Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 6
Barrister ibrahim khalil complete Chapter 6: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 6. "I'm sorry dama tsokanan ka nake, ai yanzu kai big boy ne tunda…
4,481 words
"I'm sorry dama tsokanan ka nake, ai yanzu kai big boy ne tunda kafara aje yara, kasan fa Hakima ta haihu".
"Dagaske Bro? Yaushe? Me tahaifa?" Yayi masa tambayoyin ajere yana miƙewa yakoma wajen abincin sa
"Yanzu babu daɗewa, ai nayi tunanin Mom tariga ni sanar maka, namiji tahaifa".
"A'a tun safe da mukai waya bamu sake ba, Allah yaraya shi Yaya, ina fata ni za'a yi wa takwara ko?"
Sameer yace "tabb kai awa?"
"Ni a Dadyn sa, Please Bro kasan munyi alƙawari dani da kai, duk wanda yahaihu cikin mu zamuyi ma junan mu takwara".
"A'a to ai bance maka na fari ba, ni Dad zan ma takwara sai dai kabari tasake haihuwa lokacin ma kayi naka auren, kaga sai su tashi tare ko?"
Ajiyan zuciya Khalil yayi yace
"Dama haka zakace ai, kafison Dad dani, shikenan sai kayi ta sakawa".
Dariya Sameer yasaki jin yanda Khalil ɗin yayi maganan cike da shagwaɓa, cikin dariyan yace
"Haba autan Mom Kar kayi fushi tunda nace zan saka, kuma kasan da cewa ni dama na wurin Dad ne, dole na fifita shi akan ka, amma fa ina son ka sosai fa, daga shi sai kai a zuciyata".
Murmushi Khalil yayi yace
"Uhmm naƙi daɗin bakin, ai dama Mom ta sanar dani kuma yanzu na yarda, yanzu ni dai kagaishe min da me jegon da kyau da kyau tare da My Son".
"Ok zasu ji, ya aikin naka? Dafatan komi yana tafiya normal?"
"Alhamdulillah Yaya, Ina samun duk abinda naje nema".
"To Allah yataimaka yabaka Sa'a".
"Ameen Bro, katura min photon Baby ta WhatsApp in ganshi".
Sameer yace "ok yanzu kuwa".
Daga nan sallama suka yi, yaci gaba da cin abincin sa yana latsa wayan sa. [9/12/2020, 1:32 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 17*
*WASHE GARI* *NIGERIA*
Da sallaman ta tashigo gidan, Mama dake zaune tana gyaran lagwani ta'amsa mata tare da faɗin
"A'a maraba da Zainaba"
"Mama ina wuni?"
"Lafiya lau, ya Umman taki?"
"Tana lafiya, tace in gaishe ki".
"Ina amsawa, ya wajen su Zaituna, ina fata kina leƙata?".
Murmushi Zainab tayi tace
"Eh Mama ina zuwa sosai".
"To madallah haka akeso, kishiga ƙawar taki na ciki ai, bata jindaɗi ne".
"Eyya Allah yasawaƙe, ai bani da labari".
Mama tace "ameen, ai zazzaɓi ne kuma jiya da dare ne ma jikin yamatsanta mata".
Cike da tausayin ƙawartan tasake cewa
"Mama Allah yasawaƙe bari in shiga wajen ta".
"Ameen Zainab".
Zainab na shiga taga Halwa saman gado ta kwanta tajuya ma ƙofa baya, ƙarisawa tayi kusa da ita tazauna a gefen katifan tana faɗin
"Halwa ya jikin naki?"
Halwa da tarufe idanunta batare da tamotsa ba tace
"Dasauƙi".
"Allah yabaki lafiya, shine kuma baki kiran awaya kin sanar dani ba? Yanzu da ba don naji Umma tana maganan saka ranan ki jiya ba shikenan bazaki faɗa min ba? Abin yaban mamaki ai ince kina cikin wannan farin ciki nasan da tuni kin garzayo kin fesa min".
Duk wannan surutun da Zainab take yi Halwa taƙi cewa komi illa jinta da take yi, hannu Zainab ɗin tasaka tataɓa wuyan Halwan tana cewa
"Wai jikin yayi tsanani ne haka da bazaki tashi muyi magana ba?"
Ahankali Halwa tabuɗe idanunta tatashi zaune tana kallon Zainab ɗin, cikin kasala tace
"Wani magana zamuyi?"
Zainab kallon yanda duk tayi wani yaushi idanuwanta sukayi luhu-luhu suka yi ja tayi tace
"Ƙawata me ke damunki ne? Kinga yanda kika koma? Ke da ciwo baya hana ki walwalan ki amma yanzu duk kin wani iri kamar kin daɗe kina ciwo?"
Ɗan dafa kan ta Halwa tayi tace
"Zazzaɓi ne kawai".
"To Allah yasawaƙe".
"Amin" Halwa tafaɗa tana komawa takwanta
"Banji daɗi ba ƙawata da baki da lafiya, sai da lokacin farin cikin ki yazo sai kuma gashi ciwo na son hanaki walwalan ki".
"Inji wa yace miki bana farin ciki?" Cewar Halwan tana ƙirkiro murmushi
"Hmm kowa yagan ki yasan da cewa sosai kina jin jiki Halwa, ciwon kwana ɗaya ya maidake haka, nasan da cewa da bakya jin jiki tabbas bazaki kwanta haka ba, ƙafan ki babu inda bazai zagaya wajen sanar da cewa an sanya miki ranan aure ba".
Halwa hararanta tayi tace
"Tunda an ce miki bani da kunya ko?"
Dariya Zainab tayi tace
"Anan kam ai nasan baki da kunya, zakiyi abinda yafi hakan ma".
"Ke dai kika sani". Halwa tace hakan tana ɗaura hannu asaman goshinta
"Yauwa ya maganar Assignment ɗin nan na Malam Isma'il? Kinsan yace "shine Test ɗin mu, kuma wlh na duba nawa bangani ba, ara min naki in kwafe Questions ɗin"
"Kiduba jaka na kiɗauka nima banyi ba, kije dashi kiyimin don Allah".
Miƙewa Zainab tayi tana faɗin
"Ok ba damuwa".
Inda take rataye School bag ɗin tanufa taciro, taduba littafin taɗauko tadawo tazauna tace
"Ni zan tafi gida Umma na can tana jirana zataje anguwa, amma goben zakije school ɗin? Don naga jikinki ya matsanta miki"
"Zani".
"Tom sai muhaɗe acan kenan, ina Yaya Nura? gashi zan tafi ban mishi Allah yasanya alkhairi ba".
Halwa tace "ki neme sa a waya mana, ko kin ban ajiyar sa?".
"To ai naga kece Gimbiyar tasa wataƙil kinsan inda yake, kinga ni ba jan magana zan yi ba na tafi".
Fita Zainab tayi tayima Mama sallama tatafi.
***** ***** ******
Kwance take saman gadonta ta ɗaura hannayen ta saman fuskarta, babu abinda take tunani sai Khalil, tun sanda yakawo ta gidan nan har tafiyan shi takasa samun sukuni, kullum dashi take kwana kuma dashi take tashi, tarasa meyasaka tunanin sa yake damunta kullum, kuma ta kasa gane takamaiman abinda take ji acikin ranta game dashi, tsananin kewar sa ne yake damunta ako da yaushe, burin ta kawai yanzu tasanya shi a idanunta ko ta sami sauƙin zuciyarta, ahankali tamiƙe zaune tana ƙura ma waje ɗaya idanu, can tasaki ajiyan zuciya tatashi tsaye tasanya room slippers tanufi ƙofa, tafiya take yi ahankali tana saukowa daga upstairs, tun sanda takusa saukowa tahango Mom zaune a parlour tana waya, har takusa isa kuma sai tajuya da ninyan komawa Mom takira ta
"Ina zakije kuma Nazeefa? Zo ga yayan ki kugaisa".
Jiki a sanyaye tajuyo tazo wajen Mom tana jin zuciyarta cike da farin ciki, amsan wayan tayi bayan da tazauna takara a kunne tana faɗin
"Hello Yaya".
"Nazeefa". Yakira sunan ahankali cike da salo
Hakan yasaka Nazeefa lumshe idanuwanta cikin jindaɗin muryan sa da yaratsa mata har cikin kwanya tace
"Ina wuni Yaya".
"Lafiya lau, ya jikin ki? Dafatan kina shan maganin ki akan ƙa'ida?".
Gyaɗa masa kai tayi kamar yana kallon ta, sai kuma tace
"Eh ina sha".
"Ok kici gaba da kulawa".
Shiru ne yagibta, hakan yasaka Nazeefa taɗan saci kallon Mom taga hankalinta na kan t.v, sai tace
"Yaya yaushe zaka dawo?"
Shi da har yai tunanin ko ta ba Mom ne still yaji muryan ta tana tambayan shi
"Kina so in dawo ne? Yatambaye ta cike da kulawa
"Eh Yaya nayi kewarka ne sosai". Tafaɗi maganar ahankali, don ita kanta batasan sanda tafaɗa ba, umarnin zuciyarta kawai tabi
Shi kam Khalil jin maganar yayi wani iri a zuciyar sa, sai kuma yashare tunanin da yakawo mishi rai yace
"Very soon zaki ganni, miƙa ma Mom wayan".
Ba musu tacire wayan a kunni tamiƙa ma Mom, waya suka ci gaba da yi ita kuma Nazeefa tana zaune tana sauraron su, duk da bata jin muryan Khalil ɗin but sai sakin murmushi take yi kamar an mata bushara, tunanin ta kawai yatafi wajen tuno kyakykyawar fuskar sa ne, tana jin wani iri sosai a game dashi musamman ma duk sanda zasu haɗa idanu sai taji gaban ta ya faɗi, ko kuma da zaran ta gan shi hakan ke faruwa da ita, sai dai ita batasan menene ba bare tace ga matsayin abinda take ji, sai dai tasan shi ɗin wani haske ne a rayuwanta, me haskaka mata duk wani baƙin duhun dake cikin rayuwanta, kuma Mai Taimakon rayuwanta.
_Shin zaku iya faɗamata abinda ke damunta Fan's? Don nasan kun sani ai._
~Khalil-Billy~ ~Khalil-Lubna~ ~Khalil-Nazeefa~
_Muje zuwa Fan's_
_karku manta ku suburɓuro comments fa._ [9/15/2020, 11:32 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
~Khalil-Billy~ ~Khalil-Lubna~ ~Khalil-Nazeefa~
.
*CHAPTER 18*
*TOMORROW* *MONDAY MORNING*
Halwa ce tsaye cikin ɗakin ta tana riƙe da Hijab ahannu, kayan makaranta ne ajikin ta da tagama sakawa, tanufi wajen jakan ta dake rataye taciro tasaƙala shi a kafaɗa sannan tasanya Hijab ɗin tafito waje, leƙa ɗakin Mama tayi dake zaune tana cin tuwo tace
"Mama ni na tafi sai na dawo".
"To uban wa kika bar ma abin karyawan naki?"
Yamutsa fuska tayi da yazame mata jiki tace
"Mama ni nayi latti banda lokacin cin abinci".
Harara Mama tawurgo mata tace
"Tunda an faɗi maƙiyin ki ai dole kice kinyi latti, kizo kizauna kici tun kafin in saɓa miki, ayi mutum sam baya son cin abinci? Rayuwan zata yiwun miki ahaka ne? Nura dai zai yi aiki wlh".
Buga ƙafa Halwa tayi cike da shagwaɓa tace
"Ni wlh Mama bazan iya cin tuwon nan ba, ki ƙyale ni kawai natafi".
"Wlh kuwa in bakizo kinci ba sai dai kifasa zuwa makarantan nan, shegiyar yarinya me taurin kai".
Fuska a kumbure Halwa tashiga cikin ɗakin tawafci kwanon tuwon dake ajiye agefe zata fita
"Dan ubanki dawo nan, zauna kici anan don nasan in dai kika fita sai dai kizubar".
Babu musu takoma tazauna, sai dai gaba ɗaya in kakalli fuskarta zaka gane ranta aɓace yake, haka tatsulma hannu tasoma kai abincin baki tana yamutsa fuska kamar tana cin kashi, Mama kam bata ƙara bi takanta ba taci gaba da cin tuwon ta duk tana ankare da ita, ganin tana yunƙurin yin mata amai a ɗaki ne tace
"Wlh Halwa idan har kikai min amai a ɗaki sai na mugun saɓa miki".
Gyaran murya Baba dake bakin ƙofa yayi yace
"Wai menene haka kika tasa yarinya gaba kina ta mata faɗa?"
"Kaima kasan halinta tunda an haɗa ta da abokin gaban ta, makaranta zata tafi bataci komi ba".
Murmushi Baba yayi yace
"Kiriƙa lallaɓa ta mana Hauwa, kinji tashi kije ɗakina akwai raguwan ƙosai da narage kiɗauka kitafi dashi".
Miƙewa tayi kamar zatayi kuka ta cika bakinta da tuwo amma takasa haɗiye wa
"Ungo nan riƙe wannan kiƙara ki sayi wani abun kici".
Amsan kuɗin tayi tafice dasauri, ɗakin Baban tashiga taɗauko ƙosan tafito, sai da tazubar da tuwon dake bakin ta tukunna takuskure bakin tafice dasauri, akan hanya suka haɗu da Zainab
"Ai da naji shiru baki biyo min ba nace bari in zo in duba Madam ɗin nan lafiya?" Cewar Zainab kenan
Yamutsa fuska Halwa tayi tace
"Ƙalau, Mama tatare ni dole sai na karya sannan zan fita".
Dariya Zainab tayi tace
"Ke dai har yanzu bazaki dena wannan halin naki ba sai kace ƙaramar yarinya, kullum sai kin saka Mama ta ɗaga murya akan cin abinci, Allah yakyauta miki, Yaya Nura dai zai yi aiki wlh".
"Uhm itama haka tagama cewa, ko wani aiki zai yi oho?"
Zainab tace "ai da gaskiyar Mama, kullum wajen cin abinci zai yi fama dake".
Taɓe baki kawai Halwa tayi bata sake cewa komi ba, ita kuma Zainab sai mata hira take har suka kai bakin titi suka tari abin hawa
Bayan sun kai suka sauka Halwa taciro Hamsin tamiƙa, ita kuma Zainab tajuya da ninyan tafiya Halwa tariƙo ta tana faɗin
"To uwar son banza ai ban bada da naki ba, sai ki biya sa".
Kuɗin taciro cikin jaka tamiƙa mishi suka juya suka tafi
Zainab tace "wlh ke ƴar wulaƙanci ne Halwa, nima zan rama".
Dariya Halwa tayi tana waro idanu tace
"me nayi miki kuma? Don kawai nace kibada kuɗi?".
"Oho ke kika sani". Cewar Zainab
Still dariya Halwa tayi tace
"Kiyi haƙuri to, wlh banda kuɗi ne yau, nasan kuɗin da nake dashi bazai ishe ni har nabiya miki ba, coz akwai abinda nake so nasiya dashi".
Zainab tace "uhmm naji, but kinsan da muka zo nan sai natuna da Haris? Wlh sai naji gabana na faɗi sabida abinda kikai mishi ranan Wednesday kullum mukazo nan sai na tuna, I know zai zo yarama".
Jin sunan Haris da Halwa tayi ba ƙaramin bugawa zuciyar ta tayi ba, tsoro da fargaba suka zo suka dirar mata alokaci ɗaya, nan da nan annurin fuskarta yaɓace ɓat, ɗan sauran kuzarin da take ji shima yaɓace ɓat, take tasoma jin kamar wani sabon zazzaɓi ne zai rufe ta, Zainab sai magana take mata but ko kaɗan takasa furta komi har suka shige makarantan, koda suka shiga cikin class ɗin su tunda Halwa tazauna bata sake magana ba, Zainab da tatambaye ta ce mata tayi "kanta ke mata ciwo, da alamu zazzaɓin ne ke son dawo mata", don haka Zainab ɗin bata wani matsa mata ba taƙyale ta, a ranan haka ta wuni duk bata da walwala, sai gab da za'a tashi ne wani Malami yayi musu Test sannan aka tashe su.
Lokacin da suka dawo gida, suna zuwa ƙofar gidan su Zainab, Zainab ɗin tace mata
"To ƙawata sai gobe kenan".
Gyaɗa mata kai kawai Halwa tayi tawuce gida, akan dakalin ƙofar gidan su tahangi Nura zaune shi kaɗai, ƙarisawa tayi tasami waje kusa dashi tazauna tana kallon shi tace
"Yaya har kadawo aikin yau?"
Ɗago kan sa yayi dasauri don da alamun be san da zuwan ta wajen ba sai maganarta da yaji, yace
"Uhm kin dawo? ai banji zuwan ki ba".
Murmushi tayi masa tace
"Tunanin me kake yi to?"
Ɗage kafaɗa yayi yace
"Tunanin wajen aiki mana".
Still murmushi tayi tace
"Menene abin tunani to? Ada da baka samu ba kana tunani, yanzu kuma kasamun ma baza kabar zuciyarka tahuta ba?"
Murmusawa yayi yace
"Bazaki gane bane Dear, amma dai yanzu share wannan batun, kinga kin dawo kinsha hanya kishiga gida".
"To kai kuma fa?" Tatambaye sa tana ƙure sa da ido
Ɗan kawar da kan sa yayi yabata amsa
"Ba yanzu ba, ni yanzu ma wajen Ali zani".
"Ok.. sai kadawo". Tafaɗa tana wuce wa tashige gida batare da tajira amsan shi ba
Shi kuma kallon bayan ta yayi har tashige kana yakau da kan sa yana sakin ɓoyayyen ajiyan zuciya, hannayen sa yasaka yatallabo cheeks ɗin sa yana ci gaba da tunanin sa.
**** **** **** *****
Da gudu tashigo cikin parlour'n tana kiran sunan Mami, matashiyar budurwa ce da shekarunta bazai gaza 24yrs ba, bayan ta kuma matashin saurayi ne me kimanin 20yrs, da alamun ƙanin ta ne don sosai suke kama da juna, Mami da fitowar ta kenan cikin ɗakin ta taji muryan ɗiyar nata tana kwaɗa mata kira, sai tawashe baki tana faɗin
"Oyoyo daughter".
Da gudu tazo tayi Hugging ɗin ta tana me cike da farin ciki
"Mamina I'm back". Tafaɗa tana sakin Mamin
Murmushi Mamin tayi tace
"Welcome My daughter, fatan kin dawo lafiya?"
Tana murmusawa tace
"Lafiya ƙalau Mamina" ina Dady?"
"Ai yanzu yafita". Mami tabata amsa
Ɓata fuska tayi kana tace
"Shine yafita bayan yasan da zan dawo?"
Mami tace "Ayya Daughter be yi ninyan fita ba, kiran sa akayi daga office yayi baƙi shine yafita but bazai daɗe ba zaki ganshi ai".
Matashin saurayin me suna Ahmad yace
"Aunty ga jakan ki nan tunda kin manta dani".
Juyowa tayi tana kallon shi, dariya tayi tace
"Sorry my bro, murnan ganin Mami ne".
Hugging ɗin sa tayi tasakar masa peck a cheeks ɗin sa
Mami tace "kashigar mata da kayan mana, muje ke kuma kizauna kihuta sai kici abinci ko?"
Langwaɓar da kanta tayi tace
"O'o Mami bari dai in soma wanka, na gaji wlh da yawa".
"Ok tom je kidawo" cewar Mami sannan tajuya taƙarisa cikin parlour'n, su kuma suka wuce suka shiga ɗaya daga cikin ɗakunan da suke parlour'n, Ahmad yana aje mata trolly ɗin ta yafito yadawo wajen Mami dake zaune cikin parlour'n suka soma hira
Ita kuma bayan tayi wanka tasauya kaya cikin wata ƙaramar riga ja me kwalliyan heart 💓 agaban, tasanya blue pencil jeans sannan taɗaura hula akan ta tafito parlour'n, a kusa da Mami tazauna tana faɗin
"Washhh Mamina".
Mami tace "har yanzu gajiyar ne?"
"Wlh kuwa Mami, kinsan zaman jirgi".
"To ya Maleysian? Yau dai kin dawo gida komi ya ƙare".
"Wlh kuwa Mami, kullum fatana naganni na gama karatun nan na dawo gare ku".
Mami tace "alhmadulillah gashi ai komi ya ƙare, yanzu kije kici abinci kar kuma kin dawo da yunwa".
Kallon Ahmad tayi tace
"Bro ɗauko min inci anan, bana jin zan iya tashi".
Dariya Ahmad yayi yace
"Aunty Kausar uwar son jiki, kin dawo kenan".
Itama dariya tayi tace
"Kai dai bari Baro, but yanzu fa na sauya kar kayi tunanin ko da ne".
Dawowa yayi riƙe da coolar a hannu haɗe da plate yace
"Ai bazan yarda ba sai naga kin soma aiki".
Shafa fuskarta tayi kana tace
"Wa ke maganar aiki yanzu?" Tabb ai sai na huta".
"You see? Dama na faɗa ai, kina jinta ai Mami".
Mami tace "ai kibar ma wannan maganan, don tuni Dadynku ya samo miki aiki a gidan t.v dake nan garin".
Waro idanu tayi tana tsayar da hannun ta daga zuba abincin da tasoma tace
"Mami da wuri haka? Ya Dady zai min haka bayan ni ba haka mukayi dashi ba?".
"Ai sai kibari in yazo kitambaye sa kun fi kusa".
Kaɗa kai kawai Kausar tayi taci gaba da zuba abincin, yayinda Ahmad yasaki dariya yamiƙo mata spoon yana cewa
"Aunty to meye amfanin zaman naki? Tunda kin riga kin gama karatun ki ai aiki yadace dake, ko kuma kin fi so kiyi aure ne?"
Harara tawurgo masa tana kai abincin bakin ta, sai da tagama taunawa kana takalli Mami tace
"Mami naga anguwar tamu duk tacika da sabbin gini, duk yanzu mun sami maƙota".
Mami tace "ai kam, ai gine-ginen ma sun jima, don waɗanda ma suke maƙotaka damu sunyi shekaru kusan biyu da tarewa".
Girgiza kai kawai Kausar tayi, daga nan sukaci gaba da ɗan taɓa hira tana cin abincin ta. [9/15/2020, 11:32 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 19*
*4DAYS*
Ƙarfe 10:00pm. Na dare jirgin da yakwaso su Brr. Ibrahim Khalil daga Egypt yasauke su a airport ɗin Katsina, driver'n shi yaje yaɗauko shi, lokacin da suka isa gidan kowa yana barci don ba kowa yasan da dawowan sa ba illa me gadi, bayan sun shiga yafito daga motan yanufi cikin gidan jaye da trolly ɗin sa, ƙofan parlon a kulle yake don haka sai yasaka keey yabuɗe yashiga, duhu ne dumɗun cikin parlour'n, Direct ɗakin sa yanufa yabuɗe yashige tare da rufowa, akan gadon sa yayi ma kan sa mazauni, sai da yaɗau 10mins yana hutawa kafin yamiƙe yasoma rage kayan dake jikin sa yashige toilet, wanka yayi yaɗauro alwala yafito, baƙar jallabiya me hula yasanya sannan yatayar da Sallah, magrib da isha'i yayi, bayan ya idar yayi shafa'i da wutri kafin yamiƙe yahaye saman gado cike da gajiya, babu daɗewa kuwa barci me nauyi yaɗauke sa, wanda be tashi farkawa ba sai da gari yayi haske sosai wajajen ƙarfe 11:03am.
Hasken ranan da yashigo ta cikin windon sa ne yabugi fuskar sa, ahankali yasoma buɗe idanun yana rufewa har yaware su gaba ɗaya, take hasken yaƙyalle masa idanu don haka yayi saurin juyawa yaba ma windon baya, 5mins yaɗauka ahaka kafin yamiƙe zaune yana miƙa tare da hamma, ahankali yasanyo ƙafafunsa saman shimfiɗaɗɗen carfet ɗin dake malale cikin ɗakin, bedroom slippers yasaka a ƙafan nasa yamiƙe yanufi toilet, a bakin Toilet ɗin yacire slippers ɗin yashiga bayan yasanya Toilet slippers.
Koda yafito yana ɗaure da towel ajikin sa, ya riƙe ɗaya yana goge suman kan sa, Direct wajen mirror yanufa yasoma shafa Expensive Lotions ɗin sa, bayan ya gama kintsawa yanufi sif ɗin sa yaciro kayan sa, brown t.shirt ne me gajeren hannu sai blue jeans yasaka, feshe jikin sa yayi da Parfumer's ɗin sa masu ƙamshin daɗi sannan yafito parlour hannun sa zube cikin aljihu, dainning yakalla yaga babu komi sai yajuya da ninyan komawa ɗakinsa ɗauko waya, har yariƙe handle ɗin kuma sai yaja siririn tsaki yana juyawa yanufi ɗakin Lubna, ahankali yatura ƙofan yana motsa bakin sa, shashsheƙan kukan ta ne yasoma shiga kunnin sa kafin yasauke idanun sa akan ta, tana zaune a ƙasa ta manne a jikin gado sai takifa kan ta saman gadon, shiru yayi yana kallon ta na tsawon daƙiƙu kafin yakira sunan ta in a cool voice
Dasauri taɗago da kanta face ɗin ta jage-jage da hawaye tasauke idanunta kan shi, sosai tayi mamakin ganin shi don batasan ya dawo ba, shi kam takowa yayi yashigo ciki sosai yana kallon ta yace
"Meke damun ki?"
Ahankali tasunkuyar da kanta ƙasa cikin sanyin muryan ta da be fita sosai tace
"Babu komi".
"Ke banson ƙarya ki faɗa min abinda ke damun ki nace?" Yafaɗa da ɗan ƙarfi murya a kausashe
Jikin ta har rawa yake yi tace
"Dama wasu ne suka sace min Mamana da ƙannina".
"Whatt.." yafaɗa da ɗan ƙarfi yana tsare ta da idanu
"Meyasa to?" Yasake jeho mata tambayan
Cikin rawan murya tace
"Dama.. dama sabida sun saka ni aiki ne ban musu ba shine suka kama su".
Wani kallo yasakar mata kana yace
"Wani aiki kenan?"
"Uhmm hm sun ce ne naɗauko musu duk wani abu da nagani cikin ɗakin ka kamar takardu ko Lapton ɗin ka.."
Sai kuma tayi shiru tana zub da hawaye, Khalil ajiyan zuciya yasauke har yanzu idanun sa akan ta, dama yadaɗe da zargin ta, tun sanda yashigo ɗakin sa yaga ta tsorata hakan yasaka yaɗaura ayar tambaya akan ta, daga lokacin ne yasaka Camera 📷 cikin ɗakin sa yana ɗaukan masa duk abinda take yi, wannan dalilin ne yasaka ko kaɗan baya barin ɗakin da yake aje muhimman abubuwan sa aciki abuɗe, but besan da cewa mutanen da suka saka ta aikin sun yi garkuwa da mahaifiyar ta da ƙannin ta bane, sai yaji tsananin tausayin ta ya kama shi, ahankali cikin sanyin murya yace
"Ki dena kuka Lubna, insha Allahu Mahaifiyarki da ƙannin ki zasu dawo gare ki karki damu, ki kwantar da hankalin ki kinji?"
Ɗago kanta tayi tana kallon sa kafin tagyaɗa masa kai tana jin zuciyarta na mata sanyi sosai, bata yi tunanin zai ɗau abin da sauƙi haka ba idan har yagane cin amanar sa take yi, take tasake jin ƙaunar sa na sake shiga cikin zuciyarta
"Bani wayan ki". Yace hakan yana ciro hannun sa cikin aljihu
Dasauri tamiƙe taɗauko mishi tabashi, amsa yayi kawai yafice, ita kuma tabi bayan sa da kallo tana sauke ajiyan zuciya, zamewa nan ƙasa tayi tazauna tana share hawayen fuskarta
Shi kuma Direct waje yafita yanufi motan sa yashige yafita gidan, kamar ko yaushe yana jan motan ne ahankali yana riƙe da wayan sa ahannu yana neman layin Brr. Tahir, dai-dai zai karya kwana yafita titi yaɗago kan sa don duba hanya, nan yaga wata farar Mota itama ta shanyo kwana kamar zasu yi karo da juna, dasauri yaja burki yana son kaucewa but duk da haka sai da suka gwarawa juna, aje wayan nasa yayi kafin yabuɗe motan yafito dai-dai itama tafito cikin motan ta suka kalli juna, atare kuma suka faɗi
"I'm sorry".
Hakan yasaka sukayi murmushi kafin ita tace
"Kayi haƙuri bansan da zuwan ka ba ne".
"No laifina ne ai, nima ban kula ba, but kiyi haƙuri ko".
Murmushi tayi masa tagyaɗa kan ta
"Babu damuwa". Tace dashi kana tajuya tashiga motan ta
"Shima ɗin motan nasa yashiga, sai da taja nata motan yawuce kafin itama tawuce, Direct police station yawuce yayi reports ɗin ɓatan mahaifiyar Lubna da ƙannin ta biyu sannan yawuce gidan su. [9/16/2020, 8:26 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 20*
Tana kwance saman katifan ta daga ita sai farar doguwar riga irin me taushin nan da zanen flowers ajikin rigan, kanta babu ɗankwali sai gashinta da yawargaje yazubo mata har kafaɗunta, littafi ne a hannunta tana karanta wa tajiyo sallaman ƙawarta daga waje, amsa mata tayi sannan tashigo takalle ta tana faɗin
"Ƙawata hutawa kike yi ne?"
Tashi zaune Halwa tayi tana yatsina fuska tace
"Uhm hutu kuma? Karatu dai nake yi".
"Yayi makaranciya, kinga ni wlh ban ma bi ta karatun ba don bani da lokaci yanzu, ina Mama naji kamar ke kaɗai ce gidan?"
"Eh Yaya Nura ya kai ta kasuwa".
"Kai ƙawata wlh baki ga yanda kika sauya ba, wai meye sirrin ne ni naga kamar kina ƙara wani haske ne da kyawu kamar bakijin dawan garin? Ko dai yaya Nura ne?" Zainab tafaɗi hakan tana ƙare mata kallo tare da dariya
Murmushi Halwa tayi, sosai itama take ganin sauyi daga gare ta, tayi wani haske fayau duk da ita ɗin ba fara bace, gashi kuma ko ina nata yaciko gunun sha'awa
"Hmm ke dai ban son tsegumi me kikeson cewa akan Yaya Nura?"
Dariya Zainab tayi tace
"A'a babu komi, kawai dai ina tunanin ko har yafara sauya kulawan sa ne daga gare ki tunda yaga kin kusa zama mallakin sa, kin gane dai irin uhm uhmmm.."
Dukan ta Halwa tayi a cinya tana cewa