Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 5
Barrister ibrahim khalil complete Chapter 5: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 5. _da Allah ku ƙara yawan comments yana min kaɗan, kunsan comment…
4,489 words
_da Allah ku ƙara yawan comments yana min kaɗan, kunsan comment ɗin ku shi ke ƙara min ƙwarin gwiwa har in ji ina suburbuɗo muku ba ƙaƙƙautawa, don haka sai ku bada himma, yawan comments yawan post._ 😉🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️ [9/4/2020, 7:56 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📚* ```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 14*
Ahankali tasoma buɗe idanuwan ta tana rufewa har sanda tabuɗe gaba ɗaya idanun tana kallon rufin ɗakin, ta ɗan jima ahaka tana son tuno abinda ke faruwa kafin komi yadawo ƙwaƙwalwan ta, dasauri tazabura daga kwancen da take tatashi zaune tana kallon tsararren Palon da yagaji da haɗuwa, idanuwanta akan Nura yasauka da shima yake yashe ƙasa da alamun dai shi be dawo hayyacin sa ba, a gefe da gefen sa kuwa wasu mutane ne manya dasu su biyu sun tsaya a kansa, sai kuma tadawo da ganin ta gefen ta dasauri, nan ma wasu mutane biyun ne kusa da ita, da alama gadin su suke yi
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.. ina ne nan?". Ta faɗi hakan ne a fili tana jin zuciyarta na tsinkewa, don tasadakar gidan cin kai ne aka kawo su
"Gidana ne".
Taji maganar ya doki kunnin ta, dasauri tajuyo tana wurwurga idanu, nan kuwa idanun ta yasauka akan sa, yana zaune saman kujera ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya yana sakin murmushi, daga shi sai farar singlate da gajeren wando me ruwan ƙwai da iyakacin sa gwiwa, gefen sa kuma da akwai mutum ɗaya dake tsaye yana gadinsa, wani irin bugawa zuciyarta tayi kamar zatayi tsalle tafaso cikin ƙirjinta, take wani irin tsoro yashige ta har batasan sanda tawaro idanun ta waje ba tana kallon shi, still yana murmushi yace
"Barka da zuwa turaka ta Amarya ta, yau dai gaki cikin gidana abinda nadaɗe ina fata da buri kenan".
Ahankali yatashi yanufo ta har zuwa gaban ta kafin yadakata yana ƙare mata kallo, sai kuma yasoma zagayeta yana tafa hannun sa, wanda duk taku ɗaya da yake yi tana ji ne kamar yana tafiya da bugun numfashin ta, sai da yagama zagaye ta sannan yazuƙuna agaban ta yana kallon cikin idanun ta da tatsayar akan sa ko motsin kirki takasa yi, sosai ganin shi yayi tsananin firgita ta har tana jin komi na jikinta ya dena aiki, murmushi yasaki yana faɗin
"Yau dai na baki mamaki ko? Baki zatan zaki iya zuwa hannun Haris cikin sauƙi ba?"
Sai kuma yasaki dariya yaci gaba
"Dama nace miki zan kafa tarihi cikin rayuwan ki, zanyi miki abinda har kimutu bazaki taɓa mantawa dani ba, to ga ranan tazo, yau duk zan huce wahalan da kika bani, kin bani wahala sosai Babyna".
Yaƙarike maganar yana kai hannun sa saman fuskarta yashafo gefen face ɗinta, kafin yacire hannun dasauri yana zuba murmushi
"Ohh kince in dena taɓa ki ko?" Uhmmm saboda na taɓaki kika cire hannu kika wanka min mari ko? To yau kuma bari inga wani hukunci zaki min, kin san me?"
Yatambaye ta yana matso da fuskar sa kusa da nata, sai lokacin tasami daman motsa jikin ta, dasauri taja baya tana girgiza mishi kai, nan da nan hawaye suka cika idanun ta suka soma zubowa, cikin rawan murya tace
"Don Allah.. don Allah na roƙe ƙa kayafe min, wlh bazan sake ba dan Allah kayi haƙuri".
Dariya yakece dashi yana zama dirshan a ƙasa yace
"Da wuri haka? Taya kike tunanin mayunwacin zakin da yadaɗe yana farautan abincin da zai ci, yau ya samu sai kuma yasaki abincin yatafi?" Sam wannan ba me yiwuwa bane, yau sai nacika Burina akan ki Halwa, yau zan yi maganin ishin ruwan da nadaɗe ina fama dashi cikin raina, yau zan cire duk wata sha'awan ki dake damuna".
Riƙo hannun ta yayi yana son jawo ta jikinsa, tayi saurin ja baya tayunƙura tatashi aguje tanufi wajen Nura da har yanzu yana nan kwance, girgiza shi tasoma yi cikin kuka tana faɗin
"Yaya Nura dan Allah katashi, katashi kataimake ni dan Allah Yaya".
Dariya Haris yakwashe dashi, dai-dai lokacin da Nura yabuɗe idanu yana jin kukan Halwa yayi saurin zabura yana kallon ta, saurin shigewa jikinsa tayi tana faɗin
"Dan Allah yaya kataimake ni zai raba ni da mutuncina, dan Allah yaya karka bari yacin ma burin sa kataimake ni".
Tasake fashewa da kuka har da su majina, gaba ɗaya duk tagama tsorata, shima sake riƙo ta yayi yace
"Kiyi shiru Halwa babu abinda zasuyi miki kinji, idan har ina raye babu abinda zai same ki kidena kuka".
Muryan Haris ne yacika wurin
"Kai kuriƙe min shi da Allah".
Ai kuwa nan da nan mutanen nan gaba ɗaya sukayo kan su suka damƙo Nura suka rirriƙe shi, shi kuma Haris yafinciko Halwa dake ta faman rusa kuka kamar ranta zai fita, sai roƙon sa take yi tana faɗin
"Don Allah don girman Allah kaji tausayina karka raba ni da mutuncina, wayyo Allah don Allah kayi haƙuri kataimaki rayuwata wlh ni marainiya ce".
Dariya yake yi yana jan ta yanufi wani ɗaki da ita, Nura kuwa sai son ƙwacewa yake yi yana faɗin
"A'a dan Allah karkayi kaƙyale ta, dan Allah kasake ta".
Garam haka yaji ƙaran kulle ƙofa da Haris yayi, runtse idanuwan sa yayi yana jin wasu hawaye na kwaranya a idanun sa, tsananin tausayin ƙanwar sa ce yakama shi
"Meyasa?"
Yafaɗi hakan a fili yana sake runtse idanun sa da ƙarfi jin ihun ta dake shiga kunnin sa
...... ...... ....... ........ .... Tana zaune saman gado ta ƙudundune jikinta cikin hijabin ta, ta haɗa kai da gwiwa tana wani irin kuka na fitan hankali, kuka take yi sosai tana sake matse kanta da ƙafafunta waje ɗaya, ji take yi ina ma Allah yaɗauki ran ta a yau ɗin, ko kaɗan bata fatan tasake minti ɗaya cikin duniyar nan
Buɗe ƙofan ɗakin akayi, Nura ne yashigo idanuwan sa ƙyarr akan ta, ahankali yasoma takowa zuwa wajen ta yana jin kukan ta na shiga masa har cikin ƙwaƙwalwa, sosai kukan nata ke taɓa masa zuciya, koda ya isa hannu yasaka yadafa kafaɗan ta, sai taɗago dasauri tana kallon sa da idanuwanta da suka gama rinewa sukayi jawur sai tsiyayan hawaye suke yi, dasauri tasaka hannu biyu tariƙo ƙafafunsa tatusa kanta ajikin sa tana sake fashewa da wani irin kuka me tsuma ran me sauraro, ahankali yaɗaura hannun sa saman kan ta zuciyarsa cike fal da tausayin ta, so yake yi yararrashe ta amma ko kaɗan yakasa buɗe baki, be san da wani kalma zai fara ba, ita kuwa sake tusa kanta take yi cikin kuka da ba'a jin muryan ta sosai tace
"Yaya.. Yaya ya cuce Ni, ya cuce ni Yaya ya gama da rayuwata, ya raba ni da martaba na na ɗiya mace, yaya ya gama dani wlh ya gama dani, wayyo Allana nashiga uku na lalace".
Kuka tasake kecewa dashi tana buga kanta saman ƙafafunsa, dasauri yariƙe ta yana tallabo fuskarta yace
"Ki dena kuka Halwa, kidena kuka dan Allah, kukan ki na taɓa min zuciyata, dan Allah kiyi shiru kitashi mutafi kinji".
Girgiza kan ta tasoma yi cikin kuka tace
"Yaya ina zani? Ina zani da wannan abun kunyan? Ina kake so naje yaya? Dan Allah yaya katafi kabar ni anan, katafi kabar ni zan kashe kaina ne, bani da sauran wani farin ciki cikin rayuwan nan, wlh Yaya mutuwa zanyi, zuciyata zata buga, dan Allah yaya kakashe ni nahuta.."
Saurin ɗaura hannun sa saman bakin ta yayi yana kallon ta yace
"Ki nutsu Halwa dan Allah, kinsan me kike faɗa kuwa? Ni Yayan ki ne kuma zan rufa miki asiri, babu wanda zai sani wlh har Mama, nayi miki alƙawari kuma zan aure ki, nasan abinda kike tunani kenan, Halwa babu wanda zai ji kitashi mutafi gida dan Allah".
Daƙyar yalallaɓa ta tamiƙe, yana riƙe da ita suka fito palow da babu kowa ciki, ɗaukan mata takalmanta yayi yace "tasanya" babu musu tasaka har lokacin hawaye take zubar wa, fitowa suka yi cikin gidan, wajajen babu wasu gidaje da yawa, don haka sai da sukayi tafiya sosai sannan suka kawo bakin titi, Halwa bata iya tafiya sai da taimakon Nura, gaba ɗaya ajikin sa take ya rungume ta ahaka suke tafiya, basu jima da tsayuwa ba suka sami napep suka hau, a ƙofar gida yasauke su suka fito suka shiga gidan, a cikin zaure Nura yadakata yana kallon ta yace
"Dan Allah kidena kukan nan karki sa Mama tafahimci wani abu daga gare ki, bansan me zance mata ba".
Gyaɗa kanta tayi tana saka hannu tasoma share hawayen ta, still kuma wasu na tsiyayowa, Nura yasoma shiga yaleƙa yaji shiru, sai yadawo yariƙo ta suka nufi ɗakinta, a saman katifan ta yazaunar da ita sannan yafita, sai da yataɓa ɗakin Mama yaji shi a kulle, ashe be kula bane labule tasaki takulle ɗakin, koda yatura yaga ƙofan ya buɗe, sai da yaleƙa ko ina yatabbatar babu ita sannan yadawo cikin ɗakin Halwa, tana nan kwance sai kuka take yi, ƙarisowa yayi kusa da ita yakira sunan ta, shiru tayi bata amsa ba
"Kitashi kigyara jikin ki Mama bata nan, Halwa karki sake Mama tafahimci akwai wata matsala atare dake kinji ni ko?"
Kuka tasake fashewa dashi tana ɗaura hannun ta saman fuskarta
"Wai don Allah kukan na menene? Inace duk dan ni kike yi kuma nace zan rufa miki asiri zan aure ki".
Buɗe idanunta tayi tana kallon shi, sai kuma tarufe idanun taci gaba da kukan ta, sam bazai gane me take ji cikin zuciyarta ba, amma tasan da cewa komi nata ya ƙare, Haris ya gama cutar ta har abada, bazata taɓa yafe mishi ba".
Miƙewa yayi yana kallon ta yace
"Ni zan fita, kidena kukan nan haka dan Allah, ki saka ma zuciyar ki salama Allah zai saka miki, kinsan baza mu iya faɗa dashi ba ya riga da yafi ƙarfin mu, kibar sa da Allah kinji My Halwa?"
Zuciyarta ne tayi mata sanyi, shiru tayi tana sake lafewa saman katifan sai ajiyan zuciya take yi
"Yauwa my dear dan Allah karki bari Mama tafahimci kinyi kuka bare tasan wani abu na damunki, yanzu bari in fita yanzu zan dawo kinji?"
Gyaɗa masa kai kawai tayi, shi kuma yafice, ahankali taci gaba da kukan ta, tasan da cewa sosai tayi dacen Yaya, wanene zai iya auren ta da wannan tabon cikin rayuwanta? Amma gashi Yayan ta mafi soyuwa cikin ran ta ya amince zai aure ta bayan yasan abun da yasame ta, tabbas yayan ta ya cika masoyin gaskiya, da ko wani namiji zai fahimci cewa ko wace Yarinya da hakan yasame ta ƙaddara ce Allah yarubuto mata, su gane cewa auren ta babban jihadi ne kuma sadaukarwa ne, da mata da yawa da suke kukan baƙin ciki sun dena.
Ji tayi ƙaunar yayan nata na sake ninkuwa cikin ranta
"Allah Sarki Yayana, tabbas kai me ƙaunata ne da bansan ya zanyi ba, wani miji zan aura da zai iya zama dani ahaka? Nagode Yayana ina matuƙar ƙaunar ka, Nagode Nagode sosai da karufa min asiri".
Tafaɗa maganar afili tana sakin murmushi kamar yayan nata na ganin ta, sai kuma can tafashe da kuka tana cewa
"Allah ya isana mugu azzalumi, bazan taɓa yafe maka ba, insha Allah sai anyi ma yaranka kaima abun da kayi min, mugu azzalumi kawai".
"Ke da wanene haka kike ta ja mishi Allah ya isa?"
.
_Toooo 🤔 me zai faru?_
_kuna ganin asirin ta zai rufu kuwa?._ [9/6/2020, 7:14 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📚* ```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 15*
"Ke da wanene haka kike ta ja mishi Allah ya isa?" Cewar Mama tana bankaɗo labulen
Dasauri taɗaura hannu a saman fuskarta, cikin ruɗewa tace
"Ahm Ma.. Babu kowa".
"Ya zakice min babu kowa bayan naji da kunnina kina mishi Allah ya'isa, tukunna ma me yayi miki da za'ayi ma yaran shi?"
"Mama wani ne fa yakusa yabige ni, shine sai ƙunduma min zagi yake yi, shine fa abun yanzu yake damuna".
Guntun tsaki Mama taja tana sakin labulen tace
"Shine ke kuma tunda baki da haƙuri zakizo kina taja mishi Allah ya isa? Allah yashirya ki Halwa, nima da naji ku shiru ne nafice abuna".
Ɗaki Maman tashige tana ci gaba da surutun ta, yayinda Halwa kuma gyara kwanciyan ta tayi tana sauke ajiyan zuciya cike da fargaba, rufe idanuwanta tayi tana jin wani kukan na sake zuwan mata tuna abun da yafaru da ita yau, wani irin ƙunci da baƙin ciki ne suka tokare mata wuya, take tafashe da kuka tana toshe bakin ta
"Shikenan yau an raba ta da abu mafi daraja ajikinta, wai yau ita ce wannan ƙaddara yasame ta, abinda ko a mafarki bata taɓa tunanin wannan ɓakin ranan zai zo mata ba, ya zatayi da rayuwan ta? Ji take yi kamar takashe kanta duk sanda tatuna yau wani namiji yasanta a ɗiya mace batare da aure ba
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Abinda take ta maimaita wa kenan har tasoma jin zuciyarta na mata sanyi.
.
**** **** **** ****
*WASHE GARI* *EGYPT*
Zaune yake saman Three sitter ya harɗe ƙafafunsa yana danna Lapton ɗin sa, takardu ne birjik agaban sa sai faman aiki yake yi, yana sanye cikin fararen kaya masu taushi sosai, wandon Three qweater ne sai Rigan me kamar singlate
Tun jiya da yasauka a ƙasan yake faman aiki babu ƙauƙautawa, bincike sosai yake akan mutumin da yazo don shi amma har yanzu yagaza samun koda bayani ɗaya akan sa, sosai yake cikin damuwa ko lokacin kansa baya dashi, yanzun ma aikin yake yi but tunanin sa na wani wajen daban, wayan sa da tasoma ringing yayi saurin ɗauka domin dama abinda yake jira kenan
"Hellow Poker.."
"Ok.. ok turo min da address ɗin wajen".
Cire wayan yayi a kunne yariƙe a hannu yana kallon screan ɗin wayan, 1mint sai yaji Message ya shigo, dasauri yabuɗe yaduba sannan yatashi, cikin sauri yasauya kayan sa cikin farar riga me gajeren hannu da blue jeans, sai yaɗaura jaket saman rigan baƙi ne me belt a wajen cikin sa, jaket ɗin me hula ne sai dai be sanya hulan ba iyakan yasaka Combat a ƙafan sa Black, yaɗau wayoyin sa yazuba a aljihu yafito yarufe ɗakin, kasancewar a Hotel ne ɗakin sa yana hawa na uku ne, cikin sauri_sauri yake taka step ɗin har yasauko ƙasa, yana fita yatari taksi yashige suka tafi, a wani haɗaɗɗen club aka sauke sa yafito yabiya me taksi ɗin kuɗin sa kana yamatsa gefe kaɗan yana ƙare ma wajen kallo, tsawon mintuna 5 yaɗauka awajen kafin yajanyo hulan Jaket ɗin ya'aza akan shi yasoma takawa yashige wurin, sosai ciki yake da duhu, mutane ne birjik ciki kowa na sha'anin gaban sa, ba abinda ke tashi aciki sai daddaɗan cool music da aka sanya wasu sai cashewa suke yi, yana shigowa kallon wajen kawai yake yi har ya'isa wani hill chair yazauna yana kallon mutane, tsawon mintoci yana zaune a wajen yana nazarin inda zai ga mutumin da yazo nema, sai kawai yayanke shawaran nufan wasu matasa maza da mata dake zaune gefe can saman wasu haɗaɗɗun kujeru sai kurɓa alcohol suke yi, wata matashiyar budurwa ce taƙariso kusa dashi hannun ta riƙe da cup, kallo ɗaya zaka yi mata kagane irin waɗannan gogaggun karuwan nan ne, skin ɗin ta baƙi ne but ko kaɗan batayi yanayi da ƴan Nigeria ba coz yanayin shiganta da wayewan ta
"Hi". Tace dashi lokacin da ta'isa gaban shi
Kallon ta yayi sai yaɗauke kan sa dasauri batare da ya amsa mata ba, murmushi tayi tace
"Kana son wani abu ne? Naga tun ɗazu kazo kazauna anan kamar kana neman wani ko?"
Gyaɗa mata kai kawai yayi batare da yasake kallon ta ba
"Ok ko zan iya taimaka maka?" Tafaɗi maganar tana kurɓan Juice ɗin dake hannun ta
Shiru yayi kamar bazai ce komi ba sai kuma yace
"Ina son ganin Mr. Jay pitter ne, me wajen nan, ance min in nazo nan zan same shi".
Murmushi tayi tana gyara gashinta takalle shi dakyau, sai kuma tagirgiza kan ta tana jawo kujera tazauna taci gaba da shan Juice ɗin ta, shiru ne yagibta a tsakanin su har Khalil yana shirin tashi sai yaji muryan ta ya doki kunnin sa
"Meyasaka kake neman sa?"
Ɗan kallon ta yayi sai yakau da kai be ce komi ba, ƙure shi da ido tayi tana wani irin murmushi tace
"Daga Nigeria kake ko? Nima acan nake ai".
Taƙarike maganar tana kau da kan ta taci gaba da sipping juice ɗin ta kamar ba itace tayi maganar ba, shi kam kallon ta yake kamar me neman wani abu jikinta, mamaki ne kwance acikin ran sa domin ko kaɗan batayi kama da zubin ƴan Nigeria ba, musamman ma da yaga tana mishi turancin kamar tana wani yare, sam ba wani fahimta yake ba, murmushi tasake yi wannan karon da Hausa tayi maganar tace
"Kana mamaki ko? Uhmmm kadena mamaki sabida ni da kake ganina cikakkiyar Bahaushiya ce ƴar Nigeria, Nigrian ma a Kano, sunana Fadila kuma musulma ce ni, but anan ana kira na da baby Dil".
Ɗago kai yayi sosai yana kallon ta da tsantsan mamaki a face ɗin sa wannan karon, but yaƙi furta komi
"Kafaɗa min meyasaka kakeson ganin Mr. Jay pitter?"
"Meyasa kikeson nafaɗamiki?" Yayi maganar yana kau da kai kanta
"Sabida zan taimaka maka, bazaka taɓa samun shi anan ba, koda zaka kwana kana sintiri ne, wahala kawai zakayi, but Ni kuma zan iya taimaka maka in kaika inda yake".
Khalil yace "Please kitaimaka min ina son ganin shine sabida wani bincike da nakeson yi".
Dariya tasaki tana kallon shi cike da sha'awa tace
"Sau da yawa ina ganin irinka suna zuwa nan don neman sa, kuma tun sanda naganka nagane kai ɗan Nigeria ne kuma nasan abinda yakawo ka har kake neman sa".
Da mamaki Khalil yakalle ta yace
"Taya kika sani".
Sai da tashanye sauran Juice ɗin ta'ajiye cup ɗin sannan takalle shi tace
"Idan har kana son taimakona to mubar nan wajen, Ni kuma zan faɗamaka duk abinda kakeso kasani, har da wanda ma bakaso".
Shiru yayi yana nazari kafin yace
"Ok muje to".
Tashi tayi takalle sa tana kashe mishi idanu, tamatso kusa dashi kaɗan ahankali tace
"Kabari in nafita sai kabiyo bayana".
Hakan ko akayi, sai da tafice kafin yabiyo bayan ta, daga can nesa yahango ta tsaye tana ware hannayen ta tana yarfe su, wajen ta yanufa yana kallon ta, bata bari yayi magana ba tace
"Kasamar mana taksi mubar nan".
Sai kuma tasakar masa murmushi tace
"Ko muje musaukin ka".
Wani irin kallo yayi mata, sai tawaro idanu still tana murmusawa tace
"nan zai fi sirri, coz za'a iya samun matsala ne".
Jimm yayi kana yace
"Ok"
Daga nan yatare musu taksi suka shiga suka tafi. [9/10/2020, 11:42 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📚* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 16*
Lokacin da suka isa cikin ɗakin sa na Hotel ɗin Baby Dil akan sofa tayi wa kan ta matsuguni, taɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya tajingina bayan ta da kujeran tana kallon shi, shi kuma Direct cikin Toilet yashige, be jima ba yafito yanemi wuri kan kujera yazauna kana yace da ita
"Ina jinki, Please ina son nasan komi ga mutumin nan".
Ɗan sakin murmushi tayi still tana kallon shi tace
"Ni kuma zan sanar da kai komi insha Allahu, katambaye ni duk abinda kakeso".
Gyaɗa mata kai yayi kafin yagyara zaman sa yace
"Akwai wani Alhaji Mubarak da muke Shari'a dashi acan Nigeria, kuma tabbas an tabbatar min da Mr. Jay pitter abokin harƙallan shi ne, don haka nazo bincike kuma ina son nahaɗu dashi".
Baby Dil tace "tabbas da ka isa wajen shi babu abinda zaka samu, domin Alhaji Mubarak na hannun daman sa ne, kaga kuwa babu abinda zaka samu a wurin sa illa ma kasake jagula abin, kamar yanda nace maka xan sanar da kai komi sabida nasan sirrin su ne, a baya mutane irinka sun zo kamar kai don bincike, wasu ƴan sanda ne wasu kuma lauyoyi ne, but kai bansan menene aikin ka ba?"
"BARRISTER". Yafaɗa ataƙaice
"Ok Amma tun sanda naganka naji zuciyata ta kwanta da kai sosai shiyasa nazo wajen ka bcoz nima ina buƙatar taimakon ka".
Shiru tayi tana sauke numfashi, sai kuma tasauke ƙafan ta tahaɗe hannayen ta waje ɗaya tana kallon shi, sannan taci gaba da faɗin
"Zan soma da baka tarihina duk da baka tambaye ni ba but nasan duk abinda kake nema yana da alaƙa da abinda akai min, shekaru 7 kenan da zuwata wannan ƙasan, ko ince aka sai dani a wannan ƙasan, zaka yi mamaki idan nace maka ta sanadiyan maƙocin mu nazo wannan ƙasa, mun kasance mu talakawa ne don haka maƙocin mu yake taimaka mana kasancewar sa me kuɗi, haka kawai watarana yace inxo zai sama mana aiki awani gida, dama abinda muke nema kenan musami aikin da zamu dogara dashi ni da iyayena, kwana biyu da soma zuwana, uban gidan mu yakai ni wani gida, ni dai ban fahimci ko ina ne ba amma akawai ƴan mata irina da yawa don mun kai mu sha biyu, muna ji muna gani akai mana allura wanda bamu fahimci na menene ba, tun daga lokacin hankalin mu yagushe, ashe makocin mu ne yasiyar dani ga mutumin da yasamar min aiki gidan sa, shima kuma yasiyar dani ga wani uban gidan sa".
Shiru tayi tatsira ma waje ɗaya idanu taci gaba da faɗin
"Wannan alluran da akai mana yagusar mana da hankali, anyi haka ne don su cin ma manifan su akan mu, suna harƙallan sai da coken that's why suke samun ƴan mata sufarka cikin su azuba musu coken ɗin nan aciki, alluran da ake yi yana da ƙa'ida, yana ɗaukan iya awannin da zai kai mu ƙasan da za'a kai mu ne, don haka lokacin da akai mana hankalin mu gushewa yayi bamu sake sanin inda muke ba sai a wannan ƙasar, sun kawo mu nan an kuma mana aiki an cire mana coken ɗin, sai dai basu bar mu haka ba suka sai damu ga Mr. Jay pitter, mutum ne shi da yake safaran ƴan mata ƙasa-ƙasa wasu kuma yamai dasu karuwan sa don samun kuɗi dasu, acikin waɗanda muka taho tare gaba ɗaya yasiyar dasu a wasu ƙasashe sai ni da wata yabar mu a matsayin karuwan sa, tun sanda natsinci kaina a wannan ƙasa nake kuka ina roƙon su da sumai dani ƙasata, sai dai aikin gama yariga da yagama su mutane ne da basu tsoron Allah, daga farko da sukaga ina musu taurin kai har nayi yunƙurin guduwa haka sukai ta gana min azaba, but duk da haka ban sa ran wataran zan ƙi guduwa ba, sai dai duk wani hanya da yakasance zan bar ƙasar nan sun toshe ta, ataƙaice dai zan faɗa maka babu yanda za'a yi nabar ƙasan nan batare da sanin su ba, haka nahaƙura naci gaba da zama dasu nima har lokacin da nasaba, nima nadawo nagoge azahiri namanta da komawa ta gida, sai dai abaɗini abin na nan araina, aduk sanda natuna da iyayena sai nayi kukan baƙin ciki, ina tunanin awani hali suke na rashina, shiyasaka har yanzu ban fid da raina zan koma ba".
Muryan ta da yasoma rawa ne yasaka ta yin shiru, sai da tashare hawayen fuskarta kafin taci gaba
"Shi kuma Alhaji Mubarak tare suke harƙalla da Mr. Jay Pitter, yana kawo masa ƴan mata sosai, duk wani aikin da Mr. Jay yake yi tare suke yi dashi, nasan shi sosai domin yana yawan zuwa nan ɗin, kuma insha Allahu duk wani sirrin su zan iya nemo maka inhar kayi alƙawarin zaka mayar dani ƙasata, ina son nakoma gun iyayena, kataimake ni don Allah, sosai naji zuciyata ta aminta da kai". Taƙarike maganar tana fashewa da kuka
Brr. Khalil kallon ta kawai yake yi cike da tausayin ta, sosai tabashi tausayi kuma yana ji aran sa insha Allahu sai ya taimaka mata, dama wannan daman yake nema wanda zai kawo ƙarshen masu safaran mata, koda iyakan Alhaji Mubarak da mutanen sa yakawar tabbas yasan ba ƙaramin Jihadi yayi ba, ko ba komi za'a rage yawaitan mugaye irin su, ajiyan zuciya yasauke yana tuno Nazeefa
"Yanzu shikenan da itama nan za'a kawo ta? Yarinya ƙarama, kai amma waɗannan mutanen basu da imani, Allah kaɗai yasan iya adadin yaran da suka kawo waɗanda ma basu kai ta ba".
Numfashi yaɗan ja yana kallon ta yace
"Kiyi shiru Fadila, insha Allahu zan taimaka miki kibar wannan ƙasan, zaki koma ga iyayen ki in Allah ya yarda nayi miki alƙawari".
Kallon shi tayi da idanuwanta da sukai jazur tayi masa murmushi tace
"Nagode sosai".
"Babu godiya tsakani na dake, ke dai ki aiwatar da duk abinda zan saka ki".
Daga nan yasoma bata bayanai akan abinda yakamata tayi masa, sun daɗe suna tattaunawa kafin tatafi, shi kuma tashi yayi yashige toilet yayo wanka tare da ɗauro alwala yafito, shirya wa yayi cikin farar jallabiya da dogon wandon jeans yashimfiɗa sallaya yayi sallah, sannan yamiƙe yaɗau tellphone ɗin dake ɗakin yakira Receptionist yayi odan abinci, yana zama babu jimawa akayi nocking door ɗin yaje yabuɗe ya'amso yadawo yazauna yasoma ci, abincin yake ci sai dai hankalin sa baya wajen yana nazari, wayan sa dake saman gado tasoma ringing hakan yasaka yaɗan kalli wajen kafin yasauke ajiyan zuciya, yamiƙe yanufi inda wayan take yaɗauka, ganin Bro ɗin sa ne babu ɓata lokaci yayi peacking call ɗin yana zama
"Hello My Bro".
"Hi ɗan ƙanina ya kake?"
Ɓata fuska Khalil yayi yana shafa goshin sa yace
"Bro bana so".
Dariya Sameer yayi yace
"Sabida me um ɗan ƙanina?"
Shiru yayi yaƙi magana
Still dariya Sameer yasake yi yace