Kenza eBookz

Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 15

Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 15

Barrister ibrahim khalil complete Chapter 15: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 15. Maganar Rumaisa yadawo da ita cikin hayyacin ta, dasauri…

4,484 words

Maganar Rumaisa yadawo da ita cikin hayyacin ta, dasauri tasanya hannu tashare sauran hawayen ta tanufi ƙofan tabuɗe, duk bin ta suka yi da kallo har da ƙanwar Mamanta da tashigo yanzu, ita kuma sai tasad da kai ƙasa don bata son su fahimci wani abun

Ƙanwar Maman nata ne tace "wai me kuke jira ne, ku fito motoci sun rigada sun iso".

Juyawa tayi tafita tana cewa "su hanzarta".

Kausar sai da tasha nasiha wajen ƴan uwa kafin aka fito da ita, a lokacin sai kuka take yi, Ni dai bansan ko na menene ba ni dai naga an saka ta a mota sun fice, to sai muce Allah yasanya alkhairi *KAUSAR.*

....... ....... . .. ....

Khalil kuwa tunda suka gama wayan ya'ajiye yalumshe idanun sa yana tunani, yaji babu daɗi yanda suka rabu sabida shaƙuwan da sukayi, be taɓa tunanin baza su sake haɗuwa ba idan yadawo, ya so ba yau bane auren ta ko shima yahalacci auren nata, amma gashi har anyi an gama batare da yaje mata ba, hakan yaƙara saka shi rashin jindaɗi

Allah Sarki haka shaƙuwa yake dama, a ranan kuwa haka yawuni shiru duk bashi da walwala, har yayi sallan magriba da isha'i yadawo gida komi be ci ba yakwanta, ya daɗe yana tunani kafin barci ɓarawo yaɗauke shi.

.

**** **** ***** *****

A cikin kwana biyu da dawowar Khalil sai gashi ya samu kira agidan gwamnati, koda yaje meeting akayi dashi, sun tattauna na wajen awanni kafin su gama, daga ƙarshe dai an ɗauke shi aiki a matsayin Lauyan gidan Gwamnati, ga albashi me tsoka da zai riƙa samu, duk da dama can sosai Khalil yake samun kuɗi don zan iya cewa ko mahaifin sa be fi sa kuɗi ba, sai dai shi Lauya ne me zaman kansa haƙƙin talakawa kaɗai yake ƙwatowa, Duk wani mara galihu idan har yaje gare sa shi kuma zai share masa kuka, asannu-asannu sunan sa yayi shura sosai talakawa sun soma sanin sa, gaba ɗaya gidajen talabijin da rediyo, jaridu duk maganar sa yanzu ake yi, acikin lokaci ƙalilan Allah ya ɗaukaka shi fiye da Da, kuma duk saboda ƙarin girman da yasamu ne yanzu da kuma ɗaukan sa aiki da akayi agidan gwamnati, sanin da talakawa sukai mishi yanzu har sun soma kawo masa Cases kala-kala, shi kuma don yashare musu kuka haka yake faɗi-tashi wajen taimaka musu da ƙarfinsa da kuɗin sa.

_dama akace dare ɗaya Allah kan ɗaukaki bawa fiye da tunanin me tunani, yanzu sunan Brr. Khalil ya zagaye duk faɗin garin Katsina da kewaye sabida ƙwazon sa, sosai ake ji dashi.

October 2020. [11/7/2020, 2:40 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```

.

*CHAPTER 42*

An tsai da ranan auren Brr. Kahlil da Saleema nan da Four Month, zuwa lokacin tarigada ta rubuta Final Exams ɗin ta, asannu-asannu rayuwa taci gaba da tafiya cikin nasarori da akasin sa, wasu tazo musu da daɗi wasu kuma tazo musu a yanayin da babu daɗi, ga dai shi Saleema a wannan lokacin sosai ciwon ta yatashi kullum cikin nema mata magani ake yi, wani lokacin adace wani lokacin kuma rashin sa, ga kai ya ɗau zafi karatun su ya zo ƙarshe haka take lallaɓawa take zuwa School sai dai ba kullum ba, duk ta rame sosai take jin jiki.

A fannin Khalil kuwa yanzu yana da Numban ta kuma yana kiran ta akai-akai yatambayi jikin ta tunda yasan bata da lafiya, kusan sau biyu yana zuwa gidan, shima yanzu aiyuka sun yi masa yawa baya zama sosai kullum cikin aiki yake, ahaka Allah yasa biki yaƙarato ko wani fanni tuni sun soma shiri ana hidima kala da iri, amma ta fannin Amarya babu lafiya har yanzu sai dai ba kamar da ba don yanzu jikin da sauƙi

Ummi tare tahaɗa su da Halwa ake musu gyaran jiki, itama yanzu Halwa ta soma shirye-shiryen zana WAEC da zatayi.

Yau ta kasance saura sati ɗaya biki kuma a yau ne Halwa zata soma zana jarabawan ta, haka tatsallake tatafi bada son ranta ba don ko kaɗan bataji daɗin yanda za'ayi bikin Saleema ita kuma tana Exams ba, sai idan taje tadawo ne ake Hidiman biki da ita.

Fannin su Mom yanda suka ɗau bikin nan da girma zai baka mamaki, komi cikin wadata da nuna su ɗin masu kuɗi ne don tun ana saura sati biyu ake shagulgula agidan, idan kashiga cikin gidan ko matsuguni baza ka samu ba tun kafin ma bikin yazo kenan, ƴan uwa da abokan arziƙi duk sun cika gidan.

Nazeefa kuwa damuwan da tasaka aranta har bacci bata iya yi ishashshe hakan yahaifar mata da ciwon kai me tsanani tare da zazzaɓi, duk shagulgulan da ake yi tana ɗaki taƙule taƙi fita ayi da ita, sosai take jin jiki har sai da Sameer yakaita asibiti aka dubata, koda suka dawo Mom tayi ta kula da ita tana bata drugs duk ta tashi hankalin ta, gaba ɗaya ko lokacin kanta bata dashi ga jinyan Nazeefa ga hidiman mutane, wannan yasaka taba Nazeefa tausayi sosai hakan yasa tadaure taɓoye duk abinda ke damunta tayi kamar ta samu sauƙi tana fitowa ana biki da ita, hakan yasa Mom taji daɗi har hankalin ta yakwanta.

Fannin Ango kuwa baya zama yanzu sabida Case ɗin da yake gudanarwa a Court, shiyasa duk wani shagulgula bashi ciki, sai idan ya sami kansa ko zuwa dare ne yake zuwa gidan su.

..... ...... ...... ...... ....

Gidan su Amarya su ma ba laifi ana ta shagulgula duk da babu wani armashi Amarya tana kwance babu lafiya, wannan dalilin ne ma yasa basu shirya komi ba in banda taron bikin kawai da za'a gudanar

Duk abunda ake ma Amarya anyi wa Saleema, an mata lalli an mata gyaran jiki komi an mata, sosai tayi kyau tafito a Amaryan ta duk da kuwa zallan raman da tayi

Sai ana gobe biki ita Halwa akayi mata nata Lallin sabida ranan bata da Exams, kuma a ranan akayi musu gyaran kai ita da Saleema, komi har gida ake zuwa ayi musu basu zuwa ko ina.

*** **** **** **** ****

Washe gari ya kasance Saturday aka shaida ɗaurin auren *BARRISTER IBRAHIM KHALIL ABDURRA'UF* tare da Amaryan sa *SALEEMA MUSTAPHA*

Ana gama ɗaurin auren ango da abokanan sa suka tafi Hotel inda zasuyi ƙwarya-ƙwaryan liyafan da suka shirya.

*GIDAN SU AMARYA*

Amarya tasha kyau cikin shigan ta na Material Less me ruwan Hoda da ratsin ash colour, ɗinkin riga da sket da suka ɗauki jikinta sosai, ba'ayi mata kwalliya ba don taƙi yarda shiyasa ba'a matsa mata ba

tana zaune akan gado ta ɗaura Husna ajikin ta da take ta faman wasa da kayan Saleeman, sosai yarinyan tasake girma ga wayau sosai, idan kaganta baza kace watanni tara da haihuwar ta ba

Cikin ɗakin akwai friends ɗin ta na school su wajen biyar, sai hira suke yi suna shewa, wasu kuma suna mata tsiya "gwara tawarke don dole akaita yau ɗin"

Ita kuwa ɓata fuska tayi sai sake marairaice face ɗin ta take yi, kallo ɗaya idan kayi mata zakasan ta faɗa ainun hakan yasa tasake haske sosai, bata kula su ba sai dai bin su da ido da take yi

Ana haka Halwa taturo ƙofa tashigo, dawowarta kenan daga Exams da taje tarubuta, fuskarta yalwace da murmushi take kallon Saleema da itama tasanya mata idanu tana ƙara ƙwaɓe fuska kamar zatayi kuka, takowa tayi tashigo ciki tana gaisawa da ƙawayen Saleeman sannan tanemi wuri tazauna gefen Saleema tana sake yalwata fuskarta da murmushi, sosai take farin ciki a yau ɗin tana taya ƴar uwan nata murna

Hannu tasaka tadafa kafaɗun Saleema bakin ta yaƙi rufuwa, sai kuma tamaida hannun kan kumatun ta taja tana cewa

"Haba ƴar uwa ya haka kin ɓata fuska? Don Allah ki saki ranki kiyi farin ciki yau ranan ki ne, ko so kike Angon yayi tunanin bakya son sa ne? Kinga hakan zai jawo masa matsala akasa gane kansa".

Hakan yasa Saleema tasaki dariya babu shiri saboda maganar Halwa ɗin, ita kuwa Halwa kallon ta take yi tana murmusawa cike da jindaɗi, sai kuma tamaida kallon ta kan Husna tana haɗe rai tace

"Waye kuma yakawo wannan yarinyan nan?"

Itama Saleema kallon Husnan tayi da tatsare su da idanu ta saka hannu ɗaya cikin baki tana ɓashe bakin kamar tana jin su

"Kawo ta in kaita wajen Larai, yau fa ranan ki ne be kamata kizauna kina raino ba, banda abinki ma ke da baki da lafiya?"

Ture hannun ta Saleema tayi tana hararan ta tace "to Ni nace akawo ta ina ruwan ki?"

"Haba Sister don Allah yau rana ɗaya kibarta wajen Larai". Cewar Halwa tana sake kai hannu zata ɗauke ta

Sake ture hannun Halwan tayi tarungume ta da kyau tana cewa "Ni fa nace akawo min ita, wlh babu inda zata don tana nan wajena har mu tafi".

Waro idanu Halwa tayi tana cewa "wai da ita kike nufin zaki tafi?"

"Eh mana.. da dake zan tafi?"

Sai ƴan ɗakin dake kallon su suka kwashe dariya

Zaliha tace "kai wani lokacin Saleema bata da hankali al'ƙur'an tana jinta kamar sokuwa ne".

Sai suka sake ɓarke wa da dariya, ita kuma tabi su da harara tana cewa

"Ni ce bani da hankali ko?"

"Ai da gaskiyar Zaliha idan ba sokuwa bace ke taya ma zaki tafi da yarinyan nan? Ai mijin ma sai yakoro ki". Cewar Dija Babbar ƙawarta tana sake kecewa da dariya

Halwa murmushi tayi tace "Sister wlh kuwa maganar su gaskiya ne, kema kinsan Ummi baza ta barki ki tafi da ita ba gwara ki sauya shawara".

Shiru kawai Saleema tayi bata sake cewa komi ba

Cikin lallami Halwa tasake cewa "kinga koda nan da sati ɗaya ne sai in kawo miki ita idan ma wai tafiyar da ita zakiyi".

Saleema tace "sati ɗaya ai yayi yawa, sai dai idan zakiyi min alƙawari gobe".

Gyaɗa mata kai kawai Halwa tayi don ba wai ta yarda zata kai mata ɗin ba, daga nan hira sukaci gaba dayi, sai da Saleema tace ma Halwa taje tashirya sannan tamiƙe tashiga wanka.

*****

Da ƙarfe 08:00pm. Akazo ɗaukan Amarya, tasha kuka sosai haka taƙanƙame Ummi taƙi tafiya, daƙyar aka samu aka shiga da ita mota Halwa tazauna kusa da ita tana rarrashin ta

A gidan sa aka kaita, sosai gidan yaɗau hankalin duk wanda yashigo, kamar ba gidan da akayi amfani dashi ba komi an sauya sai ƙamshin sabunta yake yi

Ɗakin ta kusa dana Khalil aka shigar da ita, haka mutane sukai ta zagayawa suna ganin abun arziƙi har da Halwa a zuwa gani, anan sukayi sallan isha'i suna ta hayaniya kamar zasu tsaga gidan

Wajen ƙarfe 10:00pm. Abokan ango suka zo tafiya dasu, lokacin ne itama Halwa takira Drever'n gidan su A wayan da Abba yasiya mata don yazo yaɗauke ta, ko kaɗan bata son bin abokan Angon sabida yanda wani yamaƙale mata ɗazu da suka zo daga ta buge sa bata sani ba, ita ta ma rasa uban wa yace musu ita ɗin Sister ɗin Amarya ce, yanzu da suka shigo parlour'n sai faman kiran ta suke yi, komi akayi sai suce "ina Sister ɗin Amarya tazo tayi musu sheda" daga ƙarshe ma tashi tayi tashiga ciki tazauna kusa da Saleema dake zaune saman gado

Har Drever yazo basu tafi ba, sannan ne ma suka soma haraman tafiya, anan ne fa Saleema tariƙe Halwa tana kuka wai baza ta tafi ba, in banda dariya babu abinda su Dija suke mata sai faman tsokanarta suke yi, daƙyar dai tasaki Halwa suka tafi suka barta ita kaɗai kamar Mayya.

.

_Nace ko ina Mijin Oho?_🤔😅 [11/7/2020, 3:02 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```

.

*CHAPTER 43*

Ƙarfe 10:30pm. Su Khalil da Brr. Tahir tare da Sameer suka shigo gidan, daƙyar ma Khalil yayarda suka biyo shi don da yace "baya son rakiyan". Shi da kan sa yashiga har ɗakin ta yace "tafito parlour" daga haka yajuya yafita, ita kuma tamiƙe jiki a sanyaye tagyara mayafinta tafito, ahankali taƙarisa tazauna aƙasa tana gaishe su, cike da fara'a suka amsa sannan ne Sameer yasoma musu wa'azi cikin raha, daga ƙarshe suka yi musu fatan alkhairi tare da sanya alkhairi a auren nasu

Har bakin Gate Khalil yaraka su da zasu tafi, yadawo yatarda Saleema tana nan zaune inda take, be ce komi ba yanufi ɗakin sa, yana shiga yasoma cire babban rigan dake jikin sa bayan ya cire Hulan kansa, agogon hannun sa yacire tare da cire links ɗin rigan sa yazube su yanufi parlour

Har yanzu tana nan zaune inda take, zama yayi kan kujera yana kallon ta, sai kuma yaɗauke kai yana kallon ledan da suka shigo dashi, miƙewa yayi yanufi kichen sai gashi ya dawo da plate a hannu tare da wuƙa, zama yayi a ƙasa kamar yanda itama take zaune a ƙasan, yajawo ledan yabuɗe yaciro Kazan ciki yasoma yanka wa cikin plate ɗin don yayi daɗin ci, bayan ya gama duk yajera mata a gabanta da su Holandia sannan yakalle ta yace

"buɗe fuskar ki kici".

Ahankali tayaye gyalen daga kanta taɗago tana kallon sa sai kuma takalli abinda ke gabanta, cike da tsananin kunya tanoƙe ko motsi ta kasa yi, ganin haka yaja baya yana ɗaukan wayan sa yasoma latsawa yana cewa

"Ki ɗauka kici nace".

Wannan karon batayi musu ba ganin ya matsa can baya kuma hankalin sa baya kanta, hakan yasa tasoma ɗauka tana ci duk da dama tana jin yunwa amma baza ta iya buɗe ciki taci ba, kaɗan taci tacire hannun ta cikin sanyin murya tace

"Na gama".

Ɗago kai yayi yakalli plate ɗin sannan yasake maida kansa kan waya yace "ki ƙara".

Hannu tasaka taci gaba taci, bata daɗe ba tasake tsame hannun ta, wannan karon da yaɗago kai miƙewa yayi yaɗau komi yanufi kichen dashi, yana dawowa yace tataso su je ɗaki, miƙewa tayi tabi bayan sa, suna shiga yanuna mata Toilet tashiga tawanke hannu da bakinta tafito, yasake nuna mata kan gadon.. ta ko haye can lungu taƙudundune da gyalen ta

Shi kuwa Toilet yashiga yayi wanka yafito yashirya cikin kaya sannan yahayo kan gadon yakwanta, shiru sukayi ko wanne yana jin numfashin juna, can kamar amafarki tatsinkayi muryan sa

"Ya jikin naki?"

Cike da jindaɗi ta'amsa masa ganin yanda yadamu da ita sosai, daga haka basu sake yin magana ba har sanda Khalil yaji numfashin ta na fita da ƙarfi hakan yagane tayi barci, juyowa yayi setting ta duk da baya kallon fuskarta hakan be hana yaƙure ta da idanuwansa ba, shiru yayi yana tunani yana bin ta da kallo, abinda be taɓa faruwa dashi ba yau sai gashi zai kwana da mace

Ya daɗe ahaka yana ta saƙe-saƙe kafin yasauke ajiyan zuciya yamiƙe yakashe fitila yadawo yakwanta, addu'a yayi yarufe idanun sa, lokaci ƙanƙani barci yaɗauke sa kasancewar baya samun hutu.

Washe gari shi yasoma tashi bayan da suka koma barcin asuba, wanka yayi yashirya yasaka Milk colour ɗin Gezna da yayi masa kyau matuƙa gaya, duk da bashi da aiki ya ɗauki hutu amma Shari'an da yake yi be rigada ya ƙarƙare ba, akwai sauran aiyukan da yake yi a Court, yana cikin saka Wrest watch yaji Nocking ƙofa, fita yayi yaje yaduba yaga drever'n gidan su ne Mom ta aiko sa da breakfast, amsa yayi kawai yaje ya'ajiye a dainning table yakoma ciki, sai da yayi rubutu a ɗan Pepper ya'ajiye mata saitin kanta sannan yaɗau abubuwan da zai ɗauka yafita.

Babu jimawa da fitan sa tafarka, ahankali tabuɗe idanuwan ta yayinda ƙamshin turaren sa suka cika ƙofofin hancin ta, sake lumshe idanun tayi tana murmushi cike da jin daɗi, sai da tajima ahaka bataji motsin sa ba sannan ne tayaye gyalen fuskarta, da takardan da ya'ajiye mata tasoma cin karo, take gaban ta yafaɗi babu shiri tayi saurin kai hannu taɗauka tana jujjuya shi, sai kuma tamiƙe zaune idanun ta har yanzu akan takardan, buɗewa tayi sai taci karo da

.

_"Aslm alaikum Ni na fita zuwa wani waje bazan jima ba zan dawo, and akwai breakfast a dainning Mom ta kawo..."_

_Mijin ki✍️_

Batasan sanda murmushi yasuɓuce mata ba, kalman Mijinki shi ke ta mata yawo a ƙwaƙwalwa, gaskiya Brr. Daban ne da sauran Mazaje, duk da kuwa ta tabbatar ba son ta yake yi ba amma kuma kulawan sa agare ta da tausayin ta ya wuce tunanin me tunani, yana da halin ƙwarai sosai, memakon yanuna mata tsangwama a'a sai yana sauke haƙƙinta akansa, wannan shi ake kira adalin namiji, tayi imani koda baya son ta zata zauna dashi ahaka domin tasan shine ɗorewar farin cikin ta na har abada

"Allah yabarmu tare".

Tafaɗa a maƙoshi tana sake faɗaɗa fara'an ta

Miƙewa tayi tasauko kan gadon tanufi ɗakin ta, Toilet tashige tawanke bakin ta tafito parlour tanufi dainning, tana jin yunwa sosai don haka baza ta iya jira har sai tagama abinda take yi ba gudun lafiyan ta, zama tayi tahaɗa tea me kauri tasha tare da ƙwai da Arish, bayan ta gama tatashi tashige ɗaki taɗauko Maganin ta cikin kayan ta taɗiba tafito tasami ruwa tasha dashi, sai kuma takoma ɗakin Khalil ɗin tasoma gyarawa musamman kan gadon da sukayi amfani dashi, duk da ita ba ma'abociya aiki bane komi yin musu ake yi, ba'a barin ta tayi komi amma aɗan kwanakin da zatayi aure sai da duk takoya abinda zai bata wahala, don bata son me aiki cikin gidan ta tana da kishi sosai

Bayan ta gama takoma ɗakin ta tayi wanka tashirya cikin farar shadda wanda tare akayi musu da Khalil ɗin, shi kuma yarigada ya saka nashi jiya, ta fito ɗas Amaryan ta sai zabga ƙamshi take yi, kallo ɗaya idan kayi mata zakaga ƙyallin amarci atattare da ita (aure ba wasa ba🤫)

Parlour takoma tazauna a lumsassun kujerun ta masu tsantsan kyau da burgewa, wayanta dake hannun ta talatsa takira Ummi, ringing biyu taɗauka

"Ummina I miss You so much". Tafaɗa cike da zumuɗi

Daga can Ummi murmushi tayi na jindaɗi tace "me too My dear, har kin tashi?"

"Eh Ummi kuna lafiya? Ya Daddy da Halwa?"

Cikin dariya Ummi ta'amsa mata tana cewa "ai ga Halwan ma anan".

"To Ummi bata mu gaisa".

Miƙa mata wayan tayi suka gaisa cike da kewan juna sannan tamaida ma Ummi nan ma sukaci gaba da hira, daga baya kuma tabuƙaci akawo mata Husna, Ummi tayi ta rarrashinta akan tabari zuwa nan da sati biyu amma sam Saleema taƙi yarda ita lallai sai an kawo mata Husna yau

"Haba ɗiyata ki kwantar da hankalin ki, ki bari zuwa gobe insha Allahu zan sa akawo miki ita, kinga yau su Gwaggon ki zasu zo zasu kai ki gidan iyayen mijin naki to wa zaki bar ma wa? Ki bari gobe sai akawo miki ita kinji".

"To Ummi amma kar yawuce gobe". Tafaɗa a shagwaɓe".

Daga nan sallama sukayi, tana nan zaune tana tunanin mijin nata sai murmushi take yi, sai da tagaji don kanta ga barci da tasoma ji hakan yasaka takwanta a 3sitter tana rufe idanun ta, babu jimawa barci yaɗauke ta

Can tasoma jin hayaniyan baƙinta tare da bugun ƙofa, babu shiri tatashi tana riƙe kanta dake faman sara mata, daƙyar take tafiya sabida yanda take jin wani zazzaɓi-zazzaɓi na son kawo mata cafka, tana buɗe ƙofan suka shigo nan tatare su da fara'a, duk ƴan uwan Abbanta ne dana Ummin ta su wajen biyar

Su suka sakata tashirya cikin wata Farar atamfa anyi mata Flower da kalan ja da baƙi, sosai atamfan tayi mata mugun kyau kasancewar ta fara, ga ɗinkin da yaɗauki jikin ta sosai na riga da zani, Hijab tasaka fari da takalmi ,sannan suka fito sukayo waje, a motoci biyu suka bar gidan.

***** Tarba me kyau Mom tayi musu cike da farin ciki sai nan nan take da Saleema, hakan sosai yafaranta ran Ƴan uwanta har basuyi fargaban danƙa mata amanar ƴar su ba, ita kuma Mom ta'amshe ta hannu bibbiyu

Basu jima ba sukace zasu tafi duk da Mom tayi musu tayin abinci amma sukaƙi ci illa ruwa da suka sha, haka suka tafi suka bar Saleema anan, sauran dangin Mom da basu rigada sun tafi ba sai shigowa ɗakin Mom suke yi suna ganin amarya, bayan sun tafi yarage daga Mom sai Saleeman, duk da Saleema tasaba da Mom abaya hakan be sa taƙi nuna kunyan ta ba, Mom kuwa sai janta da hira take yi cike da ƙaunar ta, daga ƙarshe dai da taga taƙi sakin jiki da ita sai tatashi tana cewa

"Tunda kinƙi sakin jiki dani bari in Kira miki Nazeefa tataya ki hira tunda Ni fita zanyi".

Saleema dai batace komi ba har Mom ɗin tafice.

Nazeefa tana kwance akan gadon ta duk abin duniya yabi ya ishe ta, tun sanda aka soma hayaniyan zuwan Amarya tana jin su amma takasa fita, sosai take jin baƙin ciki da kishi aranta sai dai tadage tana ta ƙoƙarin hana kanta kuka, shigowar Mom cikin ɗakin yasa tatashi tana ma Mom ɗin sannu

"Yauwa Nazeefa bakije kinga Amarya ba ga ta can an kawo ta?".

Murmushi Nazeefa tayi tasauke kai ƙasa tace "Mom banji bane barci ya soma ɗauka na".

"To tashi kije wajen ta tana nan aɗaki sai ki tayata zama ko".

Batayi musu ba tatashi sai dai bada son ranta ba tafito tanufi ɗakin Mom ɗin, ita kuma Mom tanufi wajen Dangin ta

Sallama tayi tatura ƙofan tashiga, Saleema dake zaune saman gado ta'amsa mata tana ɗan jan Hijabin ta baya da tarufe idanun ta dashi, kallon kallo sukai ma juna ko wacce da tunanin dake ranta

Ita Nazeefa tana kallon Amaryan Yayan nata ne cike da jin haushi duk da kuwa ta burge ta don kyakkyawa ce sosai wacce kallo ɗaya zakayi mata kasan cewa ba ƙaramar ƴar jindaɗi da hutu bane, coz ko kaɗan ma batayi yanayi da ƴar talakawa ba

Ita kuma Saleema tana mata kallon rashin sani ne don tasan dai ba ƴar gidan bace, sai dai ko ƴar uwan shi ne duk da babu wani kama da sukayi

Zama tayi akan kujeran dake ɗakin tana ci gaba da kallon Saleeman sannan taƙaƙalo murmushi tace "sannu Amaryan mu, kinzo lafiya?"

Murmushi itama Saleema tayi ta'amsa mata cike da sakin fuska kasancewar ta me yawan fara'a ga kowa

Daga haka shiru ne yabiyo baya dan Nazeefa batasan me zatace mata ba saboda ita ba me yawan surutu bane, itama kuma Saleeman bata sake furta komi ba tayi shiru tana sad da kanta ƙasa, ahaka har Mom tashigo da wasu baƙi tatarar dasu haka, baƙin sun zo ganin Amarya ne, haka Saleema tagaishe su cike da kunya su kuma suna ta yaba mata suna sanya alkhairi, hakan ba ƙaramin sake ƙular da Nazeefa yayi ba har takasa jurewa tatashi tasulale ɗaki batare da sanin Mom ba

koda Mom suka tashi fita bata kula ba haka suka fita ɗakin aka bar Saleema ita kaɗai tana ta zaune, daga ƙarshe kwanciya tayi sabida yanda take jin zazzaɓin jikin ta yana ƙara yawa, lokaci ƙanƙani ciwo yarufe ta ga sanyi da take ji sosai, haka ta ƙudundune jikinta sai faman maƙyarƙyata take yi

Ahaka Mom tashigo taganta, hankalin ta idan yayi dubu ya tashi nan tasoma neman wayan ta, sai tatuna tabar wayan a palrour, fita tayi dasauri babu jimawa sai gata ta dawo tare da wasu mata su biyu, su ma duk hankalin su ya tashi ganin yanda jikin Saleeman yai zafi zauuu

Mom Kiran Khalil tayi tabashi umarnin yai maza-maza yazo matar sa tana gidan ta babu lafiya. [11/7/2020, 3:33 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```

.

*CHAPTER 44*

Lokacin da Khalil yazo har su Mom sun fito da ita parlour, babu ɓata lokaci yariƙe ta suka fito waje inda motan sa yake, Mom tace mishi "yakai ta asibiti" amma ita Saleeman tace "tana da maganin ta a agida" don haka gida kawai yanufa

Suna zuwa yayi parcking yafito yabuɗe mata motan yariƙo ta tafito, duk da a halin ciwo take amma sosai taji daɗin kusancin sa gare ta, har wani sanyi take ji aranta tana jin kamar ciwon na son tafiya

Tana jingine da jikin sa har suka isa parlour yataimaka mata tazauna sannan yakalle ta cike da tausayi yace

"Ina kika ajiye maganin in ɗauko miki?"

Cikin muryan marasa lafiya tace "yana cikin trolly na Wanda nazo dashi daga gida".

Gyaɗa kai kawai yayi yanufi ɗakin nata, yana shiga yasoma wurwurga idanu, can yahangi akwatunan da yayi mata guda shida, sai yamaida idanun sa kan wani babba kalan sa daban, yana da tabbacin shine wanda take nufi

Wajen yanufa yabuɗe, duk abubuwan amfanin ta ne da tazo dashi daga gida, yana soma bincika wa yaga ledan maganin, ɗauka yayi yanufi parlour'n

Zama yayi gefen ta yabuɗe tare da nuna mata alamun tayi masa bayani, nuna masa waɗanda zata sha ɗin tayi yaciro yamiƙa mata sannan yatashi yaje yaɗauko ruwa a Fridge yabata

Har tagama sha yana ta kallon ta kamar wanda zai haɗiye ta, hakan yasa taji kunya tana sad da kanta ƙasa, be san sanda yasaki guntun murmushi ba yamiƙe tsaye yanufi kichen ita kuma tabi bayan sa da kallo cike da tsananin ƙaunarsa a ranta

Be wani jima ba yadawo riƙe da Cup a hannun sa, miƙa mata yayi yana tsaye a kanta, ita kuma tasaka hannu ta'amsa tana kallon abinda ke ciki, Tea ne yahaɗo mata, be ce mata komi ba sai dai kallon ta da yake yi har tashanye tatashi da ninyan kai Cup ɗin

"No kawo cup ɗin, je ki kwanta idan an kira sallah zan tashe ki".

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull