Kenza eBookz

Batuol mamman complete novel - Chapter 9

Batuol mamman complete novel - Chapter 9

Batuol mamman complete novel Chapter 9: Batuol mamman complete novel Chapter 9. "Nine shugabanku a harkar abinci" sai sowa da tafi yayi murmushi "Chief…

3,370 words

"Nine shugabanku a harkar abinci" sai sowa da tafi yayi murmushi "Chief cook kuke gani. Suna na Captain Ogbonna Odili. Ina da mata Mabel da yara hudu a Enugu. Ogechi, Uloma, Nneka da Kachiku muna kiransa Kachi. Kamar kowa a nan ina matukar son family dina. Musamman ma Uloma saboda tana da kokari sosai a school. Yanzu zaka rubuta mata abu indai ta karance shi daga farko zuwa karshe to ya gama zama. Da kuke ganina kudi nake nema domin na kaita wata babbar makaranta a garinmu ta gifted children. Uloma is born to be a great doctor"

"So shall it beeeee" wasu suka amsa da ihunsu na sojoji. Capt. Ogbonna yana ta dariya ya cigaba da hirar iyalinsa ana tayashi murna.

Bayan shi sai aka ce mutum daya cikin newcomers ya gabatar da kansa. Papa Dolapo ne ya fara shima yana bayani ana dariya da kuma nuna tausayi musamman da yace ya baro matarsa da tsohon ciki suna jinjina masa.

Zayyan sai ya tuna cikin jikin tasa matar ya daga hannu "I am next please, please"

Dariya suka sa ana tsokanarsa ya dake yana basu labarin Mairama da Radhiya "babban farincikina kafin na taho Alheran ta iya kiran suna na"

"Fada mana ya take cewa" wani yace sauran na goya masa baya.

"Daaadaa"

Ihunsu ya karade dakin masu baccin ma sun tashi anayi dasu.

"Kuma nima matata tana da ciki amma sai mun koma zata haihu In sha Allah. Sorry Papa Dolapo kaine za'ayi ba kai"

Hadir yayi dariya yana cewa Zayyan yayi masa wayo "muna komawa da wata tara zaka ji Zainab ta haihu"

Tafawa suka yi wani mutumin Adamawa Austin Bakari dan kabilar Chamba ya fara bada labarin iyayensa tsofaffi wanda sun dora duk wani buri nasu akan cigabansa. Labarin iyayen nasa akwai ban tausayi domin dukkansu guragu ne da basu da mataimaki sai shi kadai. Dan albashin nasa shine cinsu shine shansu. Ya sanya sauran cikin yanayi na jimami kowa na fadin albarkacin bakinsa sai su ka ji wata muguwar kara mai razanarwa.

Basu gama da wannan firgicin da ya sanyasu daukan bindigoginsu cikin sauri ba kuma sai ga daya daga cikin masu patrol na wannan daren ya shigo bindigarsa tana kan saiti ya fada musu 'yan tawayen da su ka addabi wannan sansanin nasu sun kawo musu hari.

Idan da suna jin wai-wai, yau ga su zahiri a filin daga. Harbi ne yake tashi ko ta ina suka firfito kan kace meye wannan wurin ya kaure. Anyi musayar harsashi sosai duk da duhun dare sun sami damar fatattakar mutanen har da nasarar cafke mutum daya.

Wani bacci dama babu shi a lissafi maza suna filin daga. Kwana ukun farko sunyi su ne cikin rudani da tashin hankali. Da gasken gaske 'yan tawayen suke son korar sojojin Nigeria daga wurin. Akwai wuraren da suke tsammanin samun nasara su janyo mutanen garin domin a hadu a ture gwamnatin shugaba mai ci a lokacin. Rigima ta cikin gida a ganinsu mai zai kawo wasu baki da abin bai shafa ba a matsayin peacekeepers.

Kafin wani lokaci su Zayyan sun kara gogewa da halin da suka tsinci kansu yanzu. Shine ya koma yi musu limanci bayan tafiyar Abdulwahid Gbenga wanda ya kasance da shine limamin. Duk daren da babu gajiya sosai a tare dasu suna zaman hira a daki ko a waje. Su kunna wuta su zagaye wurin suna jin dumi saboda shigowar sanyi gadan gadan. Da safe kuma masu manyan mukami su ke jagorantar training dinsu don ba zama.

Watansu daya da kwanaki annobar cholera ta shigo kauyen da yafi kusa da inda suke. Garin kai taimako wurin fitar da marasa lafiyan zuwa asibiti a cikin gari wasunsu suka dauko ciwon suka kawo musu.

Cikin kwanaki bakwai mutum tara sun kamu. Amai suke yi sosai da gudawa. Suna ta kokarin neman agajin babban sansanin domin a kawo musu magunguna sannan a dauke marasa lafiyan cikinsu zuwa asibiti amma abu yaci tura. Ba wai sakon bai isa garesu bane, yaje amma su ma suna jiran command daga babbar headquarter saboda komai na soja bisa doka da oda ake yi.

Major Mustapha da ya ankara cewa sansanin su Zayyan ne ya matsa lamba sosai ranar da za'a kai musu maganin bayan kwanaki shadaya da fara cutar yabi bayan ma'aikatan lafiyan cikinsu. Su ma din sojoji ne amma hannuwan rigarsu daga dantse akwai wani farin abu da yake nuni da alamun cewa su likitoci ne.

Major Mustapha har yanzu bashi da magana sosai amma ya damu kwarai da kannen nasa Zayyan da Hadir. Motarsu ta iso sansanin a daidai lokacin da Zayyan yake limancin sallatar gawar Papa Dolapo wanda yayi ta fama da cutar ta amai da gudawa na kwana uku kafin rai yayi halinsa. Jikin Major yayi sanyi haka na likiticin da suke tare dasu. Zagaye sansanin nasu akayi da wasu irin wayoyi masu kaifi aka rubuta musu QUARANTINE da manyan harufa. Ma'ana an kebesu daga shiga ko fita har sai an sami kyakkyawan tabbacin cutar babu sauranta a tare dasu. Ana gudun su sanyawa wasu sojijin ko kuma su sakawa mutanen wani kauyen garin kai taimako.

Likitocin kadai aka bari suka shiga suma sun rufe jiki sosai da wasu kaya hatta fuskokinsu ba'a gani. Sunyiwa kowa allura sannan aka shiga bawa marasa lafiyan taimakon da ya dace. Ta bayan wayar suke magana da Major yana tambayarsu halin da suke ciki. Nuna masa suke yi babu wani abu lafiya kalau suke.

Ta'aziyar Papa Dolapo yayi musu wanda aka saka gawarsa a cikin motar da zasu koma da ita nasu sansanin. Idan sunyi sa'a za'a bari gawar ta koma Nigeria. Idan basuyi ba kuma to a nan za'a binne shi iyalinsa su dau hakuri.

"Shekaranjiya da aka toro wani troop din wannan wasikar tazo. Ta Lt Badmus ce"

Wasikar ya dago musu kowa jiki a sanyaye domin Papa Dolapo ne Lt Badmus.

Major Mustapha ya kara da cewa "duk da ban bude ba amma an fada min matarsa ce ta haihu. Zayyan makotanku ne ko?"

Kai ya gyada ya kasa cewa komai ya juya ya bar wurin zuciya tayi nauyi.

"Follow him Lieutenant" ya umarci Hadir.

Sai da ya ga sun shiga cikin wurin da yake mazaunin dakinsu ya koma motar da ta kawusu suka bar wurin.

**********

Rayuwar matan da mazajensu basa nan a barikin babu dadi. Ci da sha bai yanke ba tunda ana basu albashinsu to amma fa kowacce kullum kwanan duniya da fargaba take kwana matsawar ba mijinta ta gani ya dawo ba.

Mairama, Mami da Zainab dauriya suke yi kowacce tana son nuna ita ma jarumar kanta ce mai hakuri da juriya. A gefe daya basu fasa yiwa mazajensu addu'a da fatan alkhairi ba.

Awwab kusan ya dawo gidan Mairama da zama. A nan yake kwana idan ya dawo daga makaranta ya lalace wurin wasa da Radhiya. Sunyi shakuwar da har Mairama tana tabawa kyuya musamman idan zai fita. Kyalesu take yi tana fama da cikinta don ma laulayin yayi sauki yanzu.

Awwab ya fita da Radhiya sun tafi wurin Mami sai Mairama ita kadai a cikin gida. Hayaniya ta soma ji daga waje ta yafa mayafi ta leka. Can ta hango Zainab da wasu matan da suke tare sun zagaye wata. Fitowa tayi cikin sauri jin kamar ana kuka.

"Innolillahi wa inno ilaihi raji'oon....Oko mi tikú" kuka Maman Dolapo take tana tumani a kasa ga danyen jego.

Mairama ta tsorata da yanayin da ta ganta, ta taba wadda ta fi kusa da ita "what is wrong with her"

"Ahhh Mama Radhiya...Papa Dolapo don die oooo"

Ita ce amsar da ta doki kunnenta taji gabanta ya yanke ya fadi. Zainab ta matso kusa da ita tana fada mata wai yanzu aka sanar dasu rasuwar tasa. Cholera ce ta kashe shi Zayyan ne ma ya sallace shi, sannan anyi masa sutura a can kasar.

Kuka su ka taya Mama Dolapo aka kaita cikin gidanta. Bayan kwana biyu sai ga 'yan uwanta da yayan mijin suka zo daukansu ita da yaranta guda hudu zasu koma Akure. Ranar ma wani sabon kukan ne ya barke a tsakaninsu domin da yawa sun sani da wahala su sake sanya juna a ido har abada. Maman Dolapo ta tafi ta barsu da kewa da kuma fargabar labarin wa zasu sake samu kuma.

**********

Jaruman kasarmu suna can suna aiki tukuru bisa umarnin da kasa ta basu na wanzar da zaman lafiya a daya daga cikin kasashen gamayyar ECOWAS.

A yayin da magidanta suke tashi da safe su je ofishoshinsu yamma na yi su koma gida ga iyalansu, su ci, su sha mai kyau, su kalli matansu da 'ya'yansu su ji dadi wadannan sojoji suna cikin dokar daji suna fama da cizon sauro da wasu nau'in kwarin, rashin abinci mai gina jiki, karancin tsaftataccen ruwa balle ayi maganar wanka kullum da sauransu. Masu aure a cikinsu suna kewar matansu amma babu halin kasancewa dasu.

Yau da gobe kunnuwa sun saba da jin harbi da karar tashin bomb. Da idanunsu suke ganin 'yan uwansu, abokansu harsashi ya huda wani sassa na jikinsu sun mutu a take. Ko kuma bomb ya tashi dasu kana kallon mutumin da kuke tafiya kuna hira dashi ya tarwatse gabobin jikinsa sun watsu ko ta ina.

Jaruman nan sun yarda sun aminci su sadaukar da rayukansu a duk lokacin da kasa ta bukata domin zaman lafiya da kwanciyar hankanlin al'ummar kasarsu. Babu ruwansu da addini, kabila ko wata al'ada. Sun hadu akan abu daya ne wato TSARO na rayuka da dukiya.

A yayin da wahala tayi wahala, anga jiya anga yau a fanin rashin makusanta ko a kama mutum a sansanin abokan gaba a gana masa azaba domin ya fadi wani sirri da za'a iya cutar da nasa 'yan uwan sai ka ga zukatansu sun bushe ana yi musu kallon mutane marasa tausayi da imani. Sai dai abubuwan da idanunsu suka gani da wanda kunne yaji wani fa har ya bar duniya bazai taba kusantar abu makamancin wannan ba.

Jarumanmu ababen alfaharinmu, sadaukanmu da babu albashin da kasa zata basu da zai wanke ciwuka na zahiri da badini da suke dawowa dasu daga filin daga. Ga kuma iyalansu a yashe madogaran nasu, bangon jinginar nasu basa nan.

Wata hudu da tafiyarsu Zayyan sun fara jiyo kamshin komawa gida wata rana da yamma gari ya hade yayi bakikkirin ruwa zai iya saukowa a kowane lokaci wani mutum yazo wurin gaje gaje dashi da shiga irin ta mutanen wani kauye a kusa dasu. Jikinsa duk raunuka yace 'yan tawaye sun yiwa garinsu kawanya suna harbi kan mai uwa da wabi.

Sun riga sun san mutanen suna yin haka shiyasa su ka shiga motarsu ta yaki su ka durfafi kauyen da hanzari. A bakin wurin da yake kamar gate dinsu ne su ka hadu da motar su Major Mustapha. Ya fake da aiki ya taho ganin kannensa.

Duk da bambancin matsayi bai hana Zayyan zuwa ya rungume shi ba. Major yayi turus yana cewa. "Stand at attention Lady"

Zayyan ya dago yana gyara rigarsa ya dan basar "Sorry Sir"

Major Mustapha sai yayi murmushi yana mikawa Hadir hannu. "My Ladies are all grown up, sun dena dariya"

Zayyan ya kara gyara fuska sai dai dole dariya ta kwace masa. Karar bomb suka ji mutumin da ya kawo rahoton yace 'yan tawayen sun kai mota shida. Su Major Mustapha sai kawai su ka bisu.

Sai da suka yi rabin tafiya kawai babu zato babu tsammani sai tashin bomb suka ji a gabansu ga ruwa ya fara sauka. Mutane ne suka fara bullowa ta tsakanin bishiyu da yawa ba na wasa ba sun zagayesu. Babu wata mafita sai fitowa suka yi suna musayar harsashi ga wuta motarsu ta kama saboda tankin mai da aka harba.

Bayan wani lokaci a cikin wannan yanayi ruwa mai karfi ya soma sauka kamar da bakin kwarya a cikin jejin gari yayi duhu baka ganin komai sai tashin kura, hayaki da wutar da ruwan bai gama kashewa ba. A gefe guda kuma Zayyan da Hadir ne suke gudun ceton rayukansu sakamakon bomaboman da suka tashi a wurin har uku ga harbin bindiga da bazasu iya tantance takamaimai daga ina yake fitowa ba.

A motocin yaki uku suka fito banda babbar range rover da suka ciko ta su Major Mustapha. A lissafe sun kai mutum ashirin da takwas amma su biyun suka rage wanda kusan da taimakon Zayyan ne Hadir bai mutu ba. Duk inda ka juya gawarwaki ne kwance cikin ruwa da jini. Kallo daya zaka yiwa wurin zuciya ta tsinke kaji inama dai mafarki ne. Duk mai imani bazai so koda makiyinsa ya tsinci kansa a wurin ba. Suna cikin wannan jeji dumu-dumu a tsakanin abokan gaba. Hankulansu a tashe kunnuwansu basa jin komai sun dode saboda karar bomb ya yi musu karfi.

Zayyan ne ya hango Major Mustapha wanda a bisa la'akari da matsayi shine shugabansu a wannan fitar. Mutumin da yake tsananin mutuntawa kwance yana daga hannu. Baya yayi da sauri Hadir yayi masa kallon mamaki don bai iya ganin komai shi saboda karfin ruwan "kada kace min komawa zakayi? Kazo mu bar wurin nan don Allah"

Kallon Hadir yayi ya sake kallon Major din ya koma gareshi a guje. Dago shi yayi da zafin nama sautin harsashi yasa shi komawa ya kifa a kansa suka fadi tare. Wata siririyar kara Major Mustapha ya saki mai cike da tsananin azaba wadda ta saka shi kai duba gareshi. Wani mummunan firgici ne ya saukar masa ganin kafar Major din ta dama a gutsire bomb ya tarwatsata. Zuciyarsa ce tayi nauyi ya soma kokarin daga shi domin su gudu.

Wata damka yaji ya kai masa ruwa yana wanke musu fuskoki "Lieutenant get out of here"

Bai saurare shi ba ya ciccibe shi duk da cewa ya fishi girma sosai ya saba shi a baya. Ture shi yaji yana yi yana dan dake muryarsa "this is my final command to you Tureta. Go!"

Sojoji sun horo da tsananin biyayya ga na gaba amma wannan karon bazai bi ba. Gudu ya soma yi dashi suka nufi inda Hadir yake tsaye hannunsa na zubar jini sakamakon harbinsa da akayi suka soma yankar daji.

Cak ya tsaya ya dena tafiya har Hadir yana cewa "muje mana"

Gabansa ke lugude ya kalli kafarsa ya dago a razane "Karbe shi ku bar wurin nan"

Major ya dan leko da kansa ta saman kafadar Zayyan "Lieutenant?"

Wata ajiyar zuciya ya sauke kafin Hadir ya karbi goyon duk da shima yana da raunuka. Matsawa yace suyi nesa dashi sannan ya dago idanunsa da suka jike da hawaye sosai. Kamar mai rada yake musu bayani.

"Bomb ne"

Su biyun duka suka kalle shi a gigice. Bai nuna damuwa ba ya cigaba da magana hawayensa suna tona asirin firgicinsa. Motsi kadan zaiyi bomb din wanda aka binne cikin kasa ya tarwatsa shi. Daya bayan daya yake kallonsu

"My friend..." yace da Hadir

"....Major am afraid this is the end"

Abinda Major ya dade baiyi ba ya soma shima sai kuka duka su ukun babu mai rarrashin dan uwansa.

Kafarsa ce ta danyi rawa cikin karaji yace su bar wurin. Ba yadda suka iya dole suka bar wurin a guje zukatansu suna kuka idanu na hawaye. Basuyi nisa sosai ba suka jiyo muryarsa mai dadin sauraro idan yana yi musu limanci.

"Mairama, Alheran waye zai dubi iyalina?"

Kuka ya fashe dashi sosai a hankali ya soma karanto kalmar shahada yana ji a ransa wannan ma dama ce da Allah Ya bashi.

Sunyi gudun rabin kilometer suka ji wata gigitacciyar kara wadda tasa su biyun faduwa su ka gangara kasan wani katon rami. Kafin su kai kasansa daga Major Mustapha har Hadir tunaninsu yana ga Zayyan Muhammad Tureta. Zayyan sarkin barkwanci, mutum mai tsananin so da kaunar iyalinsa da basu da wani wanda zasu jingina dashi suji dadi idan ba shi ba ya mutu a bakin aiki bayan yayi matukar kokari wurin tseratar da rayukansu. [5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Dattijuwa ce goye da yaro tana gurfane a gaban gadon Salame wadda take hakimce tana bata umarnin ayyukan da zata yi a cikin gidan. Banda kudi sune masu gida rana yaushe wannan mata da a shekaru zata girmi Ta Madina ace ita ce Salame 'yar cikin cikinta take yiwa rashin kunya son rai tana kada kafafu tayi daurin Mayam Babangida.

"Kada ki sake na fito baki gama aikin nan ba Kande" ta kare cikin fada.

"Sha Allahu ma zan gama da wuri." Sai ta dan kwantar da kai "nace ko na kwantar miki da Halifa tunda ya riga yayi bacci? Aikin nawa zai fi sauri"

Wata uwar harara da Salame ta galla mata ya sanya ta tashi da sauri ta fita daga dakin. Tana fitowa ta sami wani matashi yana sallama. Kallo daya tayi masa ta gane ya hada jini da matar gidan shiyasa tace ya zauna. Ruwa ta kawo masa sannan ta sanar da Salame tayi bako.

Sai da ta gama bata lokaci sannan ta fito tana takaicin hanata hutu da akayi. Tun aurenta da Salisu bazata ce ga wata rana da take cikin farinciki sosai ba. Haka dai take rayuwa daga fada sai masifa sai kuma muguwar hassadar Mairama da tayi sake ta kama zuciyarta sosai.

Dago labulen dakinta tayi ta fito. A wulakance take kallon kanin nata "ah'a Bature kai ne dama"

Zamowa yayi daga kan kujerar ya gaisheta. Bai manta zuwansu da sallah ba inda ta karesu musu tas wai sun haye kujeru abinda ba'a saba ba. Da suka koma gida kowa yana korafi suna cewa da Adda Mairama ce bazata musu haka ba banda shi don ransa ya baci. Ya dai ci alwashin idan ba aike ba babu abinda zai sake kaishi gidanta. Gaisuwar kuwa albarkacin mai aikinta da ya gani ne kada ace basu da hadin kai. Kusan halinsu daya da Mairama shiyasa Malamijo ya aiko shi don sauran babu mai yarda yazo.

"Wani abin ne ya faru kazo ko kuwa?"

Shigowar Salisu kenan yaji yadda take yiwa kaninta magana. Shi ya rasa dalilinta na kin 'yan uwanta yanzu kaf bata son mu'amala ta hadasu. Nashi dangin ma bata raga musu amma yana daf da magance matsalar nan.

Bature ya gaishe shi ya amsa a mutumce sannan yace ta biyo shi daki. Bakin nan a gaba ta bi bayansa.

"Me yake damunki ne? Yaro ya taho tun daga Sumaila babu wata tarba me kyau sai me ya faru? Yanzu ke da 'yan uwanki babu wanda zai zo don sada zumunci wurinki sai da wani dalili?" Ya jero mata tambayoyin cikin bacin rai.

Juya idanu tayi "ai dai 'yan uwana ne ba na mutum ba"

"Ni kike yiwa magana haka ko Salame?"

Bata saurare shi ba ta fice don sallamar Bature ya koma inda ya fito. Salisu ashe yana bayanta sai ganinsa tayi ya zauna yana tambayarsa mutanen gida.

"Kawo masa abinci mana Salame" ya umarceta.

Cire baki tayi ta kwalawa Kande kira.

"Ki kyale Kande aiki na ga tana yi. Kuma shi Halifa ba'a kwantar dashi ne? Kusan a bayan matar nan yake wuni ita bata huta ba shi ba'a barshi ya sake yayi wasa ba"

"Idan ta sauke shi damuna zaiyi. Kuma dai tunda biyanta akeyi meye a ciki?"

"Babu komai kuwa tunda kudinki ne Hajiya"

Magana suke yiwa juna a hasale kowa rai a bace. Bature da bashi da sha'awar kwanar musu a gida ya katse rigimar ta hanyar fada musu abinda aka turo shi ya fada. A tare suka juyo kansa. Salisu hankali a tashe Salame kuwa numfashinta taji ya tsaya na wucin gadi.

"Wane Zayyan din?" Salisu ya tattaro karfin halin tambaya.

"Mijin Adda Mairama."

"Salame kin..." kasa karasa magana yayi ganin ta tafi luuu kamar zata fadi ta saki kara iya karfinta.

Maimakon Salisu ya tarota sai mamaki ya kama shi har ya kasa motsi. Salame ce fa da yasan bata kaunar kanwarta. Me zai sa ta shiga wannan yanayi kamar ance mata shi da kansa ne ya mutu ko mahaifinta.

Bature ma abin ya daure masa kai "Adda cewa nayi mijin Adda Mairama fa ba Malamijo ba"

Zama kawai tayi dabas akan kujera tana kuka sosai. Shikenan Zayyan ashe bata da rabon zama dashi. Salisu ya kawar da kai daga gareta.

"Bature yau zaka koma ne?"

"Yanzu ma kuwa in sha Allahu. Gobe za'a tafi gaisuwa"

Zumbur ta mike "ku biyo min, ko kuma dai ka jirani na shirya"

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull