Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 25
Barrister ibrahim khalil complete Chapter 25: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 25. Kamar yanda Nafeesa tace mata zata raka ta wajen malaman, suna…
4,454 words
Kamar yanda Nafeesa tace mata zata raka ta wajen malaman, suna samun free suka tafi, taci Sa'a don wasu daga cikin malaman sun ce gobe tazo zasu yi mata, sai kuma waɗanda suka bata assignment, mutum ɗaya ne yayi mata text ɗin sa nan take, ai kuwa daƙyar ta amsa uku cikin biyar tunda babu wanda aka yi da ita, su ma ɗin wanɗanda ta'amsa turancin ta ne tagwamitsa yanda tafahimta sannan tamiƙa tafito.
Tunda tadawo gida babu abinda tatasa agaba sai karatun, sai wajen ƙarfe biyar tatashi tayi musu abincin dare sannan taƙara koma wa tadasa daga inda tatsaya tunda babu abinda zata yi. [1/5, 9:31 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*BOOK TWO*
.
_______________________________
*CHAPTER Twenty Two*
________🎓Zaman Khalil da Halwa zama ne tamkar ba mata da miji ba, babu abinda ke haɗa su sai gaisuwa, idan yatafi aiki itama sai tatafi school ɗin ta
Zata gyara gidan tayi musu girki kullum bata gajiya amma magana wannan baya haɗa su in ba ya zama dole ba
A ɗan zaman nan da suka yi a matsayin ta na matar sa tuni ta gane ta afka ƙaunar sa, bata da aiki yanzu sai tunanin sa da kuma zaman da suka yi abaya lokacin yana mata magana sosai, karatun da yasaka ta a gaba da kuma soyayyar Khalil wanda bata san sanda tafaɗa ba sun haɗe mata sun yi mata yawa, don haka gaba ɗaya yanzu ta rame ko kaɗan bata da sukunin zuciyarta, ga karatu ga tunanin da yazamar mata jaraba, da farko ta so duk yanda za'a yi ta yakice sa a ranta amma ina hakan ya gagara, wani lokacin har zuwa take yi tazauna kusa dashi tana masa magana ko wai zai riƙa kulata tasamu sukunin zuciya sabida yanda ƙaunar sa ke azalzalan ta, amma yanda tazauna haka zata tashi babu abinda ke haɗa su, hakan na ƙara saka ta shiga mawuyacin hali, har tashiga ɗaki tayi ta kuka tana tirr da zuciyar ta akan rashin adalcin da tayi mata, duk a maza ta rasa wanda zata so sai mijin ƴar uwanta da take ganin ƙimar ta sosai, wanda idan ba ƙaddara da ya haɗa su ba ba ta tunanin zata iya auren sa, a yanda tafahimta Khalil bazai taɓa son ta ba Saleema kaɗai yake so, ita kawai zata yi zaman haƙuri ne har sanda Saleeman zata samu lafiya tasan makomar ta, tunda tarigada ta saka a ranta idan Saleema bata son auren to guduwa zata yi, wannan shine kaɗai hanyan da taga zata iya guje wa auren nan.
***** Ahmad na wajen Ummi har yanzu ita take kula dashi, idan tatafi aiki sai kuma Larai tahaɗa su ita da Husna taci gaba da kula dasu, idan kuma ta dawo sai tarage mata aiki wajen amsar Ahmad ɗin, tunda aiyukan sun yi ma Larai yawa, ga aikin gida ga kuma raino.
Har yanzu dai Saleema babu labarin ci gaba, kullum iyayen ta addu'a suke yin mata Allah yatashi kafaɗun ta, idan Ummi taje aiki wuni take yi a wajen ta tunda yanzu ana barin ta tana shiga
Itama Halwa wani lokacin tana zuwa duba ta, takan yi kuka duk sanda taje taga Saleema cikin wannan halin da ba ta sanin a duniyar da take ciki.
Rayuwa taci gaba da tafiya yanzu gashi har Saleema ta shafe wata biyu curr kafin tafarfaɗo, zo ku ga murna wajen ahalin ta duk da kuwa ba wai ta dawo hayyacin ta gaba ɗaya bane tana cikin ciwo sosai, amma dai ahaka kowa ke murna da samun lafiyan ta
An ci gaba da treating ɗin ta har zuwa ɗan wani satikai inda tasamu lafiya sosai alhmadulillah sai abinda ba'a rasa ba, ciwon zuciyarta yanzu shine matsalan ta, but duk da haka an ɗaura ta akan magani
Duk idan Khalil yatashi daga aiki can yake wuce wa, wani lokacin ma idan zai tafi da safe sai ya soma leƙa ta kafin yawuce aikin sa
Haka itama Halwa daga school can take wuce wa tayi zaman ta sai dare idan Khalil yazo sai su taho tare
Hakan na faranta ran Saleema sosai, musamman idan taga ƴan uwanta tare da ita, babu jima wa aka sallame ta gaba ɗaya suka dawo gida
Tunda suka dawo sai kuma Halwa takoma kula da ita, ita take yin mata komi bata barin ta taɗauki ko tsinke, idan har ba wani muhimmin abu suke a school ba bata zuwa, tunda a yanzu ba an cika yin musu lectures bane sabida kusantowar Exams ɗin su, idan kuma suna da Lecture irin guda ɗayan nan ƙin zuwa take yi
Shima Khalil yana bata kulawan sa sosai, yana faranta mata da iyawan sa, sosai yake ƙara jin son Halwa aransa musamman yanda yaga tana ɗawainiya da Saleema ko kaɗan bata gajiya, wani lokacin sai yazauna yay ta tambayan kansa meyasaka yake mata haka? Halwa tana da kyawawan hali da shiga rai ga duk wanda yazauna da ita dole sai ta burge sa, to shi meyasaka bazai yafe mata ba? A yanzu dai ba laifin take aikata wa ba tunda ta tuba, yakamata yabata dama yacire haushin ta a ransa ya amshe ta hannu bibbiyu a matsayin matar sa tunda abinda yafaru ya rigada ya wuce, ko Allah ana masa laifi ya yafe bare kuma shi bashi ne tay ma laifin ba, kawai yayi amfani da hakan ne yana cuta ma kansa bayan kuma yana ƙaunar ta sosai a ransa, shiyasa yanzu yasassauto yake shiga harkan ta
Hakan ba ƙaramin faranta ranta yayi ba, sosai a yanzu take matuƙar farin ciki saɓanin abaya da koda yaushe take cikin damuwa
Saleema duk bata fahimci komi akan auren Khalil da Halwa ba tunda ba wai faɗa mata akayi ba, kuma Khalil ba kwana ɗakin Halwan yake yi ba, babu abinda ke haɗa su wanda zata iya zargin su, saboda tunda tadawo Halwa takoma ɗakin ta na da tadena kwana a cikin ɗakin Khalil ɗin, kuma tayi hakane duk wai saboda Saleema kar ta zargi wani abun tunda ba'a so tasani sai idan ta samu lafiya
Shima Khalil ɗin ganin haka sai yadena kwana aciki yana bin Saleema ɗakin ta, tunda dai babu daɗi ace yana kwanar mata a ɗaki shi da wata matar
Hakan yasa Halwa ta ƙara ganin ƙimar Khalil a idanun ta, tabbas Khalil mutum ne na daban, tsananin kyawun halin sa tare da kirkin sa ya wuce yanda ake zato, ɗaya ne tamkar da dubu, dole ko kana so ko baka so ka ƙaunace sa, idan har kuwa zaka yi mu'amala dashi dole ne yashiga ranka.
Ahaka har su Halwa suka soma Exams ɗin su na First semester wanda daga shi ne sai Finally, sai kuma School of Low da zata shiga.
**** ***** *****
Yau aka yi ma su Halwa hutun school don haka da wuri tadawo yau ɗin tunda Pepper ɗaya suka yi
Saleema na kwance kan two sitter ta ɗage ƙafafunta ta ɗaura saman jikin kujeran tajiyo sallaman Halwan lokacin da taturo ƙofan tashigo, tashi tayi dasauri tana mata oyoyo, suka yi Hugging juna suna dariya cike da nishaɗi sai suka zube saman kujeran
"Ai gwara da Allah yadawo dake da wuri, dama yanzu nake tunanin kiran ki in sanar miki zan je gida don yau da kewar su Abba na tashi, na tambayi Barrister ya bar Ni". Saleema tayi maganar idanun ta kan Halwa tana dariya
Yamutsa fuskar ta Halwan tayi kamar yanda yazame mata jiki tace "kai sis yanzu sai ki tafi ki bar ni kenan?"
"A'a wlh nayi tunanin ba yanzu zaki dawo ba, Ni har nayi tunanin bari sai gobe ne kuma sai ga ki kin dawo, sai mu tafi tare yanzu".
Kaɗa kanta Halwa tayi kafin tace "anya zan je kuwa wlh agajiye nike, barci kawai nake so in Yi".
Saleema tace "to ki kwanta ki huta mana, ina tunanin ma idan naje zan taho dasu Husna ne".
"Aa Iyeee wlh baza ki kawo mana aiki ba, akan me zaki ɗauko su?"
Wani kallo me kama da harara Saleema tasakar mata
"Me kike nufi?"
Halwa dariya tayi tace "wlh babu komi, amma don Allah ki bar Husnan ki ɗauko Ahmad ne".
Miƙe wa Saleema tayi tay hanyan ɗakin ta tana faɗin "kar ki damu sister Ni ban ce ki tayani rainon su ba wlh Ni kaɗai zan iya tunda Ni ce uwar su dama ai".
Bata tsaya jin amsar Halwan ba tashige ɗaki abun ta
Itama Halwa tashi tayi tabi bayan ta don taga fushi tayi da ita
"Haba Sister daga wasa?"
Turo baki Saleema tayi tana hararan ta batare da tace mata komi ba tasoma cire kayan jikin ta
Ganin dai ba tanka ta zata yi ba, sai tace "to nima zan je bari in shirya, tare zamu je taho wa dasu".
Baki Saleeman tawashe tace "dagaske sis?"
Gyaɗa mata kai Halwa tayi tace "bari ma kigani".
Tayi hanyan ƙofa tana faɗin "nima bari in je in shirya".
****
Bayan sun gama shirin su drever yakai su gidan su Saleeman
Ummi tayi murnan ganin su barin ma da taga Saleeman ta sake samun sauƙi sosai har wani ƙiba tayi na kwanciyar hankali
"Ummi ina Abba ne don Allah". Saleeman tafaɗa tana kwaɓe fuska tana kallon Ummi ɗin
Ummi murmushi tayi cike da ƙaunar diyar ta tace "ai yau Abban ki yayi nisan zango, amma ina tunanin zai iya dawowa kafin ku tafi".
Gyaɗa kanta tayi tamiƙe tana faɗin "wai ina Husna ne ban ganta ba?".
"Tana wajen Larai wlh, shima Ahmad ɗin don yayi barci ne takawo shi amma da duk suna wajen ta".
Ɗakin Larai tanufa da ɗan gudun ta tana cewa "bari inje inga Ummina".
Tun bata kai ba take kiran sunan Husnan har tashige
Ummi dawo da kallon ta wajen Halwa tayi tana dariya wanda itama Halwan dariyan take yi tace
"Ummi wlh Saleema son yaran ta yayi yawa ko kunyan ki bata ji".
"To ina kuwa zata ji kunya na? Ai Saleema sai ikon Allah, ita da tazauna tana mana kukan cikin ta ya zube wani kunya zata ji anan".
Dariya sosai Halwa take yi itama Ummin na taya ta
Ummin tace "Allah yay muku albarka yarana, yaba ku waɗanda zasu ji ƙan ku".
Halwa na murmushi ta'amsa da "ameen Ummi".
Lokacin Saleema tafito daga ɗakin Larai tana faɗin "itama tayi barcin".
Dariya Halwa tayi tace "ai da kin taso ta tunda zumuɗin ganin su kike yi".
Hararan ta Saleema tayi tana zama gefen Ummi tace "bazan tashe sun ba".
Halwa dariya kawai take mata tana tsokanar ta, ita kuma tana rama wa cike da wasa da dariya
Ummi dai tana jin su bata saka musu baki ba, yau dai tayi ninyan faɗa ma ɗiyar nata auren dake tsakanin Halwa da Khalil, sabida a ganin ta be kamata ayi ta ɓoye mata ba kuma ana cutan Halwan, idan kuma hakan yaci gaba da tafiya tasan sun so kansu da yawa tunda sun gummaci su faranta ran ƴar su sannan su cuta ƴar mutane, yanda tagan su ahaka da tsananin shaƙuwar su bata jin Saleema zata wani damu, don haka ajiyan zuciya tasauke tana aza idanun ta kan Saleeman takira sunan ta
"Na'am Ummi". Saleema ta'amsa mata tana kallon ta
Ummi tace "nasan kinsan ƙaddara Saleema kuma kinsan duk wanda yacika musulmi dole ne ya yarda da duk wani ƙaddara da tasame sa me kyau ko mara kyau.."
Gaba ɗaya shiru suka yi har Halwa suna sauraron ta, yayinda itama kuma tasoma zayyano ma Saleema duk abinda ke faruwa har da juya mata mahaifa yau sai da tafaɗa mata, kuma tayi hakan ne wai don Saleema tasake ganin girman Halwa, tasan cewa bata cancanci ɗaukan wani mataki akanta ba tunda ta taimake ta ta fanni da dama, tayi mata abunda babu wanda ya'isa yay mata shine kyautar yara har biyu, Halwa ba wacce zatayi kishi da ita bane domin ita ɗin me son farin cikin ta ne
Sai da Ummi takai aya a zancen ta kafin Saleema tamiƙe tsam daga wurin tawuce ɗakin su
Hakan yasa suka bi bayan ta da kallo cike da fargaba aran su
Matse baki Halwa tayi hawaye na cika cikin idanuwanta
Kallon ta Ummi tayi suka haɗa idanu sai Halwan tasauya fuskarta da ƙirƙirar murmushi batare da tasan cewa hawayen cikin idanun ta sun sauka saman kuncin ta ba
"Menene na kuka kuma? Bana son shirme kinji ko?" Ummi tafaɗa tana ɗaure fuskarta
Dasauri Halwan tasaka hannu tana share hawayen jin danshin su sosai saman kuncin ta wanda har ɗiga akan hannun ta suka yi, tana so tayi magana amma kalma ɗaya takasa furta wa, tana so tamiƙe tabi bayan Saleema amma ta kasa tashi
Ummi ce tatashi tanufi ɗakin, inda tasami Saleema kwance saman gadon ta danne fuskarta saman pilow, zama tayi akan gadon tasoma yin mata nasiha me ratsa zuciya tare da kwantar mata da hankali, sannan tana nuna mata koda ba Halwa bace dole ne Khalil yaƙara mata kishiya.
Halwa na zaune a inda take ta haɗe hannayen ta waje ɗaya jikin ta nata tsuma, so kawai take yi tasami damar da zata yi kuka sai dai baza ta iya nuna raunin ta anan ba, bashi da amfani ko kaɗan
Tana nan zaune su Ummi suka fito, idanu kawai taɗaura ma Saleema tana son karantan yanayin da take ciki
Ita kuma Saleema sai taɗauke kanta gefe batare da ta bari sun haɗa idanu ba
Larai ce tafito daga kichen tanufi dainning tana jera musu abinci
Cike da farin ciki Ummi tace "to ku tashi muje kuci abinci tunda an gama".
Babu musu gaba ɗayan su suka bi umarnin ta, kan dainning suka zauna Ummi na ta jan su da Surutu duk dan wai su saki jikin su ganin yanda gaba ɗayan su suka yi shiru, babu wanda ke saka mata baki sai murmushi kaɗai da suke saki, sai kuma gajerun amsa da ke fitowa a bakunan su
Bayan sun gama suka dawo Parlour
Saleema bata zauna ba ta wayance tashige ɗakin Larai akan zata wurin Husna.
Har suka gama wunin su Saleema bata sake bari magana ta haɗa su da Halwa ba, yamma na yi Saleeman tace zasu tafi ganin Ummi ma zata wuce wajen aiki, haka suka yi sallama suka fito tare da Ahmad da Larai tahaɗo masa kayan sa tunda Ummi tace baza ta tafi da Husna ba, kuma dama yanzu Husnan ta soma zuwa school ɗin ta ba ma wuni take yi a gidan ba
A cikin mota ma tsit suka yi babu me magana, Halwa ta kasa yin mata magana ne sabida fargaba, ta rasa wani kalma ne zata iya amfani dashi wajen furta ma Saleeman, musamman yanda taga ita kanta bata son kula ta bare kallon ta, sai hakan yasake saka ta damuwa da tsoro cikin zuciyarta
Suna shiga gidan suka fito cikin motan atare, Saleema na rungume da Ahmad tana ƙoƙarin jan Trolly ɗin sa da drever yaciro mata a Boot
Sai Halwa tayi saurin miƙa hannun ta dake faman rawa tace "sister bari in taimaka miki".
Saleema bata ce komi ba tabar mata tajuya dasauri tawuce
Bin bayan ta da kallo Halwa tayi har sai da tashige cikin gidan, ahankali taja ƙafafun ta a matuƙar sanyaye tanufi ciki itama cike da rashin ƙwarin jiki, tana shiga da sallama idanun ta suka sauka kan su ita da Khalil ɗin dake zaune riƙe da Ahmad ajikin sa yana masa wasa, kallo ɗaya kayi masa zaka ga farin ciki tsantsa a fuskar sa wanda ganin tilon ɗan nasa ne yasaka sa wannan tsantsan murnan
Tunda tashigo shima yaɗago kansa yana kallon ta, wani irin kallo yake aika mata dashi me cike da zallan soyayya da nuna shauƙi ga duk wanda yagani
Hakan yaƙara saukar ma da Halwa kasala da mutuwar jiki, idanuwan ta tajanye daga kansa wanda suka kawo ruwa lokaci ɗaya tana ɗaura wa akan Saleema dake wasa da hannun Ahmad
Daƙyar tasoma jan ƙafafun ta bayan tacire idanun ta daga kallon ta tashigo cikin parlour'n, bata ce komi ba tayi hanyan ɗakin Saleeman tashige don ajiye mata Trollyn
Hakan yasa Khalil yabi ta da kallo cike da wani irin yanayi ganin yanda tasauya lokaci ɗaya duk da kuwa be ga hawayen idanun ta ba, amma ya tabbata akwai abinda ke damun ta
"Me yasami Maman Husna naganta ahaka?" Yayi maganar lokacin da yamaida idanun sa kan Saleema
Murmushi Saleeman tayi tace "babu komi wlh me kagani?"
Numfashi kawai yaja batare da yace komi ba yamaida idanun sa kan t.v
Lokacin Halwa tafito tanufi ɗakin ta tashige har da rufe ƙofan da keey, ahankali tazame ƙasa a jikin ƙofan tahaɗa kanta da gwiwa tasoma rere kuka, kuka take yi sosai wanda tatoshe bakin ta da gyalen ta ta yanda babu me jin ta, ita kanta bata san kukan na menene ba, sai dai tasan yana da alaƙa da yanda Saleema tanuna mata, wannan dalilin yasaka zuciyarta take mata wani irin zugi wanda ta san cewa dole ne rabuwar ta da wanda zuciyarta take bege a halin yanzu, alƙawari ne taɗauka kuma dole ta cika shi baza ta taɓa yin sanadin da Saleema zata sake shiga ƙunci a rayuwan ta ba, wanda ta tabbatar da cewa muddun tazauna batare da son ta ba bata jin zata yi farin ciki
Bata tashi a wajen ba sai da aka yi kiran sallan magriba, tamiƙe ahankali jiri na ɗiban ta sabida tsananin kukan da tasha, har gaban ta bata iya gani haka talallaɓa tashige Toilet taɗauro alwala
Sallah tayi tazauna nan bata tashi ba, sai da aka kira sallan isha'i sannan tatashi ta gabatar.
Lokacin da Khalil yadawo daga sallah shi kaɗai yazauna a Parlour, shiru-shiru yana jiran yaga sun fito amma babu wanda yafito cikin su, tashi yayi yashiga ɗakin Saleema nan yaganta zaune tana aikin gyaran kayan Sip da tawargazo gaba ɗaya tana maida wa
"Wai baza ku fito mu ci abinci bane?" Yace da ita lokacin da yaƙarisa gaban ta yana saka hannun sa ɗaya yadogare da Sip ɗin
Kallon sa tayi tace "zan zo amma yanzu Ni dai bana jin yunwa ne sai anjima".
"Ok bari inje ɗaki nima ina da aiki". Abinda yafaɗa kenan yajuya yafice
Yana fita yatsaya yana kallon ɗakin Halwa, shiru yayi yana tunanin yaje ko kar yaje, haka kawai yaji gaban sa na faɗuwa, gashi kuma yana jin babu daɗi ganin yanda tashigo a ɗazu kuma ya san bata sake fito wa ba har yanzu tunda tashiga
Numfashi yaja yanufi ɗakin sa yashige.
*****
Ƙarfe 11:30pm. Lokacin gidan yayi tsit baka jin ƙaran komi
Ahankali Halwa dake zaune a ƙasa jikin gado tamiƙe tasaka Slippers ɗin ta taja Trollyn dake gaban ta shaƙare da kayan ta, cikin sanɗa tafito tana tafiya ahankali har ta'isa bakin ƙofan parlour tasaka hannu tamurɗa keey ɗin tabuɗe tafice
A haraban gidan babu kowa sai hasken lantarki da ya haskaka gaba ɗaya wajen, inda akwai duhu nan take raɓa wa tana bi duk da kuwa zuciyarta cike take da tsananin tsoro, amma abinda take hango wa shine kawai tabar gidan, bata son ko kaɗan tasake kwana a gidan nan
Tana isa bakin ƙofa taci Sa'a babu me gadi, sai dai ya rufe ƙofan ya shige ɗaki ya ɗan kwanta zuwa anjima sai yatashi yaci gaba da aikin sa
Ahankali tasaka hannu tazare saƙatan ƙofan taja Trollyn ta dasauri tafice batare da ta rufo ƙofan ba.
.
_uhmm wlh yau na gaji nasha typing da yawa, nayi muku har gobe ne ku karanta rabi yau sai ku bar rabin gobe😆, Asha karatu lafiya Fans, Ina matuƙar ƙaunar ku._ [1/5, 12:13 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
_Wannan shafin naku ne *Mommyn Teema* tare da *Mmn Adnan/Yusra* ku more da wannan ɗin 👇 ina godiya da ƙaunar ku gare ni._
*BOOK TWO*
.
_______________________________
*CHAPTER Twenty Three*
________🎓 Washe gari da safe Khalil ne yasoma tashi yay Shirin sa na zuwa Office, dayake yau ɗin yana da aiki sosai don haka da wuri ya shirya be tashi Saleema ba yafito Parlour, yasan cewa Halwa ce ke yin musu girki a yanzu shiyasa yanufi dainning ɗin kanshi tsaye, amma me? abun mamaki babu breakfast ɗin
Tsayawa yayi yana kallon wajen cike da tsantsan mamaki, yasan bata taɓa late ɗin yin musu abin kari ba, musamman da tasan yanzu yana yawan fitan safe sosai
Ganin dai tsayuwar sa babu amfani sai yajuya yashige ɗaki yaɗau briafcase ɗin sa yafito, kasancewar sauri yake yi duk da kuwa yana son shiga yadubo ta ko lafiya sai dai kuma be yi hakan ba yanufi ƙofa zai buɗe yafita, abun mamaki ƙofan abuɗe yagani babu keey, sosai yayi mamaki a ransa yatsaya yana tunani ko dai jiya basu rufe ƙofan bane? shiru yayi yana son tuno wa, tabbas jiya ba shi yarufe ƙofan ba maybe su Saleema sun manta ne, da wannan tunanin yabuɗe ƙofan yafice
Motar sa yashiga yaja yay bakin Gate yana danna horn
Me gadi dake zaune bakin ƙofan a saman benci yayi saurin tashi yawangale masa Gate ɗin yafice
Sai a lokacin Gate man ɗin yasaki wata wawan ajiyan zuciya, tunda yatashi da asuba yaga ƙofan abuɗe yake a cikin ruɗu, yasan dai Khalil baya fita sallan asuba sai idan ta ɗauro, kuma ajiyan yariga kowa tashi agidan bare yay tunanin wani ne yazo yabuɗe, saboda ma yatabbatar da zargin sa sai da yatambayi ma'aikatan gidan duk suka ce masa basu bane, to yanzu jira yake yi yaji ko Oga Khalil zai yi masa maganar wani abun ya faru a daren jiya but ganin ya fita batare da ya tunkare sa da wata magana ba shine yaji dama-dama aransa, domin dai yana da tabbacin ya rufe ƙofan, kuma be sake dawowa wajen ba sabida barcin da yasha jiyan.
Saleema bata tashi ba sai wajen ƙarfe 10:00am. Wanka tasoma yi sannan tashirya cikin doguwar riga na yadi me ruwan kuka, ɗinkin fitted gown ne sannan sai aka yi kwalliya da red stone a gaban rigan, ɗaura ɗankwalin simple tayi sannan tanufi kan gadon taɗauki Ahmad tazauna tasoma cire masa kaya
A lokacin yafarka yana saka mata kuka
Rarrashin sa tasoma yi tana ci gaba da kwaɓe masa kayan, bayan ta gama ajiye shi tayi tashiga Toilet tahaɗa masa ruwa a bawo tafito taɗauke sa, wanka tayi masa tadawo tashirya sa, sai da tahaɗa masa abincin sa taba shi sannan takwantar dashi tafito Parlour
Direct kan dainning tanufa sai dai ganin babu komi a wajen sai taja ta tsaya, shiru tayi na ɗan daƙiƙa kafin tasaki murmushi
Daman tasan za'a rina, Halwa zata shiga wani hali a sabida yanda tanuna mata a jiyan, ita har a zuciyar ta ba wai haushin Halwa take ji ba, tabbas dai taji kishin ta da Ummi tafaɗa mata yanzu tana matsayin kishiyar ta ne, amma kuma abinda yaƙara saka ta damuwa ce mata da akayi an juya mata mahaifa, sosai tashiga wani irin ruɗu da yahaddasa mata jin haushin Halwan a lokacin tare da tsananin kishin ta har takasa haɗa idanu da ita bare tayi mata magana, sai dai kuma ba wai tayi ne don muzguna mata ba tayi hakan ne kawai don samun damar yin tunani da zuciyar ta batare da tafito da damuwar ta fili sosai don su gani ba
A jiya kwana tayi tana sallah sabida gode ma Allah da yakawo mata Halwa cikin rayuwanta, sannan ta kwana tana roƙon Allah yaba su zaman lafiya a zaman da zasu yi, ta sani cewa zuciya bata da ƙashi duk ƙaunar da suke yi wa junan su tunda har kishi yahaɗa su tabbas sai sun ɓata, don itama jiya ba ƙaramin ƙarfin hali tayi ba da danne zuciyarta har zuwa yau ɗin da tatashi sakayau babu abinda ke damun ta, burin ta a yau ɗin tafaɗa ma Khalil yaraba musu kwana su zamto matan sa su duka.
Numfashi taja tana saka hannunta ta sosa goshin ta kafin tanufi ɗakin Halwa, tura ƙofan tayi tashiga da sallama tana wurwurga idanu cikin ɗakin ganin babu ita, bakin gadon tanufa tazauna a tunanin ta ko tana cikin Toilet, sai dai har tsawon shafewan wasu mintoci babu Halwa babu dalilin ta
Miƙe wa tayi tanufi Toilet ɗin tasaka hannu tayi Nocking, jin shiru sai tatura ƙofan tashiga taduba babu kowa, fito wa tayi tana sake bin ɗakin da kallo, a ranta kuma tana tunanin inda Halwa taje, tuna ko tana kichen ne yasaka ta fita tadoshi kichen ɗin, sai dai nan ɗin ma babu ita
"Haa'a to ina taje ne wannan matar?" Tafaɗa a fili lokacin da tafito Parlour tana sake kewaye parlour'n da kallo
Numfashi taja kafin tafice dasauri, Garden ɗin gidan tanufa tasoma dube-dube sai dai duk inda tasan zata iya ganin Halwa agidan ta duba babu ita, hankalin Saleema ya soma tashi sosai, cikin ruɗu tanufi bakin Gate
Me gadi tunda yahange ta yatashi yana muzurai
Tana isowa tambayan da tasoma yin masa sai da hantan cikin sa yakaɗa, amma cikin ƙarfin hali yabata amsa da cewa "wlh Hajiya Ni dai yau ban ga gilmawan ta ba, rabon da na ganta tun jiya da kuka dawo cikin gidan nan".
Goshin ta ta dafe cike da tashin hankali, sai kuma tasake kallon sa tace "to ko ka ga sun fita da Barrister ne?"
"O'o O'o shi kaɗai yashiga motar sa yatai abin sa".
Juyawa tayi dasauri har tana cin tuntuɓe, yanda zuciyarta lokaci ɗaya takawo mata banzan tunanin cewa ta gudu ne hakan yasaka hankalin ta yay mummunan tashi, har tana tuntuɓe tana faɗi wajen isa ɗakin Halwan da mugun saurin ta, Direct gaban Sip ɗin kayan ta tanufa tabuɗe tasoma duba wa babu komi aciki
Dayake ta dawo da kayan ta ɗakin, akwatunan auren ta kuma Khalil ya ɓoye mata a Library ɗin sa.
Wani irin mugun bugawa ƙirjin ta yayi, tana shirin zube wa ƙasa tahangi farar takarda dake kan gadon an danne rabin sa da pilow wanda tun shigowar ta ɗazu bata kula dashi ba, dasauri ta'isa wajen taɗau takardan tana buɗe wa gaban ta na faman faɗuwa, rubutun tabi da kallo kafin tasoma karanta wa