Kenza eBookz

Batuol mamman complete novel - Chapter 10

Batuol mamman complete novel - Chapter 10

Batuol mamman complete novel Chapter 10: Batuol mamman complete novel Chapter 10. Tsawa Salisu ya daka mata "koma ki zauna. Bature muje"

3,349 words

Tsawa Salisu ya daka mata "koma ki zauna. Bature muje"

Bakin gate ya raka Bature ta bashi kudin mota sannan ya koma ciki. Tana nan tana rusa kuka Kande na bata hakuri. Yana zuwa ya finciko hannunta sai da Kande ta tsorata. Dakinsa ya kaita ya jefata kan gado iya karfinsa. Fuskarsa a daure babu wasa ko kadan ya jefa mata tambayar da ta kada mata hanji.

"Tun farkon haduwarmu dama Zayyan kike so?"

Shiru tayi sai faduwar gabanta da ta tsananta.

"Ki bani amsa mana!" Ya sake yi mata tsawa sai da ta firgice.

Wasu sababbin hawayen ta soma yi yaji kamar ya rufeta da duka.

"Kin cuceni, ban dade da aurenki ba zuciyata ta bani cewa ban yiwa kaina adalci wurin zabar matar aure ba. A tunanina na auro mace mara son zumunci ne kawai da raina na kasa da ita. Ashe kin wuce haka. Salame mijin kanwarki kike so kuma har kike kishi da ita alhalin kina gidan naki mijin"

Har yanzu ta kasa magana sai kuka. Shi din ma nasa idon da hawaye saboda bai taba kawo hakan a matsayin dalilin da yasa take yiwa Mairama haka ba.

"Bazaki je Sakkwato gaisuwa ba" kallonsa tayi da sauri ya sake hade rai "ke daga yau sai abu yayi tsanani sosai zanyi miki izinin fita kina ji na. Idan kika karya min doka wallahi, wallahi sai na shayar dake mamaki"

**********

Ranar da aka sallami Mairama a ranar Mal Aminu da Jume su ka amince da a kwashe kayanta ta koma gidansu Zayyan. Idan iyayenta sun zo sai su tafi da ita gida.

"Ku wuce da ita su Mubaraka sai su zo a kwashe kayan gobe tunda zaman barikin babu amfani"

Mairama tana jin haka ta ajiye kunyarta a gefe "Kawu ina son zuwa don akwai abubuwan da nake son hadawa da kaina"

Caraf a kunnen Maikudi "ko ma meye muma din jinin Zayyanu ne. Kije ki huta ni da kaina zan jagoranci zuwa a debo kayan saboda kada wani abu ya salwanta"

Soye idanu tayi don bazata yarda a hanata zuwa ba. Ta nuna musu akwai makota da take son yiwa sallama irinsu Christie wadda bata kara gani ba tun lokacin da tace zata je yi mata girki.

Mal Aminu yace "Ka barta taje Maikudi. Daga nan ma sai mu bincika muji ko akwai wani abu da zasu bawa iyalin mamatan. Mu bari jikinta ya kara kwari ko nan da kwana biyu ne"

Ransa baya so saboda ya kula tunda ta dage sai taje akwai dukiya dankare a gidan da bai taba zuwa ko kofarsa ba.

"Ina mukullin a bani na rike saboda 'yan barka da gaisuwa kada wata ta dafe"

"Maikudi kenan, ko ma wacece ba sai dai muce Allah Ya bada sa'a ba. Sata a gidan soja, gidan sojan ma a cikin bariki kamar mutum ya tashi da burin karar kwana" Gwaggo Ladi ta gwaba masa magana.

Bai sake magana ba su ka tafi gida. Jume tasa matan su Badaru gyarawa Mairama dakin Innar Zayyan. Tana shiga ta tuna ranar sunan Radhiya da hotunan da suka yi da Zayyan da Awwab a ciki. Idanunta da basa rabo da hawaye suka fara abinda ya zame musu jiki yanzu.

Jume da kanta tazo tace mata ta shirya ta fito zata yi mata wankan jego. Jariri kuma Gwaggo Ladi ta dauka tayi masa wanka irin wanda bai samu ba tun ranar haihuwarsa saboda kasancewarsu a asibiti.

**********

"Ya muke ta bin lungu ne yaro? Nayi zaton a irin unguwannin nan da suke malale da titi gidan yake"

Rayyanu ya kalli Malamijo ya sake daure zuciyarsa a karo na barkatai ya bashi amsa akan irin wadannan tambayoyin da yake ta yi masa.

"Gidan iyayenmu ne a nan unguwar. Zayyanu a cikin bariki ya zauna da iyalinsa"

Malamijo sai murmushi "Auhooo ko da naji. Ca nake a nan Mairaman tawa ta zauna ne"

Su hudu ne a ayarin tafiyar banda Rayyanu suka biyo motar haya. Nene Marka, Malamijo, Hajjo da kuma Salisu. Gidan yanzu Yadikko da Hajjo ne kawai a gidan, ya saki Dije da Inno yana shirin karo wata. Tun a tashar Kano ana cewa a kawo kudin mota Malamijo ya shiga tarin karya, daga baya ma sai yayi gaba yana dukan kirji sai da ya hango Salisu ya biya musu kudin motar su duka sannan ya dawo yana cewa kwarewa yayi.

"Sai ji nayi wani abu siririt ya wuce min ta makoshi. Kwarewa babu dadi, ammm nawa ne kudin motar ne?"

Nene tasan dalilin tafiyar tasa sai kawai ta dauke kai. Hajjo ce ta fada an biya yayi wata barazanar zura hannu a aljihu zai dauko kudin ya bawa shi. Sal da Salisu yace ya bari duk daga ne.

Iyaye da dangi duk lalacewarsu sunfi ace baka da kowa. Sallamar Malamijo kawai Mairama taji ta sa kuka sosai. Kuka ne na ganin babban gatan da ya rage mata duk fadin duniyar nan. Shine bango abin jingina a gareta wanda take sa ran idan tayi kukan rashin miji zai rarrasheta yace ta barwa Allah komai. Idan tayi kukan rayuwar marayunta zai yi mata alkawarin matsawar yana numfashi 'ya'yanta bazasu tagayyara ba.

Jikin Nene Marka ta zube suna kuka tare. Malamijo ya tausayawa Mairama sosai ya mika hannu ya dauki Radhiya. Zayyan wanda duka gidan an rasa mai kiran sunansa har Maikudi kuwa saboda tuna musu da marigayi da yake yi matar Badaru ta kwanto daga bayanta ta mikawa Hajjo.

"Iko sai mai shi, Malamijo dubi yaron nan don Ma'aiki."

Radhiya tana gefensa ya karbi jaririn yana kare masa kallo. Salisu yazo ya karbe shi shima ya ga kama sosai da mahaifinsa.

"Allah Ya raya mana kai karamin soja

"

Mazan sun koma waje inda ake zuwa yi musu ta'aziyya matan kuma suna daga ciki. Sai dare ne Mal Aminu ya sanar da Malamijo za'a kwaso kayan Mairama sai su tafi da ita.

"A'a a bar yarinya a gidan mijinta. Idan akwai wata dukiya da bazata iya juyawa ba ni sai na tafi da ita ba wani abu."

Maikudi yayi saurin cewa "dukiyar marayu zata fi dadi a hannun dangin uba. Saboda haka gobe zamuje ayi duk yadda za'ayi ne. Gida kuma ba nasu bane na bariki ne. Tunda ya rasu dole ne su tashi komai dadewa"

A hankali zantukan nasu suka fara neman komawa rigima. Maikudi da Malamijo kowa ya nuna zalamarsa a fili. Shiyasa kowa cikinsu yake ganin dole ya tsaya akan dukiyar da basu da tabbacin akwaita.

Shabiyun rana kuwa washegari suka isa kofar gidan da ya kasance na Mairama da Zayyan kwanaki kadan da suka wuce. Ta kalli gidan Zainab a rufe har yanzu. Tana son sanin halin da suke ciki da mazansu amma yanzu babu hali sai komai ya daidaita a nata bangaren. Gidan Christie ma a rufe yake. Bayan ta bude nata gidan sun shiga da yayyen Zayyan mata da kuma Hajjo sai ga wasu cikin abokan zamansu na kusa. Gaisuwar mijinta suka yi mata da barkar Zayyan karami. Ta tambayi ina Christie wata ta bata amsa da cewa ranar da ta haihu Christie tazo tayi mata girki kuma ta farfadawa makota haihuwar. Ta koma daidai lokacin da Mairama ta suma. A nan take jin duka sojojin sun rasu ciki kuwa harda mijinta. Bata iya shiga ba ta koma gida bayan ta sauke musu Radhiya. Shine aka sami wani da ya san gidansu Zayyan aka fada musu. Ita kuma Christie ta tafi garinsu ta fadi mutuwar har yanzu bata dawo ba.

Duka matan abin tausayi musamman wadanda mazansu suka tafi a bayan su Zayyan. Suna cike da tsoro da fargabar me zai je ya dawo.

Wasunsu sun saka hannu wurin tattare kayan kitchen da na falon Mairama ana hade komai wuri guda ana fitarwa. Cikin dakin ta shiga zuciyarta tayi matukar rauni. Shikenan daga yau duk wasu memories da suka gina da Zayyan a gidan nan cikin wannan dakin sai dai zu dawo mata a tunani. Kukanta Hajjo ta jiyo ta shiga dakin da sauri.

"Haba Mairama ashe bazaki sakawa zuciyarki salama ba? Ni ko kadan ban so aka ce wai azo kwasar kaya da wuri kamar ana korarki ba. Su dakata ki sami nutsuwar zuciya sun ki"

Mairama ta bude wani akwai ta dauko envelop din da Zayyan ya bata hannu na rawa ta saka a jakar hannunta sannan aka fara hada kayan gidan.

Malamijo yana waje yaki shiga ba don kunya ba sai don bakinciki. Shi kadai a ransa yake nanata an yaudareshi aka ce masa Zayyan soja ne. To yaji sojan ne amma ba wani mai mukami bane ashe. Ji dai wannan akurki da ya ajiye masa 'yarsa ya raya a zuciyarsa. Kuma ashe ma ba nasa bane. To duka kudaden da yake masa alheri dasu a ina yake samowa? Faduwar gaba yaji da ya tuna indai fa babu wani abin kirki da ya bari komai na Mairama da 'ya'yan wuyansa zai dawo. Hodijan inji mutanensa, aradun Allah bazai iya karawa kansa nauyi ba. Yanzu fa yara goma sha bakwai gareshi. Salame ce kadai a gidan miji tunda dai Zayyan ya rasu. Gata ta tunda tayi aure ta ari rigar rashin mutumci ta saka.Tsaki yaja sai hankalinsa ya koma ciki inda yake jiyo muryar Maikudi.

"Kai wannan takadirin yaro da gani zaiyi mugunta. Me kuma yake nema a cikin mata?"

Shiga yayi da Salisu ya sami Maikudi yana fada "ki fito min da duk wani kudi ko takardun abubuwa masu mahimmanci na Zayyan. Dukiyar magada sai da saka ido. Ba wai da ka zaki dauke komai ki rike ba"

Salisu ya riko hannunsa "kaga Mal Maikudi duk abin nan ba na rigima bane. Mairama ba jahila bace da zata ci dukiyar mamaci. Sai dai fa ina so ka sani duk danginku babu mai gadon Zayyan sai Mairama da 'ya'yanta"

Kamar zai kaiwa Salisu duka ya soma fada "ni nasan ba banza ba kuka taho kwanku da kwarkwata. Ashe da manufarku. To babu wanda ya isa yayi sama da fadi da dukiyar magada muddin ina raye"

Mairama dai sai kuka. Malamijo ya zakalkale yana ta zubar musu da daraja a gaban 'yan uwan Zayyan. Idan Maikudi yayi shi za'a ce da sauran kuruciya. Shi kuwa yana mahaifinta ga jikoki har uku amma har yau bai fasa halinsa ba.

Mal Aminu da kawunsu Zayyan sun shigo sun same su ana ta mayar da magana. Sam Mal Aminu baiji dadi ba. Ga Mairama sai ajiyar zuciya kawai take yi.

"Daga can ofishin nasu nake an kaini har wurin wani babba cikinsu a nan munyi magana. A takaice dai muna da yawa da muka rasa 'yan uwa a wurin nan. Amma yace muyi hakuri ba'a turo komai daga gwamnatin tarayya ba da zasu sallami iyalan sojojin ko kuma masu rauni"

"Ikon Allah, yanzu ace mutum ya rasa rayuwarsa a bakin aikinku amma babu sallama ga iyalansa da maraici ya kama su?" Cewar Salisu

"Don ma baka je wurin bane. Mutanen da yawa wallahi. Sun ce kuma sojojin da aka rasa suna da yawa ba wai na nan bane kadai. Kuma wai gwamnati bata da kudi amma zasu neme mu idan an sami wani abin"

"Wannan ai zancen banza ne, bata da kudin take kashe mana 'yan uwa? Ni bazan hakura ba. Wannan magana kuma bazan bari ta mutu a nan ba." Maikudi yace yana tashi tsaye "idan ma an fada ne don a sa jikina yayi sanyi kada na tsayawa marayun nan wallahi sai naje" ya zubawa Mal Aminu idanu.

Murmushi yayi kawai yace motar daukan kayan tazo. Kawunsu ne ma ya rinka yi masa fadan baya son rashin kunya. To amma da yake duka talakawa ne maganarsu bata wani tasiri a wurinsa.

Abu kamar wasa Mairama da tazo barikin nan a matsayin amarya kasa da shekara biyu wai har anyi zaman an gama. Mijinta abin kaunarta ya tafi ya barta a hannun wadanda basu damu da halin da take ciki ba, kawunansu kawai suka sani.

A daren Malamijo yace su shirya da wuri zasu wuce gobe. Mairama ta roke shi alfarmar zata je gidansu Zainab kafin su tafi. Jume tana zaune tare da Mairama bayan ta yiwa Zayyan karami wankan yamma tace mata "yanzu Mairama daga yau shikenan ko? Nasan da wuya ku rinka zuwa tunda kin san ba ni bace na haifi Zayyanu. Ga bakin kishi yasa ni ban san ta yadda za'ayi na sami dangin mahaifiyarsa ba balle su san halin da ake ciki ma "

"In sha Allahu zan rinka zuwa Jume. Idan basu zo ba wa zasu nuna a matsayin dangin uba?"

"To nagode Mairama. Sai kin daura dammarar hakuri da juriya. Yanzu sabuwar rayuwa ce zata bijiro miki da baki taba zato da tsammani ba." Hawaye ya zubo mata da ta tuna rasuwar Mal Muhammadu.

Washegari da wuri Mairama ta tafi gidansu Zainab. Allah Ya taimaketa bata mance hanyar ba. Mahaifiyar Zainab din ta samu wadda ta fada mata kwana hudu da suka wuce babanta ya kaita Kano gidansu Hadir. Duk da bata san kan garin Kanon sosai ta nemi tayi mata kwatance amma anyi rashin sa'a ko sunan unguwar bazata iya tunawa ba don wahala yake mata. Mairama tana kuka tace ta fada mata tazo itama zata koma garinsu.

"Kema mijin naki yaji rauni ne?"

"Rasuwa yayi."

Idanu ta zaro "idan Hadir yaji ban yaya zai ji ba. Allah Ya zama gatanku Mairama"

Sallama tayi mata ta koma gidan domin su karasa shirin tafiya. A daren jiya ta bude envelop din da Zayyan ya bar mata. Ashe gabadaya sauran kudin gadonsa ne ya bar mata da takardun gidansa na Kano. Dasu ta fita a jakarta idan ta koma zata fito dasu ta nunawa iyayen. Dama suna rayuwa ne bayan tafiyar mazan akan albashinsu da ake bawa matan. Kudi ne da bai wani taka kara ya karya ba. Wasikarta kuwa zuciyarta ta kasa bata kwarin gwiwar karantawa har lokacin.

********** [5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Kwana biyu da rabin wuni Mairama tayi kafin ta gane inda take da babbar jarabawar da ta tunkaro rayuwarta. Ta farfado da misalin uku na rana washegarin ranar da ta haihu. Idanunta a rufe suke amma tana iya jiyo maganganu kamar ana fada. A hankali ta fara fuskantar me ake cewa wanda yayi sanadin fitowar hawaye daga idanunta, kuma har lokacin a rufe suke.

"Ni dai na fada miki gobe zan tura Rayyanu yaje garinsu ya sanar da iyayenta su zo su dauketa don bazan iya jigila ba."

"Haba Maikudi kai kuwa baka ganin ga danyen jego ga rashin lafiya. A barta ta huta mana"

Gwaggo Ladi da tayi maganar ya kalla darajar mijinta Mal Aminu ya kasa bata amsar da yayi niyya. Wani dan tunani yayi ya kara tabbatarwa gara yabi komai a hankali don samun biyan bukata.

"To naji sai ta zauna har sai ta gama takaba an raba gado. Ince ko hakan yayi" ya mayar da kallonsa ga Mal.Aminu da ya dauke kansa saboda takaicin halin Maikudi. Yaron ya fita zakka tamkar ba jinin Mal Muhammadu ba.

Mal Aminu da ya gama tofe jariri da addu'a ya dago kansa "bana son hauka Maikudi. Takaba dai tana haihuwa ta fita. Sannan tun muna shaida juna kada inji kada in gani, kaf abinda Zayyanu ya bari na matarsa ne da 'ya'yansa tunda yana da da namiji."

A fusace ya juyo "inji uban wa?"

"Inji ubanka"

Mamaki kamar ya kashe shi saboda Jume ce ta bashi wannan amsar. Akan tabarma take tana bawa Radhiya abinci. Daga jiya zuwa yau tayi wuri-wuri da ita. Rasuwar Zayyan ta tabata fiye da zato da tsammaninta. Duk wata mugunta da ta taba yiwa mahaifiyarsa dashi kansa sune suka yi mata dabaibayi. Cikinsu babu wanda ya taba nufinta da sharri gashi sun bar mata duniyar tayi yadda take so. Nadama ce ta gaske take nukurkusar zuciyarta. Ga Maikudu don abin kunya daga jiya zuwa yau banda rashin mutumci babu abinda yake zubawa a dakin. Daure fuska ta sake yi

"Saboda baka san me kake yi ba ace kaninka ya rasu amma ko a jikinka?"

"Kina ji fa aka ce yayi wata guda harda dorin kwanaki, duk dacin mutuwa ai yaci ace tayi sauki an fara fuskantar gaba"

Mairamu ta kasa boye kukan zucin ta koma yi a fili. Ashe har yafi wata da rasuwa bata da masaniya. Shine take ci tasha har tayi wasa da dariya? Ashe Sojanta ya koma ga Allah take ta tunanin dawowarsa. Yanzu shikenan nata mijin saboda soja ne ko kabarinsa babu wani danginsa da zai sani? Anyi masa wankan gawa? An sallace shi? Wace irin mutuwa yayi duk basu sani ba.

Kukanta ya tsananta Gwaggo Ladi ta tashi ta matsa kusa da ita ta tsaya a gefen gadon.

"Mairama hakuri zakiyi da yawaita yi masa addu'a"

Rarrashinta suke ta yi ita da Jume sannan Mal Aminu ya fita saboda ance ta shayar da jaririn.

Maikudi yayi qiqam kamar sanda sai da Jume tace ya fita, yayi waje yana surutai.

Yaron ta karba wanda rabonta dashi tun jiya. Yaji yunwa kuwa sai ruwa aka rinka bashi da tana kwance.

Gwaggo Ladi tace Malam yayi masa huduba da Muhammad Zayyan. Ina fata hakan yayi miki"

Hawayen Mairama har fuskar jaririn tayi murmushi "Sojana Allah Ya raya min kai."

**********

"Wai Zayyanu dai Zayyanu soja mijin 'yata Mairama kake nufi?" Malamijo yayi maganar kamar zaiyi kuka.

"Shi nake nufi. Allah Yayi masa rasuwa a kasar da suka je" Rayyanu ya bashi amsa. Shi da Badaru da 'yan uwansu mata kaf mutuwar Zayyan ta shigesu sosai. Mutum mai barkwanci da saurin manta bacin rai. Duk yadda su ke bata masa bai hana shi kyakyawan zumunci dasu ba ko da su bazasu yi masa kallon arziki ba.

Malamijo ya daga hannu ya dora a ka "Laaaaahhhh ha'ila ha ilallahu, kaico Mairama, 'yar marainiyata ta rasa miji kuma"

Lokaci kankani a tsakani zance ya bazu ko ina mijin Mairama ya rasu a filin daga. Mutane suka fara zuwa yiwa Malamiji ta'aziyya yana cewa nan da kwana biyu zai wuce Sakkwato.

A cikin gidan ma jikinsu duk yayi sanyi. Ba wani haduwa suke yi sosai ba saboda nisan garuruwansu amma duk da haka a iya lokutan da su ka ganshi anyi masa shaidar arziki. Malamijo yasa a dafa abincin sadaka ya saki bakin aljihu abinda basu saba gani ba. Cikin yaransa maza ya tura babban mai bin Mairama a shekaru yaje Balan ya sanar da Nene Marka. Idan zata bisu ta'aziyya ta taho washegari su wuce jibi. Sannan ya tura mai bi masa Kano gidan Salame.

Suna zaune shi da 'yan gaisuwa wani yake tambayar yaya Zayyan din ya rasu don shi ma akwai dan uwansa soja a kudu, yana tsoron a tura shi yaki. Malamijo bai tashi bada amsa ba sai da yaga Rayyanu ya tashi zai zaga ya soma jawabi.

"Hmm ai ba'a cewa komai Haladu. Yaron nan harbi, harbi dai da kake ji da gani a finafinan su Amita Bachan sai da aka sakar masa harsashi kusan goma amma a haka ya rinka kutsa kai cikin abokan gaba yana gamawa dasu. Bawan Allah ya tafi ya barwa Mairama da yaranta komai nasa. Ko sati batayi da haihuwa ba. Shine ma zanje domin na tattaro dukiyar na kawo nan sai na juya mata da kaina saboda duk yadda ka kai da yarda da wani ba kamar naka ba. Nakan ma mahaifi"[5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Maikudi ne tsaye a ofishin da aka tura shi cikin barikin su Zayyan akan maganar kudi ne dai.

"Jiya Babanku yazo akan zancen nan mun fada masa bamu da komai. Ya bada adireshinsa duk lokacin da kudi yazo zamu nemeku" officer din ya bashi amsa bayan ya gama jero tambayoyi.

Yana hargaginsa na rashin mutumci yace "Ashe cewa yayi shine babanmu don ya ci kudin gado. To wallahi karya yake. Babu wata alaka ta jini tsakaninmu"

Wani sojan ne ya shigo yana tambayar wancan me yake faruwa cikin harshen turanci. Sai da ya sara masa ya bashi amsa da gani ya fishi mukami.

Maikudi yana jin ana bayani duk da bai iya gane duka maganar amma ya dan fahimci me akeyi ya katse wancan "You understant Zayyan Muhammad Tureta is die? Me. Biggggggggg broza. Is me faza dinmu daya ai" ya nuna kansa yana murmushi yana so su fahimci shine babban wan Zayyan.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull