Kenza eBookz

Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 26

Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 26

Barrister ibrahim khalil complete Chapter 26: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 26. _Aslm alaikum ƴar uwata, nasan zaki ga wannan saƙon ne a…

4,486 words

_Aslm alaikum ƴar uwata, nasan zaki ga wannan saƙon ne a lokacin da nayi nisa da rayuwan ku, kar ki damu bare ki ɗaga hankalin ki, Ni naga dacewar barin ku sabida wasu dalilai na, i know zama daku a yanzu be da wani amfani sabida naga kamar ina son shiga rayuwan ki ke da mijin ki, wlh sister bani da ninyan ƙuntata ma rayuwan ki, babu wanda ya tambayi ra'ayina akan aure na da Yaya Khalil, shiyasa yanzu na gummaci barin ku akan nazauna da auren sa batare da son ki ba._

_Abu ɗaya nake roƙon ki kiyi min alƙawarin zaki kula min da kanki, kar ki taɓa saka damuwa a ranki duk inda nake zan rayu ne cikin farin ciki tare da kewar ki a raina, sannan ki roƙa min Mijin ki yasake ni sabida bana son in zauna da auren sa a kaina._

_Allah yaba ku zaman lafiya da ɗorewan lafiyan ki ƴar uwat..."_

Yanda hawayen idanun ta ke sintiri saman fuskarta yasa takasa ganin sauran rubutun, gaba ɗaya ta jiƙe takardan da hawayen ta, kuka tafashe dashi tana zame wa ƙasa tafaɗi, kuka sosai take yi wanda yahaɗe mata da tari sai yi take yi babu ƙaƙƙauta wa, magana take son Yi amma Ina da zaran ta soma buɗe bakin sai takasa furta wa sabida tari da kukan da take faman yi, babu abinda harshen ta ke iya ambata sai sunan Halwan tana wani irin kuka me cike da tsantsan firgici tare da fita hayyaci

Zabura tayi dasauri tatashi tanufi ɗakin ta da gudu riƙe da takardan a tafin hannun ta, wanda tamatse sa gamm ta kasa saki, wayan ta taɗauka tafito Parlour tasoma neman layin Khalil, ringing ɗaya yaɗauka

Kuka tasake fashe wa dashi da ƙarfi tana tattaro numfashin ta wajen har haɗa kalmomin da zata faɗa masa

"Hal..wa.. ta tafi ta gudu.. ta bar ni, ta tafi.. Halwa...".

Kasa ƙarisa maganar tayi sabida wani irin tari me haɗe da gudan jini da yataho mata

Khalil dake zaune kan kujeran Office ɗin sa, tun sanda yasaka wayan a kunne yasoma jiyo kukan Saleeman hankalin sa yay ƙololuwar tashi, tambayan ta yake yi ko lafiya duk da yaji tana magana but ya kasa jiyo me take cewa sai sunan Halwa da take faɗi, dasauri yaharhaɗa kwarmatsan sa yasaka wayan a aljihu batare da ya kashe ba, keey ɗin motan sa ya ɗauka yafito da mugun sauri duk hankalin sa a tashe, sosai yashiga ruɗu da faɗuwar gaba don yasan babu lafiya

Cikin mintunan da basu gaza 10 ba ya'iso gidan.

Saleema na nan zaune a inda take, izuwa lokacin tayi kiran Numban Halwa ya kai sau ashirin but amsan ɗaya ne a kashe yake Numban

Shigowar Khalil yayi dai-dai da sakin wayan da tayi tana sake fashe wa da kuka

Gaban sa ne yafaɗi time ɗin da ya sauke idanun sa akanta yaga jini a bakin ta, ga kuma wanda yaɗiga a ƙasa, cikin kiɗima yatunkare ta dasauri yana duƙawa gaban ta yariƙo ta tare da tambayan ta abinda ke faruwa

Amma ina ta kasa magana illa ƙara Volume ɗin kukan ta da tayi, daƙyar taɗago hannun ta tamiƙa masa takardan dake ciki

Dasauri yasaka hannu ya'amsa yana warware wa sabida yanda tacukuikuye shi duk ya yage, wani irin rawa jikin sa yasoma yi ganin abinda ke ƙunshe a takardan, idanun sa yakai kan Saleema da tuni numfashin ta ya rabu da gangan jikin ta, lokaci ɗaya sai ga hawaye sun cika masa idanu yana zama dirshan a ƙasa tare da dafe kansa da yasoma mugun sara masa, cikin wani irin sarƙewan murya yace

"Why Halwa? Why kike azabtar da rayuwana? Me na miki?"

A dai-dai lokacin da hawayen suka sauka kan kyakykyawar fuskar sa.

.

_kai gaskiya *SALEEMA* kina ganin rayuwa._

_anya baza mu bar Halwa taƙara gaba abinta ba abar Barrister da Saleeman mu? Tunda naga kamar kun fi sonta dashi._

_ko kuma daga nan Saleema tatafi tabar mana Halwan mu da Barrister._

_don haka yanzu ina son jin ra'ayoyin ku, ku zuba min ƙuri'a duk wacce tafi Fans tsakanin *SALEEMA* da *HALWA* to ita ce zamu bar ta da *BARRISTER* sai na ji ku._ 💃💃💃💃💃 [1/5, 12:23 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

```Wannan shafin naku ne masoyana Fhadeela, Fateeymuhammad, Auta Safna, Nana Faruk, Nafisa Ibrahim, Mum Afnan $ Yumna.. kuji daɗin ku da wannan page ɗin domin naku ne kyauta, na gode da ƙaunar ku gare ni.```

*BOOK TWO*

.

_______________________________

*CHAPTER Twenty Four*

________🎓 Jiki na rawa Khalil yamiƙe yanufi Fridge ya ɗauko ruwa yazo ya yayyafa mata a fuska, bata motsa ba sai da yasake zuba mata sosai kafin takawo numfashi alamun ta dawo hayyacin ta, bata buɗe idanun ta ba sai dai hawaye dake fitowa ta cikin idanun suna gangarowa gefen kunnen ta

Kiran sunan ta yasoma yi but taƙi ta amsa masa duk da kuwa tana jin sa, hankalin sa ne yasake tashi yana shirin ɗaukar ta sai wayan ta tasoma ringing, ɗauka yayi ganin Ummi ne me kiran sai yayi peacking

Daga can Ummi ce tasoma magana da faɗin "Hello My dear".

"Aslm alaikum Ummi ba ita ce ba".

"Ok Khalil Kai ne ashe, to lafiya dai ko?" Ummi tafaɗa gaban ta na faɗuwa

"Ummi babu lafiya, Halwa ce tabar gida ita kuma Saleema gata nan akwance har suma tayi sabida tafiyan nata". Yayi maganar ahankali cikin dauriyan murya da dannewar tashin hankalin sa

Cike da tsananin tashin hankali Ummi tace "innalillahi wa'inna ilaihi raji'un ta tafi kuma me yafaru ne?"

Bata jira kuma amsar sa ba sai tace "gani nan zuwa gidan yanzu insha Allahu".

Wayan takatse tana ɗaukan gyalen ta tayafa tare da jakar ta tafito Parlour

Daidai lokacin da shima Abba ya fito daga nashi ɗakin yana saɓa malin-malin, hannun sa riƙe da takardu, su yamanta shine yadawo ɗauka

Kallon sa tayi yayinda shima yake kallon nata

"Lafiya na ganki ahaka meke faruwa?"

Ummi kamar zata yi kuka saboda tashin hankalin da take ciki tace "Abban Saleema wlh babu lafiya, wai Halwa ce tabar gidan ga kuma Saleema can hankalin ta atashe har suma sai da tayi".

"Subhanallah.. mu je muje gidan". Abba yafaɗa yana yin gaba dasauri Ummi na take masa baya

*****

Shashsheƙan kukan Saleema ne kaɗai ke tashi cikin parlour'n, tana jingine jikin Ummi, Abba kuma na zaune gefen Saleeman sun saka ta tsakiya, yayinda Khalil ke zaune a kujeran dake Facing nasu

Tunda suka zo suke faman rarrashin ta but taƙi yin shiru sai ma ƙara tayar musu da hankali da take yi, musamman yanda suka ga in tayi tari jini ke fita, kuma taƙi tashi akaita asibiti illa nuna musu cewa babu abinda ke damun ta ita Halwa kawai take son tadawo, baza ta taɓa iya rayuwa babu Halwa ba, taɓara dai irin na ƴaƴan gata shi tazauna tana ta musu, yayinda su kuma suke ta faman lallaɓa ta Ummi har da ƙwallan ta, kai da gani kasan ba'a hankalin ta Saleeman take ba

Shi kanshi Khalil tsananin tausayin ta ne ya cika sa, shima yayi rarrashin but taƙi kula sa sai kuka take yi tana surutai

Abban ne yace su koma gida in yaso sai akira Doctor yaduba ta, daga nan sai anemi Halwan ko za'a ganta, don haka suka tattara gaba ɗaya har Khalil da yaɗauko Ahmad yamiƙa wa Ummi suka bar gidan, su sun wuce gida shi kuma Khalil yabi cikin anguwa ko Allah zai sa yahaɗu da Halwa

Idan kukaga Khalil a yanzu zai matuƙar baku tausayi, sosai yashiga damuwa akan tafiyar Halwan, gaba ɗaya zuciyarsa ta kasa sukuni tun sanda ya karanta takardan nan, yana ji ajikin sa ta tafi kenan, wannan dalilin ne yasaka yashiga matsanancin tashin hankali, sai dai juriya da ƙarfin hali da yake dashi hakan yake saka wa baza ka gane a halin da yake ciki ba

Yayi yawo sosai babu inda be je ba wai ko zai ganta, duk da Halwa bata da wajen zuwa but inda be yi tunanin zata je ɗin ba duk ya duba, haka yaƙarishe yawon sa yawuce gidan su, inda anan ne yafaɗa musu halin da ake ciki

Su ma Dad da Mom sun tashi hankalin su matuƙa, anan ne ma Dad ɗin yake faɗa musu labarin Halwan da alaƙan su dasu Saleema

Lokacin da Dad ɗin yagama faɗa musu komi sai kawai hawaye suka ciko idanun Khalil, miƙe wa tsam yayi yafice daga parlour'n yadoshi part ɗin su inda ɗakin su yake na Da

Akan gado yakwanta yana lumshe kyawawan idanun sa, haushi da takaicin kansa kawai yake yi

Meyasaka ya ɗau laifi ya ɗaura wa baiwar Allah batare da yasan musabbabin rayuwan ta ba? Shin meyasaka yamanta cewa ƙaddara irin wannan zai iya samun ta batare da laifin ta ba?

Shin meyasa mutane suke ɗaura laifi ga macen da suka ganta tana rayuwan ƙasƙanci? Shin sun tambaye ta dalilin da yasa har tafito gida take wannan rayuwan? ko kuma sun manta cewa wasu sanadin fyade ne yajawo musu rabuwa da gida akan tsangwama da kyara da ake musu, menene laifin su don ƙaddara ta faɗa musu ake koran su? Shin mun manta da cewa idan suka tafi zasu ci gaba da wannan rayuwan ne ko kuwa su faɗa hannun ɓata gari wani abu yasame su ta sanadiyar mu ne.. Allah dai yatsare mana imanin mu yasa mufi ƙarfin zuciyar mu, ya Allah ka kare mana zuri'armu daga faɗa wa mummunan rayuwa..

Ajiyan zuciya kawai yake sauke wa, ya jima a haka kafin daga bisani yamiƙe yaɗauro alwala jin ana kiran sallah yafice.

Wasa-wasa har dare babu Halwa bare labarin ta

Izuwa lokacin har ƙarin ruwa sai da aka yi ma Saleema, sai da akayi mata alluran barci sannan suka samu sukuni domin yanda tashiga wani hali hakan ya ɗaga wa iyayen ta hankali, babu daman tayi tari sai jini ya fito, gashi Doctor yayi musu bayanin cewa idan har taci gaba da kasancewa ahaka to tabbas akwai matsala domin zuciyarta ta gama kumbura sosai

Abba yaso akai ta asibiti but likitan yace abar ta zuwa safiya idan jikin ya sake tsanani.

Bata farka ba sai washe gari, Ummi ita ta taimaka mata tayi wanka tashafa mata mai tare da saka mata kaya, sabida ko kaɗan bata da ƙarfin jiki bata iya yin komi da kanta, sosai suke ta lallaɓa ta suna faɗa mata kalamai masu daɗi yanda zata kwantar da hankalin ta

Abinci ma abaki Ummi taba ta sannan taba ta maganin ta tasha.

**** **** **** **** *****

Tunda Halwa tafito daga gidan sai tasaka kuka, tafiya take yi batare da tasan inda zata nufa ba, ahankali take jan Trolly ɗin duk da kuwa zuciyarta cike take da tsoro matuƙa ganin yanda garin yaƙara duhu gashi babu kowa sai haushin karnuka, but bata jin zata iya tsaya wa hakan yasaka taci gaba da tafiyan ta tare da danne tsoron ta cikin rai, tafiya ɗaya sai ta waiga ahaka har tafito titi inda anan ne take ɗan ganin motoci suna wulƙa wa

Hannun ta tasaka tasharɓe hawayen fuskarta kafin tanufi titin don ta tsallaka, babu zato tahangi mota tayo kanta duk da kuwa bata san da zuwan motan ba sai ganin ta tayi kusa da ita, ƙwalla ƙara tayi amma ina tuni motan ta bige ta

Dasauri matar dake cikin motan tafito ita da ƴaƴan ta biyu suka yo Kan Halwa

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Matar take faɗa

Yayinda ƴan matan tuni sun saka kuka sabida halin ruɗe wa

"Ku taimaka min.. ku taimaka min na ɗauke ta". Matar tasake faɗa cike da rawan baki

Daƙyar suka ɗaga Halwa suka nufi motan da ita suka saka ta daga ita har Trolly ɗin ta, matar taja motan suka bar wurin

Direct asibiti suka nufa, dayake sananniya ce wajen Likitan sai yasaka Nurse suka amshi Halwa batare da bincike ba akayi Emargency Ward da ita

A reception suka zauna zaman jiran fitowar likitan

Mintuna kamar 20 yafito yanemi Matar tabiyo sa, bayan sun zauna a Office ɗin sa yasoma mata bayanin abinda ke faruwa

"Ba wani abu bane yasame ta sai buguwa da tayi akanta wanda hakan yaja mata dogon suma, amma da yardan Allah zuwa gobe zata iya farka wa".

Wannan bayanin na likita shi yakwantar wa matar da hankali, daga nan suka tattauna sannan tafito tasami ƴan matan ta suna jiran ta

Tambayan ta suka hau yi har yanzu suna zub da hawaye don ba ƙaramin tashi hankalin su yayi ba

Kallon su tayi cikin kwantar musu da hankali tace "ya isa haka babu abinda yasame ta illa buguwa da tayi akanta".

Atare suka sauke ajiyan zuciya suna faɗin "alhmadulillah".

Murmushi tayi kafin tace "to yanzu yakamata ku koma gida inyaso Ni sai in zauna da ita don baza mu tare anan ba, kuma ban ce ko waccen ku takira Daddynku tafaɗa masa ba don kar hankalin sa yatashi kuna jina?". Matar Taƙarike maganar da jan kunnen ta

Gyaɗa mata kai suka yi atare suna cewa "to Mami".

"But Mami ki bari Ni zan kwana da ita mana tunda ba wani abu me wahala bane". Cewar Safina tana kallon Mami ɗin cike da son amincewar ta

"Ok to bari mutafi gida Ni da Nafisa, but ki kula bana son rawan Kan nan naki kinji Ni? Idan da akwai matsala kiyi kiran Doctor".

Safina tace "to Mami insha Allahu".

Daga haka babu abinda suka sake faɗa illa wuce wa ɗakin da aka kwantar da Halwa da suka yi, basu fi mintuna goma ba Mami da Nafisa suka fito suka bar Safina a wajen ta.

_sai muce Allah yabaki lafiya Halwa._ [1/5, 12:58 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

_Fateema Zahra, Hauwa Ali, Wanka Yakubu Isa, Munir Y Abdullah, M. Bintu Thank You for the loving My Book._

*BOOK TWO*

.

_______________________________

*CHAPTER Twenty Five*

________🎓Washe gari da sassafe Mami tadawo Asibitin da breakfast, Safina na gaishe ta ta'amsa tace mata

"Yauwa to tashi kije yi maza Drever na jiranki ki koma gida ki shirya kar kuyi late, ki tabbatar kinyi breakfast kafin ki tafi ko kuma ki ɗiba ki tafi dashi kina jina?"

Murmushi Safina tayi lokacin da tamiƙe tana ɗaukan gyalen ta

"Mami sai kace wata yarinya haka kawai sai inje da Breakfast school?"

Hararan ta Mami tayi tace "Ni dai na faɗa miki kuma na bada sallahu idan ma baki je dashi ba Nafisa zata faɗa min, ai na faɗa miki daga yanzu na dena baku kuɗi, wuce ki tafi kar in saɓa miki uwar shiririta".

Turo baki gaba tayi tafice batare da tasake cewa komi ba

Ita kuma Mami zama tayi idanun ta akan Halwa wacce ko motsi ba ta yi tun jiya tana nan ayanda take, an naɗe mata kai da bandage sabida ba ƙaramin rauni taji ba

Ajiyan zuciya kawai Mami take sauke wa cike da tsananin tausayin Halwa, kawai aranta tunanin yanda aka yi matashiyar yarinya kamar wannan tafito gidan iyayen ta da tsakar dare take yi.

Tana nan zaune wajen ƙarfe 09:00am na safe sannan ne Halwa tafarka, don haka tamiƙe da hanzari takira Doctor coz tunda tafarka ɗin tabuɗe idanun ta bata sake motsawa ba, duk sannun da tajero mata taƙi ta amsa ta

Doctor da yazo yadudduba ta yatabbatar bata da wani matsala sannan yace aba ta abinci taci sai tasha magani

Sai da yafita kafin Mami tasoma haɗa mata abin kari, bayan ta gama takalle ta kamar yanda Halwan tazuba ma matar idanu tamkar me neman wani abu ajikin ta

Murmushi tayi mata tace "tashi kisha kinji?"

Halwa batace komi ba tayunƙura tagyara zaman ta, duk da babu abinda ke damun ta amma sosai kanta ke mata ciwo daƙyar take iya motsa shi, amsar Cup ɗin tayi tariƙe da hannu biyu ta kasa sha

Sai da matar takula da ita kafin tace "af na manta baki wanke baki ba ko zaki fi jindaɗin sha".

Amsar Cup ɗin tayi tamiƙo mata ruwa, sai da tawanke bakin kafin tamiƙa mata Tea Cup ɗin, sannan alokacin tasake ciko mata Plate da Arish da soyayyan ƙwai ta'ajiye mata akan gadon, sai tatashi tafice don tabar ta tasake

Tana fita Halwa talumshe idanunta, aranta kewar gida kawai take yi tare da tunanin makomar ta a yanzu, bata dena tunanin ba take ta tsoma bakin ta tana shan tea ɗin zuciyarta duk babu daɗi

Ta jima ahaka batare da tasan awani hali take ciki ba, har Mami tadawo tatarda ita ahaka ko rabin Cup ɗin bata yi ba, babu ma abinda tataɓa acikin Plate ɗin

Mami kallon ta tayi tana nazartan ta, kafin kuma tatamke fuska cikin serious face tace "har yanzu baki ci komi ba ashe? Bana son shashanci Yi maza ki cinye ki bani Plate ɗin da kofin".

Kallo ɗaya Halwa tayi mata ta tabbatar matar ba ta ɗaukan raini, nan da nan taji tsoron ta ya kamata ta batare da tayi mata musu ba tayi yanda tace mata tamiƙa mata Plate ɗin kamar yanda tabuƙata

"Good kinyi kyan kai". Mami tafaɗa bayan ta amsa ta ajiye sannan tafice

Da kallo Halwa tabi ta tana tunanin ita kuma wannan matar daga ina? Menene haɗin ta da ita? Ita dai tasan an bige ta to ko dai ita ce tabige ta ɗin?".

Tana cikin wannan tunanin ne suka dawo da doctor, magani yaba ta bayan ya tambaye ta "ko akwai abinda ke damun ta?"

Dayake Halwa jin ta take yi tamkar a ƙaya musamman yanda matar nan tanuna mata sai taji ta ƙosa su raba hanya, don haka tace masa babu abinda ke damun ta

Hakan yasa Doctor ɗin ce ma Mami zuwa anjima za'a sallame ta.

Ƙarfe 02:35pm. Safina da Nafisa suka kawo abincin rana, ganin Halwa ta farka ga jikin ta dasauƙi hakan ya faranta musu rai sosai musamman ma Safina, kasancewar ita akwai ta da son mutane ga fara'a ba kamar Nafisa ba, hakan yasa lokaci ɗaya tashige ma Halwa tana ta janta da Surutu

Itama Halwa sosai tasaki jikin ta zuwan su ba kamar ɗazu ba duk da kuwa ba magana take yi ba iyakan ta murmushi da bin Safinan da kallo me zuba mata surutu.

Da yamma aka sallame su suka taho gida, babban gida ne dasu me kyau sosai, kai da gani kasan ba ƙaramin kuɗi ne da me gidan ba

Suna isa Safina taruƙo mata hannu suka yi ciki, ɗakin su takai ta tahaɗa mata ruwan wanka tashiga

Itama Nafisa sai gata ta shigo da Trolly ɗin Halwa ta'ajiye mata tafice

Safina na zaune bakin gado tana jiran Halwa har tafito, murmushi tayi mata tace

"Aunty ga kayan naki nan sai ki shirya ina zuwa". Taƙarike maganar tana miƙe wa cike da zumuɗi

Gyaɗa mata kai Halwa tayi tare da mata murmushi, har tafice tana kallon ta kafin tazauna gefen gadon tana zuba tagumi, ta ɗau lokaci ahaka har Nafisa tashigo ɗakin batare da ta sani ba, sai da tataɓa ta kafin taɗago kai dasauri tana kallon Nafisan, ko kaɗan ba wai ta gane ko wacece acikin su ba duk da kuwa taji sunayen su tun a Hospital, but tsananin kaman da suke da juna baka banbance wacece Nafisa wacece Safina, iyakan dai a fuska idan kakalli Nafisa zaka iya shaida ta sabida bata da fara'a ko kaɗan, miskila ce na ƙarshe saɓanin Safina ko yaushe haƙoran ta awaje suke

Murmushi Nafisa tasakar mata ganin yanda tatsare ta da idanu tana son tantance Nafisa CE ko Safinan

"Ki taso Mami na kiran ki". Tafaɗa ahankali tana juyawa tayi hanyan ƙofa

Ɗan numfashi Halwa taja batare da ta ɗauke kanta daga kallon Nafisa ba har tafice, yanda tanuna mata ɗin tuni ta gane ba Safina bace

Miƙe wa tayi tabuɗe kayan ta taciro riga da skert na atamfa kalan Baby pink sai ratsin Milk da aka yi amfani dashi wajen zanen Flower jefi-jefi, bayan ta gama saka wa taɗau siririn gyale baƙi tayafa akanta sabida bata saka ɗan kwalin kayan ba sannan tanufi ƙofa tafice

Suna zaune gaba ɗayan su a falo, Halwa da tafito ƙasa tasamu tazauna cikin sanyin muryanta tayi wa Mami sannu

Amsawa tayi idanun ta akanta kafin takalli su Nafisa tace "ku tashi ku bamu wuri".

Babu musu suka tashi, sai ma suka yi ƙofar fita suka fice gaba ɗaya

Juyo da idanun ta kan Halwa tayi tace "yauwa so nake yanzu ki faɗa min abunda yasa kika baro gida, ayanda nafahimta da nazarin da nayi miki hasashe na ya bani kin baro gida ne sabida wani dalili naki hakane?"

Halwa da kanta ke ƙasa ta kasa ɗago kai bare ta'amsa mata, sosai matar take bata mamaki da kuma yanda halin ta yake, kai da gani kasan ba ƙaramin jarumar mace akayi a wajen ba, dakakkiyar mata me tsananin kwarjini da baiwa..

"Kinyi shiru ina magana? bana son ina maimaita ma mutum magana biyu kinji Ni?"

Dasauri Halwa tagyaɗa mata kai cikin tsananin shakkar matar da yakamata tun ganin ta da tayi

"Ki buɗe baki kiyi min magana ba gyaɗa kai nace kiyi ba".

Cikin rawan baki Halwa tabuɗe baki tasoma sanar mata da abinda take buƙatar ji a wajenta, iyakan abinda tasanar mata tafito gida ne sabida anyi mata aure da mijin ƴar uwanta, ganin tanuna kamar bata ji daɗi ba shine ita kuma tabi wannan hanyan don guje ma auren".

Jinjina kai Mami tayi idanun ta kafe kan Halwa ɗin, cikin kausashshiyar murya tace "wato kin zaɓi guduwa ne don kawai ƴar uwanki bata ji daɗin wannan haɗin ba? Kin nemi ki baro iyayen ki sabida ki faranta mata ko?"

Cikin zub da hawaye Halwa tasake duƙar da kanta, cike da raunin murya tace "nayi hakan ne kawai saboda farin cikin ta, Ni bazan so in shiga rayuwanta ita da mijin ta ba, sannan zan so takasance cikin farin ciki ko dan ciwon da take fama dashi".

Shiru ne yabiyo bayan maganar ta illa shashsheƙan kukan ta dake tashi

Wajen shuɗewar mintuna biyar kafin Mami tace "shin ke kina son Sa ko kuwa bakya son sa?"

Baki na rawa tace "Ina son sa".

Murmushi Mami tasaki tana kaɗa ƙafafuwan ta, sai da taja lokaci kafin tace "shikenan yanzu abinda Yakamata zuwa gobe zan maida ki gida saboda babu ta yanda za'a yi in barki kibi duniya akan wannan banzan dalilin naki, idan yaso in namayar dake sai in faɗa musu su raba auren tunda baki son zama dashi, kinga babu ke babu guduwa kenan, tashi ki wuce na sallame ki".

Jiki a sanyaye Halwa tamiƙe takoma ɗakin su Nafisa, tana shiga tazauna kan gadon tana ci gaba da tsiyayar da hawaye kamar an kunna famfo

Ba wai maganar mayar da itan bane yaɗaga mata hankali, jin cewa zata faɗa a raba auren ta da Khalil, ita ji take yi a yanzu ta gummaci tatafi da auren sa tayi ta yawo da araba auren, hakan zai saka zuciyarta tayi sanyi daga zugin da take mata na tsananin ƙaunar sa da take yi, auren Khalil akanta shi zai sa duk inda taje takasance cikin farin ciki, ko babu komi zata mutu da auren wanda tafi ƙauna fiye da ranta a yanzu ɗin atare da ita.

Ita kuma Mami murmushi tayi lokacin da Halwan tashige ɗaki, sosai aranta ta tausaya mata domin tunda take bata taɓa ganin irin wannan sadaukarwan da Halwa tayi ba, kina son mutum amma sabida farin cikin ƴar uwanki ki zaɓi rugujewar rayuwan ki gaba ɗaya akanta, gaskiya samun me hali irin Halwa da wahala, tana da kyakykyawar zuciya matuƙa, tana iya sadaukar da komi nata akan masoyi

(Hmm nace Mami don ma bakisan sauran sadaukarwan da tayi mata bane)

Mami tana zaune da ƴaƴan ta biyu Nafisa da Safina masu shekaru 16 a duniya, twins ne su kuma daga kansu bata sake haihuwa ba, mijinta babban soja ne sosai yana aiki a Kaduna

Baza ku gasgata maganar nan da ake cewa matar Soja itama Soja bane sai kun haɗu da Mami, Kai in taƙaice muku tsaurin idanun Mami da dakakkiyar zuciyar ta ta ninka na mijinta da shine ma Sojan, bata da tsoro ko kaɗan gata macece me tsayawa akan komi da yashafe ta da tsananin jarumta, bata nuna gazawar ta a komi, tana da fara'a sosai sai dai ba ta yin sa sai a inda yadace, shiyasa Nafisa a halayya ita taɗauko, sai dai ita Mami ba wai miskilanci ne da ita ba dakakkiyar macece da bata ɗaukar raini koda yaushe, wannan dalilin ne zaka ga tamkar bata cika wasa ba

Yanzu haka ita ma'aikaciyar gwamnati ne me amsar zunzurutun albashi don babba ce sosai a wajen aikin su.

*WASHE GARI*

Wajen ƙarfe 10:00am. Mami tasaka Halwa tashirya

Dama tuni su Nafisa sun tafi school, Safina har da kukan ta jin cewa a yau ɗin Halwa zata tafi, domin sosai jinin ta yahaɗu da Halwa ɗin a kwana ɗayan nan da tayi agidan, ta ɗauke ta tamkar babban Yayarta wacce suka fito ciki ɗaya shiyasaka tasaki jiki sosai da ita, taso Mami tabar su yau dai rana ɗaya kar suje school atafi dasu kai Halwa gida, amma ina Mami taƙi yarda, daga ƙarshe ma sai da tayi kamar zata mangare Safinan kafin tatafi school da kuka

Ita kanta Halwa sosai taji ƙaunar Safinan aranta, sai bata ji daɗin yanda Mami tayi ɗin ba, sai dai bata da bakin magana iyakan nata idanu ne domin wargi ma wuri yaka samu

Bayan Halwa tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga na Baƙin yadi da zanen Flower da aka yi da dack orange Colour, fitet ne rigan sai tayi Rolling da gyale me ruwan madara irin me taushin nan sosai ya rufe mata har bandage ɗin kanta

Janyo jakan tayi tafito Parlour inda Mami ke zaune tana jiran ta, kallo ɗaya tayi mata ta ɗauke kai tana ci gaba da latsa wayan nata

Ita dai Halwa tana nan tsaye a waje ɗaya ko ƙwaƙƙwaran motsi bata iya yi

Kamar shuɗewar mintuna goma kafin Mami tatashi tayi wa Halwa nuni da hannu alamun su je

Gaba Halwa tayi dasauri tana jan Trolly ɗin ta, koda tafita sai da tajira Mami ɗin takullo ƙofa tazo tasame ta kafin su ƙarisa wajen motan

A lokacin har me gadi ya ƙariso wajen yana kai gaisuwa wajen Mami

Amsa masa kawai tayi tana buɗe Boot

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull