Kenza eBookz

Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 14

Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 14

Barrister ibrahim khalil complete Chapter 14: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 14. Halwa tace "zaki sami House girl ne sai tayi miki".

4,465 words

Halwa tace "zaki sami House girl ne sai tayi miki".

Kwaɓe fuska Saleema tayi tace "no bana son ƴar aiki sai dai muje muriƙa yi tare dake".

"To ai nima ban iyaba wlh". Halwa tafaɗa tana dariya

Dariya itama Saleema tayi tace "haba dai? Kice duk jirgi ɗaya taɗauko mu?"

"Eh mana, ko Mama tasaka Ni bana yi har ma ta saba ta dena cewa inyi, sabida Ni dai gani nake yi tunda bana cin abincin to bazan koya ba".

Still dariya Saleema tayi tace "tabb ai kuwa dole mu saka Larai gaba takoya mana".

Ummi ce tayi sallama tashigo

"Oyoyo Ummi". Cewar Saleema tana miƙe wa ta'isa wajen ta

Ummi kuma amsan Husna tayi tana dariya tace "iyeee ga takwarata ga takwara ta".

Sannu da zuwa sukayi mata sannan tazauna tana cewa "Abban ku be dawo ba?"

Saleema tace "ya dawo ya fita ne".

"Ok".

Yarinyan tamiƙa wa Saleema sannan taɗau jakan ta, ita kuma Halwa lokacin tadawo ɗauko ma Ummi ruwa tace

"Ummi ga ruwa kisha".

Murmushi Ummi tayi tace "Yauwa na gode".

Har ta juya Ummi tasake cewa "zo riƙe wannan ledan".

Halwa amsan ledan tayi tana kallo

"Magani ne idan Larai zatayi miki wanka sai ki riƙa Using dashi".

Gyaɗa kai Halwa tayi tana komawa tazauna, ita kuma Ummi miƙe wa tayi tanufi ɗakin ta, sai da tashige sannan Saleema tace

"Menene acikin ledan?"

Kallon ta tayi taɗage kafaɗa alamun bata sani ba, sai kuma tace "ki tambayi Ummi".

Ɗan waro idanu Saleema tayi sai kuma tasaki dariya tace "ai bazan iya bane wlh".

Harara Halwa tayi mata tace "ashe kin sani kenan kike tambaya?"

.

**** ***** ***** ******

Wani irin kallo take masa har sanda yadasa aya a maganar sa sannan tabuɗi baƙi cike da baƙin ciki tace

"Wlh Nura kabani mamaki domin ban taɓa tunanin haka halinka yake ba, har Ni zaka dubi idanuwana kace kana so na? Idan har baka bar mana ƙofar gida ba wlh zan maka rashin mutuncin da baka taɓa tunani ba..'

Bata rufe baki ba Nura yace "haba Zainab wai meye laifina anan? me namiki da baza ki so ni ba? Kar ki manta fa wacce kike tunani akanta bata nan don me baza ki bani dama in maye gurbin ta dake ba, wlh ina ƙaunar ki tsakani da Allah.."

Cikin wani irin tsawa Zainab takatse shi

"Dalla kayi mana shiru, duk wani mutunci da nake gani naka wlh ka ɓarar dashi, bari kaji wlh koda maza sun ƙare a duniya Nura bazan taɓa son ka ba bazan taɓa auren ka ba, har yanzu kallon ka nake yi a matsayin saurayin ƙawata kuma Ni bana cikin maciya amana, and nasan da cewa Halwa baza ta taɓa barin ka ba coz nasan irin ƙaunar da take maka, duk inda take a faɗin duniya tana nan tare da kai aranta, idan ma har wani abu kuka ƙulla domin tabar gidan nan to wlh kun ci amanarta".

Wani irin kallo tabuga masa kafin taci gaba da cewa "kasani duk inda Halwa tatafi zata dawo wannan alƙawari ne, anan ne zan tabbatar maka da cewa ita ɗin me ƙaunar ka tsakani da Allah ne ba irin ka ba".

Daga haka tajuya tashige gida batare da tabari yasake furta komi ba, shiru Nura yayi yana kallon hanyan da tabi, ya jima anan tsaye kafin yabuɗe kyakykyawar motar sa yashiga yabar wajen, gidan da yasiya wa iyayen sa yanufa, yana zuwa yadanna hon aka buɗe masa Gate yakutsa motan ciki, bayan yayi parcking yafito yashiga cikin gidan, Mama na zaune a parlour tana faman kallon da tasaba, don tunda suka dawo gidan da zama yazame mata jiki kallon, zama yayi akan kujeran da yake Facing ɗin nata, ita kuma kallon sa take yi ganin yanda duk yasauya face ɗin sa kamar wani abu na damun sa, hakan yasaka tatambaye shi da cewa

"Lafiya Nura meke damunka ka fita cikin walwala kadawo fuska a turɓune?"

Sai alokacin yakalle ta yace "Mama Zainab ce".

Numfashi Mama taja don tariga tasan da zancen, sai da taɗan ɗau lokaci tana ci gaba da kallon sa kafin tace "wai ni Nura meyasaka baza ka nemi wata bace sai ita? Taya zaka zauna yarinya tana wulaƙanta ka amma kaƙi kasauya ta? Ni fa dama hankalina be kwanta da ita ba tunda ita ɗin ƙawar Halwa ce ƙut da ƙut, kuma dama abokin ɓarawo ai ɓarawo ne ban ɗauke tsammanin itama halin su ɗaya ba".

Cike da rashin jin daɗin kalaman Maman nashi yace "Mama don Allah ki dena aibanta ta, Ni nasan Halin Zainab baza ta taɓa aikata abinda Halwa tayi ba duk da kuwa suna ƙawaye, kuma Ni ita kaɗai nake jin zan iya aura sabida ina matuƙar ƙaunar ta tun ba yanzu ba, kawai ki taya ni da addu'a shine nafi buƙata a wajen ki".

Yana ƙarisa maganar nasa yamiƙe yayi hanyan fita, ita kuma Mama tabi shi da kallo har yafice, sai kuma takaɗa kai cike da tausayin ɗan nata a ranta tana masa fatan alkhairi

...... ...... ...... ...... . .. Tun tafiyan Halwa babu daɗewa Nura yazo ma iyayen sa da zancen zai tafi Legos wani kasuwanci acewar sa bazai dogara da aikin gwamnati ba, dama can yana siye da sayarwa ne na kayan gona, yanda yayi musu bayani akan kuɗin da zai iya samowa hakan yasaka basu wani ja maganar ba suka barsa yatafi, to be rufa watanni uku ba yadawo da zunzurutun kuɗi acewar sa sana'ar da yayi ne Allah ya albarkace sa, iyayen sa sunyi murna matuƙa da samuwan ɗan nasu, acikin lokaci ƙanƙani Nura yayi kuɗi ya buɗe shaguna da yawa ya saka masu kula dasu, kuma ya siyan ma iyayen sa gida me kyan gaske suka koma, sannan shima ɗin yasoma ginin sa inda zai yi aure

Tun dawowar sa yasoma neman Zainab a matsayin wacce zai aura, amma har yanzu ita Zainab taƙi amincewa dashi, shi kuma yaƙi haƙura da ita sabida mugun son da yake mata.

.

_To ya za'a kaya?_

_Plz Kar ku manta kuyi_

*Shere* *Vote* *Comments.* [11/1/2020, 9:20 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```

_*NANA FARUK* wannan shafin naki ne ke kaɗai, Allah yabar ƙauna🥰_

.

*CHAPTER 40*

Turo ƙofan Mom tayi tashigo cikin ɗakin, Nazeefa dake zaune tsakiyan gado ta tanƙwashe ƙafafun ta tana faman tunani taɗago kai tana kallon Mom ɗin, ita kuma ƙarisowa tayi tazauna gefen gadon tana kallon ta tace

"Meke damunki Nazeefa?"

Nazeefa kallon Mom tayi tace "babu komi Momy".

"Ban yarda ba ki faɗa min gaskiya idan da akwai abinda ke damun ki, gaba ɗaya na lura dake tun da daɗewa kina cikin damuwa, kullum cikin tunani kike kuma kinƙi kifaɗa min abinda ke damun ki, bana son in ganki cikin damuwa hakan na damuna coz Ina jinki tamkar ƴata ta cikina ne".

Sunkuyar da kanta ƙasa tayi tana jin hawaye na son zubo mata, idan da tana da daman faɗa mata abunda ke damun ta da tuni tadaɗe da sanar mata, sai dai kashhh baza ta taɓa iya faɗa mata gaskiyan abinda ke cin zuciyarta ba

Dafa bayanta Mom ɗin tayi tace "ki sanar dani kinji Nazeefa zan miki duk abinda kike buƙata idan har ina da halin yi, bazan taɓa barin hawayen ki yazuba ba zan kasance me share miki hawayen ki".

Wani irin sanyi Nazeefa taji acikin ranta tare da wani irin ƙaunar Mom na sake shiga zuciyarta, sai dai baza ta taɓa iya faɗa mata ciwon son ɗanta ne yakamata ba, "to taya?" Hawayen da taji suna son zubo mata ne tayi saurin mayarwa tana ɗago kai takalli Mom cikin sanyin murya tace

"Momy babu abinda ke damuna, idan har akwai kece ta farko da zan faɗa miki sabida na ɗauke ki tamkar ke kika zuƙuna kika haife ni, ki yarda dani Momy babu abinda ke damuna".

Shiru Mom tayi tana kallon ta, sai dai ko kaɗan bata yarda babu abinda ke damun ta ba bcoz ko wanene yaga halin da take ciki dole yatabbatar wa kansa tana cikin tsananin damuwa, sosai take mamakin abinda ke damunta har takasa bayyana mata, amma kuma tayi wa kanta alƙawari sai ta gano ko me ke damun ta kuma sai ta share mata hawaye da iznin Allah, ajiyan zuciya tasauke kafin tace

"To shikenan na yarda dake, amma duk abinda ke damun ki kiyi gaggawar sanar dani ki dena ɓoyewa kinji?"

Gyaɗa kanta Nazeefa tayi sai kuma tace "insha Allahu Momy".

"Ok tashi ki cire kayan makarantan akwai inda zaki raka Ni".

Amsa mata tayi tana tashi tare da saukowa daga kan gadon, itama Mom tashi tayi tafice a ɗakin, sauya kayan ta tayi tasanya doguwar rigan abaya Blue Black, sannan sai tayi Rolling da ɗankwalin abayan, komai bata shafa a fuskarta ba illa flat shoes da tasanya a ƙafafuwan ta, sosai tayi kyau white skin ɗin ta sai sheƙi yake yi kasancewar ta samu hutu har wani ƙiba tayi tare da ƙara girma, fita tayi ta'iske Mom a parlour suka fice, motar Mom ɗin suka hau drever yatuƙa su suka bar gidan.

A wani ɗan madaidaicin gida Drever yasauke su suka fito suka shiga, matar gidan tana zaune a parlour tatarbe su cikin fara'a tare da kawo musu Drinks, sai da suka ɗan yi hira kafin Mom tace

"Yauwa Hajja Turai maganar da muka fara dake a waya ne akan kayayyakin da zaki ɗauko min a London, don haka shiyasa nataho muyi maganar sosai sai ki faɗa min da yaushe zaki tafi?"

Cikin fara'a Hajja Turai tace "ai ina da kaya a ƙasa gaskiya ba yanzu zan koma ba, inaga sai nan da One Month, yanzu abinda yakamata dai sai kiyi min list ɗin komi kibani hakan zai fi, bari in ɗauko miki Littafi".

Miƙe wa tayi tashige ɗaki babu jimawa tadawo riƙe da Littafin tamiƙa mata, Mom amsa tayi tana cewa

"Yauwa sannan kuma zan baki saƙon ƴata ga tanan, itama ɗin kizaɓo mata kayan fitan biki masu matuƙar kyau, acikin gwala-gwalan da zaki siyo min sai ki ɗaukar mata ɗaya, Ni dai ina son ki gwangwaje ta sosai komi yakasance Expensive ne nata".

Dariya Hajja Turai tayi tana kallon Nazeefa tace "ai babu matsala Hajiya Hajara duk abinda kikeso hakan za'a yi, amma ko itace Amaryan don naga kina ji da ita?"

Mom tace "a'a ƙanwar sa ce ai".

"Allah Sarki". Cewar Hajja Turai still tana kallon Nazeefa

Mom tace "don Allah Hajja kaya masu kyau nake so sabida kinsan bikin Autana ne that's why nazo wajen ki, and sai kuma Furnitures ɗina don Ina son nasauya komi na ɗakina".

"Baki da matsala insha Allahu duk abinda kikeso zan yi ƙoƙarin naga na samo miki dai-dai da zaɓinki".

Ita kuwa Nazeefa da tun sanda tazauna tasad da kai ƙasa tana sauraron su, wani irin ƙunci take ji a maƙogaron ta, ji take yi tamkar tabuɗe baki tayi ta zunduma ihu sabida tsaban baƙin ciki, har hawaye sai da tai ta sharewa batare da sun kula da ita ba suna ta tattaunawa, bayan Mom ta gama yin mata list ɗin gaba ɗaya sannan sukayi sallama suka fito, har wajen mota Hajja Turai tarako su sai da taga fitarsu kafin takoma cikin gida

Suna cikin motan Khalil yakira Mom, bayan tayi peacking call ɗin suka gaisa take cewa

"Ɗazu ka kira bana ji ne matsalan network ne, yanzu kuma muna kan hanya ne naje gidan Hajiya Turai".

Khalil da be san ma wacece Hajiya Turan ba sai tambayan ta da yayi "me taje yi?"

Nan take faɗa masa sannan taƙara da cewa "wai kuwa kana kiran surukar tawa don nasan Halin ka?"

Shiru yayi don be san amsan da zai bata ba, shi idan har basu suke masa maganar bikin ba sam mantawa yake yi zai yi aure, kuma ita yarinyan tun sanda yabar ƙasar yamanta irin ta, ko za'a tsare sa da bindiga yafaɗa yanda take bazai iya ba, abinda yasani kawai fara ce ita but kamannin ta ya daɗe da gushe masa, sunan ta ma kanshi be riƙe ba duk da su Mom wani lokacin suna faɗar sunan idan suna waya

"Kayi shiru ko dai dagaske ba ka kiran ta?'

"Ina kiran ta mana Mom". Yafaɗa cike da sanyin murya don shi sai yanzu yasan be kyauta ba tunda ko Phone numbern ta be amsa ba

Daga nan sallama suka yi Mom ta'ajiye wayan cikin jaka, kallon Nazeefa da tatakure a jikin motan tayi idanuwanta a rufe ruf, numfashi kawai Mom taja tana ɗauke kai.

.

*** *** *** *** *** ***

Da hannu biyu tazuba tagumi tana tunani har batasan sanda Mami tashigo tatsaya a kanta ba, sai da tagama ƙare mata kallo kafin takira sunan ta

Firgigit Kausar tayi tana ɗago kai takalli Mamin nata

"Wai ke lafiyan ki lau kike yawan tunani meke damun ki ne?"

Shafo fuskarta da hannun ta tayi cikin sanyin murya tace "babu komi".

"Baza ki faɗa min ba kenan?".

"Mami babu komi fa tunanin aiki ne kawai".

Gyaɗa kai kawai Mami tayi kafin tace "to ki tashi kije Sharif na parlour yana jiran ki".

Kausar kallon Mamin tayi fuska babu walwala tace "Mami kice masa bana nan Ni bazan iya fita ba".

"Wai ke kanki ɗaya kuwa? Wai meyasaka yanzu bakison fita ne idan yazo? Ko faɗa kukayi ne?"

Kausar tace "a'a kema Mami kinsan Da da yanzu ba ɗaya bane, bana son takura ne kawai".

Baki Mami tabuɗe tana kallon Kausar, ita kanta da take Mahaifiyar ta tasan Kausar ta sauya, gaba ɗaya ta dena walwala agidan, sai tashige ɗaki ita kaɗai tazauna su rasa me take yi cikin ɗakin, kuma duk uzurin da zata kawo be da wani kan gado, ajiyan zuciya tasauke kafin tace

"Ki fito ki same sa yana parlour yana jiran ki".

Daga haka tajuya tafice batare da tajira ta bakinta ba

Ita kuwa Kausar ba'a son ranta ba tamiƙe tafito, yana zaune a parlour'n shi kaɗai, gaban sa duk an cika masa da kayan motsa baki amma be taɓa komi ba, shi kansa idan kakalle sa baya cikin hayyacin sa duk ya rame yasaka damuwa a ransa sakamakon sauyawan da Kausar tayi masa, kuma hakan sosai ke barazanan tarwatsa rayuwan sa sabida ba ƙaramin so yake mata ba, kullum ji yake yi ƙaunar ta na sake hauhawa acikin ransa memakon raguwa, ya rigada ya saka ta acan cikin zuciyarsa wanda rabuwa da ita zai mishi matuƙar wahala kuma zai taɓa masa rayuwan sa

Tunda tafito yake kallon ta har taƙariso tazauna akan kujeran dake Facing nasa, cikin sanyin murya batare da ta kalle sa ba tace

"Barka da zuwa".

Murmushi yasaki yace "yauwa gimbiyata kina lafiya?"

"Lafiya lau".

"Kwana biyu ina ta kiran wayan ki akashe na kasa haƙura dole nayi tunanin zuwa yau, shin meke faruwa ne Baby?".

Sai alokacin taɗan kalle sa kana taɗauke kai tace "kashe wa nayi".

Shiru kawai yayi yana kallon ta, sai kuma daga baya yace "wai Kausar ko dai kin samu wani ne kikeson min wulaƙanci?"

Sosai taɗago kanta a wannan karon tana kallon sa, shima ɗin ita yake kallo cike da tuhuma, sun jima suna kallon juna batare da ta sami amsar da zata bashi ba kafin taɗauke kai tare da haɗiyan yamu

"Kinyi shiru ina son insan abun da yasaka kikeson juya min baya Kausar, don Allah ki sanar dani idan wani laifi nayi miki wlh nayi alƙawari zan nemi yafiyar ki".

Sai kuma yayi shiru yana saukowa kan kujeran yayi Neeldown agaban ta yana ci gaba da cewa

"Idan ma kina so in duƙa a gaban ki ne to gani na duƙa don Allah ki yafe min, wlh Kausar ina matuƙar ƙaunar ki bazan iya rabuwa dake ba, dan Allah ki taimaki rayuwata ki faɗa min laifin da nayi miki in nemi gafarar ki". Yaƙarike maganar nasa da rawan murya

Kausar kallon sa kawai take yi don batasan sanda yazuƙuna ba, take taji hawaye sun cika mata idanu sabida tausayin sa, tasan da cewa tana ƙaunar Sharif matuƙa amma yanzu shigowar Khalil rayuwan ta tarasa soyayyan sa a zuciyarta, tayi iya ƙoƙarin ta don taga tayi yaƙi da abinda ke damun ta amma ina ta kasa, ta kasa dawo da ƙaunar da take masa aranta, burin ta yanzu kawai tazama mallakin Khalil, amma tarasa ta wani hanya ne hakan zai faru, tasan da cewa yanzu Khalil yayi mata nisa nisan da baza ta iya samun sa ba tunda yana shirin aure

Wani irin kuka yataho mata batasan sanda tasake sa ba, jikin Sharif har yana rawa wajen matsowa kusa da ita yana tambayan abinda ke faruwa da ita, gaba ɗaya ya shiga damuwa ya rasa yanda zai yi, ita kuwa kukan take yi tana toshe bakinta da hannayen ta, sosai take tausayin kanta don batasan halin da zata shiga ba nan gaba

"Dan girman Allah kiyi shiru Kausar, kiyi shiru ki faɗa min abinda ke damun ki, wlh idan har Ni ne baki ƙauna yanzu zan barki, zanyi nesa da rauyuwan ki idan har hakan zai saka ki farin ciki, bana son kukan ki".

Still kallon sa take yi da idanuwanta da sukayi jazur tana ci gaba da kukan ta, daƙyar ta'iya buɗe baki tace

"Bakayi min komi ba Sharif kuma babu abinda ke damuna, idan har ka shirya aurena to katuro".

Tana faɗan haka tatashi da gudu tayi ɗakin ta, tana zuwa tafaɗa kan gado tana sakin wani kukan da ƙarfi

Ta san da cewa hakan shine kaɗai mafita agare ta, ta hakan ne kaɗai zata sami salama tamanta shi cikin rayuwanta, hakan zai sa tayi nesa dashi gaba ɗaya.

_ ****_

A cikin kwana biyu Sharif har ya turo magabatar sa, kuma komi ya kammala har an saka rana nan da wata biyar masu zuwa, SAI MUCE ALLAH YAKAIMU LAFIYA MUSHA BIKI😅

.

_Plz karku manta da comments da Vote_ [11/7/2020, 2:21 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```

.

*CHAPTER 41*

*FIVE MONTHS AGO*

Yau ake saka ran dawowar Brr. Ibarahim Khalil, don haka Mom tashirya tarban Autan nata, Sameer da matar sa tare da ƙanwar ta Abida duk sun zo gidan su ma tarban sa, su suka taya Mom girki tare da gyare-gyaren gida, anyi soye-soye anyi duk abinda yadace sannan ne lokacin driver yatafi ɗauko sa a airport don ƙarfe 02:00pm. Jirgin su zai sauka, drever na tafiya shima Brr. Tahir yazo da nashi iyalin matar sa Suhaila da ɗan su ɗaya Adam.

Bakin Nazeefa har kunne sabida tsaban farin ciki zataga Yayan nata kuma mafi soyuwa a ranta, da ita ake aikin komi don ko kaɗan babu wanda yakula da yanda tasaki jiki take ta fara'a kamar bakin ta zai tsake becouse su ma ɗin cikin su kowa tashi murnan ya ishe sa.

Lokacin da jirgin yai landing *BRR. IBRAHIM KHALIL* yana ɗaya daga cikin waɗanda suke sauko wa ta matattaƙalan jirgin, Ni dai gaskiya bangane sa ba sai dai bansani ba Fans ɗinsa ko ku zaku gane sa, don dagaske ya sauya sosai fiye da yanda nasan shi, gold skin ɗin sa yayi wani irin haske sosai sai ɗaukan ido yake yi, hutu da kwanciyar hankali kawai nake hangowa a tattare dashi da alamun dai ƙasar tayi mugun amsar sa don ba ƙarya ya sauya ɗin, sai zuba murmushi yake yi abinda ba kasafai kake gani a face ɗin sa ba

Har sanda ya'amso trolly ɗin sa yafito haraban airport ɗin sannan ne drever yahange shi yataho dasauri yazo wajen sa yana miƙo masa gaisuwa, amsa masa yayi cike da fara'a sannan suka shiga mota sukayo gida, bazan iya fasalta muku yanda Familyn suka nuna farin cikin su ba, bayan an gaigaisa ya huta sosai sannan aka wuce dainning, anan kowa yaci abinda yakeso tukun suka dawo parlour, hira aka dasa ana ta dariya, wlh idan kukaga Khalil baza kuce shine ba domin har dashi ake ta wasa da dariya, kai sai ince har da ɗabi'u aka sauyo masa acan ɗin, Nazeefa da Abida kuwa babu abinda suke yi sai kallon sa ko wacce zuciyarta na mafarkin yakasance nata na har abada, don har alokacin Abida taƙi tacire sa aran ta duk da kuwa Hakima sai da tagargaɗe ta tamanta dashi baza ta taɓa samun sa ba coz yanzu aure zai yi, kuma itama taso ƴar uwan nata ta aure shi har mitan maganar tarinƙa ma Sameer but basu samu nasara ba.

Su Brr. Tahir suka soma tafiya sannan Khalil shima yayi musu sallama drever yanufi gida dashi, lokacin da suka isa layin su motoci yai ta gani duk sun cika layin, sai da suka matso gab gidan sa sannan ne yafahimci agidan su Kausar ake taron, ga jama'a nan burjik awaje maza da mata kowa na sha'anin gaban sa da alamu dai biki ake yi, mamaki sosai ne a fuskarsa sai dai be iya furta komi ba har Drever yayi hon agidan sa aka buɗe musu Gate motan tashige, bayan drever yayi parcking Khalil yafito lokacin duk ma'aikatan gidan sa sunyo wajen suna miƙa masa gaisuwa, haka yai ta amsa musu cikin sakin fuska sannan ne yanufi cikin gida Sale na biye dashi da trolly ɗin sa

Cikin gidan an gyara masa ko ina kuma yasan duk aikin Sale ne hakan ya faranta masa rai sosai, anan parlour yaba ma Sale umarnin ya'ajiye Jakan sannan yafice, shi kuma yaja trolly ɗin yanufi ɗakin sa, yana shiga yasaki hannun trolly ɗin yazauna gefen gadon sa, ya ɗan yi wajen mintuna 5 kafin yatashi yacire kayan sa yashiga wanka, yayi kusan mintuna talatin kafin yafito yashirya cikin farar t.shit da gajeren wando fari da ɗige-ɗigen ja, zuwa yayi yazauna kan kujera yasoma latsa wayan sa, kusan mintuna goma yaɗauka sannan yasoma laluban numban Kausar yadanna mata kira

Lokacin Kausar na zaune a ɗakin ta tare da ƙawayen ta an gama mata kwalliya, kasancewar yamma tayi har motocin ɗaukan amarya sun zo, becouse acan garin Daura zasu zauna tunda anan ne Sharif ɗin yake aikin sa, duk da dama nan ne tushen sa amma iyayen sa anan Katsina suke zaune

Tsananin firgita Kausar tayi da ganin wanda yake kiran ta har batasan sanda takusa sulmiyar da wayan ƙasa ba, sai wata ƙawarta dake kusa da ita ne tayi saurin taro wayan tana cewa

"Kee Kausar Ina hankalin ki yaje zaki saki waya ƙasa?"

Kausar da tayi mutuwar zaune sabida mamaki, ƙyafta idanun ta tayi da suka cicciko da hawaye tana bin wayan da kallo, ƙawarta me suna Rumaisa tamiƙo mata wayan da aka sake kira akaro na biyu tace

"Riƙe gashi an sake kira".

Ahankali tasaka hannu ta'amsa wayan sai dai takasa anwer call ɗin, ko kaɗan bata taɓa tunanin ganin kiran sa a wannan lokacin ba duk da tasan cewa lokacin dawowan sa yayi, tun sanda yatafi basu taɓa waya dashi ba wannan dalilin ne yasaka tashiga ruɗu da bugawar zuciya

Shi kuma a fannin Khalil tunda yatafi ya nemi layin ta sama da biyar duk sanda zai kira ta wayanta sweech off, daga ƙarshe shine yadena kiran ta gaba ɗaya don a tunanin sa ko akwai matsala ne, ita kuma kullum da tunanin kiran nasa take kwana dashi kuma take tashi, koda yaushe tana jiran taga kiran sa amma har tsawon wannan lokacin babu shi babu labarin sa kuma gashi ita bata da numaban sa na can

Batasan tana zub da hawaye ba sai da Rumaisa tadafa ta tana cewa

"Wai lafiyan ki ƙalau kuwa? Kuka fa kike yi Kausar?"

Sai alokacin tadawo hankalin ta tana kallon Rumaisa da tabi ta da kallo cike da tsananin mamakin ta, lokacin gaba ɗaya hankalin ƴan matan har ya dawo kan su, dasauri Kausar tatashi batare da ta furta komi ba tashige Toilet tana rufo ƙofa, hakan yasaka duk suka bi ƙofan da kallo suna tunanin abinda ke faruwa da ita

Tana shiga kiran yasake katsewa, sai ga wani kiran don shi Khalil ya kasa haƙura da kiran nata, sai da tajingina da bango kafin ta'amsa kiran tana sakawa a kunne, cikin ƙasa da murya tace

"Hello".

Daga can ɓangaren Khalil kuwa shima jingina bayansa yayi da kujera cikin cool voice ɗin sa me daɗi yace

"Hello Friend".

Kausar danne duk abinda ke cikin ranta tayi cikin ƙarfin hali tace "dama ashe zaka iya mantawa dani?"

Ɗan shafo sajen sa yayi yace "Kausar kiyi haƙuri nasan ban kyauta miki ba, amma kuma nayi ta neman Phone Numban ki bana samun ki".

Hannun ta taɗago tana kallon fingers ɗin ta da suka sha jan lalli, cikin son maida kukan da yataho mata tare da ɗaura jarumta a muryan ta tace

"Na gane Barrister, ya hanya to?"

"Alhmadulillah.. da fatan kema kina lafiya?"

Murmushi taƙirƙiro dai-dai lokacin da hawaye suka sauka kan kuncin ta tace "sai alheri friend".

Khalil shima cikin murmushin yace da ita "Allah ko?"

"Ƙwarai". Tataɗa tana dariya ahankali

"To bani nasha".

Sai da taja numfashi kafin tace "Allah yayi an ɗaura aurena yau".

Cikin tsananin mamaki da al'ajabi Khalil yace "haba dai serious fa?"

Kausar tace "I'm serious.."

Sai kuma taɗan saki murmushi me sauti tace "kaga na rigaka ko?"

"Sosai don ban yi tunanin hakan ba, sau da dama kina bani labari kuma ban taɓa jin kinyi min maganar samarin ki ba, ashe ashe.."

Sai kuma yai dariya yana cewa "to Allah yatabbatar da alheri gaskiya naji daɗin wannan maganan".

Shiru kawai Kausar tayi bata amsa ba, hakan ya tabbatar mata da cewa tabbas bata cikin zuciyarsa, ita kaɗai take kiɗan ta kuma take rawan ta

Murmusawa shi kuma yayi yace "Amarya kenan bari in barki haka ko? don nasan yanzu kina busy".

Share hawayen ta tayi cikin rawan murya tace "to".

Daga haka bata iya furta komi ba don idan tasake faɗan kalma ɗaya zata iya fashewa da kuka

Nocking ƙofan da akayi yasaka tayi saurin juyowa tana kallon ƙofan, sai kuma tamaida idanunta kan wayan lokacin ne Khalil yadatse kiran, lumshe idanuwan ta tayi tana jin wani ƙunci da baƙin ciki na mamaye ilahirin zuciyarta

"Kausar wai me kike yi aciki? ki buɗe mana".

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull