Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 4
Barrister ibrahim khalil complete Chapter 4: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 4. Sai kuma tayi shiru tana wasa da hannun jakan ta, ɗan ɗago kanta…
4,489 words
Sai kuma tayi shiru tana wasa da hannun jakan ta, ɗan ɗago kanta tayi takalle sa idanuwanta na cikowa da hawaye tace
"Har yanzu dai bazan daina nuna maka ƙaunar da nake maka ba, ina ƙaunarka Ib, ina ƙaunar ka sosai, ni kaina bazan iya juran yanayin da natsince kaina aciki ba shiyasa nakasa ɓoye ƙaunar da nake maka, don Allah koda sau ɗaya ne tak a rayuwa kafurta min kana sona ko zuciyata zata sami sukuni, Allah ne yaɗaura min ciwon son ka kuma kai kaɗai ne zaka iya min maganin ta, har yanzu har gobe bazan gaji ba Ib, ina matuƙar matuƙar ƙaunarka".
Tana kawo nan azancen ta tayi shiru tana jan numfashi, sai kuma tabuɗe ƙofan tafice, idanuwan shi yaɗago yabi ta da kallo, tafiya take yi tana share hawayenta da gefen gyalen ta har tashige cikin gidan nasu, kafin shi kuma yaɗauke idanun shi yana sauke ajiyan zuciya, ya sani duk acikin ƴan matan da suke nuna masa ƙauna ba wacce takai Bilkisu, yasan da cewa ita ɗin ta daban ce cikin mata, tana da hankali da nutsuwa, gata kyakkyawa babu abunda tarasa, sai dai ko kaɗan shi soyayya bata burge shi, tunda yake be taɓa son wata ɗiya mace ba, be san ma ya ake soyayya ba, shi dai kawai yasan da cewa mata suna matuƙar bashi tausayi, sosai yake jin ta cikin ran shi sai dai bazai iya yin abinda take so ba
ahankali yaja motan sa yaci gaba da tafiya, zuciyan sa cike fal da tunanin ta.
.
*Comments* *Vote* *Share* [9/3/2020, 2:24 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📚* ```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 11*
A Compound ɗin gidan sa yayi packing ɗin motan, tsawon mintuna 5 yaɗauka kafin yabuɗe murfin motan yafito, ahankali yake tafiyan nasa cike da salon burgewa har yakai bakin ƙofan main Palon yabuɗe yashiga yana motsa bakin sa, babu kowa ciki sai ƙaran T.v plasma da yacika cikin Palon sai aiki yake yi shi kaɗai, Direct ɗakin sa yanufa yashige yarufo ƙofan, asaman gado ya'ajiye briefcase ɗin sa, yazaro wayoyin sa dake aljihun wando yazube su akan gadon, sannan yacire links ɗin rigan sa yakuma cire agogon hannun sa yabuɗe drower yasaka, zama yayi saman gadon yaɗau wayan sa yalatsa yakara a kunni
"Kihaɗa ma Nazeefa kayanta kice tajira ni a palow".
Abinda yafaɗa kenan yatsinke kiran ya'ajiye wayan, tashi yayi yanufi Toilet yasillo wanka yafito ɗaure da towul ajikin sa, duk jikin sa ruwa ne ke ɗiga haka yanufi gaban mirror yazauna a stool, shiru yayi yana kallon kan shi a madubi, kyakykyawan surar jikin sa yake bi da kallo na tsawon lokaci kafin yaɗauke idanun sa, sai kuma yamayar da idanun nasa yana ƙare ma beauty face ɗin sa kallo, ya daɗe ahaka shi kan sa be san meyasaka yake kallon halittan nasa ba, amma dai yasan da cewa shi kan sa yana tsananin burge kan sa, komi nasa me kyau ne musamman ma ƴan manyan idanuwan sa masu ɗaukan hankali farare ƙal dasu, da yawa ƴan mata suna nuna masa matuƙar ƙauna kamar su cinye sa, tun yana ƙarami haka yataso me farin jinin jama'a kowa son sa yake yi ba mazan ba ba kuma matan ba, shi ba mutum bane me yawan shiga abun da babu ruwan sa kuma ba me yawan magana bane shiyasaka wasu suke ce mishi me girman kai, kuma ba haka bane sai dai in baka zauna dashi ba, anan ne zaka fahimci halin sa sosai yake da kirki da sauƙin kai.
Ajiyan zuciya yasaki yasoma shafa Lotions ajikin sa, bayan ya gama sai yaɗau kumb yataje suman kan sa yakwanta luf sai shaining yake yi, kai da gani kasan sosai kan yake shan kuɗi wajen gyara, miƙewa yayi yanufi sif ɗin sa yaciro kayan sa, sanya wa yayi yana gyara wuyan rigan tare da ɓame bottles ɗin, yadi ne fari ƙal tamkar tissue har singlate ɗin da yasaka ciki ana gani, sun bala'in ɗaukan golden skin sa, sosai sukai mishi kyau, sai da yafeshe jikin sa da farpume's ɗin sa sannan yasaka Black cover shoes a ƙafafun sa, yanufi gaban gadon sa yaɗau wayoyin sa da mukullin mota yatako yabuɗe kofa yafita
Dasauri taɗago kanta takai duban ta gare sa, haɗa idanun da sukayi yasaka hawayen dake maƙale a kurmin idanun ta daman zubowa, saurin ɗauke kanta tayi taduƙar dashi ƙasa, sosai tashiga damuwa tun sanda Lubna tasanar mata da abinda yace, duk da batasan ina zai kai ta ba but ko kaɗan bata son rabuwa dashi, bata son tayi nesa dashi, a ɗan zaman da tayi na kwana uku rak cikin gidan sa yafiye mata sauran tsawon shekarun da tayi a duniya, zaman ta gidan sa tamkar wani haske ne cikin zuciyarta
Muryan sa da yadoki kunnin ta shi yadawo da ita duniyar da taburma
"Tashi muje".
Abinda yafaɗa kenan yayi gaba, itama kuma ahankali tamiƙe tajanyo trollyn kayan ta tabi bayan sa, lokacin da ta'isa jikin motan har ya shige ya bar mata Boot abuɗe, ɗaya daga cikin ɗan aikin gidan shi ya'amsa trolly ɗin yasaka a Boot ita kuma tabuɗe gaban motan tashiga, keey yayi ma motan yaja ahankali yafice daga gidan, cikin motan ma babu wanda ke magana cikin su, Nazeefa kaɗan-kaɗan take ɗago kanta takalle shi tana sharan hawaye, tuƙin sa yake amma duk yana lura da ita, kuma akan idanun sa ɗazu hawayen ta yazuba, ahankali cikin cool voice ɗin sa yace
"Lafiya kike kuka?"
Tambayan ba kaɗai yashige ta ba don batayi zaton yasan tana yi ba, ɗago kai tayi takalle shi, sosai yayi mata kwarjini da cika idanu, sauke kanta ƙasa tayi tana ɗan saka yatsa tashare sauran hawayen nata, bata iya buɗe baki ba bare tabashi amsa, hakan yasaka tayi shiru don batasan me zatace ba, shima ɗin be sake tambayan ta ba, sai can kuma da sukayi nisa yace
"Ko dai ciwon ki ne ke miki zafi?" Yafaɗa maganan kamar me raɗa yana kallon ta
Sai da taɗago kai takalle sa sannan yakau da kanshi, cike da sanyin murya tace
"A'a, bana son rabuwa da kai ne yaya".
Jin maganan yayi ta ɗan duke shi, hakan yasaka yasake kallon ta sai kuma yaɗauke kai yamaida ga titi
"Kidena damuwa Nazeefa ba wani waje zan kai ki ba, wajen Mahaifiyata zan mayar dake zaki fi samun kulawa, ke yarinya ce yakamata ace akwai wacce zata riƙa kula dake, zaman ki gidana akwai takura da yawa, ki kwantar da hankalinki nasan kina tunanin ko mun rabu kenan".
Ahankali tagyaɗa masa kai tana ƙara share sauran hawayen nata da suka zubo mata, sosai taji zuciyar ta tayi sanyi, sai dai tafi ƙaunar zama agidan sa fiye da wani waje
A bakin Gate ɗin gidan yatsaya yayi hon kafin aka buɗe masa yashiga, bayan yayi parcking fitowa sukayi, sai da yabuɗe Boot yaciro mata trolly ɗin ta kafin suka nufi cikin gidan, Mom na zaune a palow suka shigo da sallama, amsa musu tayi tana kallon su, sai kuma tasaki murmushi tana faɗin
"Bari in cinka baƙuwa ta, ƴata Nazeefa sannu da zuwa".
Ita Nazeefa kallon Mom kawai take yi cike da burgewa, sosai taga kamannin Khalil a fuskarta duk da skin ɗin su ba ɗaya bane, take kuma taji sauran farin cikinta ya dawo mata da ganin matar, muryan Khalil ne yakatse mata tunanin ta
"Mom ai dama kinsan da zuwan ta, ba wani cinka da kika". Ya faɗa maganar ne lokacin da ya'isa gare ta yazauna agefen ta, ƙara sakin murmushi Mom tayi tace
"To ai bansan ta a fuska ba dai, tunda rowanta kake ta min sai yanzu da kaga daman kawo ta, kinji ƴata ƙariso taho kizauna anan".
Kanta aƙasa tataho ahankali cike da kunyar matar tazauna agefen ƙafarta
"Ah kin zauna a ƙasa kuma? Taso kizauna anan mana, tashi maza".
Babu musu kuwa tatashi tazauna agefen ta, yayinda suka saka Mom ɗin a tsakiya, cikin sanyin murya tace
"Ina wuni Mama".
"Lafiya lau Nazeefa, ya jiki da fatan yanzu kinji sauƙi sosai ko?"
Gyaɗa kanta tayi sai kuma tace
"Alhmadulillah dasauƙi".
"Allah yasawaƙe, kinga yanzu kin dawo gidan mu, ina fata zakiji daɗin zama dani? Kizauna anan tamkar ƴata daga yau kin zama ƴar gidan nan kema".
Murmushi kawai Nazeefa tayi tana wasa da yatsunta
"Bari in saka anuna miki inda zaki zauna ko? Kisaki jikin ki kinji daga yanzu na zama mahaifiya gare ki".
Gyaɗa kanta tayi tana jindaɗi aranta, sosai matar tayi mata, gata mace me fara'a ko kaɗan ba ƙyama a ranta, nan Mom tayi kiran me aikinta, tana zuwa tace "tatafi da Nazeefa takai ta ɗakin da tasanya ta gyarawa, bayan sun tafi ne takalli Khalil da tun soma maganar nasu yaciro wayansa yana latsawa tace
"Kai masha Allah, yarinyan gata kyakykyawa, daga gani tana da hankali da nutsuwa, da alama dai zanji daɗin zama da ita, har naji tashiga raina sosai wlh tamkar ƴata ta cikina".
Ɗan ɗago kan sa yayi yakalle ta, sai kuma yamaida idanun sa kan wayan yaɗan latsa ta kaɗan yasaka cikin aljihun gaban rigan sa yace
"Ni zan tafi Mom, ba zama zanyi ba ina da wani aiki kinsan gobe ne tafiyana, ina son inje wani waje ne". Yaƙarike maganar yana miƙewa tsaye
Mom tace "to shikenan, amma dai zaka dawo ko zuwa anjima ne don muyi hira, bana son katafi bamu sake haɗuwa ba kaji ko?"
Murmushi yasaki me kyau da burgewa, yaduƙo gaban ta yasakar mata kiss agoshi yaɗago yana kallon ta yace
"Mom ai dole ne nadawo muyi sallama, idan ma ban sami dawowa yau ba da safe zan dawo kinji".
Itama murmushi tayi tace
Ok Autana, kasan yanzu ma drever yatafi ɗauko Dad ɗin ku a airport".
Ɗan waro idanu yayi yace
"Dagaske Mom?"
Hararan sa tayi tana jan kumatun sa tace
"Da ƙarya".
Dariya yayi yace
"Sorry Mom, bari in zauna to in jira sa".
"A'a tashi katafi, kai da baka da lokaci, katafi zuwa anjiman in kadawo sai kazo ko kuma goben kamar yanda kace".
"Ok Mom ni na tafi, ki miƙa masa gaisuwa ta kafin nadawo, kice masa kuma ya'ajiye min tsarabata da kyau zanzo in amsa da kaina, kar yasoma yaba Bro".
Dariya sukayi gaba ɗayan su, sai da yasake mata kiss a goshi kafin yafice yana faɗin
"Mom byeee".
.
******* ******* ****
Ƙarfe 05:11pm. Halwa ce zaune bakin ƙofa tana yankan ƙunba wani yaro yashigo gidan yace
"Wai ance Halwa tazo?"
Ɗago kai tayi takalli yaron sai tamayar da idanunta kan yankan ƙunban da take yi tace
"In ji wane?"
"Wani ne a mota".
Shiru tayi taci gaba da abinda take yi, yaron kuma yatsaya yana kallon ta, daga cikin ɗaki Mama tace
"Wai inace dake akeyi Halwa?"
"Mama ƙyale shi yatafi, kai kaje kace bata nan". Tafaɗi hakan lokacin da tasake ɗago kanta takalli yaron
Har ya juya zai tafi Mama tace
"Kai yaron nan yimaza kaje kace gata nan zuwa".
"To". Yaron yafaɗa yana rugawa waje da gudu
"Kitashi kiwuce kitafi da Allah bansan wulaƙanci".
Zumɓuro baki tayi kamar Maman tana ganin ta tamiƙe tashige ɗaki sai magana take yi ƙasa-ƙasa, Mama kamar taji me take cewa tace
"Ke kenan kullum koran samari, inace dai dole sai an ɗaura miki aure da Nuran shine kin zama mallakin shi? Kaji min shashashan yarinya haka ake yi".
Halwa da tafito daga ɗaki riƙe da gyale a hannu tace
"To Mama meye amfanin fitan nawa tunda inada wanda nake so?"
"Kinci gidan ku, ai babu yanda Allah baya sanja ƙuduran sa, kuma fitan ki ai ba zai hana kisami wanda kikeso ba, Ni wulaƙanci ne bana so wlh, in kin fita sai kice mishi kar yasake dawowa ba shikenan ba?".
Yafa gyalen tayi kan doguwar rigan ta na atamfa me ruwan toka da akai mishi sirki da ja da milk, slippers tasanya tafice batare da tabi takan Mama dake ta surutu ba. [9/3/2020, 7:51 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📚* ```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 12*
Tana fitowa suka haɗa idanu da Yazeed da yake jingine jikin motan sa, tun sanda tafito yasoma murmushi har ta ƙari so wajen sa da sallama a bakin ta, amsa mata yayi still yana murmushi yace
"Barka da fitowa gimbiyar Mata kyakykyawar yarinya".
Murmushi tayi tace "fatan kazo lafiya?"
Yace "tun sanda dai muka haɗu dake ban sake jin lafiya ajikina ba, har kuwa fitowar da nayi daga gida nazo gare ki, but yanzu da nagan ki agabana sai naji kamar an kwaso duk lafiyan mutanen duniya ne an ɗaura min ni kaɗai, kinga kuwa yanzu zan iya ce miki lafiya ƙalau kenan".
Murmusawa tayi tana kallon shi tace
"Na kula dai kai ɗin nan kana da son wasa da yawa".
Shima murmushin yayi yace
"Gaskiya ne ƴan mata, to fatan kina lafiya kema? Ya su Mama da kowa da kowa? Kinga ban zo ba sai yau ko? Wlh kwana biyun nan aiki ne yayi min yawa, amma baki ji yanda na azabtu ba da rashin ki, ji nake kamar na shekara ɗari tare dake, sosai nashiga damuwa Burina kawai nazo nasake tozali da kyakykyawar fuskar nan taki".
Ita dai batace komi ba sai murmushi da take yi
"Ƴan mata da fatan dai za'a bani matsuguni acikin zuciyar ki, wlh sosai nakamu da ƙaunar ki, ina fata dai babu wanda yariga ni?"
Halwa tace "ai tun farko kamar in ban manta ba sai da nafaɗa maka ni ɗin mallakin wani ne, sai dai in baka haƙuri Malam Yazeed domin ma fitowan nan da nayi nazo ne nasanar maka an riga da anyi min miji".
Cikin fuskar damuwa yace
"Dan Allah wai dagaske kike yi?"
"Wlh dagske nake maka, ina da mijin aure kuma nan ba da daɗewa ba za'a sanya mana ranan aure ni dashi".
Cike da rashin jin daɗi Yazeed yace
"Yanzu shikenan wani ya rigani? Shikenan kina nufin zan rasa ki? Wlh Halwa sosai na kamu da ƙaunar ki a lokaci guda, yanzu kuma bansan ya zanyi in cire son ki cikin zuciyata ba".
Cike da tausayin sa saboda sosai tayarda dashi kuma ta ga tsantsan gaskiyar sa a fuskar sa tace
"Kayi haƙuri a sannu zaka manta dani ai, dama baka daɗe da sani na ba, don haka insha Allahu nan ba da jimawa ba zaka neme ni karasa ko tuna ni bazaka sake yi ba".
Ɗan murmushin gefen baki yasaki yace
"Kayya a naki fahimtar kenan Halwa, wlh bakisan yanda nake jin ki cikin zuciyata bane zai yi wuya nacire ki sabida ƙaunar da nake miki ya wuce tunanin ki, ni kinga ban iya saka abu cikin rai ba, kuma zan faɗamiki gaskiya ta kece macen da nafara so nafara kulawa a matsayin wacce nake ƙauna, taya kike tunanin lokaci ɗaya kuma zan inya manta ki?"
Girgiza kan shi yayi sannan yace
"Nagode sosai da faɗamin gaskiya da kikayi, Nagode da baki bar ni nasha wahala ba kinji?"
Gyaɗa masa kai kawai tayi
"To yanzu sai yaushe kuma? Ko bazamu sake haɗuwa ba? Yakamata muyi zumunci don Allah kibani numbanki".
Bata musa ba tace "ok babu damuwa".
Takaranto mishi numaban kafin tace
"Ni zan shiga gida, sai wani lokacin kuma".
Yace "to Nagode sai kin ji ni a wayan kenan, kigaida su Mama".
Kanta kawai tagyaɗa masa tajuya zata tafi, kawai tayi tuntuɓe da dutse hakan yasaka tayi taga-taga zata faɗi shi kuma yayi saurin taro ta, dai-dai lokacin da Nura yashanyo kwana yagansu ahaka Yazeed ya riƙo ta, kuma sun ƙame ahaka suna kallon juna, wani irin baƙin ciki ne yatokari zuciyar shi, take yaji kishi ya kama shi, tsayawa kawai yayi yana kallon su har sanda yasake ta suka yi magana ita kuma tashige ciki, take yaji zuciyar shi tana faɗin
"Daman yaudaran ka take yi abinda take aikatawa kenan, yau Allah ya toni asirin ta".
Take kuma yatuna da abinda yafaru jiya, nan yaharhaɗa abubuwan nan da nan yaji zuciyar shi na tafarfasa, aransa yace
"Tabbas dole nayi tunani akan maganar ka, wannan dama ce tasame ni".
Daga haka yasoma takowa yanufi gidan nasu, yana shiga suka haɗa idanu da Halwa dake tsaye bakin ƙofa tana magana da Mama da har yanzu take cikin ɗaki, murmushi tasakar mishi tace
"Yaya har ka dawo?"
Ɗan dai-dai ta fuskar sa yayi shima yasakar mata murmushin yanufo ta yana faɗin
"Kinga na dawo da wuri ko?"
"A'a Yaya, amma dai Allah yasa an dace?"
Mama da tafito daga ɗaki itama tace
"Da fatan dai an sami abinda akaje nema?"
Shiru yayi na ɗan wani lokaci, yayinda duk kan su suka zuba mishi idanu suna jiran amsan shi, sai kuma yasaki murmushi yace
"Yau dai an dace, na sami aiki insha Allah komi ya wuce".
"Alhamdulillah".
Atare suka faɗa hakan, Mama har da shafa hannu saman fuskarta, yayinda Halwa tasaki fara'a tana me cike da farin ciki da jindaɗi
Sallaman Baba yakatse Mama dake faɗin
"Masha Allah. Allah Ubangiji yasanya alkhairi".
Amsa mishi sallaman suka yi, yaƙariso yana kallon su yace
"Ya naga kunyi cirko-cirko daku, wani abun ya faru ne?"
"Malam ɗan ka yau yasamu aikin dai da yadaɗe yana shan wahala, yau an dace".
Fara'a Baba yasaki yace
"Ah masha Allah, da kyau Allah yatabbatar da alkhairi".
"Ameen duk kan su suka amsa, kafin Mama tace
"Bari in kawo maka tabarma Malam".
Ɗaki tashige taɗauko tashimfiɗa masa yazauna, itama tazauna gefen shi yayinda Halwa tazauna kan dokin ƙofa tana cire gyalen jikinta tajefa ɗaki, Yaya Nura ma zama yayi a saman kujera ƴar zuƙune dake wurin
Baba yace "ina tayaka murna, yau dai gashi ranan da muke jira tazo, to Allah yataimaka yasa kafara a Sa'a".
Gaba ɗaya suka amsa da "ameen" Baba yaci gaba da cewa
"To yanzu fa an sami abinda ake nema sai kuma aure kenan?".
Duƙar da kai Nura yayi, ita kuma Halwa wani farin ciki ne yasake kama ta jin maganar Baban
Mama murmusawa tayi tace "gaskiya ne Malam tunda babu abinda za'a jira".
Baba yace "to insha Allahu nan ba da daɗewa ba za'a tsai da ranan auren, kuma ba wani daɗewa za'ayi ba tunda dama kana aikin ka, mun dai fi so ne kakama na gwamnatin hakan zai fi, tunda gashi an samu shikenan magana ta ƙare zuwa gobe insha Allahu ko jibi za'a tsai da ranan".
Sosa kai Nura yayi yamiƙe yana faɗin
"Bari inje wajen abokina".
Dariya Mama tayi tace" ko dai kunya ne zai kora ka?"
Dariya shima yayi yace
"A'a Mama akwai dai abinda zanyi can ne, ni na tafi". Yafaɗi hakan yana ficewa dasauri
"Ɗan nema za ma kadawo ne, ke kuma me kike jira, ko ke kunyan bata kore ki bane?" Mama tafaɗi hakan tana mayar da idanunta kan Halwa
Itama tashi tayi da gudu tashige ɗaki tana dariya
Baba yace "ahh ya haka kibar ta mana tazauna, kunyan wa zataji bayan mu ne iyayen ta?"
Dariya Mama tayi tace "bari dai in kawo maka ruwa kashare waɗannan yaran duk gulma ne irin nasu".
Koda takawo mishi ruwan hira sukaci gaba da yi duk akan maganar samun aikin Nura, da kuma saka ranan su.
.
.
_shin wani abu ne yafaru jiya da har Nura yatuna?_
_Wanene yafaɗa masa maganar da har yace zai yi tunani akai?_
_wani ma magana ce?_
_JIKAR LAWALI CE_ 😉 [9/3/2020, 10:48 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📚* ```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 13*
*WASHE GARI*
ƙarfe 02:45pm. Drever'n Brr. Ibrahim Khalil yatafi kai shi airport, suna isa ba ɓata lokaci jirgin su yaɗaga dasu zuwa ƙasan Egypt.
_Sai muce Allah yaba da sa'a BARRISTER_🤒
....... ....... ........ ..... Kuka take yi sosai kamar ranta zai fita, tun sanda yafice gidan tazauna anan palow take ta rizgan kuka, sosai take cikin damuwa abubuwan duk sun haɗe mata, har yau takasa samun mafita, ta kasa samun nasara akan abinda aka saka ta, gashi yanzu mutanen nan sun sako ta gaba, sosai suke mata barazana, gefe ɗaya kuma zuciyarta ta azalzale ta da ƙaunar mutumin da besan tana yi ba, haka kawai take jin baƙin cikin tafiyan nan nasa, shikenan bazata sake ganin sa ba sai sanda yadawo? kuma batasan ranan dawowarsa ba, sai kuma tasake fashewa da kuka tuno mahaifiyar ta da tayi, yanzu da waɗannan mugayen basu ɗauke taba da tuni takoma gida, acan zata zauna har yadawo, "take tatuna sanda yakira ta yana zaune a palow tazo tazuƙuna gaban sa, sai da yagama latsa wayan sa kafin yaɗago kai yakalle ta yace
"Gobe zan yi tafiya, zaki iya komawa gida har sanda zan dawo, kiriƙe wannan ko zaki buƙaci wani abun".
Yamiƙo mata wasu maƙudan kuɗi, ahankali tasaka hannu ta'amsa tana jin zuciyarta babu daɗi, godiya tayi masa, sannan yabata umarnin "tafiya"
Shiru tayi tana ajiyan zuciya, rufe idanuwanta tayi tana sauraron bugun zuciyarta
"Meyasaka ban faɗamasa halin da nake ciki ba da yatambaye ni zuwa gida? Wataƙil yataimake ni, ya zanyi da waɗannan mutanen".
Take tasake tuno wayan da sukayi yanzu fitan shi, mutumin da yake kiran ta, shine dai yasake kiran ta yana tambayan ta, "ance zai yi tafiya, ko tasan ina zashi?"
Runtse idanunta tayi wasu hawaye na sulmiyo mata tuna amsan da tabashi
"A'a bansani ba, bansan ma zai yi tafiya ba".
Mutumin be ce mata komi ba sai yakashe wayan, da alamun kamar wani abun ne yataso shiyasaka yakatse kiran batare da sun gama magana ba, sake runtse idanun ta tayi zuciyarta na ci gaba da bugawa, tasani dole zai sake kira, amma batasan me zai biyo baya ba idan har sukasan ya tafi?
"Wataƙil ma su zo da kansu suyi binciken abinda suke nema".
Tafaɗi hakan afili tana buɗe idanuwanta, ɗaura kan ta saman kujera tayi tarufe idanunta tana ci gaba da tunani kamar yanda yazame mata jiki yanzu.
.
****** ****** *****
"My dear tashi muje kiraka ni".
"Ina yaya?" Tatambaye shi tana kallon shi
"Ke dai kitashi kiraka ni, zan amso sabon ɗinki na ne, kuma daga nan sai mu yawata kinsan mun daɗe bamu fita ba".
Washe baki tayi tace
"hakane Yaya, bari to in sauya kayan jikina".
"Ok" yace da ita yana zaro wayan sa a aljihu yasoma dannawa
Ita kuma tashige ɗakinta dasauri, tasoma sauya kayan jikinta, wata black and peach colour material me taushi taɗauko daga cikin kayan ta, riga da sket ne sunyi kyau sosai tasaka ajikinta, hakan yasaka kyawun kayan suka sake fitowa sosai sabida yanda yahaɗe da kyan ta, sai da tashafa powder tazizara lipstick a baki sannan tasaka hijabin ta sky maroon da iya kacin sa gwiwa, babu ɗankwali akan ta sai gashinta da tatufke a can ƙasan ƙeyan ta, kasancewar hijabin me hula ne don haka ba'a ganin gashin kanta, flate shoes tasaka kalan baƙi da kwalliyan tuntu asaman me ruwan zamba, fitowa tayi tana faɗin
"Yaya na fito, muje to".
Ɗago kan sa yayi yana ƙare mata kallo, sai yasaki murmushi yace
"Baby kinyi kyau, kinga yanda yarintan ki yasake fitowa?"
Fari tayi da idanun ta tace
"Dagske yayana?"
"Dagaske mana Dear".
"Ina kuma zakuje haka?" Cewar Mama da tafito daga ɗaki tana kallon su
"Mama raka ni zatayi, zan amso ɗinkina".
"To kar dai kudaɗe, nima fita zanyi zuwa sunan Asabe, saura kuma kuje kuzauna inta jiran ki baki dawo ba".
Nura yace "Mama bazamu daɗe ba ai, sai mun dawo"
Gaba yayi itama Halwa tabi bayan shi tana faɗin
"Mama sai mun dawo".
"Adawo lafiya".
Tafiya suke yi a ƙasa suna yi suna hiran su cike da nishaɗi, kallon ta Nura yayi yace
"Ko dai mutaka a ƙasan ne? Naga kamar tafiyan na miki daɗi?"
Ɗan waro idanunta masu kyau tayi tace
"A'a Yaya tare mana dai napep, akwai rana fa a gari".
"Ok my dear, dama bana son Kisha wahala, gwara dai mutari napep duk da nan kusa ne".
Lokacin sun iso bakin titi wani me keke napep dake fake ɗan nesa dasu, yatuƙo yaƙariso wajen su yana faɗin
"Tafiya ne?"
Nura ɗan kallon sa yayi suka haɗa ido yace
"Eh bakin kasuwa zaka kai mu?"
"Ok kushiga kuɗin ku saba'in ne".
"Ai mun sani". Cewar Halwa tana turo baki gaba
Murmushi Nura yayi yace
"Ke dai da neman magana kike, menene laifin sa anan don yafaɗa miki kuɗin sa?"
"Ai Yaya babu wanda be san kuɗin haka bane, tunda ba yau suka saba kai mu ba, wannan fa doka ce da suka saka kuma kowa yasan da hakan ba sai sun sake maimaita mana ba". Ta faɗi maganar ne tana shigewa cikin napep ɗin
Me napep ɗin yace
"Baiwar Allah kiyi haƙuri ni baƙo ne ai, nayi tunanin ko baku sani bane".
Taɓe baki tayi takalli Nura da shima yashigo yazauna a gefen ta tace
"Yaya daga nan mubiya cikin kasuwan mana zan siya kayan kwalliya, nawa sun ƙare".
"An gama ranki yadaɗe, komi ma kikeso sai kisiya tunda Allah ya kawo mu ko?"
Murmushi tasaki cikin jindaɗi tace
"Eh Yayana, Nagode sosai, ina jindaɗin yanda kake kula dani".
"Babu komi ai, ke ɗin ƙanwata ce kuma Matata insha Allahu".
Dariya tayi tana jin farin ciki a zuciyarta, daga nan hira suka soma yi, yayinda me napep tuni yasoma tafiya dama, gab da zasu kawo wajen da za'a sauke su napep ɗin tatsaya
"Oh shitt.. dan Allah kuyi haƙuri bari in duba naga me yafaru".
Nura yace "ai babu komi, bari musauka anan kawai tunda babu nis..".
Be gama faɗin abinda yakeson faɗa ba yaji ya shaƙi wani abu cikin hancin sa, ko sceonds biyar basu sake ba gaba ɗaya suka ɓingire cikin motan daga shi har Halwa har suna gwara kai, murmushi me napep ɗin yasaki yajuya yagyara zaman sa yatada keke napep ɗin yaci gaba da tafiya.
.
_Tofa 🤔 me kuke tunanin zai faru?_