi, kana cikin rashin fahimta tace "ban gane ba?"
Ɗan taɓe bakin sa yayi yana kawar da kai yace "nan ba da jimawa ba zanyi aure.."
Ɗif Kausar tayi gaba ɗaya tadena jin abinda yake cewa, maggin kawai take ɓarewa amma batasan ma takamaiman a halin da take ciki ba, sai da yagama maganar sa kana yajuyo yana kallon ta, ganin kamar tayi nisa a tunani sai yakau da kansa yaci gaba da abinda yake yi
Ita kuwa sosai tashiga ruɗu da jin abinda yafaɗa, ba don komi ba sai don ƙaunar da tatsinci kanta dumu-dumu aciki tana yi masa
Nocking ɗin da akeyi ne yadawo da ita hankalin ta
Khalil yace "Yes Come in".
Brr. Tahir ne yashigo ciki da sallama, sauke idanun sa yayi akan su yana bin su ɗaya bayan ɗaya da kallo cike da tsananin mamaki da al'ajabi, Kausar itama shi take kallo sai dai kawai kallon nasa take yi but tunanin ta yana wani wajen daban, maganar Khalil ne kawai ke mata yawo a tsakar kai
"Lafiya katsaya nan? Kashigo mana". Cewar Khalil kenan yana kallon sa
Ahankali Brr. Tahir yasoma takowa yana shigowa, sai da ya'iso wajen yazauna saman sofa kana Kausar tamiƙe tsaye da hanzari tana ajiye Vowel ɗin hannun ta asaman Centre table, kallon Khalil tayi fuskarta babu walwala tace
"Zan je gida".
Shima ɗin kallon ta yake yi cike da mamaki, sai kuma bai iya cewa komi ba in banda gyaɗa mata kai da yayi, ita kuma tajuya tayi hanyan ƙofa dasauri yayinda Brr. Tahir yaraka ta da idanu, sai da tafice kana yamayar da kallon sa ga Khalil yace
"Kai Man ina kasamo wannan Babe ɗin? Shin anya ba idanuna bane ke min gizau?"
"Kamar ya?" Khalil ɗin yatambaye sa yana ɗago kansa yakalle sa
_plz Share🙏🏼_ [11/1/2020, 9:10 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 38*
Brr. Tahir yace "abin ne da mamaki mace nake gani agidan ka? Taya hakan zai faru? Meye alaƙan ka da ita?"
Gajeran tsaki Khalil yasaki yana kawar da kansa, domin shi a tunanin sa ko wani abun yagani don har ya tsorata shi
"Kayi min bayani mana meye alaƙan ka da ita? Kar dai ace.."
Wani kallo da Khalil yasakar masa ne yakasa ƙarisa abinda yayi ninya, sai yatsaya kawai yana kallon sa batare da ya ɗauke idanun sa akan sa ba, Khalil kuma juyar da kai yayi yaci gaba da abinda yake yi kana yace
"Ba abinda kake tunani bane, maƙociya ta ce".
"Maƙociyar ka?"
Brr. Tahir yamaimaita maganar kamar be fahimta ba, sai kuma yasaki murmushin gefen baki yana cewa
"Kayi min bayani yanda zan gane har yanzu ban fahimce ka ba?"
Tsaki Khalil yaja yana hararan sa, nan dai yabashi labari yanda suka haɗu da alaƙan sa da ita
dariya Brr. Tahir yakece dashi yana cewa "Cab ɗi.. wai dama ka iya sakewa da mata har haka?"
Kallon banza Khalil yayi masa yace "me kaɗauke ni to?"
Ɗage hannu Brr. Tahir yayi yace "No babu".
"Kafaɗa karta kashe ka, ai nasan duk abinda kake tunani".
Shi dai Brr. Tahir dariya kawai yake yi, sai da yagama dariyan sa son ransa Khalil be sake kula sa ba, sannan daga baya yace
"Kasan me? na samo maka shawara, me zai hana kawai kakai ma Dad ita a matsayin wacce kake so tunda naga taku tazo ɗaya".
Idanun Khalil kamar zai faɗo ƙasa sabida kallon da yake yi masa, Brr. Tahir da yabuɗe baki zai ci gaba da magana Khalil yayi saurin katse sa da cewa
"Banso don Allah kadena wannan maganar, ce maka akayi ina son ta? ko ce maka akayi ita tana so na? Babu wani abu da zai haɗa mace da namiji ne sai soyayya? Ni kawai burge Ni take yi ba wani abu ba".
"To ai hakan shi ke kawo ƙauna, don me zata burge ka idan har babu ƙauna aciki?"
Ɗaure fuska Khalil yayi yakawar da kai don bazai iya biye masa ba, kuma yasan halin Brr. Tahir idan yakama abu to baya jin bari
"Uhm Ni kawai shawara nake baka, idan kuma kafison wacce Dad zai baka ai shikenan , ta yiwu ma kaje kaganta batayi maka ba".
Shiru dai Khalil yayi be ce komi ba, amma tunanin maganar Brr. Tahir ɗin yake yi da yayi a ƙarshe
Brr. Tahir yakatse masa tunanin sa da cewa "katashi kashirya mana mutafi, in kuma ka fasa ne sai nayi tafiyana don ina da abin yi".
Miƙe wa Khalil yayi still be ce masa komi ba yanufi ɗakin sa, sai da yayi wanka yashirya cikin wani farin Gezna da yayi masa kyau ainun, yasaka baƙar hula me ƙube tare da baƙin Sandal shoes, babu abinda ke tashi ajikin sa sai sassanyan ƙamshi, car key yaɗauka tare da wayoyin sa yafito parlour, Brr. Tahir kallon sa kawai yake yi ganin yanda yayi masa mugun kyau
"Kai Abokina kaga yanda kayi kyau? Ni namiji kenan ina ga mace ta ganka? wannan wanka gaskiya Amarya dole tabiya mu".
Tsaki Khalil kawai yaja yanufi ƙofa batare da ya tanka sa ba, shi kuwa Brr. Tahir biyo sa yayi yana ta tsokanar sa yana faman dariya
A cikin motan Khalil ɗin suka fita, mintuna ashirin yakaisu gidan Alh. Mustapha, suna yin hon aka buɗe musu Gate don dama gateman ɗin yasan da zuwan su, lokacin da sukayi parcking duk kan su suka fito alokaci ɗaya, Brr. Tahir sai gyara wuyan rigan sa yake yi yana faman doka murmushi sai kace shine aka rako, Khalil kuwa in banda harara da yake aika masa babu abinda yake yi, ahaka akayi musu iso har zuwa Parlour'n Alh. Mustapha inda anan ne aka sauke su, me aiki aka saka takawo musu abin motsa baki, babu abinda suka taɓa sai hira da Brr. Tahir yake jan Khalil dashi, shi kuwa sai latsa wayan sa yake yi ko kula sa be yi ba
A ciki kuwa Saleema ce taci uban kwalliya cikin wani tsadadden less me ruwan toka, ɗinkin riga da sket ne da yayi mata kyau matuƙa, tayi ma fuskarta Light makeup Wanda yaƙara fito da tsantsan kyau ɗin ta, dama Saleema ba baya ba wajen kyawu, Halwa na zaune tana kallon ta har tagama shiryawa tayafa gyale fari ƙal me kwalliyan stone, haka ma flat shoes ɗin da tasaka a ƙafafun ta fari ne, murmushi kawai Halwa take zubawa kafin tace
"Gaskiya kinyi kyau My sister, anya baza ki zautar da Angon nan naki ba yakasa manta ki?"
Washe baki kawai Saleema take yi cike da farin ciki, kana tace "dagaske nayi kyau Sis?"
Halwa tace "wlh sosai kinyi kyau Sister, kuma ina da yaƙini dole ki shiga ran sa alokaci guda, don babu wanda zai ganki be yi fatan ki zamo matar sa ba".
Dariya Saleema tayi tace "Thank you My Sister, bari inje kar suji Ni shiru tunda nace kizo muje kinƙi".
Girgiza kanta Halwa tayi tana murmushi tace "O'o Ni bazan iya zuwa ba, ke dai kawai kije ke kaɗai, idan yasake dawowa watarana sai mu gaisa".
"To na tafi, sai na dawo Sis".
Daga nan fita tayi ita kuma Halwa kwanciya tayi tana sauke ajiyan zuciya cike da tunani a ranta, Saleema tana shiga Parlour'n da sallama Brr. Tahir da yatsare ƙofan da idanu ya'amsa mata yana sakin murmushi, a ransa kawai "masha Allah yake faɗa". Don ba ƙarya Abokin nasa ya dace da zaɓi, Saleema kanta a ƙasa ta'iso tazauna kan sofa me facing nasu, sai tagaishe su alokaci ɗaya tana ɗago kai tana kallon su, dai-dai da shima Khalil ya ɗago kai yasauke idanu kanta suka haɗa idanu, sauke kanta ƙasa tayi cike da tsananin kunya tare da zallan farin ciki, shi kuwa taɓe baki kawai yake yi amma yakasa ɗauke idanun sa akanta, Brr. Tahir kuwa cikin murmushi ya'amsa mata tare da tambayan ta "ya take da ƴan gidan?" Amsa mishi tayi, sai Brr. Tahir ɗin yakalli Khalil dake faman ƙare mata kallo, hakan yabashi dariya yayi saurin ƙumshe bakin sa yana cewa
"To Abokina ga fa Amarya ta iso, Ni bari in fice in baku space don kutattauna ko?"
Sai lokacin Khalil yaɗauke kansa yamayar ga Brr. Tahir, be ce masa komi ba hakan yasaka Brr. Tahir yatashi yafice
Shiru ne yabiyo bayan fitan Brr. Tahir, ita Saleema tunani kawai take yi yanda Khalil ɗin yasauya mata sosai fiye da yanda tasan shi, wani irin kyau da kwarjini yasake yi tare da wani irin gogewa yasake ƙiba, kai da gani kasan hutu da kwanciyan hankali tare da kuɗi sun zauna masa, so take yi tasake ɗago kai takalle sa amma ta kasa domin yanda take jin idanun sa masu matuƙar kaifi suna yawo ajikin ta, shi kuwa a nashi fannin zuba mata idanuwa yayi yana ta kallon ta, a haƙiƙanin gaskiya dogon tunani yafaɗa har be san iya adadin mintocin da suka wuce ba, Saleema dai har ta gaji taɗago kanta tana kallon kyakykyawar fuskar sa da yatsare ta da kallo, cikin sanyin murya tace
"Ko in Kira Abokin ka ku fara cin abincin ne?"
Sai alokacin yaɗan ƙifta idanun sa da alamun yadawo tunanin sa, kallon ta yayi yana ɗan jije leɓe, ba ƙarya ayanda yafahimta yarinyan zatayi sauƙin kai, duk da ba wai tayi masa yanda yake so bane kuma ba wai yaji ta a ransa bane, but ta kwanta masa arai kuma zai iya zama da ita a matsayin matar sa, ajiyan zuciya yasauke kafin yace
"Kina lafiya?"
Saleema da har tagaji da shirun nasa tasad da kai ƙasa tana wasa da yatsun ta, jin sassanyan muryan sa me daɗi yasaka ta ɗago kai tana kallon sa kana ta'amsa mishi cikin biyayya da son burge shi
"Nasan kinsan me yakawo ni nan ɗin don nasan an riga da an miki bayani? Any way ni sunana Brr. Ibrahim Khalil Abdurra'uf, ina fata.."
Shiru yayi don be san me zai faɗa ba, ita kuwa kallon sa kawai take yi tana jin yanda muryan sa me tsananin daɗi yake shiga kunnuwan ta, kamar an matse bakin sa sai yace mata
"Me kike karanta a School?"
Cike da farin ciki ta'amsa masa da "Pharmacy".
Gyaɗa kansa yayi sai kuma sai kuma yayi shiru yana ajiyan zuciya, wayan sa yaɗauka kana yaɗago kai yana kallon ta yace "kiyi haƙuri ni ba gwanin iya soyayya bane Thats why ban iya hiran ba".
Murmusawa tayi kawai tana sunkuyar da kai, sosai yaburge ta hakan na nufin kenan be taɓa budurwa ba kamar yanda itama bata taɓa yi ba? Duk kallon da take masa bata taɓa tunanin yana da sauƙin kai irin haka ba
Brr. Tahir yakira yace masa "yashigo". Babu jimawa kuwa yashigo yana kallon su yana murmushi yace
"Har an gama hiran?"
Khalil be basa amsa ba sai miƙewa da yayi yana saka wayan sa a aljihu hakan yasa Brr. Tahir cewa
"To Amarya mu zamu tafi, sai kuma gani na gaba".
"To bakuci komi ba".
"No karki damu next time idan muka zo zamuci yanzu muna sauri ne".
Gyaɗa kanta tayi tana tashi tsaye, daga nan raka su tayi har wajen motan su kafin suka sake sallama tataho gida.
.
_More Comments More post._🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️ [11/1/2020, 9:23 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 39*
*AFTER SEVEN MONTH*
A wannan watannin da suka shuɗe abubuwa da dama sun faru, ciki kuwa har da haihuwar da Halwa tayi, ta haifi yarinyan ta kyakykyawa me ban sha'awa, sosai yarinyan take kama da ita, sai dai kuma ta ɗakko abubuwa da dama na mahaifin ta wanda idan kakalle ta tabbas zakasan ƴar sa ce, sunan Ummi aka saka mata kamar yanda Saleema tabuƙaci asaka, wato Asma'u suna kiran ta da Husna, duk wani hidima kama daga kan kayan Baby zuwa na uwar Babyn babu abinda Abba be siya musu ba, komi ya wadata su dashi tamkar tana gaban iyayen ta, tun sanda tahaihu kuma Ummi tace "baza ta shayar da yarinyan ba". Don haka da madaran kanti ake shayar da ita, Halwa sosai taji daɗin hakan ko ba komi an ɗauke mata wani nauyi kuma an taimake ta, duk wani hidiman yarinyan Saleema ce me yi, kullum yarinyan tana hannun ta ita take kula da ita, ita take mata komi sai dai wanka da Larai ƴar aikin su take mata, ita kuwa Halwa sai dai taci tasha takwanta hakan yasaka gaba ɗaya tasauya tasake ƙiba tayi kyau gunun sha'awa, dama gashi tana tsaka da jego ne kuma ga hutu da yayi mata yawa
Yanzun ma zaune take agaban madubi tana shafa lipstick a ƙananun laɓɓan ta, fuskarta babu wani kwalliya illa powder da tashafa sannan tazizara kwalli cikin idanuwanta, miƙe wa tayi tana gyara zaman rigan ta, doguwar riga ce na atamfa tasaka Milk and Coffee colour, sosai rigan yayi mata matuƙar kyau duk da kasancewar ta bata da hasken skin, Halwa irin Chocolate Colour ɗin nan ce me ɗan haske, tana da kyau na ban sha'awa da burgewa, idan har zaka ganta to dole sai ka sake kallon ta coz yanayin ta da komi nata yana da kyan kallo, bata da wani tsayi amma tana da ɗan kauri kaɗan tare da sura me kyau da ɗaukan hankalin me kallon ta, duk da kuwa ita ɗin ba ma'abociyar son cin abinci bane, kallo ɗaya idan kayi mata zaka fassara ta da me sanyi don ko a maganarta ne cikin sanyi sosai zakaji muryan ta, sai dai kuma akwai ta da tsiwa sannan tana da surutu matuƙa sai dai idan bata sami wajen yi ba
Tana cikin ɗaura ɗankwali Saleema tashigo ɗakin, itama ɗin doguwar riga tasaka iri ɗaya da na Halwa har ɗinkin da komi, Ummi taba da aka ɗinka musu wajen kala bakwai lokacin da Halwan tahaihu, itama ɗin sosai yayi mata kyau kasancewar ta fara ce, murmushi tasakar wa Halwa kana tace
"Kinyi kyau Sister".
Murmushi Halwa tayi tana kallon ta tace "Thanks".
"Ok Ina kayan Husna? Larai ta gama mata wankan za'a shirya ta".
"Ban ciro mata ba". Halwa tabata amsa tana saka Room Slippers a ƙafafuwan ta da suka sha lalli ja da baƙi
Saleema wajen kayan Husna tanufa tana cewa "but sai da nace miki ki ciro kafin in dawo fa"
Ƙarisawa kusa da ita Halwa tayi tana taya ta cirowa tace "I'm sorry Sis, ban gama shiryawa bane shiyasa".
"Ok".
Fita sukayi gaba ɗayan su bayan sun gama ɗaukan abinda zasu ɗauka, suna fita parlour Halwa zama tayi akan sofa ita kuma Saleema tawuce da kayan ɗakin Larai, can kuma sai gata tafito ɗauke da Husnan a hannu, an shirya ta tsaf-tsaf cikin kayan ta masu kyau, zuwa tayi tazauna gefen Halwa tana cewa
"Kinga Babyna yau tayi kyau sosai, har carbing mukayi mata".
Halwa kallon yarinyan tayi sai kuma taɗauke kai tana yamutsa fuska kamar yanda tasaba
Kallonta Saleema tayi tace "Yauwa Sis idan nayi aure kema zaki dawo gidana ko? Sai mu zauna tare".
Murmushi Halwa tayi tace "to sai mu bar Ummi da wane? Kinga ke kin tafi dole zasuyi kewarki".
Gyaɗa kai Saleema tayi kana kuma tace "but duk da haka dai zaki riƙa zuwa kina min sati ko fiye da hakan, kinga kuma Ni ban ma iya girki ba idan naje wanene zai min?".