Batuol mamman complete novel - Chapter 25
Batuol mamman complete novel Chapter 25: Batuol mamman complete novel Chapter 25. Tafiya ya soma yi kawai batare da sanin inda zashi ba ta bishi suna tafe…
3,362 words
Tafiya ya soma yi kawai batare da sanin inda zashi ba ta bishi suna tafe gefe da gefe.
"Alheran" ya kira sunanta daga can kasan makoshi sai da taji a jikinta.
"Uhmm"
"Bana son ki zama soja"
Bata ga alamun wasa ba a fuskarsa shiyasa taji gabadaya ya karyar mata da gabbai. Yau sau biyu yana cewa bazata yi soja ba. Na dazu haushi ya bata sosai amma yanzu da ya fada sai taji tana son sanin dalilinsa na fadin hakan. Me yasa shi da take tunanin zai taimaka mata ta sami biyan bukata zai rinka neman rabata da abinda ta girma dashi a ranta. Kafin ta tambaye shi ya cigaba da yi mata bayani.
"Ban taba tunanin zanyi wani karatun da bai shafi zama soja ba. Infact son da nake yiwa duk wata harka ta military ce tasa na zama pilot. Na rasa abubuwa da yawa saboda aikin soja. Mahaifina ya dawo gida da kafa daya da lalurar da taso dauke masa dukkan tunaninsa, Baba Hadir yana zaune a wheelchair babu motsi babu magana" tsayawa yayi ya juyo sosai yadda zasu fuskanci juna. Ba tsayinsu daya ba amma itama tana da tsaho daidai gwargwado, duk da haka sai taji kamar ta kankance a gabansa "na rasa mutum na biyu a rayuwata da na baiwa matsayin uba sannan kike tunanin Awwab zai iya bari ki zama soja?"
Tambayar ta soki zuciyarta kamar yadda maganganun suka yi tasirin da ya sanya taji kamar tayi kuka. Babu wani abu daya da zata iya tunawa game da mahaifinta idan ka cire kamaninsa na hoto. Amma labaran da take ji game dashi ya sa take da burin zama kamarsa. Tana so nan gaba ko me ta zama idan an tashi ace 'yar Zayyan Muhammad Tureta ce.
"I may be selfish Alheran amma daga jiya zuwa yau keman kin sani cewa bazan so wani abu da zai taba min ke ba."
Kallonsa tayi ta ga idanunsa kyam a kanta sai tayi murmushi "me kake so na karanta?"
"Are you serious? Kin hakura?"
"Ba dole ba kana yi kamar zaka yi min kuka" tace tana dariya. Hamma yafi karfin komai a wurinta zuciyarta ke sanar da ita.
Da sauri tayi hanyar gida dama ba nisa suka yi ba yabi bayanta yana murmushi har suka shiga soron. Tsayar da ita yayi ya koma mota ya dauko ledar tsarabarta ya damka mata.
"Ga naki kayan ledar Allah Yasa komai yayi miki"
Tayi murna sosai ta dauko takalmi daya ta gwada yana haskawa da wayarsa don ta gani saboda hasken soron bashi da yawan da zata gani da kyau. Guda uku ne takalman biyu da jakarsu sai turare biyu, dankunne da sarka da tarkacen kayan kwalliyar da bata san yaya zata yi dasu ba.
Sai da ta gama godiyarta ta karbi wayarsa tace ya buda mata hotuna ta gani. Daya bayan daya take binsu wani tace yayi kyau wani ta tsokane shi. Da sannu ta iso wurin hotunansa da uniform dinsa. Nan fa ta rude tana ta yaba yadda kayan suka burgeta.
Murmushi yayi mata yace "ko dai ta kusa kare miki ne zaki hakura da dreba"
"Sai soja ko likita"
"Time will tell"
"Me kace?"
"Babu komai"
Cigaba da kallon tayi ta budo wani yana tsaye da members na cabin crew dinsa a wata tafiya da suka yi da ta dace da birthday dinsa. Shi ya ma manta kafin a budewa fasinja su shiga jirgin suka kawo masa cake da gifts saboda yadda suke jindadin aiki dashi. Yana sakewa da kowa ayi raha ya wuce. Kasa yin gaba tayi da hoton duk da yayi kyau sosai amma 'yan matan air hostess din sun wani saka shi a tsakiya. Tayi gaba a hankali sai da ta gwammace bata yi ba. Wata cikinsu ce take tura masa cake a baki sauran suna tafi aka dauka. Abinda bata taba ji bane a rayuwarta na tsananin kishi ya saukar mata a lokacin. Ji tayi ina ma Ghazalatu ce ke bashi akan wannan mai dan skirt din da tasha kwalliya kamar 'yar tsana.
Gani yayi tayi shiru ya fada mata lokacin da aka yi hoton. Daga murya tayi ba da niyya ba sai dai bacin ranta a lokacin ya kai makura "ita ma wannan matsayinsu daya da waccan ne?"
"Waccan?"
Da gatse tace "Matar da zaka aura ba"
"Abokan aikina ne fa"
"To" tace muryarta tana rawa. Duk yada taso boyewa kasawa tayi hawaye kamar famfo suka shiga sintiri a kumatunta. Karbe wayar yayi ya haske mata fuska tayi saurin rufewa da tafin hannunta da kasan hijab din tana kara sautin kukan.
"Ya Allah, me nayi miki kuma?"
"Babu komai"
Hankalinsa a tashe yace "amma kike wannan kukan, akwai abinda yake damunki ne?"
"Nima ban sani ba" ta sake bare baki kukan yana karuwa.
Hoton ya kula tana kallo ya dawo da wayar saitin da zata gani sosai. Gabadaya hotunan ranar birthday din nasa akan idonta yayi marking ya gogesu. Babu kunya murmushi ya bayyana a saman labbanta.
Dage gira yayi yana mata wani irin kallo "silly girl! Kishi ko? Ko dai ta kare miki dinne ban sani ba?"
Dinke fuska ta sake yi ta tashi. Yayi ta kiranta haushin kanta da kukan da tayi yasa taki amsa masa. Samun kansa yayi da sakin murmushi shima yaji dadi ta damu dashi. Girgiza kai yayi lokaci guda yana kwabar kansa da cewa ya kiyayi wuce gona da iri akan kanwar tasa. Duk abinda yake yi mata 'yan uwantaka da shakuwa ce
********** [5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Rtd Major Mustapha tun a hanya suna ta waya da Baffa Habubakari da babban dansa da ya rako shi wan Zakari. Da kuma wannan soja wanda a yanzu yake rike da mukamin Captain shima kansa. Rikon amana da cigaban zamani yasa bai taba gazawa a wurin karbar sakon Major ba.
A harabar Giginya Hotel inda suke sa ran yin masauki suka hadu. Da motoci biyu hilux cike da sojiji majiya karfi wanda kallo daya zaka yi musu duk wani burbudin fitsara da rashin kunya su kama gabansu Captain Onomza ya zo wurin.
Ya gaisa dasu Daddy ransa a matukar bace yace a yanzu fa zasu wuce a kamo mutumin.
"Calm down Captain, muyi hakuri zuwa wayewar gari"
"I am sorry Sir, I cannot wait Sir" ce amsar da ya bayar yana 'yar dariya saboda har yanzu yana girmama Major.
Major ma burinsa ya ga Maikudi a hannu. Tunanin wadanda suka zo dasu yayi ga gajiya ga kuma firgicin ganin sojojin. To su ma sunyi na'am da a tafin shiyasa babu bata lokaci suka wuce gidan.
Jume ce tsaye jikin bango domin baiwa kanta kariya kada ta fadi saboda zafin kalaman Maikudi.
"Kannenka kayi musu tsawa nima kayi min tsawa ina mahaifiyarka?"
"Idan bakya so sai ki bar wannan magana. Abinda ya faru ya riga ya faru amma sai tado zancen kike. To wa zaki burge cikinsu? 'Yan uwan matar nan suna da arzikin kula da ita da yaranta, meye don nima naci daga arzikinsu. Ba wan ubansu nake ba?"
"Hakkinka ne da zaka ci?"
"Ho Jume, kin ma manta lokacin da ki ka matsawa Zayyanun da kanki akan ya baki kudin gadonsa."
Sai da taji ba dadi da ta tuna irin abubuwan da ta rinka yi wa Zayyan a wancan lokacin. Gashi ya tafi ya bar mata duniyar dan cikinta ya zame mata kadangaren bakin tulu.
"Kinga ni tashi zanyi daga gidannan nan da sati guda zaki huta da ganina. Gobe zan zo da masu aikin kwashe kaya" yana kaiwa nan yasa kai ya fita ya bar mahaifiyarsa da kunar rai.
Majalisarsu yaje ya zauna gefen wani gida inda suke wuni suna buga karta, gulmar duk mai wucewa da kallon 'yan mata. Hira suke gasu dai magidanta amma babu mutumci a tare dasu sai kyakyata dariya suke abinsu. Da yake lungun motoci bazasu iya shiga ba daga gefen titi suka yi parking sojoji suka rinka durowa daga motar harda masu bindigogi kirar AK47. Hankulan jama'a tuni suka tashi ana tunanin yau ko lafiya unguwar. Da karfinsu suke tafiya Baffa Habubakari da dansa Manu nadamar biyo wannan zugar sojoji suke yi. Tsoro suke kada su manta cewa tare suke a kafta musu hancin bindiga.
Su Maikudi sai gani suka yi mutane na shigewa gida da sauri ga sojoji suna tafe da sassarfa. Wasu cikinsu zasu tashi ya ce su zauna.
"Meye abin tsoro a soja, kanina ma har ya rasu soja ne. Ko wane mai tsautsayin suka biyo har cikin unguwa don jaraba wa ya sani"
Kamar ance ya kalli tsakiya ya hango wani mutum cikin shadda dinkin tazarce ya karkace hula yana rike da sanda ruwan kasa daga samanta da yake a lankwashe kasan kuma baki ne. Dogo ne kakkaura mai cikar haiba da zati.
"Banten uba" Maikudi yace da ya tabbatar wannan mutumin ne da suka zo neman Radhiya da uwarta kwanakin baya. Jikinsa har mazari yake don tsoro garin sauri ya bar wurin ya cambala kafa a cikin kwatar gabansa. Bai ko damu ba ya soma sauri. Captain Onomza ya gane shi da sauri ya bada dokar a damko masa shi.
"Don't let him get away" yace da karfi.
Mutum daya ne yayi kukan kura ya kwaso Maikudi gabadayansa sai gashi kwance a gaban Captain Onomza.
Hanjin cikin Maikudi ya buga wani uban sauti shi ba na yunwa ba shi ba na lalacewar ciki ba. Kallonsu yake tsakanin Major Mustapha da Captain Onomza wanne ne zaifi dan dama dama wurin sassauci. Yawun bakinsa duk ya kafe ya laso lebe ga gumi ya fara jika shi. Muryarsa kamar an takewa muzuru jela da takalmin karfe yace da Major "me yayi zafi ne haka ranka ya dade? Yarinyar nan da kaina zan kaika garin da suke. Ko makon da ya gabata naje na fada musu kazo kana nemansu shine uwar tace babu inda zasu je. To amma yanzu tunda anyi haka ina maka rantsuwa irin ta addinin Islama ko a ka ne zan dauko Radhiya na kawo maka. Kai harda kanin nata Zayyanu."
Gigitacciyar tsawar da Captain Onomza ya daka masa ita ta janyo mararsa ta saki fitsari ya soma tsartuwa. Mutane har sun fara fitowa kallo tunda sun fuskanci an kama wanda aka zo dominsa.
"Nine ka yiwa kerya yace min wife na Lt Zayyan yayi aure, baby ya mutu and you have the girl with you. Ko ba anyi haka ba"
Idanun Maikudi kamar an kasa kwai a faranti sunyi tsilli tsilli yace "ni ban fahimci me kake cewa bare na baka amsa"
Wawan mari ya dauke Maikudi dashi sai ji kake garam-garam masu leke suna komawa inda suka fito ana rufe kofofi. Captain Onomza da ko cikin sojojin ma ana tsoronsa saboda baya sassautawa mara gaskiya shine Maikudi zai kawowa wargi.
A take habo ya kama Maikudi. Major ya kawar da kansa su Baffa jiki ya hau tsuma. Da sunsan abin zai hada da sojoji babu abinda zai fito dasu daga rugarsu.
"Ka fahimta wanna ko"
"Kuyi hakuri yallabai yanzu me kuke bukata?"
"Bundle him up"
Mutum biyu ne suka taho kan Maikudi aka cukwikuye shi guda ya saba shi a kafada yayi gaba dashi.
Major da Captain Onomza suka sake gaisawa Captain din yace zai kira shi ya tabbatar masa a daren yau kafin gari ya waye Maikudi zai fadi ina kudaden marayun suke. Gidansu na Kano ma zai fadi me yayi dashi haka zalika idan yana da hannu a dauke kafar da 'yan uwan Innar Zayyan suka yi shima duk zai fada da bakinsa. Da sassarfa suka bar lungun sannan Major yace su shiga gidan.
Jume bata yi mamaki ba bayan ya gama mata bayanin me aka yiwa dan nata.
"Yanzu sai yaushe zaku sake shi?" Ta tambaya cike da jimami ga matarsa da yara suna kuka don labari ya iso gidan tun kafin shigarsu ma.
"Sati daya zaiyi in sha Allah"
"Yanzu babu wani abu da zaku iya yi a fitar dashi?"
Wani murmushi Major yayi da ya tabbatar musu babu wani abu da zasu yi da zai sa ya fito da Maikudi. Dole Jume taji babu dadi amma dan nata yana bukatar saiti ita kanta ta sani. Su Major sun tafi akan idan da wani abu zai nemesu.
"Uhmm nace ko zaka nemi Mal.Aminu. Aminin Malam ne da suke zuwa Nijar din tare, dashi akayi komai na auren Malam din da ita Innar Zayyanu"
Godiya Major yayi mata suka rabu zasu dawo washegari a raka su gidan Mal. Aminu.
Captain Onomza baiyi sanya ba wurin ganin Maikudi ya samu tarba irin wadda ta dace da macuta irinsa. A wannan daren ya bambance aya da tsakuwa, ya gane waye soja da hatsarin dake tattare da shiga hurumin sojoji ko da a bayan ransu ne. Mutane ne masu hadin kai da tsayawa juna domin kare martabarsu koda a bayan idanunsu ne. Abinda ya kara tunzura Captain Onomza shine takaicin ace dan uwa na jini ne da wannan muguntar. Kuma ya rasa wa zai ha'inta sai iyalin Zayyan dinsu.
**********
Matafiya suna ta shiri an gama wanka da cin abinci. Ummi da Mami ake jira basu gama hirar da suka dauko ba bayan wayar da suka gama da Mama Zainab. Zuwansu asibiti jiya likitan da suke gani ya gama bincike akan likitocin da ake kira neurosurgeons inda cikin sa'a ya sami wani kwararre da zai je Kuwait sati biyu masu zuwa. Likitan dan asalin kasar Philippines kusan yawo yake kasa kasa yana duba patients. Matsalar dai bata wuce samun shiga gurbin appointment dinsa ba karamin abu bane. Yini guda suna ta cuku cuku aka cusa Hadir a matsayin patient na karshe da zai gani a wani babban asibiti a Kuwait. Ba komai yaja hankalinsa ya karbe shi ba sai dadewar da Hadir yayi da lalurar da kuma jin cewa soja ne da ya sami rauni a filin daga. Tsananin rabo da addua suka sami alfarmar nan. Kudi dai Zainab zata kashe ba na wasa ba abu ya tasarwa miliyan tara. Zuciyarta ta karye hankalinta ya tashi. Idan ta bayar da wannan kudaden hakika zata tagayyara jarinta. Allah Ya taimaketa akwai kayan da tayi order daga China dake kan ruwa da basu sauka ba. Sune zasu riketa idan tayi sa'ar kasuwa.
Mami ta kwantar mata da hankali za ta sanar da Major domin nauyin ba nata bane ita kadai. Ummi bata bata lokaci ba itama wurin neman Innawuro a waya. Shanu biyar cikin abinda iyayen nata suka bata bayan ta koma hannunsu manya manya ta roki alfarmar a saka a kasuwa a ga nawa zasu samu. Dama ajiyarsu take saboda karatun 'ya'yanta da auren Radhiya idan ya taso.
"Abinda za'ayi Mami ku tafi da Karami domin su hadu da Ibrahim su taimaka mata. Bikin namu na kwana daya ne ana kai amaren washegari zamu tafi Kanon mu jira har su tashi"
"Baiwar Allah wallahi ina tausayin Zainab. Hadir ya godewa Allah bana jin zai taba haduwa da matar da zata kaunace shi rabi rabin yadda Zainab take yi"
Murmushi Mairama tayi ta bata labarin da Zayyan ya bata tun yana raye na ainihin waye saurayin Zainab din. Sun sha dariya su biyun yadda abotar su ta kasance.
Kowa ya shirya sun fara fitowa amma babu Radhiya har Mami sai da tayi cigiya.
"Tana kwance inda tayi sallar asuba tana bacci"
"Bacci kuma?" Mairama tace tana mamaki don Radhiya ba mai baccin safe bace musamman ma dai na yau da su Mami zasu koma.
"Taso ta Fauziyya tazo kuyi sallama"
Mami tayi saurin hanata "A'a wallahi ku dauko kayanku mu tafi. Nasan bai wuce gajiya ba"
Kusan kwana tayi tana kukan hotunan wayar Awwab. Duk da ya goge takaici take don me yasa ya tsaya har mace ta saka masa abinci a baki. Wannan ma salon ya jawo musu zagi ne ace yayanta bashi da kamun kai. Ko mutum nawa ne suka gani? Mata nawa ya bawa ko suka bashi abinci a baki? Alawar da ya bata ma sai da ta tuna ko sun taba yin haka da wata kafin ita. Wannan yafi tsaya mata a rai taci kuka ta godewa Allah shine fa bacci yayi awon gaba da ita da asuba.
Ghazalatu dama jira take kowa ya fita daga dakin ta zauna kamar tana gyara daurin dankwali. Zahra na fita ta fiddo wayarta taje ta zame hijabin Radhiya da babu dankwali ta kasansa a hankali wani bangare na kan ta ya bayyana tayi saurin daukarta a hoto tana kunshe dariyarta. Awwab zata nunawa kawai don ta rage karfin alakarsu duk ta yadda ya samu.
Awwab da yasan yadda ya rabu da kanwar tasa ya shigo tsakar gidan ya kai sau biyar ko zai ga gilmawarta. Da yaji ance bacci take yi hankalinsa tashi yayi fiye da zatonsa. Ta yaya zai tafi bai sake ganinta ba sai nan da sati biyu. Walwalar fuskarsa gabadaya ta bace yana jin kansa sukuku suka fito. Rakiya harda Malamijo shima yana cigiyar jikarsa mai fitina akace tana bacci.
"Kun taba jikinta kuwa lafiya take babu zazzabi? 'Yar sojan ce zata yi bacci har goma na safe indai ba kwaya ta soma sha ba". Dariya ya basu sosai.
"Mami ko dai bata da lafiyar? Hancinta na gani yayi swelling da saman idonta" inji Zayyana.
Ummi tace "ko ma meye ku bari su tafi a taso ta don yanzu tana zuwa sai ta bata musu lokaci"
Ba dai kukan ta sake yi ba Awwab ya tambayi zuciyarsa. Tamkar kada su tafi haka ya rinka ji. Ghazalatu motarsu ta koma Zahra ta shiga wadda su Mami suka zo don kada a barta ita daya.
Kusan awa daya da tafiyarsu bayan Radhiya ya soma damunta saboda kwanciyar kasa ta bude ido tana mika. Dakin shiru babu kowa ta tashi da sauri babu jakunkunansu sun gyare dakin da katifar. Nauyin bacci gareta shiyasa bata ji motsinsu ba. Gabanta na dukan uku-uku ta garzaya dakin Hajjo wurin Ummi.
"Ummi sun tafi ne?" Tace cikin tashin hankali.
"Ina hankalinki ne, babu sallama babu gaisuwa"
Fita tayi ta dawo cikin sauri ta gyara kuskurenta sannan ta maimaita tambayar da ta riga tasan amsarta tunda bata ga Mami ba kuma babu kayanta.
"Sun tafi kina can kina bacci. Ko baki da lafiya ne?"
Hawaye ne ya taho mata tayi kokarin boyewa "shine basu tashe ni ba?"
"Kiji dadin isarsu da surutu ba. Sun wuce da Karami zai zauna a Kano..."
Alamun kukan Radhiyan taji ta dakata tare da mika hannu inda take jin sautin tun yana tashi a hankali har yayi karfi. Wani irin kunci da bacin rai take ji hade da gagarumar kewar Hamma Awwab. Me yasa bai ce a tasheta ba sunyi sallama. Me yasa daga zuwansa zuciyarta take shiga mabambantan yanayi daga tsananin farinciki sai bacin rai irin na jiya da ta ganshi da mata. Yau kuma don bai damu da ita ba yayi tafiyarsa.
"Ke menene?"
"Ummi ba komai" ta amsa muryarta na sake karyewa. Ta dauki kanta jarumar mace mai dauriya amma lokaci kalilin ta zubar da hawaye fiye da tunaninta. Ita kanta bata san me ya sameta ba sai an mata karin bayani.
Tun Ummin ta na rarrashi har ta koma fada amma taki cewa komai sai kuka. Daga karshe karamar wayar da Mami ta bar mata ta dauko. Ba kudin sayen bane dama ta rasa sai dai karancin wadanda zata kira. Emzee da Radhiya kuwa taki saya musu ne duk da tasan ana yayinta sosai tana jiran su gama sakandire.
"Ungo ki kira Mami da sauran 'yan uwanki ku gaisa kiyi musu sallama kinji 'Yar sojan Daaadaa"
Ba wuya anci galaba a kanta. Bare kuma rarrashi daga Umminta sai tayi dan murmushi.
"Kyalesu ni na fasa tunda basa son tawa sallamar" ta basar a zuwan taba damu ba.
"Ke dai ki karba kafin ki zo da kanki na hana"
Sautin dariyar Radhiyan taji ta girgiza kai. Wannan yarinya sai addu'a. Radhiya na kira da taji ta shiga sai kuma kunya ta kamata ta mannawa Umminta wayar a kunne. Dauka Mami tayi tana fada mata inda suke yanzu.
"Tsakanin ke da Maman yara bansan wanda ya koyawa yarinyar nan shagwaba ba. Ba karamin abu kesa aji kukanta ba. Yanzu kuwa kukan gaske take min wai bakuyi sallama ba"
"Allah sarki Radhiyata, bata wayar mu gaisa"
Karba tayi ta gaisheta kamar ba ita ke kukan ba ta kuma gaisa da Zahra "ina su Adda Fauziyya?"