Barrister ibrahim khalil complete - Chapter 8
Barrister ibrahim khalil complete Chapter 8: Barrister ibrahim khalil complete Chapter 8. "But nasan maganin ka tunda naga kamar har yanzu baka yi hankali…
4,485 words
"But nasan maganin ka tunda naga kamar har yanzu baka yi hankali ba, tun yaushe muke wannan maganar da kai amma dayake baka ɗau maganar ta wa da wata muhimmanci ba shine ka shashantar dashi, yanzu gashi har Sameer yana da yaro kai kazauna kana son kazama tuzuru, to na baka nan da lokacin da zaku gama wannan shari'an, katabbatar ka sami matar aure idan ba haka ba ni da kai ne, kana ji na?"
Dad ɗin yaƙarike maganar yana riƙe kunnen sa tare da kallon sa
Ɗan turo baki gaba yayi kana yagyaɗa masa kai
"To tashi katafi, Allah yamaka albarka".
Ciki-ciki ya'amsa yamiƙe yafita daga parlour'n, girgiza kan sa Dad yayi yana ɗaukan Jaridan da yake karantawa yace
"Wannan yaron in ba haka nayi maka ba, to naga alaman ba auren ne a gaban ka ba, in ba ma rashin wayau ba ya zauna har War haka be yi aure ba".
Shi kam Khalil daga fitan shi ɗakin Mom yashige, tana zaune a gefen gado tana gyara drowan ta data hargitsa tana neman sarƙan da zata saka, yashigo fuska a turɓune hannun sa cikin aljihu, ɗago kai tayi tana kallon sa, sai da takaranci yanayin sa kafin tace
"Yah ya Me yafaru ne? Me Dad ɗin naka yafaɗamaka naga fuskar ka ta sauya?"
Ahankali yatako yazo kusa da ita yazauna kafin yasoma magana ciki-ciki
"Wai Dad ya bani nan da bayan gama Shari'a na da Alhaji Mubarak in fito da mata, sai kace neman matan sauƙi ne dashi".
Murmushi Mom tayi tana riƙo hannun sa ɗaya da yaciro su daga aljihu yaɗaura saman cinyoyin sa yadunƙule su
"Haba My Son ya zaka ga laifin Dad ɗin ku? Ai ni inaga ya baka lokaci sosai tunda ba yau yasaba maka maganar ba?"
Kallon ta yayi yace
"Mom kwanaki ne fa suka rage? Meyasa bazai ƙara min zuwa nest year ba?"
Hannu taɗaura a saman kan shi tana shafa baƙin gashin sa da yasha gyara yakwanta luf gunun sha'awa tace
"Wai to menene na tada hankalin ka ne Son? inace Kai ɗin me farin jinin ƴan mata ne, duk wacce kazaɓo acikin matan da suke son ka da gudu zata aure ka, ko acikin Family ne sai kazaɓa ɗaya kaga hakan ma sai yaƙara mana ƙarfin Zumunci, don ban faɗa maka bane kwanaki ma Hajja Mero tazo har nan, takawo min maganar ƴar ta Shukra, me zai hana a haɗa auren ku tare, kaga in ka amince kawai sai in Kira ta in sanar da ita, cikin lokaci ƙanƙani sai ayi komi a gama ko ba haka ba?"
Kwaɓe fuska Khalil yayi yace
"Wai menene haka Mom, ya na kawo miki magana don ki rarrashi Dad yaƙara min time kuma kike mayar da hannun agogo baya? Ni in rasa ma waɗanda zan aura sai yaran nan da basu da kunya, kullum idanun su a tsatstsaye kamar zasu cinye mutum, ina Allah yakyau wlh". Yaƙarike maganar kamar yaga abin ƙyama
Dariya Mom tayi tace
"Ban da abin Auta to menene laifin su? Kuma menene laifin wanda ke son ka, in ma kana tunanin sun yi maka yara ne ai naga hakan kuka fi so yaran zamani, kuma sun fi daɗin zama ai, zaka ji daɗin zama dasu wlh".
"To ni Mom bance miki Ina son yara ko manya ba, Ni kawai har yanzu ban ga wacce nake ƙauna bane, and Mom kuma ki dena maganar yaran nan ma kar suji su ce zasu raina ni".
Mom tace "to shikenan na daina Autana, yanzu dai katabbatar ka samo matar da zaka iya zama da ita tun kafin Dad yazaɓo maka".
Marairaice fuska yayi yana faɗin
"Yanzu Mom baza ki roƙe sa ba?"
"Kasan halin Dad ɗin ka, in yariga yaba ma mutum dama kasan bazai saurare shi ba, don haka kawai kayi abinda yace maka, but insha Allahu dai zan yi masa magana yaƙara maka lokacin yanda zaka samo min suruka me kyau da hankali kamar kai, wanda take ƙaunar ɗana kuma takula min dashi sosai".
Murmushi Khalil yayi yace
"Mom kenan, to amma dai bari ince ameen".
mom dariya tayi tana jan kumatun sa tace
"Ja'iri kawai, kana so kana kai wa kasuwa ko?".
Shima dariya yayi kawai yana sosa kan shi
"To tashi kaje kar kayi late da yawa, kaga har 08:00am. Ta kusa".
"Ok Mom".
Sai da yayi mata peck a cheeks ɗin ta kafin yamiƙe yayi mata sallama yafice, har yakusa isa ƙofar da zai fita daga Parlour Nazeefa tafito daga kichen riƙe da plate a hannun ta, tana hango shi takira sunan shi
"Yaya".
Har yariƙe handle ɗin ƙofan yajuyo yana kallon ta, saurin ɗauke kan ta tayi daga kan shi ganin kallon da yake mata, ita kan ta batasan me zatace mishi ba takira shi, sai dai kuma bataso yatafi batare da ya ganta ba, ko da magana ce yahaɗa su
"Ina kwana Yaya". Tace dashi tana ɗago kan ta takalle shi
"Lafiya, ya jiki?"
"Alhamdulillah Yaya".
Fita kawai yayi batare da yasake furta ko kalma ɗaya ba, ita kam murmushi tasaki tana jin daɗi a ranta, juyawa tayi tanufi ɗakin ta.
Lokacin da ya'isa yayi parcking yafito, ahankali yake tafiya har ya'isa office ɗin sa, har yakama handle ɗin ƙofan zai murɗa sai yakalli setting office ɗin Billy dake rufe, taɓe bakin shi yayi kawai yashige office ɗin sa yamayar da ƙofa yarufe, ahankali ya'isa jikin window yana saka hannu ya yaye cooten ɗin, gyara tsayuwan sa yayi yasanya hannayen sa cikin aljihu yana ƙure waje da idanu, a zahiri titi yake kallo but a baɗini tunanin mafita yake yi, tsawon mintuna yana wajen kafin yataka yanufi kujera yazauna, buɗe computer'n sa yayi, sai kuma yadunƙule hannun sa biyu yaɗaura a haɓar sa yaci gaba da tunanin sa
Nocking Brr. Tahir yayi yashigo, har yazauna Brr. Khalil be san ya zauna ba, sai da yakaɗa masa hannun sa a setting face ɗin sa tukun yaƙyafta idanu yana kallon shi
"Wai tunanin me kake yi ne har nashigo baka sani ba?"
Ajiyan zuciya Brr. Khalil yayi yana gyara zaman sa yace
"Wlh Dad ne yake son tada min da hankali".
"Me yafaru?" Brr. Tahir yatambaye sa
"Wai cewa yayi nan da lokacin da zamu ƙarƙare Shari'a nafito da matar da zan aura, ko wa yace mishi na damu da auren yanzu, kawai zai jagula min lissafi wlh".
Dariya Brr. Tahir yayi kana yace
"Wlh kana bani mamaki Ib, wani lokacin har tunani nake yi ko dai ba lafiyanka ƙalau ba, ni a ganina kai kakeso katakura kan ka but ban ga aibun Dad anan ba".
"To me kake nufi kenan?" Khalil ɗin yatambaye sa yana ɗaure fuska
"No babu komi, but ni dai shawaran da zan baka kafitar da wata cikin matan da suke ƙaunar ka, ko da kai ba ka ƙaunar ta".
Khalil yace "kana nufin kenan in yi auren rashin ƙauna?"
"Eh mana tunda har yanzu baka sami wacce tayi maka ba duk acikin matan da suke son ka, ba mamaki kai irin mazan nan ne da basu gane meye so sai lokacin da suka auri matar, sannan alokacin zasu gane sun faɗa tafkin ƙauna".
Shiru Khalil yayi yana tunani
Brr. Tahir yace "kar ka matsa ma kanka Ib, me zai hana ka amince wa Billy, tunda ita kaɗai naga alaman zatafi dacewa da kai, kuma kai kan ka sheda ne yanda take matuƙar ƙaunar ka, zata iya yin komi sabida kai, don haka kawai kaba ma zuciyar ka dama takoyi son ta kafin zuwan lokacin, idan har kaji zuciyar ka bata kwanta da ita ba zaka iya sauya wa".
Still dai shiru Khalil yayi yana nazarin maganganun Brr. Tahir ɗin, kuma daga baya sai yace
"Shikenan zan yi tunani akai".
"Ok".
Daga nan tattauna wa sukaci gaba da yi kafin Brr. Tahir yatafi yabar shi, shi kuma yaci gaba da aiki har zuwa lokacin tashin shi, ahankali yamiƙe cike da gajiya yatattara kayan sa yafice, a hanya suka haɗu da Brr. Tahir har suka ƙarisa wajen motan su
Brr. Tahir yace "yau baka tambayi mutumiyar ka ba? Kuma kana gani yau ɗin baka ganta ba".
Ɗan taɓe fuska kawai Khalil yayi yabuɗe motan sa yana shirin shiga, riƙo murfin motan Brr. Tahir yayi yace
"Kenan baza ka tambaya ba ko?"
"To tunda kayi ninyan faɗa min menene kuma sai na tambaya?" Khalil ɗin yafaɗa yana tsare shi da idanu
Murmushi Brr. Tahir ɗin yayi yace
"Gaskiya baka da dama Abokina, in ba ni ba babu wanda zai iya da halinka".
Harara Khalil yayi masa kamar wani mace yace
"Tunda gani me baƙin hali ko? Dole kace babu wanda zai iya dani".
Dariya yayi yana rufe bakin sa yace
"Rufa min asiri don Allah wasa nake maka, but seriously Billy ɗin ka bata da lafiya fa, yanzu nima nake ji wajen Brr. Kuma".
Wani irin kallo Khalil yayi masa, be ce komi ba yajanye murfin motan sa yarufe, leƙo da kai Brr. Tahir yayi yace
"Bakace komi ba zaka tafi?"
"Me kake so nace maka Umhm?" Khalil ɗin yafaɗa yana ma Motan keey
"Muje mu gaishe ta mana, kaga daga nan sai kashigar da kanka ka gane ai". Brr. Tahir yace hakan yana dariya ƙasa-ƙasa
Gajeran tsaki yayi tare da jan motan sa yayi gaba, shima dai Brr. Tahir ɗin motan sa yanufa yashiga yana ci gaba da dariya tare da girgiza kan sa. [9/18/2020, 9:47 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 24*
Lokacin da ya'isa gida yayi parcking motan sa, sai da yayi kusan mintuna 5 kafin yabuɗe motan yafito, ahankali yake takawa har yashiga cikin gidan, akan sofa yazube yana kwantar da kan sa cike da gajiya, dafe goshin sa dake ɗan sara masa yayi yana lumshe kyawawan idanun sa, few minutes ago yacire hannun yana tashi tsaye yanufi ɗaki, koda yashiga wanka yasoma yi sabida yaji ƙarfin jikin sa, don sosai yake jin sa kamar an mishi dukan tsiya, bayan ya shirya cikin brown ɗin jallabiya da Three qweater sai yafito parlour yanufi kichen kai tsaye, shiru yayi yana tunanin abinda zai dafa, don sosai yagaji da cin indome, kuma so yake yaci abu me ɗan nauyi coz yunwan dake ƙwaƙulan sa, tea yafara haɗawa yazauna nan kichen ɗin yashanye cikin ƙanƙanin lokaci, kana yasoma girka makaroni, shi ba wani ma'abocin iya girki bane don be taɓa yi ba in banda indome da yake dafa wa, but haka dai yayi karanbanin sa yasoma ƙoƙarin girka wa, sai da yaɗaura tukunya a wuta sannan yakurma ruwa rabin tukunyan, yana soma zafi yaɗauko makoroni biyu yasake, don yana son yagirka ne har dare yahuta da ɗame-ɗame, bayan ya sake ne sai yaɗauko Maggi yazuba sannan yaɗauko kayan miya, blanda yaɗauko yasoma yunƙurin blanding ɗin sa, lokacin duk zufa ya ishe shi hakan yasaka yatashi yafice, rigan jikin sa yacire yajefa saman sofa, yadawo daga shi sai singlate ajikin sa yasoma blanding kayan miyan, bayan ya gama duk yasake cikin tukunyan, yazauna nan yana jiran yanuna, gaba ɗaya ya manta da cewa ko mai be zuba ba, sai da yabuɗe yaga yana ta zaɓarɓaka yatuna ai be zuba mai ba, ɗauko wa yayi yadiddila yamayar yaci gaba da zama, sai da yabashi good 30min kafin yabuɗe, lokacin tuni ya nuna sai dai ruwa da yayi yawa hakan yasaka yacaɓe, but be damu ba yaɗauko plate yaɗiba yarufe sauran, ɗauka yayi yafito yanufi saman dainnig ya'ajiye, sai yaje yaɗauko Faro water da kwalin Juice yadawo yazauna, spoon yaɗauka yana kallon abincin, kamar baya son ci sai kuma yasaka spoon ɗin yaɗiba yakai bakin sa, taunan farko yadakata yana taɓe baki, ahankali kuma yaci gaba da taunawa har yahaɗiye, kana yasoma tsakalan abincin kaɗan-kaɗan yana ci, ko kaɗan babu daɗi but yakasa dena ci sabida yunwan da yake ji, yayi dana sanin dafa wa, da tun farko yayi indome'n sa da tuni yacinye lafiya lau duk da ba wani iyawa yayi ba, but yafi wannan jagwalgwalon, sai da yaji cikin sa yasoma murɗa masa yana mishi ciwo kafin yamiƙe yaɗau plate ɗin yakai kichen tare da sake sauran cikin tukunya
Parlour yadawo yazauna yana ɗaukan wayan sa dake ajiye yasoma latsawa, ahankali yatsai da abinda yake yi yana nazarin abinda yake son aikata wa, tsawon minti 3 kafin yaci gaba da latsawa sannan yakara a kunne
"Assalamu alaikum".
Jin muryan ta a cikin kunnen sa yasaka shi lumshe idanun sa yana gyara zaman sa tare da ɗaura kan sa saman kujeran
"Wa'asalaikis Salam". Ya'amsa mata cikin cool voice ɗin sa me daɗin sauraro
Shiru ne yabiyo bayan amsa sallaman nasa, domin ita a fannin ta mamaki ne yakusa kashe ta, abinda bata taɓa gani ba ko da a mafarki ne wai Brr. Khalil zai kira ta.. katse mata tunanin ta yayi da faɗin
"Baki iya gaisuwa ba?"
Bilkisu da rawan baki tace
"Ina yini?"
"Lafiya, ke fa yakike?"
Tace "lafiya lau".
"Ke da akace min baki da lafiya kuma shine kike Son yin min ƙarya?"
Batasan sanda tasaki murmushi ba cike da tsananin farin cikin da yakusa kashe ta tace
"Ai naji sauƙi, dama zazzaɓi ne".
Taɓe baki yayi sai kuma yagyaɗa kan sa, still kuma yace
"Ai naga alama tunda gashi kina min dariya".
Kamar yana ganin ta tayi saurin rufe bakin ta tana faɗin
"Wlh ba da kai nake yi ba".
"To da wa kike?" Yatambaye ta yana wani rage murya
Bilkisu ta kasa magana fa, sai kace ba abinda take nema bane yasamu amma kun ji tayi gumm kamar munafuka
"Kin yi shiru kuma? Ko bazaki faɗa min ba?"
"Uhm babu kowa".
"Ok dama nakira naji jikin ki ne, tunda kin sami sauƙi naji daɗi, bye".
Be jira cewar ta ba yakatse wayan.
Ita kam Bilkisu tana jin yakashe kiran sai tawani kurma ihu tana burgima saman gadon ta, Allah yasa ita kaɗai ce a gidan da har waje sai an ji
"Wayyo Allana yau daɗi zai kashe Ni, wai Ib ne yakira ni? Wayyo ko dai mafarki nake yi?"
Sai tamiƙe daga kwancen da take tana rarumar wayar ta taduba, washe baki tayi ganin dai ba mafarki bane, kwanciya takuma yi tana rarumo pilow tamatse tana cewa
"Wayyo daɗi kashe ni, wayyo ni Billy yau duniyar ta kai min inda nake so, gaskiya yau na kasance me Sa'a, wayyo Allana Wayyo Allana wa zai taya ni farin ciki?"
_(Ni kam nace *NAFEESA GROUP FAN'S* su taya ki, ko kuma *BRR. IBRAHIM KHALIL FAN'S* don Ni dai ban da lokacin ki lol😅 💃💃)_
Shi kuma da gama wayan miƙe wa yayi yaɗau rigan sa yasaka kafin yashige ɗaki, alwala yaɗauro yafito yanufi masjid, bayan ya idar da sallah yafito yakamo hanya, gab da yakusa isa gidan sa yahango Kausar tafito daga gida, tana sanye ne cikin wata Farar riga me dogon hannu zuwa cinyan ta, sai wani burgujejen wando Three qweater me manyan aljihu kalan Orange 🍊, sai tasanya hula facing cap shima kalan wandon, kitson da tayi guda biyu jelan tazubo shi gefe da gefen kafaɗan ta, tunda itama tahango shi tanufo shi da murmushi a fuskar ta, tana iso wa wajen sa tace
"Yanzu nake tunanin ka a raina sai ga ka".
Yanda tayi maganar ne yasaka shi ɗan murmusawa yace
"Zaki bani wani abu ne?"
Sai ta langaɓar da kan ta tace
"Eh in dai kana so".
"Why not?" Yafaɗa yana waro idanun sa
Sai tayi murmushi kana tace
"Dama ina so muhaɗu ne kawai, coz akwai tambayan da zan maka".
Be ce mata komi ba sai dai ƙure ta da idanu da yayi, yana jiran abinda zatace
"An bani labarin kuna Shari'a da wani Alhaji Mubarak mai kuɗi, and nan da five days zaku koma Court, shine zan iya zuwa muyi hira akai, ina nufin ina son nasan komai". Taƙarike maganar tana ɗan kwantar da murya tare da ƙifƙifta idanu
Shiru yayi still har yanzu idanun sa akan ta, sai tasake cewa
"Please kaji?"
"Ok". Yafaɗa ataƙaice yana ɗage kafaɗa
"Tom gidan ka zamu je yanzu ko?" tayi maganar cike da zumuɗi
"No kibari zuwa gobe sai kizo".
Daga haka yayi gaba, ita kuma tatsaya nan tana kallon shi har yashige, sai tasaki murmushi tanufi wajen gidan su tatsaya, dama abinda yafito da ita kenan shan iska, a cewar ta gidan yayi mata zafi, tana nan tsaye tana kallon tsare-tsaren gidajen mutane tana tunane-tunanen ta, wayan ta yasoma ringing, cirowa tayi cikin aljuhu takalli fuskar wayan, sunan HONEY ne yafito ɓaro-ɓaro hakan yasaka tasaki murmushi tana amsa call ɗin, tajuya tashige gida.
........ ........... .......... Washe gari wajen ƙarfe 03:30pm. Kausar tashigo gidan Khalil, yau tana sanye cikin wata doguwar riga ce mare nauyi red colour, sai ɗankwalin shi da tayafa akan ta kawai, tansaya Hill shoes a ƙafafun ta, tana riƙe da wayan ta iPad fara, nocking tasoma yi amma shiru, hakan yasaka taci gaba da yi babu ƙauƙautawa, tafi minti goma a wajen tana nocking, sosai tagaji but kuma taƙi tafiya
A ciki kuwa tun da yadawo aiki yakwanta barci, sama-sama yake jiyo nocking ɗin daga ɗakin sa, ahankali yabuɗe idanun sa yana sake jiyo nocking ɗin, tsaki yaja yatashi zaune yana miƙa, sai da yafi 3min a zaune kafin yamiƙe yafito daga shi sai baƙar singlate ajikin sa, da gajeren wando yellow, ƙofan yabuɗe suka haɗa ido da ita, dasauri tasad da kai ƙasa tana jin matsananciyar kunya, cikin sanyin murya tace
"Sorry ban san kana barci bane, bari in koma zan dawo".
"Kishigo". Abinda yafaɗa kenan yajuya yashige ɗakin sa
Sai da taji ƙaran rufe ƙofa tukun taɗago kan ta, leƙawa tasoma yi kafin tashiga, saɗaf-sadaf haka take tafiya kamar wata munafuka, har ta'isa kan kujera tazauna tana kallon parlour'n, sosai tsarin gidan yayi mata kyau, har yaso yafi nasu duk da su ma nasu yana da kyau, but wannan komi kakalla kasan ba ƙaramin abu me tsada bane, sosai aka kashe kuɗi cikin parlour'n duk da ba wani kaya ne a ciki ba, tana nan tana kalle-kallen ta kamar wacce bata taɓa ganin irin sa ba, yafito sanye da riga me ruwan zuma da zane-zanen fari ajiki, sai wando Three qweater fari, ƙariso wa yayi yazauna a kujeran dake facing ɗin ta yana kallon ta, ɗago kai tayi itama tana kallon shi tace
"Ina yini?"
"Lafiya". Ya'amsa ataƙaice yana jingina bayan sa da kujera yalumshe idanu
Ita kuma sai tatsaya tana kallon shi cike da burgewa, komi nasa me kyau ne, yana da matuƙar kyau da kwarjini, babu macen da zata gan shi batayi fatan samun shi ba, buɗe idanun sa yayi yasauke a kan ta, sai tawayan ce takau da kai
Yace "me zaki sha?"
Sai tamaida idanun ta kan sa, kamar bashi yayi maganan ba
"I'm ok". Tace dashi tana mayar da idanun ta kan wayan ta da taɗaura saman jikinta, tasoma latsawa kana tace
"Ko zamu iya farawa?"
"Ok".
Daga nan yasoma bata bayani akan komi, har zuwa sanda suka gama yamiƙe yanufi hanyan kichen, wata iriyan yunwa yake ji, komi be saka a cikin sa ba tun tea ɗin safe, kuma da yadawo barci sosai yarufe masa idanu sakamakon jiya be yi ishashshe ba
Yana tsaye cikin kichen ɗin yana ƙoƙarin ɗaura tukunya, yaji muryan ta a bayan sa
"Me zaka dafa?"
Juyowa yayi yana kallon ta, don be tsammaci zuwan ta ba, murmushi tayi masa tatako ta'iso wajen sa tana faɗin
"Kaje sai in yi maka girkin".
Tayi maganar tana ɗaura hannun ta saman tukunyan tana gyara mishi zama
Babu musu kuwa yajuya yatafi, be san meyasaka yarinyan take son shige masa ba, but ko kaɗan ba ta bashi haushi sai burge shi da take yi, yana nan zaune a Parlour yana kallo har tagama tazubo mishi, a gaban shi ta ajiye saman Centre table tace
"Bismillah ko". Tayi maganar tana kallon sa da murmushi a face ɗin ta
Shima kallon ta yayi sai yakalli abincin, taliya ne me manygaɗa da yaji cUrry da yankakken ƙwai a sama, murmushi yasaki yace
"Thank you, kema ki zubo naki kici".
Yarfe hannun ta tayi tace
"No ni na ƙoshi, ina sauri akwai inda zan je".
Gyaɗa mata kai kawai yayi, sai tajuya tatafi shi kuma yabi ta da kallo, sai da takai bakin ƙofa tajuyo tana kallon sa taɗaga masa hannu sannan tafice. [9/23/2020, 7:28 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️ *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* ♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il* _(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖ *FEENAH WRITER'S ASSO📖* ```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH``` _ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA* _na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR* ```NAFEESAT LABARIN DEEBIZAH JARUMAI RAYUWATA NUSNIM BUTULCI SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 25*
*FEW DAYS*
"My dear kiyi sauri Kar kiyi late kuma?"
Halwa dake cikin ɗaki cikin sanyin murya tace "to Yaya ga ninan".
Fitowa tayi riƙe da Bairo a hannun ta tana kallon yayan nata, shima kallon ta yake yi cike da tausayin ta, gaba ɗaya duk ta rame sabida zazzaɓin da yasako ta agaba kwana biyu, tayi haske kallo ɗaya zakayi mata kagane sosai take cikin ciwo, itama Mama dake zaune kallon ta tayi tace
"Ni kuwa idan ba yazama dole bane Halwa a fasa zuwa makarantan nan mana, kinga yanda kika yi kuwa? Ba fa sauƙi kika ji ba?"
Kallon Maman tayi kawai tana marairaice fuska kamar zatayi kuka
Nura yace "Mama wannan jarabawan fa tana da muhimmanci tunda na fita ne, haka nan zata lallaɓa tayi har su kammala, kinga jiya ma taje tayi tadawo lafiya, zaki ga sauran ma kamar yanzu ne har an gama".
"Um um Nura, yau kaduba kagani sosai take jin jiki ko abinci ta kasa ci, ga wahalan da zataje tasha, me zai hana abari wani shekarar sai tarubuta".
Nura yace "kai Mama har shekara sai tayi ta zama agida? Kema kinsan halinta ba yarda zatayi ba".
Halwa tace "Mama ki dena maganar nan ma, kuma Ni haka nan zan je in zana jarabawa ta, sai dai in ciwon ya kwantar dani ne amma banga abinda zai hana ni zuwa ba".
Murmushi Nura yace "to kin ji dai".
Kaɗa kai Mama kawai tayi tace "ai shikenan Ni dama tausayin ki nake ji, yanzu ku hanzarta kutafi kar lokaci yaƙure".
Fita suka yi, A mashine ɗin Abokin Nuran yakai ta har cikin makaranta, yasauke ta a bakin ajin su.
Bayan kamar mintuna 20 aka zo raba musu pepper, lokacin ne kuma sosai jikin Halwa yayi tsanani, jikin ta sai kakkarwa yake yi zazzafan zazzaɓi yarufe ta, kasancewar mutum ɗaya-ɗaya ake zama a sit shiyasaka babu wanda ya lura da ita, tana can kusa da baya ajikin bango ta takure waje ɗaya, sai takifa kan ta a table tana hawaye, ita kan ta takasa jure yanayin da take ji, sai da Wani Malami yazo miƙa mata Pepper yakira sunan ta
"Halwa lafiyan ki lau kuwa? Za'a yi jarabawa kina kwance".
Ahankali taɗago kan ta tana ƙanƙame jikinta, face ɗin ta duk hawaye, kuma sai rawan ɗari take yi
"Subhanallah.. baki da lafiya ne?" Malam ɗin yafaɗa yana kallon ta
Gyaɗa masa kai tayi don takasa magana ma
"To yanzu ya za'a yi kenan? Zaki iya yin jarabawan?"
Shiru tayi bata iya cewa komai ba, su kuma ƴan ajin yawancin su hankalin su na wajen, har da Zainab aciki, duk tausayin Ƙawartan ya kamata, ɗaya daga cikin Malaman dake tsaron su yace
"Ku me kuke kallo ne baza kuyi abinda ke gaban ku ba?"
Sai kowa yamayar da kan sa ƙasa suka soma duba peppern, Malam Isma'il dake can bakin ƙofan yace
"Ai kabar su Malam Kamal, time na cika amsa zamuyi mu wuce".
Malam Jamilu dake tsaye har yanzu kan Halwa still yace da ita
"Halwa ko dai bazaki iya bane? In ciwon yayi tsanani kije ki amso magani kisha kinji?".
Cike da ƙarfin hali tace "zan iya Malam".
"Ok to gashi".
Aje mata yayi a gaban ta, yaja gefe nan yana kallon ta tare da kula da waɗanda suke wajen, ita kam ahankali tajanyo pepern ta'aza Bairo akai, tayi shiru ta kasa rubuta komi, sai da tayi kusan mintuna 5 kafin tasoma rubuta sunan ta daƙyar, bayan ta gama tasoma amsa Questions ɗin, Number One taɗauka tafara dashi, ahankali tatsayar da hannun ta daga rubutun da take yi tana runtse idanu, wannan karon jikinta sosai yake rawa har da hannun ta, Malam Jamilu dake tsaye yana kallon ta yace
"Gaskiya bazaki iya wannan jarabawan ba, tashi kije kisha magani, inyaso sai asamo wani yarubuta miki".
"Halwa". Malam Isma'il da yaƙaraso wajen yakira sunan ta
Zuwa lokacin kuka take yi kan ta a ƙasa ta kasa amsawa
Yace "wai meke damunki ne? Ciwon me kike yi sai a amso miki maganin?"
Still shiru babu amsa sai kukan ta dake daɗa ƙaruwa
Malam Jamilu yace "Zainab taso kije da ita tasha magani".
Dasauri Zainab tataso tataho wajen tariƙo Halwa dake langaɓe wa, ta rufe fuskarta still tana kuka, suna fita tasoma sheƙa amai kamar zata amayo hanjin cikin ta, sabida babu komi a aman kasancewar bataci abinci ba, nan da nan hankalin Malaman yatashi suka fito waje suna mata sannu
Malam Kamal yace "gaskiya wannan ciwon be kamata abarta anan ba, yakamata amaida ita gida".
Malam Isma'il yace "Eh haka za'a yi kuwa, tunda nasan gidan su bari inje in kai ta".
Daga haka yajuya dasauri yanufi inda suke parcking yaburgo mashine ɗin sa yataho wajen, da taimakon Zainab aka ɗaura Halwa akan mashine ɗin, zuwa lokacin duk ta galabaita bata ma iya tsayuwa
Malam Jamilu yace "Zainab kihau bayan ta kuje tare, sai ku dawo tare da Malam Isma'il".
"To Malam". Cewar Zainab kenan, kana tahau bayan mashine ɗin
Sai da sukaga tafiyar su kafin Malaman suka koma ciki.
Koda suka isa gida bayan sun sauka, Zainab tariƙo ta suka shiga cikin gidan, Mama na ɗaki tana kwance tajiyo sallaman Zainab, amsa mata tayi tana tashi zaune, ahankali suke tafiya har suka isa bakin ƙofar Maman, Zainab taɗaga musu labule suka shige
"Subhanallah.. lafiya Zainab me yafaru da ita?" Mama tafaɗa tana tashi tsaye cike da ruɗewa
"Mama wlh jikin ta ne yayi tsanani, shine Malaman sukace adawo da ita gida".
Mama tariƙo ta tana zaunar da ita saman gadon ta, kana tace
"Dama tunda naga jikin nata da tsanani na san bazata iya taɓuwa komi ba, sai dai taurin kanta ya saka taƙi haƙura, gashi an dawo dake ai".
Zainab tace "Mama bari inje, Allah yaƙara lafiya".
"Ameen ameen Zainab, mungode kinji?"